Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 8
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels WATA KUSAN RARAINE TIS 3 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ****** ****** ****** 2 H ayaniyar surutai da sallallamin da Lake yi ne ya sa Goggo ta kasa kunnuwanta, don fahimtar shin daga ina ta ke jiyo surutan, wadanda suka hada har da kara. Tashi ta yi tsam ta fito daga dakinta a bakin kofane suka ci karo da Suwaiba da ta kwaso a guje zuwa dakin Goggo. Suka dubi juna Goggon na tambayarta Lafiya? Wai me ke faruwa ne? Ta sa hannu ta share zufar fuskarta da ke barazanar tona asirin rashin gaskiyarta akan abin da ya faru tace, wallahi muna daki ne da bakuwata kawai muka ji shigowar Baban Baffa, kafin in fito ne na ganshi ya fadi kasa warwas. Ai Goggo bata bari ta karasa fadin wata kalma ba ta garzaya dakin Suwaiban da gudu har tana hardewa da zaninta. Tana shiga ta ganshi a kasa warwas babu motsi ba alamar motsi ko numfashi a tare dashi. Ta gurfana 3 WATA KUSAN 3 Rahm gabanshi ta dago kanshi tana ambaton sunansa amma ko gezau ta tashi a rude ta nufi hanyar fita gidan ta iske Jumona duke yanata, wanki tace, masa, "Jume taho ka taimakamin mai gidan ne ya fadi, mai gadin su na jin haka shi ma a rude ya rufawa Jume da Goggo baya zuwa dakin Suwaiba, suka iske uban gidan naşu tamkar yadda Goggon ta gaya musu su ma sumbi sahun Goggo don tabbatar da shin akwai rayuwarşa ko, babu, a dalilin rashin motsi da yake yj don ko numfashi ba kowa bane zai iya gane shin ya na yi ko ba ya yi. Tabbatar da a raye yake ne yasa Goggo ta sauke ajiyar numfaşhi tare da rage koke-koke da salallallami da ta ke yi ta umurci su Jume su kama shi zuwa mota don tafiya da shi asibiti, Nan ne kuma aka fara tunanin to- wa zaj tuka motar zuwa asibiti? Dama a gidan daga, mai gidan sai Muneeba ne suka iya mota Suwaiba bata tsaya ta koya ba tafi gane idan zata Anguwa a kaita.ors wdad 4 ど WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Jume ya dubi Goggo ya ce "Bari mu sashi a mota in tuka ni ma ina dan taba tuki idan na sami mota, tunda har wani gari ina zuwa sun kama shi ne suka ga hannunsa na hagu ya tafi yaraf ya fadi Jume cikin firgici yace "Subhanallahi ai hannunsa na dama a karye yake". Goggo ma ta sake rudewa tana fadin "Yau mun shiga uku wannan wata irin faduwa ce har da karaya, kuma ga rayuwarsa ma ba mu da tabbacin samunta. Haka dai suka taitaye shi suka saka a bayan mota Goggo ta zauna a gefensa Jume ya shiga mazaunin Direba tare da Suwaiba a gaban motar sai gursheken kuka takeyi har suka isa asibiti da ya zama nan ne suke ganin likita. Dakin taimakon gaggawa (Emergency Room) aka shige da shi, manyan likotoci ne suka yi taron rubdugu akan ceto rayuwarsa wanda suka shafe awani akansa suna bincike. 5 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Zama suka yi jigum-jigum a bakin fakin da aka shige da shi. Goggo addu'o'i take yi a bayyane akan Allah ya agajeta ya tashi kafadar Muneebu, wanda take ganin idan ta rasa shi a halin da take ciki a yanzu ba karamin gibi ta samu a rayuwar ta ba kasancewar shine bango abin jinginarta. Ita kam Suwaiba babu baka sai kuka ne babu abin da ta ke yi sai sharban Kuka tare da tunanin makomarta a dalilin Garanbaramar da ta yi na fallasar sirrin rayuwarta wanda har Mujeeb din ya ji da kunnuwansa kuma tabbas abinda ya ji shine sanadiyyar wannan mummunar al'amari da ya same shi ita kam bata saduda ba dole cikin satin nan ta saci jiki ta sulale zuwa gurin Boka don ta yi masa bayanin katobarar da bakinta ya yi har kunnuwan mijinta ya ji sirrin da aka ce idan ta bari ya ji to ta yi kuka da kanta ga dukkan irin bainda zai same ta, shi ya sa tun ma kafin abin ya risketa ko akwai abin da zai iya yi mata a mantar da 6 MI NIHCU C Rahmatu Hassan Zaria kwakwalwar Mujeeb abin da ya ji in ma hakan ba zai yiwu ba to zata iya yin gammo ta dauki dakon zunubin sa wa a dauki rayuwarsa in har hakan zai zamo mafita ga halin ha'u'la'in da zai sami rayuwarta, tunda hausawa ma cewa suka yi amfanin Zunubi romo to ta gwammace ta sharbi romon zunubinta da tushe tunda kwabarta ta riga ta yi ruwa. Goggo ta kaikaita ta dubi Jume dake tsaye a gefensu wanda ke cike da tsananin damuwa tamkar yayansa na jinniske cikin ha'u'la'in data samu uban gidansa haka yake ji a ransa, kasancewar Mujeeb mutum ne sak mai kyautatawa na kasa da shi tare da tausayawa al'amuran da suka sami wanda baya da shi musamman ma su da ke karkashinsa ko yaya ya gankaa wani yanayi ya dinga tambayarka kenan akwai matsala ne ko baka da lafiya ne idan kace lafiyarka kalau to nan take zai jika maka aljihunka don yasan matsalar Talakan Najeriya 7 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria bata wuce bushewar aljihunsa ruwa shike nan za ka nemi damuwarsa ka rasa kuma duk abin da zai basu ba wai cikin albashinsu bane a'a ihsani ne kawai irin nasa uwargidansa Muneeba ma haka take mai yayyafin alkhairi, shi ya sa kullum suke ciki da bakin cikin rashinta a gidan, amma suna nan ba dare ba rana sun dage da addu'ar Allah ya maidota gidan. Sabanin amarya Suwaiba mai Kankanan tsiya, sam bata iya alheri ba, komai kankantan canji idan ta aike su sai ta amshe abinta gata da yawan aike don sai ya jera kwana biyu zuwa uku tana aikensa Dukku, daga kudin mota ba za ta iya kara masa kwandala ba don ya sha ruwa a hanya ba shi ya sa a dole yake zuwa Dukkun albarkacin uban gidansa. Ta cewa Jume "Jume ka taho da waya ne? ya laluba aljihun wandonsa ya fiddo wayar yace "Eh gata nan a Aljihuna wani za'a kira miki? "Eh Isah nake son 8 „WATA KUSAN 3 イ 1 Rahmatu Hassan Zaria idan kana da numbarshi ka kira min shi ka bani in yi masa Magana, Nan da nan ya laluba Numbat Isah ya kira shi bugu daya biyu ana üku ya dauka sai ya mikawa Goggon ya ce, Ga ya nan ya daıki wayar Goggo ta kara wayar a kunneta ta amsa sallamar da Isan ke yi ta kara da cewa "Isah ba Jume bane Goggonku ce, so nake duk abin da ake yi ka barshi ka taho gombe yanzu ka same mu a asibitin da muke ganin likita gamu nan yayanku ne ba lafiya. Isah ya hau fadin "Innalillahi wa inna ilahirin rajiun Goggo me ya sami yayan? Ta ce "Ka bar bata lokaci ka taho kawai? Jikin Isah babu inda baya rawa da ya ji wannan abin tashin hankali da ya same su Mintunabasu gaza hamsin da biyar ba suka sada shi da Gombe. Ba'a jima da zuwan Isah ba aka gunguro Mujeeb akan gadon daukar mara Lafiya zuwa wani daki na musamman. A lokacin ne Baffa Adamu 9 WATA KUSAN E Bohmute Ne suka tso daga Dukku kasancewar da Isah zai taho ya biya ya gaya musu shi yasa basu yi Kasa a gwiwa bu su ma suka tahu har da Mustala yayan Muncta. Cabe. dayansu 'yan wwan snka hewaye gedon da Mujeeb ke kwance sny kallon sarautar Allah tart da yi iasa addu'a samun sauki likitah Re ya nemi son ganin wani cikin su Baffa sai Baffa Adaty ya unmrci Mastafa da cewar "Mustafa jekn ga likitan a madadinmu tunda kaine ke jin Turanci sai Meji bayanin wannan wane trin ciwo ne ya sami yaron nam gushi tamkut matacce bi rat be slaniir rai". Mustafa ya iske likitan a Ofis, a nan ne ya soma yi masa bayani Gaskiya dan nwanku yana cikin mawuyacin hali domin faduwar da ya yi ya huifar masu da manyan matsaloli guda úku na furko akwał (Stroke) da ya sare shi gefen sa na dama baya aiki gabadaya, sannan zuciyarsa ta sami tabwwa sakamakon wani abu da ya firgita shi wanda ku ne kuku san ho meys WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ya firgitashin ya sashi ya fadi har ya sami mutuwar barin jiki, sannan matsala ta uku da ya samu itace karaya da ya yi a tsintsiyar hannunsa na hagu kaga kenar hannuwansa duka biyun sun sami matsala amma Insha Allah zai sami lafiya don mun yi masa duk abin da ya dace mun gyara masa karayar an yi mata filasta muna fatan mu yi nasara a dukkar taimakon da muka bashi a cikinj yardar Allah. Mustafa zuciyarsa a dagule da jir iftila'in da ya sami dan uwansa ya y naunauyan ajiyar zuciya ya ce "Allah ya sa likita amma don Allah a hasashenku na manyan likotoci kana ganin dar uwana zai warke ya dawo normal mutum irin yadda ya ke da can tamkar kowa Likitan ya gyara zaman glas din da ko idanunsa sannan ya soma Magana, El muna da tabbacin akan haka Insh Allahu tunda mu Musulmai ne muna yir İya iyawarmu ne akan larurar mara 11 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria lafiyarmu sai mu barwa Allah sauran lamarin shi, shi kadai ya san yadda zai yi da bawansa idan munga nasara to daga gare shi ne, idan mun ga akasin haka nan ma daga gare shi ne. Ya dan yi wani rubutu a Fayel din da ke gabansa sannan ya tsaida idanunsa akan Mustafa, "Abin da na ke son yanzu muna so ku kula da shi sosai, ya kasance ko da yaushe akwai mutum a kusa da shi saboda zai iya yiwuwa idan zai farfado ya motsa jikinsa to sai a rike shi tunda ya na da karaya a hannunsa mai lafiya kada ya lalata aikin da muka yi masa. Zai kuma iya yiwuwa idan ya farfado idanu kawai zai bude abin da bama fata kenan saboda haka sai kuje kuyi ta addu'a ALLAH ya bashi lafiya. Mustafa ya aje ajiyar rai yana kada kai damuwa ce fal a ransa yayi wa Likitan godiya ya bar ofis din. Ya yi wa Su Baffa bayanin komai da likita ya gaya masa, anan ne Baffa 12 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Adamu ya tsare Goggo da idanuwansa cikin tuhuma yace 'kin dai ji bayanin likita ya yi ? to ina son sanin abin da yaron nan ya ji har ya firgitashi yayi irin wannan faduwar tunda abin a gida ya same shi?. Goggo ta share kwallar dake shatato mata a kunci, zuciyarta cike tsananin damuwa tare da dora zargin komai akan Suwaiba tace, Wallahi ni ban san me ya ji ba tunda abin a dakin matarsa ya same shi, nima ita tazo ta kirani, ita ya kamata a tambaya. Baffa ya ce "Mu bamu da ikon da za mu titsiye matarsa mu tuhumeta tunda ke da muke da iko a kanki baki sani ba sai mu bar maganar, mu barwa Allah al'amarin mu yi masa addu'ar samun lafiya koma me ya ji ya firgita shi idan Allah ya ba shi lafiya ai za mu sąni ba ma sai mun bata lokacin mu ba wajen bincike bа. 13 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Suwaiba dake rakube a gefen su duk tana jin abin da aka fada jikinta ya yi la'asar ita kam addu'a take kada Ailah ma ya tada kafadarsa ya sa daga wannan baccin zai yi tazarce ne don kuwa tasan samun lafiyar sa na cikin tonon asirinta sannan kuma karyewar asirin da ta yi masa tunda boka ya gargadeta da cewa kada ta kuskura mijinta ya ji sirrin dake tsakanin ta da shi, gashi kaikayin baki ya sa ta yi baranbaramar da ya ji komai har hakan ya yi sanadin shigarsa halin ha'u'la'i. Ita kam za ta yi gum da bakin ta ne a kada a raya babu wandá zai ji wannan ta'asar da ta aikata da boka, tunda ta san Goggo sam ba za ta yarda a ci amanar auren danta ba ta hanyar yin fasadi da boka, duk iya biye biyen malamanta da bokaye, ita ma Hajiyarta ba za ta goya mata bayan yin zina da Boka ba, bar su dai da binne binne da yanke yanke ko zuba asiri a abinci, amma ba za su yarda da 14 WATA KUSAN 3 Rabmatu Hassan Zaria aikata wannan babban Fasadin ba da igiyar aurenta da komai. Tana matsar Kwallan munafunci ta dan langabar da kai ta ce, ni kam Baffa wallahi ban.san cikin firgicin da ya dawo gida ba ila dai ina daki ina sa wa Walceda kaya na ji faduwarsa a falo ni wallahi ban ma san ya shigo ba, ko ma me ya firgita. zuciyarsa ina ganin daga waje ne". Baffa ya jinjina kai, "Ko ma mencne mu kam mun bar wa Allak lamarin mmu yanzun fatanmu ALLAH ya tashi kafndarsa ya bashi lafiya don wahnan ciwo nase akwai tararrabi". Mustafa kam tunda ya ji bayanin Likita da kunnuwansa na cewa kada a bari ya farfado ba kowa a gurinsa shi ya sa ya yi saurin barin gurin su Cogge ya koma dakin de Mujeeb din yake duk Isah na can ya daifi son shima yana kusa. Ya ja kujera ya zauna daf da fukar Mujeeb din, ya Rura masa idanu yana SON 15 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria ya gano ta inda numfashin Mujech fin ke fita, wanda duk iya kwakkwafi da kurilarka, ba za ka iya tantance ta inda numfashi ke fita bah. Don dai likitoci sun tabbatar, musu yana da raine; gaskiya da ba zai yarda Mujeeb na da rai ba. Ya kaj hannunsa yana shafar bannun Mujeeb din zuwa Kafarsa wadda likita ya ce basa aiki ya kai ganinsa ga daya hannun wanda yake nade, eikin Alasta shima a karye ya ke,yn, girgiza kai Aikin jin tausayin halin da rayuwar,Mujeeb di ke ciki bai san lokacin da hawayg ya ziraro, a kuncinsa ba. Ya lalibo wayarsa a aljihu ya kira Layin Muneeba wadda yake kyautata zaton bata,san me ke faruwa ba tunda bata Dukku tana nan Gomben. Bugu Daya, biyu sai ta dauka tana salamu Alaikum Baban Inna" banda yn ji ta fara da wannan bark wancin na kiransa, Baban Inna ya san bata san komai ba dangane da abinda yasami 16 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria mijinta (Sunan Innarsu aka sakawa diyarsu shine ta lakaba masa Baban Inna) don yace baya son a kira 'yar da Inna Shine take tsokanarsa da Baban Inna idan tana jin barkwanci). Yau bai biye ma barkwancinta ba saboda yana cikin tashin hankali "Kina ina ne yanzu". Ta amsa ina gida yanzu na dawo daga kasuwa a gajiye ina kishingide ina hutawa" "Ok, to ki tashi yanzu ki shirya ki zo nan asibitin da kuke amfani da shi muna nan tare da su Baffa, Mujeeb ba Lafiya yana cikin mawuyacin hali, me ya same shi? Ka tabbatar yana raye? Ya ce, yana raye ke dai ki zo ki same mu. Gaba daya jikin Muneeba ya yi sanyi tana daga zaune ta kasa tashi sai jujjuya ciwon na Mujeeb takeyi a ranta, shin wane irin ciwo ne ya same shi? A iya saninta da shi ba shi da wani na gama gari ko na kullum kullum to ko wane irin ciwo ne ya same shi? Oho!. 17 Ta sami Mama Amina na a daki ta yi mata bayarin wayar da. Mustafa ya yi mata, ta kKara da cewa "Ni yanzu da ya kirani me zan je in yi a asibitin tunda su suna can sannan ga Guggo ga matarsa, ne iyakaci kawai in je in gaishe shi in dawo". Mama ta girgiza kai "yaro Man Kaza to in ma kinje kince zaki yi jinyarsa, ko Mustafa yace kizo kiyi jinyarsa da wanda zai hana ki ne ko yayi miki shamaki da shi ina ce har yanzu a matsayin mijinki ya ke to bana son sakarci maza ki shirya ku tafi da Hibba ku dubo shi, muma gobe za mu je mu duba shi Allah ya bashi lafiya. Muneeba ranta bai so zuwa ba a dalilin irin wulakancin da tozarci da Mujeeb din da Guggo da Suwaiba suka dinga yi mata kafin barinta gidan tana ta hakuri da su, har dai ta kare da bakinsa yace kada ta dawo gidansa sai ya nemeta neman da bai yi mata kenan ba ya jingina aurensu babu ko waiwaiya to ita kam don meye zata waiwaiye shi don ba shi da 18 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria lafiya ita ma fa tayi ciwo kuma an gaya masa kila ko don bata kwanta a gadon asibitin bane yasa bai zo gaisheta ba?. Nuku - Nukun ta dinga. yi har kusan magariba hakan ne ya tunzura zuciyar Mama Amina ta zọ ta rufeta da fada, Haba Muneeba ban sanki da zuciyar rikon dan uwanki Musulmi irin haka ba, dan uwan naki ma na jinni kuma Mijin aurenki ki juya wa duk abin da ya faru baya, kije ki duba shi domin Allah kuma domin zumunci in ba za ki je don auratayya da ke tsakaninku ba ciwo ai ya kori komai kuma tunda kika ga har Mustafa ya kira ki ai abin ba karami bane. Oya maza sa Hijjabi ku wuce tun dazu idi keta jiranku. Ba tare da tayi Magana ba ta suri Hijjabi ta zira sai wayarta da ta dauka tayiwa Mama Sallama suka tafi. Yanayin yanda ta riski halin da Mujeeb ke ciki abun ya firgitata ya bata tsoro har sai da ta zubar da hawayen 19 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria tausayawa a gareshi. Ta iske su Baffa duk sun koma Dukku sai Mustafa ne ke zaune tare dashi a dakin a lokacin Goggo ta fita yin sallar Magariba. Muneeba ta dubi yayanta Mustafa zuciyarta a tsinke da al'amarin tace "wai yaya Mustafa wannan wane irin ciwo ne ya same shi ga dai mutum a kwance tamkar matacce amma wai yana da rai ya dade yana ciwo ne? ya girgiza kai "A Yadda Goggo ke gaya mini da na zo lafiyarsa kalau don ko ciwon kai bai wayi gari dashi ba har ranar illa lokacin da ya dawo gida ne abin ya same shi a dakin Matarsa, ita kam bata san me ya faru ba, Suwaiban ce ta garzayo take gaya mata gashi can ya fadi a falonta, wai ita ma bata san ya shigo ba sai dai faduwarsa ta ji". Muneeba tayi tsam da ranta cikin nazari sannan tayi Magana, "A binciken likitoci da suka duba shi me suka bincika da ya kawo masa faduwar da ya yi sannan me ye alakar hakan da abin da ya shafi 20 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria a zuciyarsa "Eh to likita ya kira ni yayi min bayani cewar ya sami. (Stroke) bangarensa na dama baya aiki sannan ga karaya a hannunsa na dama kinga kenan dama da hagunsa sun sami matsala sai zuciyarsa ta sami tabuwa lafiyarta a dalilin wani abu da ya tsoratar da żuciyar tasa, wanda shine muke ta bincike don mu gano me ya ya yi har yaba shi tsoro haka. Goggo kam ta dora zarginta akan Suwaiba tunda a dakinta abin ya faru a cewar ta lallai wani abin ya ji suna fada ita da bakuwar da ta yi, amma ita suwaiban ta musanta hakan`shi yasa na roki Goggo da ta bar maganar tunda babu tabbas kada rayuka su baci, mu dai muyi ta addu'ar Allah ya bashi lafiya samun lafiyarsa ya fiye mana komai Tunani Muneebа Mujeeb ne na lallai zaiji ya darsu duk a wani zuciyar abu da mummuna daga bakin dSuwaibato bazai ras Goggonsa a ciki ba, S 21 alaka da kasancewar duk WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria wani fadi tashinsu da biye-biyensu tare sukeyi da uwarta da Goggon da ita Suwaiban ko ma dai meye su suka sani ita kam kankararta a kunne har ta manta da matsalolinsu, kawai matsalarta yanzu ciwon mijin nata, duk da dai bata da tabbacin zata koma gidansa tunda har baffaninsu sun fara maganar za'a nemo shi don ya bata takardanta zaman nata a gaban iyaye ya isa haka gashi nan ya janyo mata sintirin mazaje gani suke auren nata ya mutu ne ko ta gayawa masu biyo ta ko aikowa cewa da aurenta karyatawa suke yi shine fa dalilin da yasa Baffansu yayi ta bambancin fada yace lallai dole a san abinyi idan auren yake ta koma gidansa in baya yi ya bata takardanta don ga masu so nan fal a gari, ba zai yiwu ya jingine ta ba kamar tsohuwar riga. Shigowar Goggo dakin ne ya katse mata tunaninta suka risina a gaban Goggon ita da 'yar rakiyarta Hibba suka gaisheta tare da tambayarta ya mai jiki da sakin 22 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria fuskarta da komai ta amshi bakuntar tasu har tana karawa da cewa "Kinga yadda Allah yai ikon sa kan mijinki ko? Larura farat daya ta same shi bamu san Musabbabin ba sai shi sai Allah, sai kuma matarşa da abin ya faru a dakinta, ta yi gum da bakinta ta ki fadar gaskiyar me ya faru Allah dai ya bashi lafiya zai fadi koma mene ne da bakinsa". Muneeba ta yi saurin ratar numfashin gogon "Abin da kawai zamu yi tayi addu'a kenan samun lafiyarsa koma meye sanadin ciwon nasa sai ayi hakuri a barwa Allah shi ai baya bacci. Goggo ta gyara abin Sallah dake gefe zata fara Sallah Muneeba tace "Inna Amina tace a gaida mai jiki, ta so mu zo tare to baba baya nan kuma bata sami wayarsa ba gobe suna nan zuwa To Madalla ai babu komai yau da gobe duk daya ne a gurin Allah Allah ya kaimu goben". 23 WATA KUSAN 3 Rahmatu Haşsan Zaria Muneebata dubi Mustafa yace Yaya Mustafa ka je ka yi Sallah idan ka dawo ni sai inje in yi kada ka rasa jam'i ya fita zuwa masallacin dake Harabar asibitin da Goggo ta idar sai ta ce suje suyo alwala zata zauna kusa da shi. Har tara na dare ta 'wuce Muneeba na asibitin bata da alamar zata tafi, Mustafa ya yi mata Magana Dare fa ya soma ku zo ku tafi gida ga Isah nan tunda ya dawo sai ya kaiku a motata idan ya sauke Goggo sai ya saukeku ni za mu kwana da shi". Ran Muneeba a kumba ya ke ne yadda za ta iya barin asibition nan alhalin tana ganin yadda yanayin jikin mijinta yake a kwance tamkar mutum-mutum a tunaninta idan ta tafi da kyar zata dawo gobe ta iske shi da sauran numfashi. Ta san dole ta tafi tunda koda tana gidansa ne zai yi wuya ta dinga kwana da shi a asibitin tunda ga su Mustafa da Isah nan ko Isah ma kaďai zai iya kwana da shi. 24 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria Kafin su tafi sai da ta tsaya akansa tayi masa addu'o''i ta tofa masa sannan suka tafi da suka koma gida a tsaye a tsakiyar falo suka iske Inna Amina tana ganinsu ta sauke ajiyar zuciyar tace, Haba Muneeba kunje kunyi dare ina nan hankali na a tashe tunda kin san Idi ya tafi babu mai zuwa dauko ku ai da sai ku dawo da wuri ya mai jikin?. Ta sabule hijjabin kanta tana cewa Jiki sai godiyar Allah amma gaskiya yana jin jiki don baima san wanda ke kansa ba balle shi ma ya san a inda yake bashi da Maraba da matacce illa ta hanyar numfashi wanda sai ka yi tsananin lura ne zaka gane yana numfashin. Inna Amina cikin tashin hankali ta ce? Wane irin ciwo ke damunsa. "A dakin matarsa chin uo some shi a cewara wai ta a ji ta fito kinga dai ya sami karaya a hannun hagu, gefen damansa kuma baya aiki ya 25 WATA KUSAN 3 Rahmatu Hassan Zaria sami (Stroke) sai Zuciyarsa da ita ma ta sami matsala a cewar likitan wani abu ne ya firgita zuciyar tasa Allah ma ya sa bata gefen hagun ya sami mutuwar rabin jikin ba da shi kenan zai iya kamowa da matsanancin ciwon zuciya in ma ya zo da Karar da kwana bugawa kawai zata yi sai dai aga gawar mutum a rasa meye sanadin mutuwarsa". Inna ta dau salati ta dire tana nanata "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un Allahumma ajurni fi musibati wa aklifni hairan minha wannan wane irin iftila'i ne ya fadawa rayuwar yaron nan? Allah ka kawo masa agajinka ka bashi lafiya ka tashi kafadarsa. Wannan Suwaiban ta zame wa mutane jafa'i su kam ko za su gane makircinta

Chapter 1 of 8