Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 8
mai tsanani saukin abin ma bata haihu ba don da ta haihu son da zai yi mata sai ya fi haka. Ita kuma Muneeban ga ladabin tsiya da iya kanainaye miji da soyayya ji take tamkar ta hadiye shi saboda so sai kace ita kadai aka halittowa shi shi ya sa za ta iya yin ko wani irin abu ne komai muninsa don ta farraka wannan soyayyar. Mutum na biyu da za ta bada sunansa wa boka shine Isah kai wannan yaro yana shiga mata hanci a kudundune ya tsaneta itama ta tsane shi, abu daya ke sa tana raga masa don yana son Waleeda amma in bayan wannan wallahi za ta iya sawa ayi masa danyar aika-aika amma duk da haka zata sa boka ta saita mata shi kota sa kiyayyarsa a zuciyar yayan nasa ta 108 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria yadda ma zai koreshi a gidan sai taga ta karyar zumunci tunda abin na takamar 'yan uwantaka ake nuna mata. Ita kam Goggo ko da baki za su gama da ita to amma itama dole akwai Iblis (Boka) sunanta duk da irin muhimmiyar rawa da ta taka har ta tabbatar Mujeeb ya aureta sam bata son irin ladabin da yake wa Goggon ko da yake abin ya ragu sosai ta dalilin wani aiki da ta sa aka yi mata. Har ta raka Hajiyarta ta tafi ta dawo daki tana ci gaba da sake-sake. 109 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ****** ****** *******. T Ranar wata Asabar da hantsi misalin goma na safiya Dr. Aminullah ya zo duba jikin Mujeeb jiki kam yanzu Alhamdulillah sai godiyar Allah don har yana iya mota hannuwan sa da kafafunsa a dalilin tsayuwa da muneeba ta yi wajen shafa masa man zaitun mai addu'o'i a ciki kuma tana bashi yana sha gashi ma har ya fara magana kadan-kadan. Muneeba kaďai ya iske zaune a gefen da Mujeeb ke kwance tana aikin mutstsika masa man zaitun din a kafafunsa da jikinsa. Bayan ya yi sallama ya shigo suka gaisa da Muneeba ya cigaba da yaba mata akan wannan irin kokari da take yi "Wallahi kina burgeni abisa irin wannan jajircewa da kika yi akan kula da jinyar mijinki in dai Aljanna ake nema a dugadugan miji to muna miki kyakkyawan zato kin sameta kin gama saboda Kalmar farko da mijinki ya fara magana da ita a bakinsa 110 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria da ya fara magana ita ce sanya miki albarka gaskiya kinyi babbar nasara a rayuwarki ina fatan zaki dore akan aikinki na alheri. Mujeeb sai murmushi ya ke yi ya ji ana yabon Muneeba, ita ma murmushin take yi tare da amsa addu'ar da aka yi mata da Ameen Ameen Dakta kaima Allah ya baka ladan wannan dawainiya da ka yi da shi Allah kada ya gajishsheka". Ya fiddo abin awonsa ya auna lafiyar Mujeeb din yanayin jininsa da dumin jikinsa ya tabbatar komai nasa normal yake sannan ya dubi Muneeba ya ce "Ina Isah yake" Та сеe, "yana makaranta suna da Tes ne amma zuwa azahar zai dawo". Ok dama keken zama nazo da ita zamu fara saka shi a ciki ana yawo dashi a falo zuwa harabar gidan, nan bana son yana yawan kwanciyar nan ina son a dinga fita da shi yana shan rana kafin ta 111 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria yi zafi don tana da muhimmanci ga lafiyarsa. Muneeba ta fadada fara'arta 'Sannu da kokari likita mun gode Allah ya saka da alkhairi wannan dawainiya ta yi yawa wallahi Allah ya bar zumunci'. Da kansa ya fita ya dauko keken a bayan motarsa ya dawo ya iske Muneeba har ta kira Goggo dama tana bayi ne itama Goggon godiya da shi albarka ta dinga yi masa ya dauko Mujeeb cak daga kwance ya saka shi a keken sannan ya soma tura shi yana zagaye falon da shi da yake falon babba ne sosai. Mujeeb sai murmushi yake yi yana ta motsi da bakinsa alamun yana magana. Muneeba ta matsa ta kara kunnenta a bakinsa ta ji yana cewa "Nagode Dakta na gode na gode kalman da yayi ta maimaitawa kenan. Muneeba ta gayawa Dakta abin da ya ke ta fadi Dakta yayi murmushi yana dubansa ya ce, babu komai yadda nake 112 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria tausaya maka wannan matsalar data sameka wallahi zan iya yin komai don ganin lafiyarka ta dawo kamar da ka dawo cikakken mutum kamar kowa". Tun daga wannan rana sai ya kasance Muneeba da wuri take zuwa don ta fito dashi harabar gidan ya sha hantsi nan zasu zauna suyi ta hirarsu duk da maganar tasa bata fitowa bata fitowa sosai kuma a sarke take ba kowa ke iya ganewa ba yawanci sai ita Muneebance ke ganewa. Wannan abu na ciwa Suwaiba tuwo a kwarya shi yasa ma ko sau daya bata taba dauko shi ta fito dashi ba. In har ba Isah ko Muneeba ne suka fito dashi ba, in kuma ba sa nan to ranar a daki zai wuni a kwance don ba ya iya hawa shi kaďai sai an taimaka masa. Ranar wata Juma'a gidan shiru babu kowa Goggo ta je sallar Juma'a ita da Isah Suwaiba kuma na dakinta tana bacci sai Muneeba ce kadai a dakin Mujeeb hakan ya sa ta gungurashi zuwa 113 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria bayin dakin baccinsa a zaune akan kekensa tayi masa wanka dama tunda aka kawo keken akai take masa wanka. Tana gama masa suka fito ta zo ta goge masa jikinsa ta shafa masa mayukansa masu kamshi ta saka masa kaya ta fesa masa turare shi dai yana ta binta da kallo yana murmushi. Ya riko hannunta ya yi magana "Zan kwanta". Ta yi sauri ta matsa da shi gurin kwanciyarsa ta kamashi ta kwantar da shi ya yi mata ishara da hannunsa cewa ta zo ta zauna kusa da shi ta yi kamar yadda ya umurceta sai ya sa hannun mai lafiya ya ja ta zuwa kirjinsa ya kwantar da ita har sai ta dinga jin bugun zuciyarsa ke yi cikin kunnenta ya dinga sauke ajiyar zuciyar irin ta yaron da aka lallasa aka bashi wani abu da yake so har yayi kuka kafin a bashi abin. Itama sai taji wata irin natsuwa da ta manta rabon da ta ji irinta a tare da mijin nata idan ta yi alamun za ta tashi sai ta ji 114 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ya hanata da hannunsa dole ta hakura ta kyale shi tunda ta lura hakan yake so hakan ya haifar masa da natsuwa a zuciyarsa. Ta yi masa magana a kunne "Ka yi hakuri ka san gidan nan bamu kadai bane, sannan kuma Goggo sun kusa dawowa daga masallaci kada su shigo su ganmu a haka ido da kunya". Rufe bakinta ke da wuya sai ganin shigowar Suwaiba suka yi tsulum a falon wannan dama dabi'arta ne babu sallama a cewar ta ita da dakin mijinta babu wanda ya isa ya yi mata dokar sai ta yi sallama, sannan za ta shiga, ta manta cewar dokar Allah ce yin sallama a guri kafin ka shiga. Wani uban ashariya da ta zunduma shi ya firgita Muneeba har jikinta ya dauki tsima "Kan uba can dama jarabar da ke kawo ki gidan nan kullum kenan kina like masa ana cin amana ta ni ga hoto an ajiye ina ganinsa a mara lafiya 115 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ashe garau yake tunda har ya iya lunkumeki a jikinsa. Lallai yau za'a yi tsiya a gidan wallahi bari Goggo ta dawo ta zo ta ga shedancin da ake yi a gidan nan tana ruwan tijarar ne Goggo suka dawo ta maimaitawa Goggon abin da ta zo ta gani yake faruwa har sai da ta kara gishiri tana kukan munafunci. "Wannan ai zalinci ne ni ina zaune da shi bai bani nawa hakkin ba wata da watanni ina ta hakuri shine ke zan sameki yana baki naki hakkin to wallahi sai dai a raba kwana ki dawo dakinki ki zauna a dinga gungurashi ana kaishi dakin wadda take da girki ko kuma mu dinga biyo shi dakinsa in kuma ba haka ba wallahi zan tashi hankalin kowa a gidan nan don ba zan yarda da cin kashi ba”. Goggo ta hau bata hakuri "Ki yi hakuri ai ban san haka ce ke faruwa ba wannan ai rashin kunya ne don an san bana gidan shine za'a zo a tilasta shi yin abinda 116 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria baiyi niyayya ba yana fama da kansa in abinda ki ke muradi kenan ai sai ki dawo dakinki. Muneeba kuka ta saka tana karyata wannan sharri da Suwaiba ta yi mata Isah kuwa hasala yayi yace "Haba Goggo haba Goggo wannan maganar bata dace ta fito daga bakinki ba yanzu ke har za ki yadda da karya da sharri irin na Suwaiba in ma hakan ta faru ai mijin ta ne ita me ya sa ba za ta zo ta zauna kusa da shi ba in har son gaskiya take masa wallahi Muneeba ba ta da rashin kunyar da za ta iya yarda hakan ta faru alhalin ta san gidan nan ba su kadai bane. Gaskiya Goggo idan kika yarda da maganar nan baki yi wa Muneeba adalci ba a irin yadda ta tsayu tsayin daka akan kula da lafiyar danki wadda kike so din gata nan bata tsinana masa komai ba sa mummunan halin da take bullo da shi kala-kala. 117 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Mujeeb ma hawaye yake yana karkadawa Goggo hannu a nufinsa nuna mata ya ke Karya Suwaiba ke yi Muneeba ta soma hada duk wani abu da ta san nata ne a dakin Isah ya tari gabanta yana cewa "Aunty Muneeba wai me ki ke shirin yi kenan ba fa za ki tafi ba akan wannan 'yar maganar to meye ma abin damuwa ina ce mijin ki ne ai gara ya nuna mata ke ya fi so tunda har ya kasa hakuri da al'amarinki dama duk abinda ya faru baya ba yin kansa bane, ina ganin yanzu alkadari ne ya karye don girman Allah ki yi hakuri ki manta da wannan shirmen in ni ne ma wallahi a gabanta zan yi abinda na ke so sai dai ta mutu. Muneeba ta rataya jakarta ta dubi Isah ta ce "Ka yi hakuri Isah dole in tafi ba zaka gane irin radadin da ke zuciyata bane kwarai na san Mujeeb miji na nane kuma don in yi jinyarsa in sami lada gurin Ubangiji na ya sa nake zuwa gidan nan ba don wani abu ba amma tunda an fara yi 118 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria min bita da kulli to gara in dan ba gidan iska idan aka kwana biyu na dawo. Haba Aunty wallahi dama haka ake so zuwanki ne bata so ke kuma don girman Allah kada ki yi fushi ki tafi ki bar ladanki tunda ba don ita ki ke yi ba domin Allah ki ke yi abinda take kwakwazon an yi mata dinma in har an yi ma ai shine daidai tunda hakan zai samar masa da natsuwa kuma natsuwarsa tana cikin nasarar samun lafiyarsa. Duk yadda Isa ya so ya tsayar da tafiyarsa Muneeba bai sami nasara ba don har rantsuwa ta yi masa cewa sai ta tafi tunda har zancen Suwaiba ya yi tasiri a zuciyar ta ke tana ta kurawa danta yana yin abinda bai yi niyya ba kenan a cewarsu ita jarababbace wannan kalma ita tafi komai kona mata zuciya. Shi ma Mujeebun kukansa ya tsananta har da shessheka, saboda ya yi ta magana babu mai jinsa Isah ne ma ya kai. kunnensa bakin ya ji yana masa 119 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria umurnin kada ya bari Muneeba ta tafi ya bata hakuri. Shi kuma ya yi-ya yi ta ki hakura itama Suwaiban bata fasa fadar maganganu ba wa wadanda suka dada tunzura hakurin Muneeba ganin Goggo tana jinta bata iya tsawatar mata kasancewar tana shakkar kada Suwaiban ta gayawa uwarta Hajiya Harira. Muneeban na barin gidan Isah ya dubi Goggo yace "Shi ke nan Goggo mai yi miki jinyar danki tsakani da Allah ta tafi ni kuma kin san ba zama na ke yi ba saboda makaranta, saboda haka ta barki da Suwaiba wallahi ko kaffara ba zan yi ba ba za ta kula da jinyarsa kamar Muneeba ba kina gani kwana biyu ma bata zo gurinsa ba ya kauracewa abinci yanzu kuwa sai abin da Allah ya yi. Shi ma daukar littafinsa ya yi ya fice ya bar musu dakin Muneeba na isa gida Inna Amina ta lura da yanayin fuskar shine fa ta biyo ta daki ta isketa kwance akan gadonta tana tsiyayar hawaye ta zauna a 120 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria gefen gadon tana cewa Lafiya kike kuka jikin nasa ne ya tashi"? Ta girgiza kai, to mene ne? Gaya min don kin jefa zuciyata cikin damuwa ta kwashe duk abinda ya faru ta gayawa Inna Amina ta kara da cewa "Na hakura da zuwa jinyar tasa duk randa Allah ya sa ya warke idan yana da muradin cigaba da zama da ni ya zo ya neme ni, amma na gaji da wulakancin matarsa ta yi min Goggo ta yi min, wallahi da a ce ina biyewa halin matarsa da kullum sai an ji mu amma yau ta kaini makura don wallahi na tsani abinda ban yi ba ace na yi,. Inna Amina ta yi dan murmushi ta ce "Ke don Allah share hawayenki in ma ya kwanta da ke ba mijinki bane, in ita ta gaza da al'amuransa ke ma sai ki gaza wannan ai ba zai yiwu ba. Wallahi mama babu abinda ya faru tsakaninmu kawai ta shigo ta ganni kwance a saman kirjinsa ne kuma wallahi ina zaune kusa da shi ne ya matsa min sai 121 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria na sa kaina a kirjinsa, da na ki ma shi da kansa ya kamo ni ya kwantar da ni shi ne fa abinda ta gani", Inna Amina ta kamota ta tasar da ita zaune tana share mata hawaye "Yaro dai yaro ne in banda abinki Muneeba ai abinda yake so ya fi haka a gurinki tunda kullum fa kece a kusa da shi sannan ki duba tsawon watannin da yayi yana jinya idan aka haďasu da watannin da kika yi a gida ma ai kun haura shekara rabonki da shi to meye in kin nuna mararinku akan juna, kawai kishi ne ke damun zuciyar Muneeba saboda haka ba zaki daina zuwa ba karewa ma dakin zaki ko, ai ba sakinki yayi ba, in ya so idan ya warke ya ga baya son zamanki sai ya baki takardanki. Muneeba ta ce Ni gobe ma Dukku zan tafi garin nan ya fita raina sai na kwana biyu zan dawo "B a zan hana ki tafiya ba amma ki kwantar da hankalinki wannan ba wani abin damuwa ba ne da zai sa ki dami zuciyarki tun bayan dawowarta 122 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Isah ke 'ta kiranta a waya tana tsinke kiran nashi daga bisani ma sai ta Daina taba wayar har ya hakura. Ashe ba hakura ya yi ba sai gashi a daren ya zo sake bata hakuri mujeeb ne ya matsa masa yazo ta ce masa ita ta hakura gobe ma tana nan zuwa a tunanin Isah da gaske za ta zo bai san ta kifeshi bai bai ne ita gobe ma kauyen su ta nufa. Washe gari kuwa ta kama hanyar Dukku ta isa da wuri innarsa na ta mamakin ganinta da ta yi da akwatin kaya kuma ta ce sai ta kwana biyu zata koma inna ta ce kwana biyun Malam Bahaushe ko kwana biyun gaske". Ta ce kwana biyun Malam Bahaushe", shi kuma majinyacin kin daina kula dashi kenan kin bar ladan ko? Ta ce inna na dinga zama da shi kenan ga goggo sannan ga matarsa Isah ma yana nan tare da shi indai ba makaranta ya je ba”., Ta ce "Na san duk suna nan amma wannan ai ba Hujja bace da za ta sa ke ki 123 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria taho ki bar wa wasu ladanki kin, kuwa san ladan wanda ya yi jinyar wani balle ma ladar jinyar miji ga matarsa? Zan dai fi yarda idan kika ce min wani abu ne ya faru kika ki zuwa amma ba haka kurum ba" Da kyar ta gayawa Innan abinda ya faru sai gani tayi Innan ta girgiza kai ta ce "Allah ya kyauta amma wannan aiba abin jin zafi bane balle har ya sa ki yi fushin da zaki bar miliyoyin ladanki da bama kisan iya adadinsu ba shike nan ki zauna duk ranar da zuciyarki ta lafa sai ki koma. Kwana daya biyu Isah bai ga Muneeba ba gashi kuma jikin Mujeeb yayi tsananin tashi ta yadda komai ma sai an yi masa don ko kekensa ba'a dora shi ya daina cin abinci ko wanka ya ki yarda a yi masa yana kwance kawai sai aikin tsiyayar hawaye. Hankalin kowa a gidan ya tashi musamman Isah da Goggo wadanda suke ganin ta leko ta koma ga samuwar lafiyarsa Isah da ya je gidan Inna Amina 124 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ita ke shaida masa Muneeba ta tafi Dukku ya zo ya shaidawa Mujeeb shine fa yace maza a lokacin yaje Dukku su taho tare. A Dukkun sun yi ta tafka Muhawara da ita tace sam ba zata koma Gombe a lokacin ba ya tafi za ta zo shine yaje ya shaidawa Baffa Adamu abinda kenan. Baffan ya jinjina kai ya ce ita Rahin din ce ta turo ka ka tafi da Muneeban don ta yi jinyar danta? Lallai duniya da abin mamaki take shin tamanta lokacin da ya ce ta zauna sai ya neme ta na kirata a matsayinta na mahaifiyarsa na ce ta lallashe shi ya zo ya dauki yar uwarsa ta ce ita babu ruwanta a kyaleshi me. daki shi ya san inda yake masa Yoyo? In ta manta ka je ka ce na ce ka tuna mata ko kuma ni da kaina zan tuna mata. Ai dama zuru na yi mata don ko zaman jinyar da Muneeban ta je ta yi kyalewa kawai na yi sabo da tausayin 125 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria halin da yake ciki amma ba don zumunci ba. Ka tashi ka je ka shaidawa mata Muneeba ba zata dawo ba har sai ranar da ita da kanta ta tako gidan nan ta bamu hakuri akan irin cin kashin da suka yi wa yarinyar nan in kuma ba haka ba to ta je ta yi jinyar danta ai ita ta haifi abinta ba wani ya haifar mata shi ba kamar yadda take fada. Isah ya raunana murya "Baffa don girman Allah kayi hakuri ni kaina na san Goggo bata kyauta muku ba amma ku yi hakuri ku duba makomar rayuwar Yaya Mujeeb wallahi a halin yanzu rayuwarsa tana cikin hatsari sosai ta kai fagen ma sai dai a kwantar dashi sai dai a tayar da shi abhinci sam baya ci duk dalilin rashin Muneeba a kusa dashi”. Baffa Adamu ya ce "To dama ai mutum yana da ranarsa kuma ba'a sanin yana da rana sai bayan baya guri ko idan ya mutu tunda yanzu ta san akwai ranar da 126 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria muneeban za ta yi mata to ni ban hana Muneeba kowa ba jinyar mijinta ba amma da sharadin sai ta rahin din ta zo nan da kafafunta ta bamu hakuri kuma ni da kaina zan dawo da ita ka tashi ka je ka shaida mata sakona don mun gaji da cin kashi a tsakar ka da akewa yarinyar nan da me za ta ji da rashin haihuwa da Allah bai bata ba suke mata gori ko kuma da kwarzabarsu ita da abokiyar zamanta"., Isah haka ya taso gwiwa a salube ya yi sallama da Baffa Adamu ya dau hanyar Gombe wannan sako na Yayanta bai risinar da zuciyar Goggon ba sai ma tayi mirsisi da sharadin daya gindaya mata na cewa sai ta zo da kanta ta ba su hakuri sannan Muneeba zata dawo a cewarta ai idan ta yi haka ta zubar da girmanta ace ita da kanta za ta je ta ba Muneeba hakuri to ita meye nata tunda ba įta ta kore ta ba. Isah har kuka yayi shi da Mujeebun suna rokon Goggo da ta je 127 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Dukku amma taki saima ta suri gyalenta ta bar gidan. Dr. Aminullah ne ya zo ya iske abin dake faruwa Isah ya gaya masa yadda rigimar ta samo asali Dakta ya kada baki yace "Alhamdulillah aimu likitoci abinda muke son ji kenan saboda muna tunanin gaban nasa ma ba ya aiki a dalilin matsalar da ya samu dama jira na ke ya warke in akwai matsala sai a san abin yi, yanzu ko ba abin da ya faru tsakaninsu muna kyautata zaton yana nan garau. Yanzu kana ganin idan muka saka shi a mota muka je gurin Baffan naku ba zai bashi ita ba tunda dama tun farko shi suke son ya je?. Isah ya ce "Eh to ban sani ba ko Baffa zai yarda bari mu gwada mu gani". Suka kama shi suka kaishi cikin mota suka saka kekensa sannan suka dauki hanyar Dukku basu iske kowa a kofar gidan ba hakan ne yasa suka fito da keken Mujeeb suka ciccibeshi daga mota suka 128 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria dora shi akai, sannan Isah ya gungura keken suka shiga cikin gida. Salallamin da matan gidan suka hau yi saboda ganin Mujeeb yasa Baffa Adamu fitowa daga turakarsa ya hau Isah da fada "Haba Isah don me za ka dauko yaron nan ka zo da shi yana cikin mawuyacin hali irin wannan ai ni bashi na ce ya zo ba ita Rahin din na ce sai ta Zo Dr. Aminullah ya risina yana gaida Baffan sannan ya ce "Ni nace mu taho da shi, ita gwaggo ta ki bada hadin kai tazo, kayi hakuri Baba matsalarsa tana bukatar a tausaya masa". Baffa ya matsa jikin keken ya dafa kafadar Mujeeb ya ce "Sannu Mujeebullah haka ciwon nan ya maida kai? Allah yasa kaffara ce kayi hakuri matarka zata dawo amma sai Rahin ta zo dole saboda akwai maganganun da zan yi da ita akan matarka ni kuma bata isa in bita inda take ba". 129 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Mujeeb ya soma sana'ar tasa ta tsiyayar hawaye saboda ya san ko yayi magana ba dole bane a jiyo sautin maganar tasa duk matan gidan da yaran gidan sai aka hau koke-koke ganin kukan da Mujeeb ke yi ga shi ya zama abin tausayi mutum lafiyayye kakkarfa mai kwarjini da cikar halitta ga kudI, amma yau shine a na kashe cikin keken guragu ana tura shi ya rame ya kwantsame ya fiya hayyacinsa. Kai duniya ina za ki da mu duk wanda bai ji tsoron Allah ba wallahi ya yi babban asara duniya da Lahira". Baffa ne ya ke ta nanata wannan Kalmar da hannunsa ya tura keken Mujeeb ya shiga da shi turakarsa shi ma sharar kwalla yake yi yace Isah ya shigo da bakonsa. Isah ya dubi Baffa yace, "Wannan likitansu ne a can asibitin da ya kwanta to shine yake zuwa gida koda yaushe yana duba shi, ko wannan keken ma shi ya siya ya kawo masa". 130 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Baffa ya sake mikawa likita hannu suka yi musabaha yana cewa "Mun gode da dawainiyya Likiya Allah yayi albarka ya shirya zuri'arka ya jikan magabata ya kara maka budi a al'amuranka. Dr. Aminullah ya amsa da Ameen Baba" tare da nuna jin dadinsa bisa ga wannan addu'ar Baffa ta kanshi ya amshi abinci yana ba Mujeeb yana lallashinsa da cewa in dai ya ki ci ba zai bashi matarsa ba, ai yana jin haka ya hau hadiye tuwon laushin da aka bashi kafin kace meye har ya cinye. Duk sai abin ya basu mamaki. Baffa da kansa ya kira wayar Goggo da kyar ta iya dauka saboda a duniya tana shakkar sababin yayan nata, don ta san halinsa, ko gaisuwar bai amsa ba ya ce "Wallahi Rahin ki kiyayi rudin duniya tunda har ni zance ki zo ki ki zuwa saboda ba kya ganin kowa da gashi, to wallahi ki yi wa kanki karatun ta natsu ga Mujeebu abokinsa likita ya 131 MATANUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria kawo shi bikon matarsa ni kuma na yi rantsuwar ba za ta koma ba sai kinzo nan gaba na da Kafarkı sannan za ta koma in kuma kinki zuwa har shi ita sun bar maki gıdan za su zauna anan gurina sai kici uwar da zakı ci Gomben. Ya kashe wayarsa ya barta da saluba6ben jiki ko Suwaiba bata gayawa ta shirya ta baro Dukku a motar haya zuwa Gombe zama akayi na musamman anan gidan su Baffa zaman da ya hada da duka su Baffan da Babansu Muneeba da Innarsu da ita kanta muneeban ga Mujeeb likita Isah ne kawai ya fita. Maganganu sosai aka yi akan abubuwan da ke faruwa a gidan Mujeeb din an bukaci Goggo ta fadi in akwai wani abu da Muneeba ke mata na 6atanci ta fada ayi wa hanci Tufka. Sai ta kama kame-kame zance babu na kamawa balle a yanke wani hukunci. A karshe dai yayyin nata suka yi mata fada sosai tare da nasiha akan muhimmancin 132 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria zumunci itama Muneeban sun yi mata nasiha akan ta ci gaba da ba Goggo tata girman a matsayin na uwar mijinta kuma yar mahaifinta duk da yake sun san irin girmamawar da take mata amma suna so ta kara akan wadda take mata. Shi ma Mujeeb sunyi masa tasa nasihar tunda yana jinsu akan ya kamanta adalci tsakanin matayen nasa daga karshe aka rufe zaman da yi masa addu'ar Allah ya bashi lafiya. Baffa Adamu ya yi wa Muneeba umurnin ta bi Mijin ta, ya ce idan sun isa Gombe su biya su dauki Innarta Amina ta rakata dakinta suka dingumo su hudu suka taho gombe Isah da likita sune a gaban motar Mujeeb da Muneeba a baya hakan ne ya bashi damar da yayi kwance a cinyar Muneeba 'yar hirarsu a hankali. Likita yana tuki yana kallonsu ta madubi yana murmushi saboda shi sha'awar soyayyar su yake yi don shi bai taba tunanin suna da wata matsala a 133 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria rayuwar aurensu ba bisa ga yadda yake ganin kulawar da Muneeba ke bashi a asibiti, ashe matsaloli ne cinkus a rayuwar auren na su sai da ya shigo cikin rayuwar ne ya ga hakan wanda yana fatan Allah ya sa karshen matsalolinsu ya zo kenan. Ganin su da Suwaiba ta yi a tare sannan har da Inna amina kuima kai tsaye Muneeba ta bude dakinta su Jume da Maigadi suka hau aikin sharewa da gogegoge ya tabbatarwa Suwaiba bikon Muneeba aka je wato don munafinci har da Goggo da shi Mujeebun da bashi da lafiya lallai dole ta dauki babban mataki tunda Munmeeba ta dawo gidansu. Komawarta daki ta yi babu wanda ta yi wa sannu a cikinsu sai da Inna Amina ta tabbatar an gyara ko'ina na dakin Muneeba sannan ta kara yi musu nasiha daga bisani ta tafi. Muneeba ta shiga kicin dinta ta shiryawa Mujeeb lafiyayyen abinci da abin sha sannan ta zauna ta tsala kwaliya wadda 134 WATA KUSAN З Rahmatu Hassan Zaria rabonta da yin irin tatun barinta gidan ko turaruka ta fesa yayi kala goma sai kamshi ya iya rikita kwakwalar mutum. Ta dauki tiren da ta shirya kayan abinci ta isa dakinsa, Isah na ganinta ya hau murmushi yana fadin "Kai Auntyna wannan kwalliya ai sai ki rikitamin kwakwalwa yaya ko da yake idan yana ganin irin wannan sai ya fi saurin warkewa tunda ya kwana

Chapter 5 of 8