Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 8
da Goggo ne ke gabansa suna kokarin ya ci abinci amma fafur yaki karba suka shiga falon ita da Mustafa suka gaisa da Goggo, Suwaiba bata amsa gaisuwar ba sai wani cin magani ta ke yi har sai da Muneeba tayi mata tata gaisuwar ta daban sannan ta amsa da kyar. Shi kam Mujeeb bin Muneeba yake yi da kallo tamkar ranar ya soma ganinta hakan ya kular da zuciyar Suwaiba ta tsuguna gaban katifar da yake zaune an jingina shi da bango itama idanu ta kura masa tamkar yadda yayi mata kuri da nasa idanun tayi magana, "Ya jikin naka? Duk da ta san ko an gaishe shi ba iya amsa ya ke yi ba amma ya san yana jinta kuma akwai alamun amsawar da yake yi mata idan ta gaishe shi lumshe mata idanunsa yayi sannan ya sake budesu a fuskarta tare da bayyanuwar wani kallo na soyayya wanda ita kadai tasan sirrin kan dake cikin kallon a duk lokacin da yayi mata. L 82 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Ta sake tambayarsa "An ce min kwana biyu kaki cin abinci me yasa? Ka yi hakuri ka dinga cin abinci saboda shi abinci yana karawa mara lafiya kuzari tare da sake gina masa garkuwar jikinsa da ta soma rugujewa a yayin da yake cikin halin rashin lafiya uwa uba ma ita. kanta lafiyar da ake nema ta samu ga mara lafiya tana samuwa ne idan mara lafiya na cin abinci kaji ko abokin. ??? Bata iya karasa sunan da take kiransa dashi ba, kasancewar Goggo na gurin kuma dama daga ita sai shi takeе kiransa da abokin rayuwa yanzu ma da ace tayi subul da bakan fadan sunan to la shakka wani shahararren gori Suwaiba zata yi mata, gara da Allah ya taimaketa bata gama ambatar sunan ba tayi birki. Abincin dayaki ci ta dauko ta debo cokali daya na shinkafa da miya ta kai bakinsa sai ta ga ya girgiza kai alamun ba zai ciba tace "Ba zaka ci ba to me kake 83 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria so? Ya sake lumshe idanunsa take ta gano manufarsa ta mike ta isa inda kayan Ti suke ta debi garin Kostad na gwangwani ta je kicin din ta ta dama masa tazo tasa Madara da suga kadan sannan ta soma bashi sai gashi ya saki ciki yana shan Kostad din nan har sai da ya kusa shanye kofi daya. Suwaiba dake zaune nan da nan ta kullu ta kai iya wuya da ganin wannan abin al'ajabi abinka ga mara hakuri sai da ta bara ta hau sababi 'Kwarai lallai kam na dage na yi maka abinci na musamman harda hadin Salad a ciki amma kaki ci sai na wadda ba'a gidanka take ba tana yi maka harka shanye to wallahi da sake ba zai yiwu ba kina dai gani da idonki Goggo sannan idan naki zama kusa da shi ayi ta min surutu ni dama ai irin wannan kisisinar nake gudu". Muneeba itama bata kyaleta ba ta bata amsa cikin lumana ba hayaniya irin nata "Ayya kiyi hakuri kinsan mara lafiya 84 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria baya son abu mai karfi shi yasa da naga ya nuna baya son shimkafar na dama masa kuma ko bana gidansa ai hakki nane in kula da lafiyar tunda har yanzu miji na ne idan kinyi hakuri ma ni ba zama na zo yi ba anjima zan tafi in barki da shi kiyi hakuri ni tamkar bakuwace a gidan nan. Tsaki Suwaiban ta ja ta na kunkuni ni ina ruwana inma zama kika zo yi tunda dama can ba ni na kore ki ba, wannan kuma tsakaninki da mijin ne shi ya san me kika kunsa masa ya kore ki. Murmushi kawai Muneeba tayi bata sake kula Suwaiba ba don ta san idan taci gaba da kula ta to`za su yi tanki in tanka ne hakan kuma bai dace ba. Ta gogge masa bakinsa da (Tissue) ta dauki mafici ta shiga yi masa fifita duk da ga fanka na kadawa. Hakan da Muneeba ta yi ya sake tinjirar da zuciyar Suwaiba a ganinta Muneeba na nuna mata ta fita iya kula da miji kenan ta kale 85 1 a a a a n WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria su ta watsar sannan ta tashi ta buga uban tsaki ta juya zata fita Goggo tace "Wai Suwaiba me ke damunki ne yanzu mijin naki kike yi wa tsaki don rashin sanin darajarsa lallai kin kyauta. "In ma shi na yi wa tsaki Goggo ai na yi daidai tunda a gabanki ya nuna ni bani da muhimmanci a gare baki tayani nuna masa yayi daidai ba basai nice yanzu zakuce nayi masa ba daidai ba tunda shi naki ne ni kuma ba taki ba ce ai wallahi zanga yadda za a yi tusa ta hura wuta. Ta juya Fuuw! Ta fice har tana gwabje Mustafa da suka shigo tare da Isah. Isan ya ja tsaki ya ce Lafiyarki Malama kin bangaje mutum ba ko sannu kin wuce? Tа kalleshi shekeke tace "Tunda ba kai na gwabza ba sai ka kama bakinka ka barshi yayi magana". Ai wallahi ke ma kinsan dani kika gwabza haka da kinga Karyar wulakancin ki na gidan nan". Shi dai Mustafa ko ta kansu bai bi ba ya shige dakin dama tun 86 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaría zuwahsu da Muneeba suka fita da Isah shi yasa ma badakalar da akayi tsakanin Muneeba da Suwaiba basa nan. Yana shigowa Goggo ke tambayarsa kai da waye kake hayaniya? Yayi kwafa yace "Ni da yarki ne mara mutunci da bata san darajar na gaba da ita ba, yaya Mustafa fa ta gwabje inace wan mijinta-ne amma ta yi wucewarta ko ta kalleshi balle ta yi masa sannu ita ga wulakantatta don takamarta ta sami daurin gindi" ya sake yin kwafa ya ja uban tsaki. Goggo ta numfasa ka kyaleta nima din ai bata raga min ba balle wani tunda rashin arziki ta zaba sai mu zuba mata idanu kada ka dinga biye mata kuna sa'insa ka kyaleta ka fuskanci kuła da lafiyar dan uwanka shine a gabanka.. Har aka yi kiram Sallar Magriba Muneeba na gurin minjinta don sai da ta tabbatar ya ci abinci da ta yi masa da kanta faten dankali wanda ya ji hanta 87 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zarja sosai shi ta yi masa ya ci ya koshi sannan hankalinta ya kwanta. Ana kuwa kiran Magriba ta mike tana duban Mustafa tace "Yaya Mustafa ka tashi mu wuce kai da za ka wuce Dukku ga shi har dare ya yi maka mu je ka aje ni sai ka wuce tunda ban fito da mota ba. Ganin duk sun mike har Muneeba ta saka Hijabi ta rataya 'yar Jakarta sai gani su ka yi hawaye ya tsinkewa Mujeeb dukansu sun san dalilin Muneeba za ta tafi ta barshi ne yake hawaye. Tana ganin haka sai ta yi saurin barin gurin ta nufi kofa za ta fita muryar Mustafa ce ta tsayar da ita "Muneeba kada ki fita dawo ki gani ta juya tana duban Mustafa ya yi mata nuni da Mujeeb ta dube shi ta ce "Na ganshi Yaya Mustafa amma ka san dole in tafi gida tunda dare ya yi sannan ni ba anan zan kwana ba, hakuri zai yi gobe zan dawo”. Ta dawo ta gurfana gaban Mujecь din ta soma lallashinsa "Kayi hakuri Yaya 88 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Ya ce "Dole ke zan fara tambaya tunda ke ce a gidan ita ba zuwa take ba iyakacinta asibiti har sai da aka kawo shi gida sannan ta zo gidan nan kinga kuwa bani da Hujjan tambayarta saboda haka idan kin san kudin nan na gurinki ki bada don shima kudin ba nashi bane kudi na Ofis dinsu ne a ranar ya shigo da su a Jaka a ranar ciwo ya same shi shi ya sa ma daga Ofis suka nemi bayanin kudin tunda sun tabbatar gida yazo da kudin. In kuma kina ganin su zo su yi bincike da kansu to zan basu izini tunda ni kam na san basa gurina ko sun yi bincike ba za su kama ni da laifin taba musu dukiya ba. Za su gwada yatsu ne a durowar da aka dauki kudin kuma dole su gano yatsun wanda ya bude durowar indai yana gidan saboda haka tun kafin su tozarta ki a idon duniya gara ki dauko kayansu ki basu. WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Abinka ga dakikiya ai nan da nan ta tsorata da jin kalaman da ya shirya. Kudi kam tabbas ita ta dauka ta kirga su Dari biyu da hamsin ne har ta gayawa Hajiyarta sun yanke shawarar yanda za su yi da kudin sai gashi an yanka ta tashi balli ya huje idan tana son tsira da mutuncinta dole ta fito da kudin nan. To amma abin da kunya ace yadda suke tsama da Isah shine ya kamata DumuDumu da halin bera, dole ta yi wa abinda tayi ma abinda tayi kwaskwarima ya zamo ba halin bera ba. Sai ta ce "Eh kudin kam na gansu suna nan cikin dakin na boye su babu abinda zanyi dasu illa idan ka hanani kudin hidimarmu ni da waleeda in dauka in yi tunda kudi na miji na ne, amma yanzu kasancewar ka ce ba na shi bane zan maida inda na dauka. Isah ya yi murmushi ganin ta zurma tarkon da ya dana mata ya juya ya fita a dakin yana fita ta dauki wayarta ta kira WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Ya ce "Dole ke zan fara tambaya tunda ke ce a gidan ita ba zuwa take ba iyakacinta asibiti har sai da aka kawo shi gida sannan ta zo gidan nan kinga kuwa bani da Hujjan tambayarta saboda haka idan kin san kudin nan na gurinki ki bada don shima kudin ba nashi bane kudi na Ofis dinsu ne a ranar ya shigo da su a Jaka a ranar ciwo ya same shi shi ya sa ma daga Ofis suka nemi bayanin kudin tunda sun tabbatar gida yazo da kudin. In kuma kina ganin su zo su yi bincike da kansu to zan basu izini tunda ni kam na san basa gurina ko sun yi bincike ba za su kama ni da laifin taba musu dukiya ba. Za su gwada yatsu ne a durowar da aka dauki kudin kuma dole su gano yatsun wanda ya bude durowar indai yana gidan saboda haka tun kafin su tozarta ki a idon duniya gara ki dauko kayansu ki basu. 91 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Abinka ga dakikiya ai nan da nan ta tsorata da jin kalaman da ya shirya. Kudi kam tabbas ita ta dauka ta kirga su Dari biyu da hamsin ne har ta gayawa Hajiyarta sun yanke shawarar yanda za su yi da kudin sai gashi an yanka ta tashi balli ya huje idan tana son tsira da mutuncinta dole ta fito da kudin nan. To amma abin da kunya ace yadda suke tsama da Isah shine ya kamata DumuDumu da halin bera, dole ta yi wa abinda tayi ma abinda tayi kwaskwarima ya zamo ba halin bera ba. Sai ta ce "Eh kudin kam na gansu suna nan cikin dakin na boye su babu abinda zanyi dasu illa idan ka hanani kudin hidimarmu ni da waleeda in dauka in yi tunda kudi na miji na ne, amma yanzu kasancewar ka ce ba na shi bane zan maida inda na dauka. Isah ya yi murmushi ganin ta zurma tarkon da ya dana mata ya juya ya fita a dakin yana fita ta dauki wayarta ta kira 92 WATA KUSAN З Rahmatu Hassan Zaria hajiyarta ta shaida mata abin da ya faru. Hajiyar ta hauta da sababi tana fadin amma dai ke shashashace in banda ke shashasha ce ya za'a yi duk tuhumar da zai yi miki ki nuna kudin nan ke kika dauka alhali kin riga kin san abinda za mu yi da kudin aiki ne babba a gabanmu tunda da kanki kike shaida min kina ganin asirin da muka masa na kyamar matarsa Muneeba ya sake shi. To yanzu idan kika bada kudin kina da wasu kudin ne koko kina da hanyar samun wasu kudin da zamu je gurin boka ne?. Kinfa san aikin da za'a yi masa yanzun sai ya fi na baya wahala tunda na lura Tufka muke yi ana mana warwara wannan karon so nake yi ayi mai dungurungum ko dai ya saketa saki uku mu yar da kwallon mangwaro mu huta da kuda ko kuma duk idan haka ta gagare shi mu sa yadda za mu da shi tunda dai 93 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ko yanzu kasuwa ta tashi dan koli yaci riba. Suwaiba ta marairaice to yanzu Hajiya ya kike ganin zan yi tunda har na nuna masa kudin na nan a dakin Mujeeb din na boye su? "Ai komawa za ki yi ki gaya masa ke fa kin duba inda kika ajesu baki gansu ba in ma tuhumar zai yi sai ya tuhumi kowa dake gidan har kuwa da uwarsa tunda ai ba ke kadai bace a gidan ko kuwa ke kadai ke shiga dakinsa. Inma banda ke sokuwa ce har zai zo yayi miki burgar 'yan Ofis dinsu Mujeebu za su zo bincike akan dubu dari biyu da hamsin me akayi akai dubu dari biyu da hamsin a irin kudin da Mujecbu ya tara. Saboda haka ki natsu ki san abinda kike yi in kuma ba haka ba wallahi ke kika sani muddin kika kuskura kudin nan suka subuce a hannunki don na gaji da daukar kadarata in je saidawa don neman miki biyan bukata alhalin ke kin kasa aje 94 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria kadarar komai tamkar ba mai kudi ki ke aure ba. Kina dai kallon tsinanniyar yarinyar nan babu abin duniyar da bata tara ba amma ke kina zaune ita ba aiki take ba balle a ce albashi take dauka ki tabbatar yau kin gaya masa abin dana tsara miki gobe ina nan zuwa zan yi wa hanci tufka kada ya kuskura ya kara lakaba miki sata don ban haifi barauniya ba in kuma ba haka ba to kotu ce za ta rabani da shi tunda uwarsa na kalo ya wulakanci iri iri amma ta kasa tsawatar masa". Koda Suwaiba ta gayawa Isah zancen ta duba kudin bata gansu ba murmushi ya yi ya ce, baki gansu ba? Ai kuwa dole ki gansu tunda ba kafa ce da su ba balle su gudu daga inda kika aje su. Saboda haka tun wani bai ji zancen nan ba gara ki fito da kudin nan tunda ke da bakinki ki ka ce kin adana su. Inma wani ne ya zuga ki ya ce kada ki bayar to zai kaiki ya baro ina 95 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria jiranki zuwa yamma idan na ji shiru ba bayani zan dauki mummunan mataki wanda ba zai yi maki kyau ba. Ya juya ya fice a dakin ya barta duk wannan badakalar da suke tafkawa Goggo bata sani ba har saida Hajiya Harira ta zo. Sanyin fuska karara Goggo ta gani a fuskar Hajiya Harira, ko ga yanayin yadda suka gaisa. A tunanin Goggo kila daga can Dukku ne wani ya bato mata ranta. Batatambayi Hajiya Harira komai ba har sai da suka kebe a dakin Goggon bayan sunyi Sallah suna zaune suna cin abinci sannan ne take tambayarta "Ni Haj. Harira na ganki ne wata iri yau halan wani ya tabo ki ne? Ta gyara zamanta tare da zubar da Kashin kazar da take ci cikin wata roba sannan tace "Ni a Dukku babu wanda ya batamin rai anan gidan ne aka batamin rai shine ma musababbin zuwa na don ba zan yarda ba gara in biyo ba'asi. 96 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Goggo ta ware idanu, "Anan gidan? Wane ne shi kuwa wannan amma bani da masaniya ko? Ta yatsina fuska "Ta yiwu kila kina da masaniya tunda dan autan ki ne ya aikata abin. Ni kam na rasa wannan irin kiyayya da Isa ke wa Suwaiba tamkar wadda ta kashe masa gyatuma sam ba ya kaunarta, yanzu har ta kaima ya lakaba mata sharrin don kiyayya. Goggo ta dafe haba, "Isah ne da yiwa Suwaiba Sharri ? lalli yaron nan yana son ya zinguro sama da Kara, abin da kuma ba zai yiwu ba kenan. Gaya mini me Isah ya aikata?. Hajiya Harira ta zauna ta warware Goggo abinda ya faru ne 6acewar kudi a dakin Mujeeb, tare da tuhumar da Isah ke wa Suwaiba wai ita ta dauka tunda babu wanda zai bude dakin ya shiga in ba ita ba. Goggo ta hangame baki cikin kakabi da al'ajabi ta ce, "Wallahi Hajiya 97 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria bani da masaniyyar akan wannan al'amari Isah sam bai gaya mini ba sannan ita ma Suwaiban ai bata gaya mini ba, in da ta gaya mini da tun kafin ma ta gaya maki zan yi wa tufkar hanci. In banda. Isah shashasha ne yaushe ne zaka yiwa matar dan uwanka kuma uwar 'ya'yansa irin wannan sharrin zai kuwa ci kaniyarsa yau a gidan nan". Suwaiba da ke gefe ce tayi tsulum ta ce "Yaushe ne zan gaya miki tunda yanzu ba kya ganin laifin 'ya'yanki jiyan nan a gabanki nayi abinci har dake muka yi ta lallashin Mujeeb ya ki cin abincin, alhalin rabon sa da cin abinci tunda aka sallameshi daga asibiti. Kiri da muzu ya ki ci amma wannan kinibabbar (Muneeba take nufi) na zuwa ta dama masa Kostad tsaf ya shanye har girki tayi masa ya ci amma ni yaki cin nawa wai dama saboda bata zo ba ne kwana biyu yaki cin abinci har sai da ta zo Goggo duk tana kallo bata tsawatar masa 98 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ta nuna masa yayi ba daidai ba tunda ai yana jin duk abinda ake cewa. Ni yanzu a gidanan ai na shiga uku bayan sharri ma wata ran Isah duka na zai yi ana kallo ba za'a hana shi ba tunda ya tsane ni Hajiya Harira ta hau girgiza kai "Ai kuwa da yaga danyen aiki muddin ya ware hannu ya buge ki zan nuna masa ke 'yar gata ce "Tab dijam! Dama haka ce ke faruwa a gidan kika kame baki kika yi gum baki gaya mini ba har sai yaron nan ya yayi maki lahani. Goggo ta luguiguita murya ta shiga ba aminiyar ta hakuri Haba Hajiya Harira ke ma kin san idan ina nan da raina haka ba zata taba faruwa ba kiyi hakuri bari in kira Isan. Ta mike ta leka waje ta kwalawa Isah Kira, ya fito daga dakin Mujeeb ya zo gurin kiran da goggon ke masa yana ganin yanayin fuskokinsu Hajiya Harira da 'yarta yayi saurin gano makasudin wannan gangami. 99 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Goggo ta dubeshi ta ce, Isah 'Meke faruwa ne a gidan nan tsakaninka da Suwaiba har ban sani ba"?. Ya ce "Abin da ya faru naga tsakani na da ita shi yasa ban gaya miki ba, kuma da ta dawo da kudin kamar yadda ta ce ita ta adana babu wanda zai ji, tunda ko yanzu ma ai bani na fasa maganar ba. Kudi kam dole ta maidosu tunda ta ce ita ta dauka ta adana ni sam ba zan yarda wai ta je dauko su a inda ta aje bata gansu ba wannan tatsuniya ce". Goggo ta harzuka ta nuna Isah da yatsa ta ce "Kul! Ka kiyayeni ni Isah wannan wace irin magana ce za ka yi wa yarinya sharri bata ji bata gani ba wai ma wadanne kudi ne kake magana a kansu" Tiryan - Tiryan ya zayyanewa Goggo yadda ya ga kudin da inda ya adana su har yazo bai gansu ba da tuhumar da yayi mata da yadda ta amsa cewa eh ta gansu amma ta sake musu ma'adani a 100 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria 5 dakin Mujeeb amma daga baya take gaya masa bata gansu ba. Goggo, "Ni yanzu abin da nake so da kai tunda har ta duba bata gansu ba to abar maganar in dai har na isa da kai, kada in sake jin tashin maganar nan". "Yanzu Goggo shike nan ta ci bulus? Wannan ai an daure mata gindin gobe ta yi fiye da haka kenan. Babu ruwanka in ma ta ci kudin ai na mijinta ne, tana da hakki akan dukiyarsa babu ruwanka, wuce ka bani guri saura kuma inji maganar nan a wani guri" ya wuce yana yan surutai na takaicin wannan abu"Shikenan na kyaleta garin banza ai a farau farau din banza yake karewa. Hajiya Harira ta kanne wa yarta idanu suka dan yi murmushin cin nasara magana ta mutu, an kashe wannan Bos din. amma a zahiri sai ta ci gaba da sababi, "Haba wannan zance ai ya fusatani ya ban takaici kazafin sata! In 101 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ma banda yaron nan ya mu Suwaiba aiba ita kadai ba ce macen aure a gidan nan da zai ce ita ta dauki kudin mijuinta 'yar uwarshi ba gata nan me yasa ita bai tuhumeta ba sai Suwaiba don ita ce marainiya wayonsa. Ke ma Hajiya Rahin na ga beken ki da har za ki yi sake kina kallo Isah na ma Suwaiba cin kashin mahaukaciya da bakya masa birki matar fa yayansa ne duk da yake ganin ya girmeta, saboda haka, ke da kanki za ki ganar da shi kurensa kuma ya san cewa tana da babban matsayi a gidan nan inma ya manta ne". Goggo dai sai ban hakuri take ta yi wa aminiyarta har sai da ta sauko suka hau hirar duniya cikin raha sannan hankalin ya kwanta Suwaiba sun sami kaďaicewa ita da mahafiyarta a can kuryar dakinta Suwaiba ta dubi Hajiyarta ta сe "Kai amma fa hikimarki ta manya ta yi amfani Hajiya, cikin dan kankanin lokaci harshenki ya yi kokarin kwato mana yancin mallakar dubu 102 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria S dari biyu ni kam har na soma jimamin yadda zan mayar masa da kudin ta leko ta koma ashe ba za ta koma ba. ta ja tsaki “An gaya miki ni Hajiya ta wasa ce wai gwari ta bada magani an sha an mutu ai ni nan da kika ganni kura ce mai tsohon laifi na bara bai wuce ba ga na bana ya zo, Rahin ta sanni sarai bana shayin koma don zan iya fitowa ince kin dauka din kuma ba za ki bayar ba in sun isa kotu ta amsar musu, ita ai ta san da kunya ma ace wannan maganar ta fito yanzu abin da za'a yi tashi maza ki dauko min kudin nan tunda kura ta lafa babu sauran tashin tashina don na lura ke sokuwa ce yaron nan zai iya zuwa ya sake tsorata ki har ki fito da kudin nan ki bashi alhalin kinsan aiki ne Jawur a gabanmu dole ne mu sake sabon shiri akan wannan gawa taki rami, ni da zai mutu ma kowa ya huta don na san idan ya warke to watan jin kunyarmu ya tsaya kenan tunda ya riga ya ji hirar da kika 103 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria saki baki kina yi da kawarki alhalin kina sane boka ya gargadeki. Yanzu fa tunda ya ji aikin da aka yi masa ya karye sai dai a sake sabo, kuma sabon dole zai ja kudi za'a rufe bakinsa ne ya kasa fadin abinda ya ji ko a mantar da shi gabadaya sannan dole ki sake mallakarshi, in yiwu mallakar ma ta fi ta da kuma asa ya yi wa kaskar matarsa din nan saki uku don kada mu barta ma tsautsayi ya sa ta haihu a gidan nan ni ba yanzu ma buri na ya yi ya warke in ganki da wani cikin gara ko zai mutu ya zamana kin sake haifo wani da namijin wannan shine babban burina" uded Suwaiba ta mike tana bincike cikin durowar kayanta tana cewa "Aini Hajiya ban taba ganin mara zuciya irin matar nan ba miji ya wulakantata dake a gidan ku hảr mutane na miki daukar bazawara wadda aurenta ya mutu amma don rashin zuciya sai ki zo ki tare a gindinsa wai da sunan jinya, yanzu fa idan ya warke sai ta koma 104 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria こ gida simi-simi ba ko kunya tunda ba shi ya ce ta dawo ba". Ba dole ta koma ba, aini na fi son ma ayi mai gaba daya ne haihuwa da 'ya'yan hanji yayi waje rod da ita ta bar miki gidanki daga ke sai 'ya'yanki itama tsohuwar nan dole ki tubure masa ya maidata Dukku don ba dole bane zamanta tare da daku tana muku ido don na lura yanzun ta soma canza halayya" Suwaiba ta dauko kudin daga cikin tsummokaran da ta yi boyon a cikinsu ta mikawa Hajiyarta tana amsa ko duba su bata yi ba ta danna su cikin Jakarta da tazo da ita tana cewa "Ai kin gani abu yayi kyau sai kiyi kokari cikin satin nan ko karyar zuwa asibiti kiyi ki zo mu je mu ga boka, ayi mana aiki cikin gaggawa tun kåfin bakinsa ya bude ya tona maki asiri mu sa a daure bakin nasa ko a dasa masa mantuwar abin da ya faru a zuciyar in kuwa ba haka ba muddin ya fallasa aika-aikar da kika yi uwarsa ma kadai ba 105 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria zata lamunta ba duk da cewa tare muke fadi tashi da ita amma ai bata san an aikata wannan danyen aikin ba, nima din da muka je tare daga baya kika gaya min duk da dai kona sani ba zan hana ki ba, in ana neman mafita koma ma yi ake in yaso ayi istigfari daga baya tunda Allah da kansa ya ce shi mai jin tuban bayinsa ne (Wa'iyazubīllah kunji fa jama'a Allah ka shirye mu baki daya Ameen) Nima fa na taba haduwa da irin wannan tsinannan bokan shege gasu basu da tausayi idan mutum ya je hannunsu sai sun galabaitar da kuzarinsa ke lokacin da cikin Waleeda shi yasa kika fito bukkar nan wujiga wujiga ni dama sai da zuciyata ta gaya min kila fa bokan nan ya gwada miki halin su na 'yan akuya don wallahi bokayen nan duk haka suke da su da Malaman Zaure masu tsubbu basu da aiki sai turmushe matan mutane wai in dai kana son biyan bukata cikin gaggawa to suma dole ka biya musu bukatarsu. 106 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Tsinannu a haka suke kwasar ciwon alakakai su likawa mutum bai sani ba, saboda haka ki kiyaye duk inda za mu je duk rintsi kada kazamin banza ya sake yaudararki yana shanye romon jikinki gara komai yawan kudi mu basu tunda akwai su". Suwaiba na jin hudubobin mahaifiyarta kuma ta yi amanna da su don ita kam yadda take ji ma a zuciyarta in akwai abinda yafi wanda ta aikata a baya ko shakka babu za ta yi in zata sake mallakar zuciyar Mujeeb a tafin hannunta. Kai ita fa so take yi mulkin mulaka'u a gidan mijinta fiyema da wanda ake yamadidin Hajiyarta ta yi, in son samunta ne ta raba Mujeeb da kowa har mahaifiyarsa don a yadda take jin tsananin sonsa a zuciyarta bata son ya hada sonta da na kowa a fadin duniyar nan bata son ya samma kowa in ba 'ya'yan da ta Haifa masa ba, shi yasa duk 107 i WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria rintsi duk wuya zata san hanyar da zata bi ta raba shi da kowa koda zata rasa komai nata ne mutum na farko da take kishi ta tsana a duniya ita ce Muneeba Saboda a zahirance ta san Mujeeb ya fi son muneeba da ita shi ya sa ta tsaneta tsana

Chapter 4 of 8