Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 8
shigo dakin ta dubi Isah a gadarance da nuna'isa ta ce "Wallahi wulakancin da kake mani da nuna iyaka ya isheka haka in ba wulakanci ba inzo duba mijina sai ka rufemin kofa kace in tsaya a waje sai kun gama, ko kafini kusanci da shi ne a yanzu da har baka son in ganshi a halin da yake ciki? In ma wankan za'a yi masa ai mu ya kamata mu yi masa kai bai dace kaga tsiraicinsa ba sai mu nan balle.......??? Ke! Dakata don Allah ya isheki haka wannan wace irin sakarcin magana ce mara kan gado maganar da bata dace da bakin mai hankali ba in ba sakarai ni dai baki isa ki raba ni da dan uwa na ba in kina takamarki raba 'yan uwa saboda haka ki bini a hankali kawai. "In kuma na ki fa? Na ce in kuma naki fa? Ta sake maimaitawa ya gyada kai yace "Zamu ci gaba da 'yar tsama da ke kinsan sanni bani da mutunci ga duk wanda bai rike mutuncin kansa ba tunda 54 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria girman danake baki a matsayin matar yayana ke bakya gani duk da na girmeki a shekaru to zan watsar da girmamawar dama ance idan tsoho baiji kunyar hawa jaki ba to shi kuma jakin ba zai ji kunyar nana shi da kasa ba Ta yi kwafa "Shi kenan muci gaba da zubawa za'a gawanda zai fasa". Da yake Muneeba na bayin cikin dakin bata san wainar da suke toyawa ba, Goggo kuma na gida shi yasa aka rasa mai shiga tsakani ya tsawatar musu har suka yi suka gama. Karshen badakalar Muneeba ta fito ta riska shine fa tayi ta basu hakuri tare da nuna musu ishara akan abinda -ya samu Mujeeb wanda ya ishi duk mai hankali yasan mutum ba'a bakin komai yake ba duk matsayinsa. 55 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ****** ****** ******* Alhaji Ayuba da mijin Inna Amina sun hadu sun tattauna dangane da fita da Mujeeb da za'a yi kasar waje sun tsayar da matsaya akan za'a kaishi kasar (CAIRO) wato (Egypt). Sun tattauna da likitocin asibitin da za'a kaishi har sun basu Appointment Date din da zasu isa can za'ayi tafiyar ne da Muneeba sai can akwai wani abokin mijin Inna Amina zaune yake da iyalansa shi zai jagorance su. Ranar wata Laraba wadda kwanan Mujeeb kusan Talatin kenan a halin da yake ciki Muneebace ke tsaye a kansa tana shafa masa rowan zamzam mai dauke da addu'o'i kamar kullum yadda take masa, cikin ikon Allah ta shafa masa a fuska kawai sai ta ga idanunsa na motsi alamum kamar yana son ya bude su. Yayi motsi da idanun a hankali har Allah ya taimakeshi ya bude su tangarau 56 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria amma shi sai yana ganin mutane dusudusu sai dai hakan baisa ya kasa gane fuskar Muneeba ba. Ya tsura mata ido tamkar yana karantar wani abu a fuskanta tata ko kuma yana son ya gano wani abu murna ta kama Muneeba ta daga hannuwa tana yiwa Allah hamdala ta kwasa da sassarfa tayi waje a harabar dakin Inda Goggo suka shimfida tabarma suke zaune ita da Suiwaba Isah kuma yaje siyo wata allura da za'a amfani da ita. Goggo ta tsorata da yadda ta ganta a sukwane ta soma tambayarta "Lafiya" me ya faru Goggo zo kuga ikon Allah Yaya Mujeeb ya bude idanunsa har yana motsi da baki kamar zaiyi magana. Ai Goggo tamkar zata kifa haka ta táso da saurinta Suwaiba ta rufa mata baya suka shiga daki kewaye gadon sukayi suna godiya ga Allah ya kurawa Goggo idanu kyar ta soma kiran sunansa yayi alamun kamar yana amsa mata amma sam baka 57 e ir a a u a a WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria jin me yake cewa sai dai bakinsa dake motsi. Ya soma alamun zai daga hannunsa mai Karaya Goggo tace Muneeba yi sauri ki kira Likita". Likirta tare da wasu Nosis guda biyu suka shigo dakin suka umurci dasu Goggo su basu wuri zasu duba shi kowa ya fita ka barsu. A waje Isah ya dawo ya gansu suka shaida masa abin murnar da ya same su shi ma daga hannu sama yayi yana wa Allah Godiya daya nuna musu wannan rana. Ya tambayi Muneeba yayi magana ne? Ta ce, Bai yi magana ba amma yanata motsa bakin alamun yana son zaiyi magana ai Insha Allahu sauki ya fara samuwa kenan addu'o'i takobin mumini ce Isah ya dubi Muneeba muna mika godiyarmu ga ALLAH mara iyaka sannan kuma mika godiyarmu gareki saboda jajircewarki da tsayawarki a kansa da addu'o'i babu dare ba rana wallahi ina 58 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria alfahari da samunki a matsayin 'yar uwa kuma mata ta gari Jaruma abar so ga Yayana Allah ya kara maki karfin guiwa ki kara tsayuwa akan al'ummuran mijinki tsakani da Allah, muna nan tare dake Insha Allahu". Likitan da mukarrabansa sun dauki lokaci suna duba shi daga bisani suka fito tare da yi masu umurnin su koma dakin su zauna tare dashi ya sami komawa bacci amma bazai dade ba zai sake farkawa kada suyi nesa dashi sun kewaye gadon nasa suna kallon ko daga yadda yake sauke numfashi sun tabbatar lafiya ta soma samuwa sabanin da ba baka iya gane ko yana numfashi ko ba yayi sai kayi tsananin lura zaka gane hakan. Bai wuce mintuna ashirin ba ya sake bude idanunsa ya dinga binsu da kallo daya bayan daya daya kali Muneeba sai kawai suka ga ya kura mata idanu hawaye na ambaliya a kuncinsa ya 59 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria dade cikin yanayin zubda hawaye wanda basa raba daya biyu hawayen nadamar abubuwan daya dinga yi mata ne a gidansa da jingineta da yayi a gaban iyayenta. Itama sharer kwallar ta shiga yi idanunsa na kaiwa fuskar Suwaiba sai suka ga yayi sauri ya rintse idanunsa bai sake budewa ba sai dai hawaye da yake gangarowa ta gefen idanun sa. Dukansu mamaki ne ya kamasu na yadda Mujeeb baya son kallon fuskar SUWAIBA hakan ne nuni da wata ayar tambaya a tsakanin al'amarin nasu wanda babu wanda yasan amsar hakan sai su biyu sai Allah da ya halicce su. Wannan al'amari ya daurewa kowa dake gurin kai na yadda da zarar Mujeeb ya bude idanunsa sunayin arba da fuskar Suwaiba sai ya rufe idanunsa ga dukkan alamu ma kila da yana iya sarrada harshensa da yayi umurni kada ya sake ganinta kusa dashi. 60 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaría Idan yayi ido hudu da Goggo ma hawaye yake yi Muneeba ma hawaye amma Suwaiba rufe idanu kai wannan abu da ban al'ajabi Muneeba tayi masa addu'o'i kamar kullum tana tofa masa data gama kuma ta lura har ya sake komawa bacci sai ta koma gefensa ta zauna ta dauki wayarta tana ta kiran yan uwa da abokan arziki tana shaida musu cigaban da aka samu lafiyar Mujeeb hatta Ogansa sai data kirashi ta layinsa da ke wayar Mujeeb din ta gaya masa tunda wayar na hannun Isah. Kafin wani lokaci 'yan uwa da abokan arziki na kusa sun fara isowa asibitin don taya murnar wannan cigaba da aka samu Alhaji Ayuba shine na farkon isowa asibitin tare da wasu abokan Mujeeb din. Fuskokinsu cike da murna a lokacin da suka yiwa gadonsa zobe suna yi masa sannu tare da addu'o'i shi kuma yana bin kowannensu da idanu tamkar 61 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria yana amsa sannu da suka masa ne. likita ya sake shigowa ya duba shi sannan suka fita tare da Alhaji Ayuba zuwa Offis. Likitan ne ya soma masa bayani "Kaga cigaban da aka samu na samuwar Lafiyar Mujeeb ko Alhaji"? Ya gyada kai "kwarai na gani likita kuna nayi murna sosai muna yiwa Allah godiya tare da Addu'ar Allah yasa lafiyar ta dore mu dinga ganin ci gaban lafiyar tasa kullum. Ya amsa Ameen shi ya sa ai da ku ka zomin da maganar zaku fita dashi na baku hakuri daku dan saurara ku bamu lokaci tunda muma muna iya bakin kokarinmu bisa ga tamu kwarewar munasa ran da izinin Allah zai sami lafiya anan din ba tare da kunyi wahalar kaishi wata Kasa ba. Wallahi Alhaji can din ma idan kuka je zaku iske kwararrun likioci duk 'yan Najeriya ne irinmu abin da zasu masa acan muma irinsa zamu yi masa bambancin 62 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaría daya ne sun fimu ingantattun kayan aiki a kwarewa suka fimu ba, muma da gwamnatinmu zata wadata manya asibitoci da kayan aiki a inganta mana albashi da alawusoshinmu wallahi da babu wanda takaici zaisa ya tsallake kasarsa ya tafi yana hidimantawa a wata kasa da arziki a garin wasu ai gara a garinku mukam muna nan zamu ci gaba da taimakawa al'ummar kasarmu da ita kasar kanta mu baje kolin basirar da Allah ya azurta kwakwalmu dashi muna fatan mu samu sakayya ranar gobe kiyama. Alhaji Ayuba ya numfasa tabbas zancen Dr. Aminulalah gaskiya ne shikam har yaji bashi da sauran burin kai kansa ko iyalansa ko wani nasa asibitin ketare gara ya nemi ko wane asibitin ne in dai a fadin Najeriya yake tunda ko Zaria akaje (A.B.U.T.H. Shika) akwai zakakuran likitoci masu gani har uwar daka ga babban asibitin koyarwa na 1 1 63 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Malam Aminu Kano ga Babban Asibitin Ibadan inma kashine yayi gardama ga asibitin Kashi na Dala a Kano to me ya. rage!. Ya dubi likitan yace "Gaskiya na gamsu da bayaninka likita don wallahi bayaninka ya warware min kullin damarar da nayi ta fita da yaron nan kasar waje ka ruguza komai dana tsara saboda haka zamu barshi a gurinku muna rokon Allah ya taimaka muku ya baku sa'ar shawo kan matsalar ciwon yaron nan Allah ya bashi Lafiya likita ya amsa da "Ameen Alhaji haka muke so a dinga karfafa mana guiwa hakan na kara mana karsashi ba a nuna mana kasarmu ba alhali muna iya bakin kokarinmu akan duk wani majinyaci da za'a kawo mana cikin kwanaki bakwai da samun saukin Mujeeb likita yayi umurni da a fara bashi abinci amma mai ruwaruwa kamar ti ko kunun ko koko amma mara kauri. 64 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Muneeba jikinta har rawa yake yi jin wannan umurni na likita ta fiddo kayan Tin dake lode cikin Loka, Isah ya tsiyayo ruwa a Filas ta hada masa Ti mai kauri ta aje a gefe don ya huce sannan tace Isah ya dauko Roba da ruwa a buta tasa makilin a burush wani Nos ya taimaka musu suka tada shi suka jingina shi jikin allon gadon. Muneeba ta sa Burosh a hankali ta goge masa bakinsa da kyar ta samu ta tura Burosh din tsakiyar harshensa ta wanke shi sai ba uhm ba uhum yana dai ta binta da kallo har ta yi ta gama. Isah dake fifita Tin ya miko mata ta dan kurba don ta ji yanayin zafinsa Isah ya yi dan Murmushi ya сe "Kai Aunty ai ba zan bari ya kona mai baki ba" Itama murmushi ta yi tace, "Ai na ga ka kosa a bashi ne ba ka san na fi ka kosawa ba fiye da wata guda mutum bai sa komai a bakinsa ba sai dai Karin ruwa in banda sun ce akwai abinci a karin 65 e i e a n E 1 Π Π D a a WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ruwan ai da mutum ya mutu kai ai ciwo bai yi ba Allah ya rabamu da ciwo. Ta soma bashi kadan kadan yana sha har sai da ta ga yana kin karba sannan ta aje kofin ta amshi (Tissue) da Isah ya gutsiro ta goge masa baki Nan fa ya soma sana'arsa ta zubda hawaye Muneeba ta girgiza masa kai tace "Don Girman Allah Yayana ka daina yawan zubda hawaye nan kada damuwar dake saka hawaye ta sake jefa zuciyarka cikin wani halin. In har kana ganin wani laifi kayi min da ke saka zubda hawaye idan ka dubeni to ni baka yi min komai b in ma kana ganin ka yi mani to wallahi ni tuni na yafe maka ban kullaceka da komai ba in kuma ni ce na yi maka laifin to ka yi min afuwa ka ya fe min. Alamun murmushi ne ta gani ya bayyana a fuskarsa ya dan lumshe idanunsa ya bude su tar akan nata hakan da ya yi sai da ta ji wani sabon sonsa ya malalu a zuciyarta ta dinga tunano rayuwar 66 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria aurensu ta baya musamman zaman amarcinsu. a Dukku yadda ya dinga riritata da nuna mata so da kauna duk da ba ita bace zabinsa amma ya yi marhabin da shigowarta rayuwarsa da zamansu na Gombe kafin zuwan Suwaiba wadda ta rikirkita komai ta damawa kwakwalwarsa lissafin har aka kai matsayar da ya dinga hantara da kyamarta har dai ya kare ya nuna baya sha'awar cigaba da zama da ita. Hakika da anbi ta ra'ayinsa da yanzu ya guntule igiyar aurensa dake kanta tunda biris din da yayi da ita a gaban iyaye ba waiwaiye alamu na su neme shi ya bata takardan kuma da an neme shin daya aikata hakan, shi ya sa hakuri ke da ranarsa in ka ga hakuri bai yi wa mutum rana ba to kadan ya yi bai da yawa ba. Tun daga wannan lokacin sai Mujeeb ya dinga samun sauki daga Allah tare da kulawa ta Musamman. daga 67 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria matarsa Muneeba sannan ga Isah shi ma yana nan tsaye in baya nan to ya je makaranta Suwaiba kam sai ta rage zuwa saboda yadda ya nuna sam baya son ganin fuskarta har gara in tana rike da Waleeda to zai yi kallon Waleeda amma ita sam ba zai yadda su yi ido hudu ba. Dr. Aminullah ma ya yi tsayuwar daka akan ciwon Mujeeb din babu dare babu rana sannan ko yana hutun aiki ne ya kan zo ya duba shi har a hutun karshen mako haka nan ya dada karfafawa Muneeba gwiwa akan cigaba da yi wa Mujeebun addu'o'i da ta ke yi tare da shafa masa zaitun a gabobinsa tanbayi tana mummurza gabobin saboda su farfado su koma aiki yadda ya kamata kuma ana ganin nasara tunda har ya fara motsi da 'yan yatsunsa na kafar da bata aiki. An yi nasarar gyaran aka yi wa Mujeeb na karayar hannunsa an kwance Filasta hannun ya yi daidai yanzu matsalar da za'a fuskanta itace ta ganin sashen 68 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria jikinsa ya soma aiki wanda ana sa ran hakan ta faru a kowane lokaci tunda har yatsunsa sun soma motsi sai Babbar matsala ta rashin maganarsa, amma ko me aka fada yana ji tangarau. Goggo ta bada shawarar tunda hannunsa ya warke kuma har an sayi keke an gungura shi a ciki ana fita da shi yana shan iska to kamata ya yi a maidashi gida aje a cigaba da yin maganin gargajiya tafiya da maganarma Insha Allahu zai yi su tunda har kafar na motsawa bakin ma yana motsa shi alamun yana son ya yi magana Allah ne bai bashi ikon yi ba. Wannan shawara ta yi tasiri a gurin su Alhaji Ayuba da baffaninsa na Dukku hakan ne yasa suka gayawa Dr. Aminullah kudirinsu da farko bai bada goyon baya Ba amma a karshe-karshe dai ya amince musu ya basu sallama tare da basu sharuddan da za'a dinga bi wajen kula da shi da bashi magungunansa akan 69 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria lokaci tare da an tabbatar ana kawo shi (Clinic) don ganin likita. Kafin su wuce gida Isah ne ya fara tafiya suka hadu da Jume da mai gadi Malam Bilya suka gyara dakinsa suka share suka goge duk wata kura kasancewar ba'a bude dakin shi yasa kura ta sami muhallin zama. Goggo ce ta ba Isah umurnin yin hakan tunda nan dakin nasa za'a kai shi Isah ya yi tsaye a dakin baccin Mujeeb din a gaban durowar gefen gadonsa yana cike da ta'ajibin rashin ganin makudan kudin daya adana wa Mujeebun tun ranar da ciwo ya sameshi Goggo tace ya rufe dakin ya aje makullin a hannunsa to shine daya shiga dakin don ya fidda abubuwan cikin Firij din Mujeebun ya ga kudaďen a jakar Ofis dinsa shine ya kwashesu ya zuba a durowar ya rufe ya cire makullin sai gashi yanzu yaga babu makullin a jikin durowar yana dubawa ya ganta a bude babu kudin babu dalilinsu. 70 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Tabbas ko kaffara ba zai yi ba Suwaiba ce ta bincika ta kwashe kudin nan in banda shi babu wanda ke shiga dakin, shi kadai ke da makullin dakin kila itama tana da safaya ne bai sani ba. Haka ya koma asibitin cikin al'ajabi wannan al'amari ko Goggo bai gayawa ba don ya san tun a asibitin za ta iya fasa maganar dama tun a ranar ya gayawa Goggo maganar kudin sai ta ce ya aje su kawai kada ayi amfani da su tunda ba'a sani nashi ne ko ba nashi bane. Amma fa Isah ya sha alwashin zai binciki Suwaiban in har ya tabbatar ita ta dauka to dolenta ta dawo da su don ba hakkinta bane, in ma banda rashin tausayi mutum na kwance cikin halin haula'i sai ki bi dukiyarsa ki dauke babu ko tausayi. Sun baro asibiti sun dawo gida a nan falonsa aka saka masa madaidaiciyar 71 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria katifa a nan ne zai zamo gurin jinyarsa, saboda jama'a masu zuwa gaishe shi. A ranar Muneeba yini ta yi hidinmarsa har bayan Magriba sannan ta yi sallama da su ta tafi tana lura da Majeebun na tsiyayyar hawaye tun da ya ji za ta tafi gida. ******* ******* ******** Tun ranar da aka salami Mujeeb daga asibiti Muneeba ba ta sake zuwa gidan ba har kwana biyu. Tana kiran Isah a waya ta tambayeshi mai jiki ya yi mata korafi rashin zuwan nata amma sai tana kawo masa uzurori wadanda zuciyarsa taki amanna da su su dai kawai ya kyaleta. Wannan rashin zuwa na Muneeba ya kawo cikas da koma baya ga lafiyar Mujeeb da ake ganin an samu, tunda har ya 72 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria haifar masa da kin karban abinci idan aka bashi nan da nan sai jikin na sa ya rikice, zazzabi mai zafin gaske ya rufe shi har yana wata irin jijjiga. Kowa fa ya rude hankula suka tashi Isah ya dubi Mustafa da ya zo a ranar ya ce "Yaya Mustafa ko zamu kira wayar Dr. Aminullah ne tunda ya bani wayarsa yace in da wata matsala in kira shi in gaya masa? Ya ce "Eh mana yi maza ka kira shi muna murna sauki yazo sai kuma wata sabuwa ta bullo. Bugu daya biyu Doktan ya dauka suka gaisa da Isah tare da tambayar ya jikin Mujeeb din ya ce, Wallahi Dakta jikin nasa nema ya tashi shine nace bari in kira ka ko da wai taimakon da za ka yi mana in babu matsala. "No babu wata matsala ai na ce idan da matsala ka kirani. Ku saurareni gani nan zuwa yanzu don yau ina Up ne bana asibiti mintuna kalilan suka sa da 73 2 a a WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Dr. Aminuklah da gidan Mujecb kasancewar Anguwanni su na makwaftaka da juna ya yi masa aunc-aune ya dan dudduba shi sannan ya dubi Isah, "Me kuka yi masa har ya shiga damuwa haka?" Isah ya ce "Mu kam Dakta me za mu yi masa? Ai mu duk wani abu da zai dorar da lafiyarsa shi muke so kuma shi za mu yi masa ka ganshi nan ya ki cin abinci tun jiya sai dai zubda hawaye mun rasa gane kansa". Dakta ya dan yi shiru cikin nazari sannan ya yi tambayi Isah "A tunanin me kuke ganin ya dami zuciyarsa a yanzu, don ya zama dole mu san ko mene ne don mu magance shi ko mu hana faruwarsa gareshi. Mustafa ya yi karaf ya amshe Dakta gaskiya matarsa ce da ke jinyarsa bai gani ba kwana biyu tun ranar da aka dawo da shi daga asibiti mu a zaton mu rashin zuwanta gareshi shine musabbabin tashin ciwon nasa har ya kauracewa cin abinci. 74 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Likita ya сe "A'a to ita meye dalilinta na tsallake zuwa unguwar kwana alhalin ta san tana da mara lafiya wannan ai bai dace ba gashi ta jefa mijinta cikin cikin wani hali gaskiya ku gaggauta kiranta a waya tayi maza-maza ta dawo yau don kula da lafiyar mijinta lafiyarsa ai tafi mata komai. Suka dan yi jim sannan Isah yace "Eh to gaskiya Likita sun dan sami matsala ne tun kafin ya fara ciwo shi da kansa yace ta zauna a acan gaban iyayenmu sai ya nemeta to tana can dine ciwo ya same shi bata ji haushin komai ba ta zo ta yi ta jinyarsa shine yanzu da aka dawo da shi gida ita ma ta koma can gida inda take. Dakta ya dafe kai yana kakabin wannan al'amari 'yanzu babu yanda za'a aje aba iyayenta hakuri su taimaka ta dawo ta zauna dashi saboda dorewar lafiyarsa? Kun dai ga yadda jikin nasa ya koma. A gaskiya idan abin ya cigaba to 75 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria za'a koma yar gidan jiya gara tun abu baiyi nisa ba asan abinyi in ta kama aje dani can durin iyayenta nata ne sai mu je don in yi musu bayani amma ai dole mai irin wannan ciwon ya kasance da matarsa kusa da shi, saboda wata kulawar da lallashi sai ita. a Isa ya ce "Yana da wata matar gata can a dakinta, amma bata da wani amfani tunda ba za ta iya zama ta kula da shi ba, Muneebar ce kadai dama me dawainiya da shi kamansa ita ce tunda ita 'yar uwarsa ce shi yasa tafi jin ciwon nasa a zuciyarta. "Haba ba mamaki ai alaka jinni daban take balle kuma an hada da auratayya matarsa ashe su biyu ne to gaskiya kam ku san yadda za'a yi ta dawo gare shi don yana cikin hadari". Mustafa ne ya hau motarsa ya nufi gida Inna Amina wurin Muneeba. Dukansu a falon gidan ya iske su har Muneeban aka gaggaisa sannan ya kebe da Muneeban a dakinta ya shaida mata halin da ake ciki da 76 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria S bayanan da likita yayi musu da irin gudunmuwar da ake son taje taba mijinta tunda ya fi kusanci da ita fiye da kowa. Halin da aka gaya mata ya shiga ya soki Zuciyarta sai dai tana ganin ba zai zamo dole ace sai ita zata je ta zauna da shi ba alhali yana da wata matar, matar da mahafiyarsa ga kaninsa aiko su sun isa jinyarsa. Ita kam a wani matsayi za ta je ta zauna a gidansa tunda bai ce ta dawo gidansa ba duk da ba sakin ya yi ba. Ta dubi Mustapha ta dan kauda kanta gefe tace, Yaya Mustafa kayi hakuri gaskiya ba zan iya komawa gidan nan ba in zauna ba tunda bashi yanemi in koma ma, ka da ya warke ya sake kora ta gara dai in zauna gaban iyayena kamar yadda ya bukata zaman da nayi dashi ma a asiiti ai na yi kokari ida ka yi la'akari da yadda ya wofintar da aurensa ya share ni a babin rayuwarsa, ni din har ciwo na kwanta na yi kuma an kirashi a waya an gaya masa, ko sannu a waya baice mini 77 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ba balle ya tako ya zo ya gaishe ni balle in sa ran zai saya min magunguna, Su Mama Amina ne ke ta dawaniya da ni har na warke haba Yaya Mustafa in maye ya manta ai uwar da ba zai yiwu ta manta ba. Mustafa ya sauke numfashi "Mun san haka Muneeba, amma kiyi hakuri ki bar wani tone-tone idan ana sallah ai ba'a magana, ki bar tuno abin daya faru a baya ya wuce mu fuskanci abin da ke gabanmu yanzu kowa ya san abinda kika yi kin yi ne domin Allah kuma domin zumunci sannan har yanzun a matsayin matarsa kike tunda ba sakinki yayi ba babu wanda zai ce don me kika koma dakinki ki yi hakuri ki tausayawa dan uwanki wallahi likita yace komai zai iya faruwa ga rayuwarsa a halin da yakė ciki. Kwalla ce ta cika idanun Muneeba ana tausayin mijinta, itama tana tausayin kanta to amma dole ne ta dan dinga ja baya tun kafin Goggo ko Suwaiba wani cikinsu 78 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria bayanan da likita yayi musu da irin gudunmuwar da ake son taje taba mijinta tunda ya fi kusanci da ita fiye da kowa. Halin da aka gaya mata ya shiga ya soki Zuciyarta sai dai tana ganin ba zai zamo dole ace sai ita zata je ta zauna da shi ba alhali yana da wata matar, matar da mahafiyarsa ga kaninsa aiko su sun isa jinyarsa. Ita kam a wani matsayi za ta je ta zauna a gidansa tunda bai ce ta dawo gidansa ba duk da ba sakin ya yi ba. Ta dubi Mustapha ta dan kauda kanta gefe tace, Yaya Mustafa kayi hakuri gaskiya ba zan iya komawa gidan nan ba in zauna ba tunda bashi yanemi in koma ma, ka da ya warke ya sake kora ta gara dai in zauna gaban iyayena kamar yadda ya bukata zaman da nayi dashi ma a asiiti ai na yi kokari ida ka yi la'akari da yadda ya wofintar da aurensa ya share ni a babin rayuwarsa, ni din har ciwo na kwanta na yi kuma an kirashi a waya an gaya masa, ko sannu a waya baice mini WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ba balle ya tako ya zo ya gaishe ni balle in sa ran zai saya min magunguna, Su Mama Amina ne ke ta dawaniya da ni har na warke haba Yaya Mustafa in maye ya manta ai uwar da ba zai yiwu ta manta ba. Mustafa ya sauke numfashi "Mun san haka Muneeba, amma kiyi hakuri ki bar wani tone-tone idan ana sallah ai ba'a magana, ki bar tuno abin daya faru a baya ya wuce mu fuskanci abin da ke gabanmu yanzu kowa ya san abinda kika yi kin yi ne domin Allah kuma domin zumunci sannan har yanzun a matsayin matarsa kike tunda ba sakinki yayi ba babu wanda zai ce don me kika koma dakinki ki yi hakuri ki tausayawa dan uwanki wallahi likita yace komai zai iya faruwa ga rayuwarsa a halin da yake ciki. Kwalla ce ta cika idanun Muneeba tana tausayin mijinta, itama tana tausayin kanta to amma dole ne ta dan dinga ja baya tun kafin Goggo ko Suwaiba wani cikinsu WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ba tun da ba ni ke da iko da ita ba masu iko da itane suka bani amanar ta zauna a hannuna sune iyayenku idan suka yauyauta koma wallahi ina murna da hakan ai munfi kowa son ta koma dakin mijinta ta zauna to amma dole a nuna musu Muneeba ma ‘ya ce ba baiwa ba, muna sonta tamkar yadda Goggon ke jin tana son Suwaiba, ai tana gidan ake ta wulakanta Muneeban bata tsawata ba shine sai yanzu za'a ce ta dawo saboda zata taimaki danta ai dama ko kare yana da ranarsa balle dan Adam mai daraja. Ka kyale Goggo taje ta samu 'yan uwanta babu ruwanka". Mustafa yace ni dama ba zuwa zanyi ba, ai ban isa in tunkari su Baffa da wannan maganar yadda suke cike da Goggon ko nan da nazo bata san nazo bani ne dai da likita muka ga dacewar ta zauna kusa dashi. Inna Amina ta lallashi Muneeba suka tafi tare da Mustafa sallamar kadai Mujeeb ya ji ya wani saki ajiyar zuciya a WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria lokacin Suwaiba

Chapter 3 of 8