Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 8
biyu baiga irin wannan ba. Ya yi saurin amsar tiren hannunta sannan ga lafiyayyen abinci gaskiya kin kyauta gara ki dage ki rike gidanki da mijinki ke kika fi sanin me yake so menene baya so?. Ta zauna daf da mijinta tare da fadin 'Ya jikin naka ina can ina hada maka abincin ne dana gama na yi wanka na yi Sallah shi yasa na dade". ta dubi Isah 'Ka kawo masa ruwa yayi alwala ne? ya ce, Eh har Sallah ma ya yi abinci kawai ya rage zai ci ni bari in fita gurin budurwata tunda yau kin dawo ke za ki 135 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria kwana dashi". Ta Harare shi Lallai Isah baka da Kunya a gabanmu kake fadar zaka gurin budurwa to sai ka dawo ka gaisheta". Yayi dariya yana sosa keya, ya wuce ya tafi Muneeba ta janyo tiren ta soma zubawa Mujeeb abinci shi kam yayi sakato tamkar wani sakarai yana ta aikin kallonta har sai da ta dago suka hada ido suka yi wa juna murmushi. Ta dinga bashi abincin yana ci tana bashi lemu yana sha sai ganin Suwaiba suka yi a gabansu tana huci ta dubi Muneeba shekeke ta се "То tunda kin dawo dakin mijinki yau sai a san abinyi raba kwana za'a yi yau yana can gobe yana can ko ayi kwana bibbiyu don ba zai yiwu kullum kina leke da shi ba tunda ba ke kadai bace matarsa ehe!. Muneeba ba ta ce Uffan ba Illa ma ta cigaba da ba mijinta abinci a baki yana ci Suwaiba ta sake kulewa ta ce "Kinafa ji na ina magana in kuma tare zamu dinga kwana da shi dukanmu sai in ji. 136 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Sai da Muneeba ta gama bashi abinci ya sha ruwa sannan tayi magana "Duk yadda kika ga dama ki yi, amma ni kam yau da gobe zan kwana da mijina in kula da shi jibi da gata naki ne, in kinga zaki daukeshi zuwa dakinki ko ki biyo shi duk daya". Jin Muneeba ta maida kwanan bibbiyu yadda suke yi sai ta ja Uban tsaki kawai ta fice. A kwana biyun da Muneeba tayi tare da Mujeeb har wata kiba yayi ya sake murmurewa kasancewar duk dare a kirjinta yake kwana kuma duk wani abu da yake so tana yi masa sai dai ta lura ba ya da wani kuzari irin na sauran maza kila sai yaga likita ko ya na da matsala ne ta wannan fanni ba su sani ba. Washe gari ta nemi shawarar likita akan tana son ya fara gwada tafiya tunda ta ga ya dafa bango ya mike Dakta Aminulla ya ce ta jira shi gashi nan zuwa zai nuna mata yadda za su yi. 137 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Ba'a fi mintuna talatun ba sai ga Dr. Aminun da Sandunan koyon tafiya guda biyu Muneeba bana ganinsa ta hau murmushi tana cewa Sannu likita da dawaniya kullum baka gajiya daga maganar za'a fara koyon tafiya shine har ka taho da gudunmuwar kafa. Yayi murmushi ai gara ayi koyon tare da madogari don kada a sami matsala ya zo ya fadi idan yana bin bango gara idan da wannan sandar ba zai fadi ba Insha Allah Allahu za ta zamo masa abin dogarewa shi yasa na zo masa da ita. Likita ya mikar da shi tsaye ya bashi sandunan ya amsa ya dogara ya soma takawa a hankali. Muneeba ta yi saurin zuwa ta tsaya a bayansa likiya ya yi dan Murmushi ya ce "Kai Madam kina son abokin nan nawa da yawa kin dauka zai fadi ne kika taro bayansa itama murmusawa ta yi cikin jin kunya ta ce "wallahi gani nayi kamar jikinsa na rawa shi yasa na zo bayansa kada ya fadi. 138 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Jikinsa kam dagaske rawan yake yi amma Dakta ya hana Muneeba ta rike shi ya ce ta barshi ya yi tafiyar da kansa. Haka ya yi ta zagaye falonsa a hankali a hankali, amma fa yayi zufa kashirban don har diga take yi daga fuskarsa ya dubi Dakta ya yi magana can kasan makoshi "Na gaji zan zauna kada na fadi" jin haka ya sa Dakta ya kama shi ya zaunar da shi a gefen kujera ta zaman mutum biyu. Gaskiya ka yi kokari yanzu shikenan ba zaman keke tunda ka fara tafiya kullum abin da za'a yi kenan koyon tafiya sai ka gaji da za'a maidaka keke ko a zaunar da kai a kushin. Ranar da Suwaiba ta amshi girki jarfa aka sha da ita wai lallai Muneeba ba zata zauna gurin Mujeeb ba sai dai idan ta gaishe shi ta fita ta bar dakin tunda ba girkin ta bane. Muneeba ta tashi tayi tafiyarta daki Isah da ya dawo ya iske shi kadai a 139 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria dakin yana ta kici-kici hawa kekensa amma ya kaga shi ba murya ba balle yа Kwalawa wani kira. Isah ya kama shi ya dora shi bisa akan keken sannan ya nufi dakin Muneeba yake ce mata ya aka bar Mujeeb shi kadai daki gashi nan saura kiris ya fadi garin hawa kekensa. a Muneeba ta gaya masa yadda suka yi da Suwaiba da safe Isah ya ce wannan ma sam ba zai yiwu ba ita ba zata zauna ta kula da shi ba sannan ta ce ke ma kada ki zauna to bata isa ba ai ba kwana kika ce zaki yi da shi ba tunda ita abinda ke ranta kenan ba kula da lafiyarsa ba. Bari in je gurin Goggo sam ba zai yiwu a barshi ba, shi da ke neman taimako ya je ya sami Goggo da maganar sai ta nuna gara a kyale Suwaiban in yaso duk ranar girkinta Muneeban ta dinga fito da shi harabar gidan zai ta zauna tare dashi. Isah ya ce yanzu Goggo shi kenan duk abinda matar nan keso shi za a yi mata a 140 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria dinga jin maganar ta tamkar ana tsoronta tana juya mutane son ranta". Ta ce Isah kaga bana son neman fitina ka je ka yi abin da nace tunda na lura yarinyar nan neman tashin hankali take yi da kowa a gidan nan, Isah ya koma dakin Mujeeb ya sako shi kekensa ya fito da shi harabar gidan ya je ya kira Muneeba ya ce ta zo inji yayan na sa yana can harabar gidan. a A can ta same su da Isan shi yana zaune a kekensa isan na zaune a kujerar roba a gefensa ma wata kujerar ce anan Muneeba ta zauna suka shiga hira abinsu don muryar Mujeebu ta soma fita. Wannan abu ya bata ran Suwaiba, saboda tana hangensu ta window dakin baccinta ta yi kwafa ta fada a fili "Lallai ma isan nan wato tunda na hana abi min miji daki shine ya fito da shi waje don su haďu to zan bullo masa ta bayan gida bai sani ba kenan". 141 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Sabon salo ta fito dashi idan ita ke girki sai ta kama kofar falon Mujeeb din ta rufe shi a ciki in har bata dakin don kada wani ya shiga sai da suka yi tsiya-tsiya ita da Goggo akan ta ce sam ba zai yiwu ta dinga rufe shi a daki ba Isah ma yayi mata nasa tijarar sannan aka sami saukin al'amuranta. 142 2 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ****** ***** ***** Jikin Mujeeb yayi sauki sosai don yanzu ma ya rike sanda shi kadai yake tafiya maganarsa ma tangarau take fitowa hannun sa da ya karye ne kadai wani lokacin yake yawan masa zogi ko yayi masa nauyi. Har a wannan lokacin bai koma bakin aikin ba kasancewar jikinsa bai gama koma masa daidai ba, kuma yana son zuwa ganin Likita a (Egypt) Ko da yaushe Mujeeb ya kalli Suwaiba sai ya dinga jin kyankyaninta a dalilin badakalar da yaji da kunnensa ta yi da boka har ta kai ga shima ya shiga cikin kokwanto lafiyarsa kasancewar duk bokayen nan zandikan fasikai ne masu dauke da cututtuka zamani iri iri, in kuwa haka ne yana rokon Allah ya rufa masa asiri bata je ya kwaso cuta ta lakaba masa ba sannan shi kuma ya lakabawa Muneeba. 143 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Maganar ma ya fadawa wani wannan laifi da tayi masa ma duk bai taso ba don a ganinsa hakan tonon silili ne garesu gara kawai ya barwa cikinsa zai bari idan ya je Egypt a yi masa gwajin jinni don a tabbatar da lafiyarsa. Babban tashin hankalinsa na yadda dole itama Muneeba sai an yi mata gwajin don kuwa ya san itama ba za ta shallake siradin da ya afka ba tunda duk sun gauraye da juna sau ba adadi tun bayan Suwaiban ta ba boka kanta, ya daga hannuwansa biyu sama yana addu'a ya Allah ina rokonka in har za ka jarabeni da ciwo a rayuwa kada ka jarabci ni da wannan cuta da jama'a ke Kyamarta ake kyamar mai cutar ya Allah don alfarmar son da kakewa Annabinka ka kawo mana al'amura masu sauki a rayuwar mu ta duniya da lahira". Ya yi Salatin Manzon Rahama sannan ya shafa addu'ar ya cigaba da yin istigfari ga Allah. 144 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria A bangaren Suwaiba kuma tunda ta ga Mujeeb bai tunkare ta ko ya tuhumeta da hirarta da Larai kawarta da ya ba wadda jin hirar ne ya haddasa masa larurar da ta same shi sai ta ayyana a ranta lallai aikin da tace boka ya yi mata na rufe masa baki kada ya tada maganar shine ya yi tasiri a kansa tunda gashi ko a fuska bai muna mata ba illa dai abu daya da ke bata mamaki tunda ya warke ko sau daya bai taba nemanta ba, kuma tana binsa kwana dakinsa. Babban takaicinma har da kanta ta tallata masa kanta sai ya juya mata baya yace shifa ta kyale shi bashi da lafiya ta barshi ya sami isasshen lafiyar. Cikin daren nan ta tashi ta saka masa kuka tana surutai "In wani abu na yi maka ba sai ka gaya mini ba da zaka dinga zaluntata a kalla yanzu an sami shekara da wannan larurar taka haka nan na daure ina hakuri tunda ba dutse aka hallice ni ba, yanzu kuma ka warke garau amma ka ce min 145 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria 1 1 kai baka da isasshiyar lafiya alhalin matarka babu abin da bakwa yi tun ma kana jinya, sai ni ce da baka kauna za ka ce min baka da lafiya wallahi na gaji ba zan yarda ba hakuri na ya kai makura ya Kare. Ya tashi zaune yana mata kallon mamaki ya ce "Wani ne ya gaya miki abin da ke faruwa tsakaninmu da ita koko labe kike mana da har kika san ina mata abinda ke bana maki?. Allah ya kyauta in yi muku laбе gani na yi ita hankalinta a kwance kullum cikin annashuwa take ta yi kiba ta yi kyau abin ta ni kuwa ina cikin tashin hankali alhalin in duniya da gaskiya ita ya kama ta fini shiga damuwa ita da ta dade bata gidan miji. Mujeeb ya yi murmushi cike da al'ajabin kalaman Suwaiba ya ce, "Sa rai ga koshi ai shi yake kawo jin yunwa, ita bata sa ranta ga wannan abin ba shi ya sa bai dameta har ta kasa sukuni ba balle ta 146 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria shiga cikin garari kinga ke da ki ka kallagawa kanki ai gaki nan kin lalace kin hana kalanki sukuni har kina zargin da ita ake harka ke ba a yi da ke. To bári in gaya maki larurar da ta sameni ta yi sanadiyar tafiya da lafiyar kuzari na, in kinga za ki iya hakurin zama da ni a haka har in samu lafiya to in kuma kinga baki iyawa to hanya a bude take gare ki. Saboda haka ki barni in yi bacci in baki iya bacci tare dani to kama gabanki don bani da kuzarin da zan iya tsinana miki komai. Yana gama fadin haka ya ja bargo ya rufe jikinsa ya hau bacci ya kyaleta na zaune. A haka aka cigaba da zama a gidan kuma duka 6angarorin biyu baya iya hasala komai ba wai don bashi da lafiyar bane kamar yadda yace lafiyar tasa ba isasshiya bace sannan bangaren Suwaiba ba kyamarta ya ke ji ita kuma Muneeba tausayinta yake ji kila. ya kwaso cuta kada ya lakaba mata yanzu in har da can 147 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria bata dauka ba saboda haka dole sai ya tantance lafiyarsa shi da su. Shi da Muneeba ya ke ta yi musa shirye-shiryen tafiyarsu Egypt wanda ko ita Muneeban bata sani ba Passpot ma a Jakarta ya dauka bata sani ba har aka gama komai sannan ya gaya mata. Ta zauna daf da shi a doguwar kujerar falonsa sannan tace da gaske ka ke yi da ni za'ayi tafiyar ya gyada mata kai amma kana ganin ba za a sami matsala da Suwaiba ganin tunda ka aureta baka taba ko'ina da ita ba a gani na ita ya kamata ka tafi da ita sai barin Waleeda in yaye ta tunda na ga ta isa Yaye. Ya sauke numfashi "Bada ita na tsara tafiya taba saboda haka kadama ki sake cewa in je da ita, in ba zaki min rakiyar bane sai in tafi ni kadai kila ma Allah ya tausaya min wata balarabiya ta like min in aureta a can kinga sai ta yi jinyata. 148 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Muneeba ta kankame shi tana kukan shagwaba da 'yan tsalle-tsallenta irin na yaran goye tace, Insha Allahu Allah ba zai tausaya maka ta wannan fannin ba kafata kafarka tunda na gano ba neman lafiya zaka ba neman aure za ka je gara in bika in kashe maka kasuwa. Shi ma dada matseta ya yi a jikinsa har sai da ya ji notinan jikinsan sun fara kwancewa sannan ya yi saurin sakinta don kada ta jika masa aiki shi kam mamakinta yake ji na yadda bata taba yi masa korafi irin na Suwaiba ba duk da dadewar da suka yi rabonsu da juna wanda akalla an kai kusan Shekara daya da rabi kuma tsaf ya lura tana cikin tsananin bukatarsa daurewa kawai take yi a dalilin kunya irin ta matan Hausa Fulani duk da duka bane suke da irin wannan kunyar sabanin irinsu Suwaiba wadda ta fito karara ta nuna masa maitarta a fili na gazawar hakurinta. 149 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Tunda maganar tafiyarsu Egypt din nan ya bayyana sai Suwaiba ta hau adawa da al'amarin ta fito karara ta nuna bijirewarta wai ita sam bata yarda da wannan rashin adalcinda ake nuna mata ba dole sai dai ayi tafiyar da ita. Rigima sosai suka yi da shi har sai da ta kaisu gaban Goggo. Goggo ta hau sulhu a tsakanin su, "Kai meye dalilinka da ba zaka je da ita ba? Ya karkata yana duban Goggo kina sane jinya zan je in yi a kasar nan, ko dole ne in tafi da wadda ta san muhimanci na a gareta kina kallo jinyar da na yi ta kusan shekara daya yarinyar nan bata damu da kula da al'amurana ba dai fi kula da in an yi min abu ta tada kayar baya tayi haukan kishi akan abun shi yasa ni kuma zan tafi da wadda zata kula dani. Goggo ta jinjina kai, "wannan kuma kana da gaskiya, tunda ni ganau ce ba jiyau ba, kuma na yi ta fama da ita tun a wancan lokacin tayi kokari tana kulawa da kai 150 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria kamar yadda abokiyar zamanta ke yi amma tayi biris da batuna yanzu ai ga shinan wa gari ya waya ni ba zan hana shi ba tunda laifin kine in kinga zaki gyara don gaba to sai ki gyara'. Suwaiba ta zumburi baki ta ce "Ai dama na san bayansu za ki goya tunda su 'ya'yanki ne kuma wallahi ban yafe ba hakki na ake tauye min". Ta mike Fauu! Zata fita Mujeeb ya damkota a fusace yace "Uban wa kike cewa baki yafe ba ko akwai sa'anki ne a nan? Banza mara kunya mara tunani fice ki ba mutane guri sakarya" Ya hankadata har sai da ta kusa faduwa Goggo ta haushi fa fada Mujeeb meye haka kada ka ji mata ciwo mana su mata in suna shirmen su ai ba a biye musu tunda in mutum yace zai biye musu sai ya zama irin su hakuri ake yi da sha'aninsu. 151 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Tun daga ranar ya fita sabgar Suwaiba ya maida hankali kan shiryeshiryen tafiyarsu. Ranar Juma'a ana saukowa Masallaci yayi sallama ya shigo gidan rike da hularsa a hannu, Jume ne ke biye dashi da wasu kaya a bayansa saukowarsu kenan daga Sallar Juma'a Jumen ne yake tukashi yanzu tunda ya warke ciwo. A dakinsa suka iske Muneeba tana 'yan goge-goge tana ganin shigowarsu ta aje abinda take yi ta nufo shi tana masa sannu da dawowa ta kai hannu ta amshi hular hannusa. Jume ya gaisheta ya aje ledojin da ya shigo da su ya fita ta yi saurin dauko ruwa me sanyi a Firij ta tsiyaya a kofi sannan ta isa ta kafa masa a bakinsa ya shanye duka yana dubanta yace. Wallahi Muneeba kina sangarta ni a hakan ne zan iya tafiya wani guri na tsawon lokaci in barki? Kawai so kika yi ki kwareni Allah ya taimake ni Goggo bata 152 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria bada goyon bayan in tafi da wata ba in bake ba itama tana son in ririta mata danta. Ta murmusa "Ai dama abin da kake so kenan a riritaka a dinga shagwaba ka ga abincinka can bisa tebur ko nan zan kawo maka don na ganka ne a gajiye Tubus". Ya ce "wallahi a gajiyan nake kafin mu je masallaci Anguwan muka je daga can na wuce gurin amsa bizarmu tafiyar Insha Allah gata litini da yamma kinga gobe sai ki je Dukku ki yi musu sallama don jibi bana son ki fita ko ina sai mu yi shirin kayanmu ko ya kika gani?. Ta fadada fara'arta yadda kace haka za'a yi Allah ya nuna mana ranar" Ta dauko kayan abincin ta aje masa bisa kafet din tsakiyar dakin ta zuba masa sannan ya sauko ya soma ci. Ya dubi Ledojin da Jume ya aje ya ce. Baki duba ledojin can ba akwai 153 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria danyen kifi an gyara ki fita da shi kada ya bata min daki kiyi mana farfesu sai kaji suma an gyara kiyi mana dambun naman da za mu yi guzuri daya ledar kuma kayan kwalama ne tunda ke da 'yar (Waleeda yake nufi) baku san komai ba sai kwadayin cin kayan zaki. Ta bishi tana masa godiya ai kuwa mun gode ni da 'ya ta bari in kai wannan kicin ai ban san kayan karni bane muka barshi a daki". Yace Shaf na manta kin san fa ni idan ina kallonki komai mantawa nake wai ina Waleedar ne na ji gidan shiru? Ta ce, "Ta gama kiriniyarta da na lura bacci take ji shine na kaita aka bata nono ta yi bacci tun dazun". Ya ce wai ba zaki je ki dawo da Karime bane? Ta ce, 'Mun yi waya da mamanta rannan mun tsaida matsaya cewa zata dawo amma sai mun dawo daga tafiyar nan don na tambayi Suwaiba maganar dawowarta ta ce bata da bukatarta za'a kawo mata wata daga 154 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Dukku kaga dawowarta yanzun baida amfani tunda ni kawai za ta yi wa Aiki. Ya kada kai, Shike nan gara a barta sai mun dawo din, yarinyar na da hankali gata da aiki ta ce, "ga son yara ga iya dawainiya dasu, yace Insha Allahu nan da dan kankanin lokaci za ta yi dawainiya da naki dan ko 'yar". Ta yi shiru, yace banji kince amen, ni fa bana san wannan fillancin kawai duk inda kika ji an yi mana wannan addu'ar ki amsa da amen kika sani ko ki amsa a bakin Mala'iku. Murmushi kawai ta yi ta suri ledar kajin nan ta fice a dakin tana jinsu yana mata korafin ta yi ta dawo ta yi masa tausa domin bacci zai yi. Washe gari suna ta shirye shirye tafiya Dukku don tare da Mujeeb din za su tafi shi ne ta ce mana "Su Waleeda ba za su Dukkun bane? Ya tabe baki Ai gaki ga su nan idan za su je wa zai hana su" 155 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Muneeba ta shiga dakin Suwaiba ta sameta a falon ta tana kallon film a Tibi ta ce "Yaya Mujeeb yace, ki shirya za mu je Dukku gaba dayanmu". Ta yi shiru tamkar ba zata yi magana ba, sannan dai ta dubi Muneeba a wulakance ta се "Duk zuwan da nake yi ai ba wani ke sa ni ba nake saka ranar da zan tafi ki gaya masa ba zani ba in kuma za a yi mani dole ne to nada ganmo ki daukar masa ni aka" Muneeba ta cika da mamaki "Yi hakuri babu zancen dole a wannan tafiyar Allah ya huci zuciyarki sai mun dawo ta ja dogon tsaki "Aikin Banza kawai, kinibabbar mata da can ke kike kaini garin namu idan idan zan je wato ga 'yar rakiyar raka ku yi wa dangi sallama lallai sai na yi maganin matar nan shiga hancinta yayi yawa". Muneeba ba ta iya gaya masa bakar maganar da Suwaiba ta fada ba illa ta се masa Suwaiban ta ce bata jin dadi su gaida mutanen Dukkun. Murmushi kawai 156 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria yayi ya kaďa kai don ya san kwanan zancen ya karanto hakan ne a fuskar Muneeban duk da kokari da ya lura take yi na saisaita yanayinta. Babu inda ba su je ba a gidajenmu 'yan uwa har gidan Diddi sun je tana ta yi wa Mujeeb tsiyar wai sai dai ya tafi da ita ya bar Muneeba in kuwa ba haka ba zata sake shi don zai tafi mata wata Kasa da igigoyin aurenta akayi ta barkwanci ana raha. Da za su tafi ta yi ta musu fatan alheri na Allah ya kaisu lafiya ya dawo da su lafiya yasa ayi nasara akan abinda ake nema. Sun je gidan Adda zuwa a gidan Adda Fadima ne Muneeba tafi sakewa saboda yadda suke dasawa anan ma taci abincin rana a kwano daya ita da mijinta Adda tana ta yi musu tsiyar wannan soyayya tasu da basa jin kunyar nunawa a gabanta don sun maida ta abokiyar wasansu. 157 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Nan suka Sallaci azahar sannan suka wuce gidan Goggo Hinde. Itama ta dinga ina taka saka ina ta ka aje da su ta cika gabansu da cima iri iri dolensu suka ci don in ba haka ba sai sun sha fadanta akan ta basu abu basu ci ba. Ba su suka baro Dukku ba sai yamma Likis haka suka shigo gida a gajiye tubus Muneeba wanka da Salloli kawai ta iya yi don ko abinci ba ta nema ba kasancewar cikinta a cike ya ke ta ta zo ta yi kwance dai dai a tsakiyar falonta tana shan iskar A.C. tana kallon tauraron dan Adam sanin ranar ba ita ke da miji ba balle ta je ta mammatsa masa jikinsa kuma ta san kwarai abin da yake bukata kenan a lokacin saboda irin gajiyar da suka kwaso a Dukku wajen yawon zaga dangi. Mujeeb ya dade kwance cikin gajiya yana ta juyi ga wata uwar yunwa da ke kwakular cikinsa amma shiru ba Suwaiba babu dalilin ta duk da yana tsananin kyamar cin girkinta a dalilin abin da ya ji 158 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ta taba bashi ya ci bai sani ba, amma ko dai fura ce ai idan ta bashi zai iya sha. Ya yi ta kiran layinta da kyar ta daga ya ce, "Wai baki san mun dawo ba ne da ba ząki iya zuwa yi min sannu da dawowa ba". Ta yatsina fuska tamkar yana ganinta ta ce "Au kun dawo? Ai ban sani ba ko da yake ko na san kun dawo me zanyi maka tunda baka cin abinci na ba ka hada jiki da ni ban san dalili ba ai gara nima inyi nesa da kai tunda kusancinmu zai iya sa ni in sa rai ga abin da ba zan samu ba. Na yafe ka nemo matar so ta ciyar da kai babu matsala kaga gobe sai ku dora daga inda kuka tsaya yau tana gama fadin haka ta kashe wayarta ya yi shiru a kwance yana nazarin maganganunta, daga bisani ya latso wayar Muneeba tana daga kwance ta amsa kiran nasa "Matar so ki taso ki zo 159 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ki bani abinci kafin yunwa ta yimin lahani. Ta ce "Don girman Allah kada ka Kara kirana da wannan sunan don yin hakan zai haifar maka da husuma a cikin gida ko ni ai bana kiranka da abokin rayuwa sai in muna mu biyu",. Ni ma ba ni na sa miki sunan ba yanzu na kira kanwarki ta bani abinci shine ta ce ba zata zo ba ta yafe maki ni inje matar so ta bani, wai an yafe ni kamar wani kaya'. Ta ce, to In kinshinta yasa ta ce haka kai kuma sai ka biye mata? Don Allah tashi ka je ka lallaso ta ka san mace idan ta butsare sai da lallashi. Ya ja tsaki "Au kin goyi bayanta kenan? Yanzu tsakani da Allah yadda na kwaso gajiyar nan ai inso samu ne a cika ruwa mai zafi a Baf a sakani a gargasa mini jiki na sannan ayi min wanka idan na fito kuma a shafe ni da man zafi a bani abinci da dumi inci sannan a kwantar dani 160 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ana min matsar jiki har in yi bacci amma an barni nan bisa kafet ina, ta juyi cikin yunwa da tsamin jiki tamkar mara galihu" To ni yanzu ya kakel so inyils Yı ua dai ka san ba duty/nasbaneoindanawæ nemmok duk wadannan abubuwadakaslissafduk dare su nake maka ko kosookakesin stigaas hurumin da banawasbal Ydrjesajiyar r 1sd ki tausayamin ki zo ki baniabindazancimsb wallahi ita ta ce ta yafe miki ke ki żo kiaret ba ni. Yanzu kai ba ka san gatse ba In ma gatse ta yi ni ina ruwa na zan zauna da yunwa ne alhalin duk kuna gidan. Kinga don Allah damo min furar da muka zo da ita ki dan gaso min irin gashin naman nan mai romo romo da kike min" Та се "Hum ai bakinka ne romoromon ya yi dariya 'ke ma ai bakinki da romo-romon". Ta katse wayar tunda ta lura ya koma fagen zolaya. 161 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Dolente ta ta shiga kicin Allah yasa firizarta a kashe ta ke hakan yasa bata sha wahala ba wajen ciro nama ta yanka shi yadda take yi ta sa a farantin gashi tare da su magi albasa da kayan ya ji ta gama hada komai sannan ta soma gasawaub se Ta koma ta dauko furar ta dama masa da wadataocen Yougurt mai sanyi har dayar ayaba kadan ta saka a wajen damun furar ta juye a Jug ta dora a faranti tare da kofi ta jira har sai da naman ya gasu sannan ta dibar masa nasa ta zuba sauran a wani filet din don ta kaiwa Goggo. Tana kai masa yayi saurin tashi daga kwancen da yake yana cewa sannu matar so Allah ya yi miki albarka ya kara min sonki a zuciyata" Ta dan Harare shi ta ce "Yanzu don girman Allah

Chapter 6 of 8