Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 8
ba za ka daina ba? Ya ce ya za ayi in daina ni ma ai irin naki zan yi sai muna mu biyu zan dinga gaya miki sunan. In kuma kika dame ni in dinga fadan gaban kowa. 162 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Ta juya zata fita ta na masa sai da safe yayi magana cikin tsokana 'Ba zaki tsaya in gama ki gasa min jikin bane ita fa tace ta yafe maki har da kwanan". "In baka sam gatse ba aini na sani yunwa dai ba zan iya barinka da ita ba amma ma gasa jiki ka yi abinka ka kwanta tunda ka iya, saida safe". Kafin yayi magana har ta fice ta bar masa falon ya ja namansa da fura ya ci ya sha yayi hani'an sannan ya je ya yi wanka yayi kwanciyarsa. 163 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria **** **** ****** Sun isa kasar Egypt lami lafiya, sun sauka a masaukin da abokin maigidan mujeeb wato Alh. Ayuba ya tanadar musu wani hotel. Washe Gari shi mutumin ne da kansa ya zo ya dauki Mujeeb a masukinsu ya kaishi asibitin da zai ga likita. Duk ya gayawa likita matsalar dake damunsa, yadda hannun sa ke masa zugi da nauyin da yake masa sannan matsalar ta rashin samun kuzari a matsayinsa na da namiji. Sai dai ba ko da yaushe bane yake jin rashin kuzari ke dawo masa lokaci zuwa lokaci. Ya kara da cewa, "yadda abin ke mai in har zan dade jikina bai rabi jikin mace ba to babu yadda za'a yi inji sha'awar komai sannan ko jikin namu ya hadu ba lallai bane inji wata יי sha'awa sai dai in abin ya zo min" Tunb daga ranar likita ya dora shi akan shan magani, hannunsa kuma aka 164 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria saka shi cikin wata na'ura aka gyara masa kashin sa da bai daidaitu ba, sannan suka bashi ranakun da zai dinga zuwa ana masa gashin hannun. Yabawa da asibitin yasa Mijeeb suna kwance a wani dare yake shawartar Muneeba akan matsalarta. "Muneeba ina ganin ya kamata gobe muje asibitin nan da ke, mu kai musu kukan matsalarki ko Allah zai sa a dace". Ta yi dan jim sannan tace, Ni kam na hakura da zuwa duk wani asibiti in dai akan matsalar haihuwa ce tun da babu irin maganin da ba mu yi ba na asibitin da na gargajiya, ina ganin gara mu hakura kada muyi ta ma Allah shishshigi akan abin da ya tsara kila bani da rabon haihuwa ne a duniya." Nan da nan hawaye ya ciko a idanunta. Mujeeb ya lura da hakan, sai ya jata jikinsa ya rungume yana lallashinta, ki yi hakuri mu je goben ai ba a san inda za a dace ba tunda shi magani gwadawa 165 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ne inda ma sunan shi ya samo asali kenan inji bahaushe wai bari ma gwada ma gani, kuma Atlah shi ya saukar da larura kuma yace a nema ni magani don babu cutar da bata da magani sai mutuwa da tsufa. Da wannan shawarar suka kwanta ba amma ita a ganinta da ya kyale ta kada ya yi asarar kudinsa tunda ko a asibiti sunce bata da matsalar komai lokaci kawai zasu jira, to me zai sa su wahalar da kansu da ba za su jira lokaci da Allah ya tanadar mata ba. Shi ba gashi nan ba da na sa lokaci ya yi Allah ya kaddare shi da kara aure kuma har ya sami haihuwar. Washe gari da wuri suka shirya suka tafi asibitin, ita bangaren likitar mata aka kaita, wadda likitar ma mace ce 'yar kasar Pakistan kuma musulma ce, shi yasa Muneeba ta saki jiki ta dunga zayyane mata matsalolinta. 166 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Anyi mata duk wasu gwaje-gwaje masu matukar muhimmanci, sannan aka ce su dawo gobe. Shi ma Mujeeb din an yi masa nasa gwaje-gwaje tunda sai da suka nemi ganin mijinta, amma ta shaida musu shi ba ya da matsala yana haihuwa itace mai matsala. Likitar ta kwantar mata da hankali cewa ta yiwu ita ma bata da wata matsala kila jinkiri ne kawai daga Allah lokaci na yi zata ganta dauke da ciki, har ta bata shawarar ta je ta ci gaba da addu'a don addu'a na maganin matsalolin rayuwa, bawai sai magani ba. A washe gari da suka koma sakamakon gwajin da aka yi wa Muneeba ya nuna bata da matsalar rashin haihuwa, komai nata lafiya yake, amma zasu dora ta akan shan magunguna saboda su karawa kwayoyin haihuwarta karfi ta yadda zasu kyankyasar da 167 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria halittar mutum ba tare da ana yin asararsu ba a yayin saduwar aure. Kuma sun bata shawarar ta yawaita Mu'amularta da Mijinta a yayin da take shan magani, zai iya yiwuwa ta sami ciki amma fa idan Allah ya kaddara. A masaukinsu zama tayi tana ta tunanin hanyar da zata sanar da Mujeeb abin da likitarta ta bata shawara na yawan mu'amular aure yayin shan maganinta, gashi ya sami rauni ta wannan bangaren yanzu yaya kenan. Ashe faduwa ce tazo daidai da zama shi kuma nasa magunguna masu karfi ne, ta yadda har sun fara tasiri a jikinsa dama likitan ya gaya masa da zarar sun fara aiki to zai dawo daidai dinsa koma yafi da samun karfi da kuzari. A wannan daren ya ga tabbacin abin da likitansa yace, don ya kasa sarrafa kansa har sai da ya tabbatarwa da matarsa hakan sakamakon kyakkyawar mu'amular da suka gudanar a tsawon daren ranar. 168 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Har. sai da ya dinga bata hakuri ganin lafiyar da ya samu har tana barazanar yi masa yawa, koda yake hausawa sunce komai yana ginsar mutum amma banda lafiya. Amma fa kafin wannan ranar sai da yasa likita a boye ba tare da sanin Muneeba ba yayi masa gwajin (H.I.V) sabo da zuciyarsa ta kasa natsuwa da nagartar lafiyarsa. Bai sami natsuwa ba har sai da aka tabbatar masa lafiyarsa kalau Jininsa baya dauke da ko wace irin cuta sannan ne fa hankalinsa ya kwanta kuma Ya tabbatar ma Muneeba cewa lafiyarta kalau,' Suwaiba ce kawai yake Kokwan to akan tata lafiyar kila a tsawon shekara gudan da yayi yana jin ya ta sake zuwa ta aikata wata masha'ar tunda bokaye sune abokan mu'amularta su kuma basu da aiki sai na fasikanci da duk wata la'ananniyar da ta kai kanta gurinsu da 169 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria sunan neman biyan bukata, za su yi miki aiki sannan za su miki aika-aika. Wata guda su Muneeba suka kwashe a birninm Egypt, sun yi kyau har sun gaji don idan ka gansu zaka dauka sababbin amare ne da suka zo yawon amarci saboda yanayin da suka tsinci kansu na shauki soyayyar junan su, kansu ji suke yi tamkar yanzu ne suka yi aure saboda nishadi da suke ciki koda yaushe. In ba asibiti za su je ba to basa fita ko'ina suna nan gida manne da juna, sai gab da zasu dawo ne ma suke fita shaguna don sayen kayayyakin da za su yi tsaraba. Ranar laraba da daddare suka sauka gida Nigeria sun tarar da kowa lafiya, sai dan abin da ba za'a rasa ba na matsalolin cikin gidan Mujeeb na irin rashin kunyar da Suwaiba kewa Goggo, don ma isa na tsakanin zaman nasu kila da wata rana sai ta mari Goggo. Θ 170 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Σ 3 १ Tsananin gajiya yasa Muneeba ko ina na jikinta ciwo yake mata har ta kasa tabuka komai a washe gari sai aikin bacci. Mujeeb ya shigo fakinta shima sanye yake cikin riga da wando masu tsananin taushi na bacci, ya same ta tayi dai dai a tsakiyar gadonta tana bacci ga sanyin A.C da ya ratsa dakin. Ya kalli agogon dake aje gefen gadonta yaga sha Biyu da kwata na safe, a tunanin sa ma ko karyawa bata yi ba. Ya zauna a gefen gadon ya soma bubbugata a hankali, ta bude idanunta da suka yi jawur ta dube shi sannan tayi kokari ta tashi zaune tana cewa," Wallahi ko ina a jikina ciwo yake yi, har yanzu a gajiya ta ki saki na yadda kasan an yi mini dukan tsiya haka nake jin jikina ya yi min nauyi. Yace,"Ai kwanciyar ba za ta magance miki wannan gajiyar ba, ki daure ki tashi ki yi wanka da ruwa mai 171 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria zafi, ki ci abinci don na san baki karya ba zaki ji dama-dama." Ta yi mika tare da yin salati, sannan ta sauko ta wuce bayi tayi wanka da ruwa mai zafi sannan ta fito ta same shi a zaune inda ta barshi. Ya dube ta yace," Me zaki yi mana mu karya da shi nima fa har yanzu ban karya ba." Baka karya ba? Ina Suwaiban?" yace, "Na tambayeta tace bata yi dani ba, sun cinye abunsu." Muneeba ta tsura masa ido sannan tace "Wai don Allah laifin me kake yi wa matar nan take butsare maka, ya kamata ka gyara" Ya murmusa, "To yaya muneeba za'a gyara insha Allahu." Tayi Dariya "au abin ma na zolaya ne? babu batun zolaya, ni wane laifi kike ganin zanyi mata? Kin fa san halin yarinyar nan ba sai anyi mata laifi ba take wulakancin ta ba. ke laifin ki ke mata take miki abin da take miki? Don Allah ni zura riga kawai ki shiga kicin ki 172 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria sama min abinda zanci, cikina ya riga ya horu da cin abu mai dadi bana son Jagwalgwalo, garama ta daina bani zan fi son haka" Muneeba tace, ka gani ko ai daman a san da taka matsalar wallahi gara ka gyara don nima na kusa daina baka abincin ranar girkin ta". Ya yi dariya," Haba yarinya ai baki isa ba da kinga yadda ake kuka da birgima a dakin nan har sai kin bani". Ta dauko doguwar riga mai gyale ta saka ta murza 'yar hoda, ta yafa gyalen sannan ta dube shi, "Don Allah ka koma falonka idan na gama zan kawo maka". Ya kura mata idanu, "wai kinga farin da kika kara kuwa? Kin kara wani irin kyau jikinki ya yi lukui-lukui tamkar bayan tarwada, gaskiya kasar Egypt ta amshe ki, kina kuwa kallon madubi? Ta girgiza kai, "Bana kalla, ni dai tashi ka tafi zan kawo maka". Yace, "Au korata dai ki ke yi to bari in tafi, idan baki yi sauri ba zan 173 لم WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria dawo" hakika ita kanta Muneeba ta ji sauye-sauye a jikinta, kasancewar bata jin ciwon komai sai ta alakanta yanayin sauyin jikin nata da gajiyar tafiyar da suka yi, amma tana kokwanto akan hakan a dalilin yau kwana goma kenan da bata ga al'adar ta ba, sai dai ta kasa gasgata abin da zuciyarta ke saka mata. Ta dauko wayarta ta kira lambar wata kawarta nos ce da ke aiki a asibiti sister Hadiza tace," sister kina gida ne ko asibiti ina son ganinki" tace, "Gani nan yanzu zan fita zuwa asibiti lafiya ko?" Tace, "lafiya kalau so nake kiyi mini gwajin fitsari". Tana jin saukar ajiyar zuciyar Hadiza sannan tace, "Gani nan biyowa gida in yi miki Allah yasa muga alheri kai na yi murna." Tace, "Ni fa ban tabbatar bane ina dai zato ne." Tace, "Ai wannan kyakkyawan zato ne, gani nan zuwa yanzu-yanzu". Mintuna kalilan suka kawo sister Hadiza gidan, gwajin farko na fitsarin ya 174 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria nuna ciki, Muneeba tace ita fa bata yarda ba, ta sake yi mata wani shima dai ya nuna akwai ciki. Murna ta baibaye sister Hadiza ta dube ta tana rike da abin gwajin tace, " wallahi shima wannan cikin ya nuna, meye naki na kokwanto to abu ya nuna kansa baro-baro abu ne fa ake nema ido rufe sai gashi Allah ya kawo, ba sai mu godewa Allah ba mu addu'ar Allah ya raba ku lafiya”. Muneeba hannuwa biyyu ta daga sama tana yi wa Allah godiya. Hadiza ta dubeta tace, "Gaskiya wannan albishir din ni zan yi wa mai gidan ko a bani babban goro mai tsoka". Muneeba tace, "ki yi hakuri Hadiza ba yanzu za'a gaya masa ba kin dai san komai dangane da zaman gidan nan, bana son a san ina da cikin nan, don idan aka san ina dashi tun bai kwari ba komai zai iya faruwa, shi kuma yanzu idan aka gaya masa na san ba zai iya yin shiru ba saboda murna kowa sai ya ji." 175 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Hadiza tace, "Gaskiya kuma da wannan don wannan wai an tura tsohon banza biko". Yanzu gaya min irin matsalolin da kike fuskanta a jikinki don insan irin magungunan da zan kawo miki" Muneeba ta yi mata bayani nauyin jiki da kasala sai yawan bacci, sai yawan cin abinci sau ba adadi, in ta ji yunwa ma bata ci sai ta fara ganin dusu-dusu jiri na dibarta, amma sam bata wani ciwo in banda wadannan. Hadiza ta hado mata magunguna da zata dinga sha wadanda zasu rage mata nauyin jiki da kasala, amma cin abinci wannan ya zama dole saboda dan dake cikinta ya sami koshin lafiya. Cikin har ya shiga watanni biyu da 'yan kwanaki Mujeeb bai sani ba, sai dai yana yawan mata korafi akan yawan baccin da take yi wanda sam bata gajiya, da yawan cin abincita gashi nan ta yi kiba ta yi wani irin fari mai ban sha'awa. 176 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Abin fa ya soma ba Mujeeb mamaki, rannan suna hira miyau ya dinga cika mata baki yana shaketa. Ta je ta zubar ta dawo ya dubeta yace, "ke ni fa bangane wannan miyan ba shin wata cuta ce ta same ki ta zubar da miyau ban sani ba?" Tace, "To nima dai haka na tsinci kaina kila ciwon ne". Ya suri. makullin motarsa yace, "Tashi mu je mu ga likita, wannan ai babbar cuta ce a ce mutum ya kasa (controlling) miyau a bakinsa" Asibiti suka nufa yai wa likita bayanin matsalarta, likitan ya kara yi mata wasu tambayoyi daga bisani ya bata wata kwalba yace ta shiga bayi ta yi fitsari ta kawo masa. Yana gwada fitsarinta ya dubi Mujeeb yace, "Ina taya ka murna madam na da shigar ciki wata biyu". Wasu hawaye ne masu sanyi suka ziraro daga idanun Mujeeb, ya mike yana Hamdala ga Allah sannan yace, "Likita da gaske 177 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ka tabbatar cikin ne don kada in sa rai ga abinda ba zan samu ba? "Likita ya yi murmushi yace, "Tabbas abin da gwajin fitsarinta ya nuna min kenan, amma idan kana tababa bari in yi mata (scarning) sai kaga zahiri”. Tare suka shiga dakin yin hoton, su uku, likita ya yi mata hoton ya ga tabbacin cikin sannan ya nuna masa shi ma ya gani. Tun a dakin a gaban likita Mujeeb ya rungume Muneeba yana murna tare da godiya ga Allah. Tun a asibitin ya kira wayar Goggo ya shaida mata, ya kira mutanen Dukku ya dinga shaida musu kowa aka gaya masa sai yayi murnar wannan abin farin cikin. A mota take shaida masa gwajin sister Hadiza ta yi mata har ya nuna tana da ciki. Ya dubeta ta baki bude yace, "shine tun a lokacin baki gaya mini ba? Oh, dama kin riga kin sani shine kika boye mini? To me hakan ke nufi kenan? 178 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Ta raunana murya saboda ganin ya ji zafin rashin gaya masa din tace, "yi hakuri ka maida wukar, wallahi ni ina ta kokwanto ne sai ina ganin kamar ba gaske bane shi yasa na yi gum da baki na, amma kayi hakuri tunda ya tabbata yanzu a yafe min". Ya murmusa tare da shafo cikin nata yace, “Ai ni yanzu babu wani laifin da za ki yi min in ji zafinsa saboda wannan abin farin cikin da kika dasa mini a zuciya wace irin kyauta kike so in baki a duniyar nan, gaya min ko me ye indai bai fi karfi na ba zan baki". Ta ruko hannunsa da har yanzu yake bisa ruwan cikinta tana shafar hannu nasa tace, "Babban abin da nake so yanzu a gurinka shine addu'arka gare ni Allah ya bamu lafiya ni da abin ke ciki na, ya sauke ni Lafiya idan ka dinga yi mini komai a duniya". Yace " wannan ya zama dole a gare ni, dama addu'a kullum ina yi miki 179 1 1 1 1 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria a duk salloli naki fadi wani abun". Tace, ni kam babu wani abu da nake so tunda duk wani abu da mace ke so a gurin miji na ji dadin rayuwa babu wanda ban samu ba sai soyayya da kulawa duka na samu, to me kuma zan nema sai dai godiya Ga Allah kawai". Yace, "zan ci gaba da nuna miki so da kulawa zanyi miki gata zan sangarta ki zan ririta ki, ke da abun da zaki Haifa tamkar kwai a kan fa" Haka ya yi ta gaya mata kalamai dadadan zuciya har suka iso gida, A harabar tsakar gidan suka iske Goggo ta tare su da murna tana tambayan su, "Mujeeb da gaske ne abun da ka gayamun Muneeba na da ciki? Ya ce wallahi Goggo da gaske ne nama ga Hoton da akai mata a asibiti cikin watansa Biyu da kwanaki. Ya dauko hoton Scarning din daga aljihunsa ya mika ma Goggo ta amsa tana cewa to ni me zan gane a hoton ba boko na iya ba, Allah mun gode maka kaine abin godiya ta 180 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria juya ga Muneeba, sannu kinji Muneeba Allah ya raba ku lafiya sai ki dage da cin abinci ki kula sosai da lafiyarki". Ita dai Muneeba sunkuyar da kai tayi saboda kunya bata iya cewa komai ba. Suna shiga daki Muneeba alwala ta yi nafila ta yi godiya ga Allah da ya bata wannan kyauta na ciki sannan tai addu'ar Allah ya raba su lafiya”. Shi ma Mujeeb a nasa dakin Sallan nafila ya yi don nuna Godiyarsa ga Allah da ya bashi wannan kyauta da ya dade shekara da shekaru yake nema sai yanzu da suka fid da tsammani sai gashi Allah ya basu. Suwaiba tunda Goggo ta gaya mata maganar cikin Muneeba ta shige daki, saboda wani kugin firgici da cikinta ya dauka, har sai da ta zaga bayi saboda rudewa da ta yi. Ta dauko wayanta na kuka w'iiw'ii ta kira Hajiyarta ta shaida mata abun bakin cikin da ya same ta. 181 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Haj. Harira ta dunga nanatawa, "Muneeban da ciki? Ciki dai ciki dai anya kinji da kyau ita din aka ce? Cikin rashin kuka, tace ita din fa akace Goggo take gaya mun, a lokacin suna asibiti ya kira Goggo yake shaida mata, yanzu haka gasu can sun dawo sai murna Goggo take yi tamkar ba'a taba haifar mata jika ba". Haj. Harira ta kurma ashar, kan Ubancen Rahin din ce ke murna dan Muneeba na da ciki lallai dole gobe ki zo muje mu ga boka dole a zubar mana da cikin nan dan ba zai yiwu ba ta haihu a gidan nan dan a gidan nan da 'ya daya tilo har yau shiru ba wani bayani". Suwaiba ta ja tsaki, "Ai yau zamu yi ta da shi a gidan nan, ni fa zaune kawai nake a hoto ce min yayi bashi da lafiya, tun kwanciyar jinyarsa na ke zaune haka har ya warke sukai tafiya suka dawo, yanzu zai gaya mun in a ruwa Muneeba ta sha cikin ko kuma a yi wacce za a yi”. 3 오 182 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaría Haj. Ta yi saurin kwabarta. "Akul kikai masa tijaran da zai sake ki, ki bi komai a hankali, in kika tada kayar baya ya sake ki ay ba muci riba, ki barni da su kowa sai ya kwashi kashinsa a hannu". A daren ranar ta same shi a falonsa, yana zaune da remot a hannu yana lallatsa tashoshi yana ganin ta ya san ba lafiya tunda ya san ba Girkin ta bane koda yake ita babu ruwanta duk lokacin da take da bukatan kanta zata shigo dakinsa kuma sai ta ga dama take sallama. Ta zo.kansa ta tsaya kerere ta tsaya ya na dubanta yace "Ke! Lafiyarki kalau za ki zo kaina ki tsaya min kerere ko ladabi tamkar sa'ar ki ko wani kanin ki? Ta yi ya tsine, "magana nake san yi da kai ba zama na zo yi ba. Ay nima bace wa na yi ki zauna ba, ki matsa daga gefe sai ki mun magana amma ba zai yiwu ki tsaya mun akai ba". 183 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Ta ja gefe tana 'yan girgije girgijen kafada ta soma magana dama zuwa na yi in san matsayi na tunda ance mun Muneeba nada ciki alhali kace baka da lafiya kila a ruwa tasha, in kuma ba a ruwa ta sha ba kenan ni ake zalinta an danne mun hakkina idan nai magana ka ce bani da hakuri ni wannan ya dama ai gashi ita da be dama ba har ta yi ciki saboda haka ba zan yarda ba dole ka bani Hakkina kamar yarda kake bata ni ma ai matarka ce. "ya yi dan murmushi sai daga can jira nake Allah ya kawo irin wannan rana to bari ki ji in gaya miki abin da kika san na sani shiru kawai na yi miki, bara nayi miki matashiya. Ranar da na fadi a dakinki dawowa na yi in dauki wasu takardu a dakinki da na ajiye shine na tsinkayi maganar da kike yi da kawarki tun farkon hiran takì inajin irin naman da kikasa a gabanki wanda har kikai mun miya da shi alhanin kun yi 1 3 184 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria fasikancin ku da boka kin hada janabarsa da tawa. Abin da kika nema lokacin kin samu tunda kin mallakeni iya yanda kike so, kinsa na wulakanta matata ina ci mata zarafi har sai da na koreta a gidan. Kin dauki alhakin mu ni da ita, dan rashin kunya ni ban yi miki Allah ya isa ba kullum za ki dubi tsaban idona ki ce wai baki yafemin ba danne miki hakkin ki da na ke yi ba. Bari kiji in gaya miki ni ba zan kara yarda na hada jikina da naki ba saboda tsananin kyamarki da nake yi ga tunani (H.I.V) dan ban aminta da lafiyarki ba, ban sani ba ko bayan kwanciya na rashin lafiya kin koma ki na aikata masha'arki ba, ni ko a Egypt na sa an auna jinina an tabbatar banda cutan komai an tabbatar lafiyarki kalau kila in cigaba da zama dake amma ba tabbas dan Al'amarin yana bani tsoro, saboda haka gobe ki shirya mu je asibiti dan bokayen WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria nan da kuke zuwa kuke basu kanku duk suna dauke da cutan kanjamau. Ni kam na gode ma Allah da be Kaddara kin lika mun ba in ma kin je kin kwaso. Saboda haka dole gobe mu je asibiti ki san matsayinki. Kuka ka shirban Suwaiba take yi tunda ta ji ya ambaci cutan H.I.V dan bata san tana jin tsoron cutar ba sai da ya bata matashiya. Duk wata tsiwa da ta dauko damaran kwance masa sai gashi ta tattara abinta ta wuce sumui sumui tana kuka. Muneeba dake dakin baccin sa tana jin su, daskarewa ta yi a kwance cikin dakin dan ita kanta Suwaiba ba ta san Muneeba na dakin ba dama ta zo yin tijara ne bata dauka za'a ai mata wannan bankada ba sai gashi allura ta tono garma. Mujeeb ya shiga ya sami Muneeba a gefen gadonsu ta zuba uban tagumi ya kai hannu ya sauke tagumin da tayi, yace meye abun tagumi? Na san duk kinji maganganun mu da suwaiba, wallahi ban Σ WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria yi niyyar in tona maganar nan wani ya ji ba, amma sai gashi yau ta kaini makura har kinji, sai godewa Allah kaikayin abin da ta yi miki ya koma kanta dama haka bokanta ya gayamata, wallahi irin kiyayarki da na dinga ji a lokacin irin ta yanzu. nake ji a kanta ke fiye ma da wadda na yi miki. Gobe zan kaita asibiti ayi mata gwaji, in Allah ya taimake ta bata jijjibowa kanta cuta ba to ta yi babbar sa'a, hakan kuma ba shi zai sa in ci gaba da zama da natsuwa da ita ba zan dinga jin zarginta a zuciyata". Muneeba tace, "indai ance bata da wata cuta gara ka hakura kaci gaba da zama da ita, tunda uwar 'ya'yan kace kuma akan san da take maka ta je ta aikata wannan danyen aikin". "sam wannan ba hujja bace, ke din Baki fita sona ba, amma me ya sa ke baki taba tunanin kwatanta wannan sabon ba sai ita da yake jahila ce". 187 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Tace, "To ai ka san kowa da irin nasa tunanin, ka yi hakuri ka mata afuwa ta yiwu yi mata afuwar ya sa ba za ta sake ba. Fita falo ya yi ya bar Muneeba tana ci gaba da nazarin wannan al'amari mai ban mamaki da daure kai. Washe gari babu yadda Mujeeb bai yi da suwaiba ta zo su je asibiti ba, amma fafur tace ba za ta je ba, ya kyale ta kawai, ita tsoron da take ji kada a auna jininta ace tana dauke da cutar kanjamau, shi yasa ta ga gara ta hakura taci gaba da zama haka agidan ko ba zai mata komai ba rufin asirinta kenan tunda ba zai kore ta ba. Ya dubeta yace, " in kuwa ba zaki ba to kada ki "kara cewa na danne miki hakkinki, don kuwa ba zan kusance ki a wannan matsayin kila wa kalan da kike ciki ba. Inma kina tsoron kada ace kina da cutarne, to na yi miki alkawarin ko da ance kina da shi wallahi ba zan gayawa kowa 188 스 2 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ba, zan kuma iya barinki ki cigaba da zama a gidan nan sai dai kin san babu wata mu'amular aure da zata gitta tsakaninmu”. Ta share kwallar dake malala a kuncinta tace, "Gara dai ka barni a cikin rashin sanin dana ke ciki, da in je inji abin da zai hana rayuwa ta kwanciyar hankali, ka barni kawai”. Dole haka ya tafi ya kyale ta, kenan ya sami maslaha ta wannan bangaren bata da damar da zata sake yi masa korafin ana danne hakkinta, tunda it ta zabi ta zauna haka don rufuwar asirinta, inma ta ga ba zata iya zama ba, shi kam a shirye yake da ya bata takardanta idan ta nemi hakan, sai ya amshi waleeda ya damkawa Muneeba don ba zai so ta rayu a hannun Suwaiba da Haj. Harira ba ko dan kada tarbiyyarta ta gurbace irin tasu. 189 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria 飲飲飲 **** ****** Cikin Muneeba yana ta bunkasa cikin lafiva da kanciyan hankali, harma ta fara zuwa awon saboda yanayin girman da cikın ya vi. Kowa a zuri'arsu fatan alheri da sauka lafiya ya ke yi mata tare da addu'ar Allah ya sauketa lafiya. A bangaren Mujeeb kuma tsananin kulawarsa yake nuna mata tare da tsabar zumudinsa tamkar ba'a taba yi masa haihuwa ba duk wani da ya san za a bukata na jariri sun saye shi kuma komai bibbiyu ya saya, idan Muneeba ta tambaye shi dalilın iyan abu biyu da yake yi sai ya ce shi a yadda ya ke ganin girman cikin kila ba da daya ke cikin ba, duk da cewa an yi mata hoto a asibiti ance da daya ne na miji amma shi sam ya bai yarda da hoton ba. Ita kam Muneeba sai dai ta yi masa murmushi idan yana dokinsa, duk da ita ma tana dokin amma na ta ba irin nasa 190 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria bane

Chapter 7 of 8