Reading KIDA A RUWA BOOK2 COMPLETE BY BILLYN ABDUL Chapter 4 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya fara zuba musu harara da faɗin, “Sannunku ƴan wrestling ko ƴan boxing ma zance ban sani ba nikam”.






*_💦KIƊA A RUWA...!!💦_*




*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*


*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._


*_GENERAL FICTION_*

_Wannan labari ƙirƙirarre ne. Sunaye, wurare, da abubuwan da suka faru duk ƙirƙira ne, ba su da alaƙa da gaskiya ko wani, koda Bilyn Abdull ce 😂._


*_BOOK 2_*
_Chapter 10_

__________________

_A KANO KI KE…? Kina neman inda zaki siyi abinci mai daɗi? Kina ƙiyar yin girki gashi zaki yi baƙi?, kina neman inda zaki yi order abinci mai daɗi wanda zaki fita kunya?. Masu abinci suna suka tara, akwai abinci mai daɗi akwai a lallaɓa. Kina son ki siyi abincin da zaki ɗauka a saudia ki ke? Kuna son ku siyi abincin da in kuna ci zaku dinga murmushi saboda daɗi da khamshi?. LEEMARS_DELICIOUS itace kat a wannan ɓangare, tazo muku da nau’in abinci kala-kala na gargajiya da na ƙasar waje. Tana siyar da MANDI RICE, GRILL CHICKEN, CHICKEN BIRYANI, FUNKASO, ALELEN GWANGWANI, BREAD POCKET da sauran su. Fannin abin sha akwai natural ZOƁO mai zaƙi, wanda aka yi shi da ingantattun kayan marmari masu ƙara lafiya, akwai wanda bashi da zaƙi domin masu ciwon sugar da masu gudun ƙiba._



_me ku ke jira? Maza ku garzaya shafin ta na instagram ko TikTok domin ku ganewa idanun ku, ku danna wannan link din domin yin magana da ita kai tsaye. Ko ku neme ta a number wayar ta da take ƙasan rubutun nan._

INSTAGRAM
👇🏻👇🏻👇🏻
https://www.instagram.com/leemars_delicious?igsh=MWRzZWtnYXM4ZHB2dw%3D%3D&utm_source=qr
CALL/WHATSAPP
👇🏻👇🏻
wa.me/2349030398006

TIKTOK
👇🏻
https://www.tiktok.com/@leemars_delicious?_t=ZS-90ZQJ2mNJKc&_r=1




Kar ku sake a baku labari, siyan na gari mai da kuɗi gida.❤️❤️🫶🏻
__________________


*_TELEGRAM GROUP_*

https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk


*_WHATSAPP CHANNEL_*

https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F

*_TIKTOK_*

https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/

*_INSTAGRAM_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

______________________

........Su Nimrah dake laɓe da tunanin za'a sake maganar makarantarsu jin shiru su Mammah ma sun ɗauki wani zancen daban suka bar wajen. Suna shiga ɗaki Nimrah ta ce, “Trouble Buddy! Kin san mi zamuyi?”.
     “A'a sai kin faɗa”.
  “ALLAH in dai Daddy ya dage sai ya kaimu Boarding ɗin nan randa aka kaimu samun wata Senior ɗin zamuyi mu lakaɗa mata dukan da a washe gari za'a kirashi ace an koremu gaba ɗaya. Idan mun dawo gida mu dage masa kan bamu san munyi ba aljanu ne damu da gaske.”
      Sai da Ruky tai dariya sosai sannan ta ce, “Sai da ke Hot Pepper! Amma fa ni kin san wani lokacin ina da ɗan tsoro, kada muje wajen ƙaryar aljanu a samo wani ustazu ya daki banza da sunan Rukya, ko'a ƙara na kwanaki yace zai aurama su maigadi mu.”
         “Ai ke banza ce. To bari kiji ALLAH bazasu bari a dake mu ba. Balle ma in har za'a Boarding ɗin nan dole muyi sanadin da za'a haɗa harda Fiddo da Bintu”.
     “Muguwa naga mu kaɗai mukai laifin? ALLAH ki dinga jin tsoron ALLAH Ninah”.
     Itama dariya tayi yanzun kam, ta wani juya idanunta manya cike da iyayi, “Yo da tsoronki nake ji Ruky. Bazaki gane ba idan muka haɗu mu duka sai Boarding ɗin ma tafi daɗi idan ta zama ƙaddarar mu. Mu haɗu mu dinga darje bakin ƴan iska da duk suka nuna mana yatsa.”
      Tafawa sukai suna dariya....

Nace ALLAH dai ya shirya waɗan nan yara🏃🏼‍♀️. Daddy Imran ka rufa mana asiri ka barsu a Day school ɗinsu, kada wataran suja maka ka sake komawa inda Dada yake.🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️😂.

____________★

         Aiki gida dai ya tabbata akan ƴan caskalen gidan Mammah, dan kuwa a bazata washe gari tunda safe sai ga Imran a gidan, suna tsaka da barcinsu ya saka Aunty Biebah taso masa su. Da farko sai faman layi suke suna ma Biebah kukan shagwaɓar ta barsu su barci suke ji, amma suna cin karo da Daddy suka watsakke, a tare suka zube suna gaishe shi. A taƙaice ya amsa musu tare da faɗin, “Oh barci ma kuke yi har zuwa yanzu? Batun breakfast, shirya ƙannenku zuwa school duk wa zai yi?”.
      “Daddy kayi haƙuri, ALLAH bamu san barci ya sake ɗaukar mu ba”.
    “Na baku mintuna goma ku wuce ku shiryo su Abees”.
     Kafin ma ya gama rufe baki sun fice a sashen. Kai tsaye sashen su Yaya Ja'afar suka nufa kamar zasuyi kuka, dan suyi sauri sai suka rabu. Nimrah ta shiga sashen Yaya Ma'aruff ita kuma Ruky na Yaya Ja'afar. Shigowar Nimrah dai-dai da fitowar Aunty Lailah daga ɗakin su Aheel, fuskata da murmushi ta ce, “A'a Ninah miya faru ba'ai shirin makaranta ba?”.
     Kamar Nimrah zata saki kuka ta ce, “Ammie kin manta muna suspension? Zan shirya su Aheel kije ki kwanta kawai”.
       “Oh na manta, amma Ninah aikin zai muku yawa, ga haɗa breakfast ɗin gida gaba ɗaya, ga gyaran sashen ku. Kije kawai bari na shirya su kinji”.
      “Ammie Dady fa na nan”.
Cikin ɗan waro idanu Aunty Lailah ta ce, “Gidan Yayan yazo da sassafen nan?”.
     Kai ta jinjina mata. Dai-dai da fitowar Yaya Ma'aruff ya ce, “Wayo yazo da sassafe?”.
      “Wai ya Imran”.
  Murmurshi kawai Yaya Ma'aruff yayi yana girgiza kansa da faɗin, “ALLAH yanzu gaba ɗaya Yaya Imran ya canja zuwa Dada, da dai babu ruwan shi da faɗa amma yanzu ya gaje halin twiny sa. Ninah zo nan”.
       Sum-sum Nimrah ta iso inda yake, zama tai a ƙasan lallausan carpet ɗin tace, “Uncle good morning”.
      “Morning sarakin ƙiriniya, ke dai ke da Ruky ku saka mutane surutu shine jin daɗin ku ko. ALLAH idan baku canja ba duk randa Dada ya dawo gidan nan sai kun gane Yaya Imran bai iya komai ba”.
       Caraf Nimrah ta ce, “Uncle kenan Dada shi mugu ne?”.
      Dariya yanda tai ɗin yaso saka Ma'aruff, amma sai ya danne ya murmusa kawai. “Dada ba mugu bane, amma baya son rashin ji, ku tambayi Ammar zai baku labari dan shi ma da rashin ji ya fara Dada ya saita shi da horon sojoji. To kuma idan baku nutsu ba duk randa ya dawo jiki magayi”.
           “In sha ALLAHU zamu ma bari, amma dan ALLAH Uncle wai shi Dadan yana wace ƙasa ne? Yaushe kuma zai dawo? ALLAH ina son na ganshi, kaga sai a hoto muka taɓa ganinsa shima sau ɗaya ne Mammah tasa aka tattare hotunan aka ɓoye”.
      Sai da Yaya Ma'aruff ya haɗiyi yawu mai ɗaci sannan yay ma Nimrah murmurshi kaɗan. Bayan su masu hankali har yanzu daga Mu'azz har su Nimrah basu san Dada na prison bane, kawai ance musu yana wata ƙasa ne yin wani aiki mai muhimmanci. Dan ko Biebah ba komai ta sani ba sai kaɗan-kaɗan daga cikin lamarin shima dan ya watsu a media ne lokacin...
      “Ninah in sha ALLAHU Dada zai dawo, ina ji a jikina nan kusa ma kuwa zai dawo gare mu. Ku dai ku cigaba da addu'a kawai. Dan zuwansa garemu zai iya zama tamkar haɓo ne kinji”.
        “ALLAH yasa Uncle, kuma in sha ALLAHU kullum zamu dinga zama mu da su Abees muna addu'ar”.
    To ALLAH yay muku albarka. Ina Sisin taki?”.
    “Mun raba aiki ne tana can zata shirya su Abees”.
        “To kinga tunda ga Ammien ku na shirya su Aheel anan tashi muje, ni zan janye Yaya Imran ɗin sai kuyi sauri ku haɗa breakfast kawai”.
    Sosai farin ciki ya kama Nimrah, koda suka fito suka leƙa sashen Yaya Ja'afar sai suka sami Rukyn ma ba aikin take ba, tana gyarama Afrah gashi ne dan har an musu shirin makarantar ma. Sai kawai ta kamota suka fito zuwa sashen Mammah, ta ƙofar baya ta kitchen Yaya Ma'aruff yace su shiga, shi kuma ya zagaya riƙe da hannun Afrah dake zuba masa surutu, dan itama dai akwai baki ta gado su Nimrah ɗin.....

Tun a haɗa breakfast Nimrah da Ruƙayya suka san ALLAH ɗaya ne. Masu aiki kuwa na ƙoƙari kwarai-ƙwarai da gaske. Suna wayyo-wayyo Uncles ɗin nasu da Auntys na dariya suka jera a babban family dining table ɗin makeken falon Mammah. Dan dama haka suke cin abincinsu a tare tun daga na safe har na rana ga wanda suke a gida. Na dare kuwa dama kowa yana nan. Kowa na ƙoƙarin kammalawa ya wuce aiki suko suna haƙilon gyaran kitchen, ga Mu'azz ya saka rayuwarsu gaba. Daya motsa sai ya ƙwala musu kira.
       “Ninah bani kaza, Ruky baku ajiye abu kaza ba”.
     Suko takaici ya ƙulesu sai su ɗakko a hasale su dangwarar masa. Dariya kamar ta kashe su Aunty Shariffa. Aunty Biebah ce ma suka bata tausayi bayan tafiyar Daddy Imran tace su gyara falo kawai bari ta tayasu gyara bedrooms tunda dai can ai babu camara balle Yaya Imran ɗin ya gani. Dan koda zai wuce sai da ya sake jaddada musu idan ma basuyi ba zai gani ta cctv Camaras dake zagaye da gidan tako ina. Wannan ya sake sasu tsorata suka dage. Duk da taya sun da Aunty Biebah tayi basu kammala komai ba sai 12 da wani abu, a wahale sukai wanka sukazo falo inda su Aunty Shariffa ke hira dan su basa zuwa aiki, shiyyasa koda yaushe suna sashen Mammah suna ɗebe mata kewa. Balle yanzu hirar na armashi Mu'azz yana gida zaune kafin ya wuce University. Yau kuma anyi sa'a Aunty Biebah ma dake gab da kammala master nata bazataje school ba. A ƙasan lallausan carpet ɗin falon suka zube kowa na maida numfashi.
     Mu'azz ya kwashe da dariya cike da mugunta. “Oh ALLAH yau ga mata sunyi aikin gida. Ku a haka za'ai muku aure kuje kunayi, dan ALLAH ji Ninah kamar an tsamo mage a ruwan zafi, gara-gara ma Ruky”.
        Kamar Nimrah zatai kuka ta ce, “Mammah kin jisa ko, wai nice mage a ruwan zafi”.
      “Shi kuma muzuru ko?”.
Cewar Biebah na jifansa da filo. Cafewa yay yana dariya da faɗin, “Kai small Mom muzuru kuma. Dan ALLAH kar ki saka yaran nan su raina ni mana. In ba haka ba ALLAH zan zuga Daddy a kaisu boarding school ɗin nan mu huta. Su Ayyan sun ishe mu”.
       “Idan su basu tafi Boarding school ba ai kai ka tafi, tunda baka san inda za'a cillaka karatun ba”.
     Kallon Aunty Shariffa mai maganar yayi da faɗin, “Kai Mamy banda fata, kin san bakin iyaye da saurin kama ɗa, in sha ALLAHU nikam ina nan cikin garin nan babu inda za'a kaini”.
         Mammah dake fitowa a ɗaki ta ce, “Ni dama za'a kaika wani ƙasan da yarana sun huta da damun su da kakeyi babban banza”.
     “ALLAH Mammah na tafi kema sai kinyi kewata. Suma haka kuma, dan sun san ina rufa musu asiri a gidan nan. Amma tunda kun shigar musu yara duk zaku gane kuran ku. Daga yanzu ko tarin banza kukayi zan fara rubutawa ne, kuma Dada zan ajiyewa yanda zaku fi caskaluwa dan na Daddy mai armashi ne yanzu”.
     A tare suka kwashi fillo suka shiga jefa masa. Gashi sun kasa tashi saboda ƙafafinsu sunyi dayin wahalar aiki. Aiko mi za'ai in ba dariya ba. Da ƙyar Mammah ta raba faɗan nan ta hanyar janyesu ta shafa musu man zafi a ƙafafu. Ga shi lokacin yin girkin rana yayi. Haka suka shiga kitchen ɗin suna sharɓar hawaye, ga camaras da suke ji kamar su fincike su su yardar su samu a tayasu. Amma ba dama, dan duk bayan wani ɗan lokaci sai Daddy Imran ya kira waya ya tabbatar musu duk yana kallonsu dan yayi connecting da wayarsa, suma kuma sun san haka ɗin ne tun ma ba yanzu ba..........✍️


Gaskiya kuzo muje balling Trouble Buddy da Trouble Queen kafin Daddy Imran ya kaisu gadon asibiti🤣🤣.

   

_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._

*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_My NITA_*

*_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_*

_Shaidar biya👇_

*_Whatsapp number_*
*_+227 98 94 12 81_*


*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*

*9032345899*
*_Moniepoint MFB_*
*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*

*_KATI MTN (1k)_*
*_09032345899_*


*_Shaidar biya: 👇_*
*_Telegram Number 09032345899_*


*_AREWABOOKS (Vvip)_*
*_Chapters & Audio_*
@BilynAbdull

*_WHATSAPP (500)_*

*1487616276*
*_Access Bank_*
*_Bilkisa Ibrahim Musa_*


*_Kati MTN:- (500)_*
*_09032345899_*


*_Shaidar biya:-_*
*_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*


*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*

*_WhatsApp Number 👇_*
*+234 805 568 7449*
*_Telegram Number👇_*
*+234 903 234 5899*


*_ASSALAMU ALAIKUM MUTANE NA MASU ALBARKA_*

*_Maza ku matso MASOYAN Bilyn Abdull da IDANU suka hana karatun novels...._*


*_Tofa Bilyn ku ta samo muku hanya mai sauƙi da kina aiki, ko kina kwance kina hutawa, ko kina inda baki son yawan surutu earpiece ɗinki kawai zaki maƙala a kunne ko Bluetooth kisha sauraren littafin KIƊA A RUWA.... Cikin sauƙi.... 💃_*


*_Kar dai na cika ku da zance. Zamu fara saida littafin KIƊA A RUWA.... Na saurare (Audio) kenan akan farashi mai sauƙi da rahusa._*


*_Akwai VVIP AREWAPEN kenan 💃_*


*_Akwai VIP Telegram 💃_*

*_(Ƴan WhatsApp ku haƙura kawai ƴan ta'addar bati sunfi yawa a cikinku gaskiya tsoron rashin m ɗinku nake 😂🤣)_*


*_Telegram Audio 2k ne kacal ba tsada 💃. Sai kusaka ta wannan account ɗin👇_*

_(2k)_

*9032345899*
*_Moniepoint MFB_*
*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*

*_KATI MTN (2k)_*
*_09032345899_*


*_Shaidar biya: 👇_*
*_Telegram Number 09032345899_*


*_Ƴan NIGER🇳🇪 kuma bazamu barku a baya ba in sha ALLAHU zaku biya (Telegram vip 1,500 CFA) domin littafin KIƊA A RUWA..... na ji Audio-vocal. Sai ki biya tanan👇_*.


_(1,500 CFA)_
*_+227 98 94 12 81_*
*_My NITA_*

*Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 1,500 CFA vip telegram

_Shaidar biya👇_

*_Whatsapp number_*
*_+227 98 94 12 81_*


*_AREWAPEN (Vvip)_*
*_Chapters & Audio_*
@BilynAbdull



*_Ƴan WhatsApp kuzo muyi shawara idan zaku iya amana ayi harkar nan daku 😂, dan bana son a barku a baya duk da dai bakwa ji, ba raga min zakuyi ba na sani duk da ƙaunar da nake muku 🤣😂._*






*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

11

.........Kwanaki kusan biyar su Nimrah na cin ƙaniyarsu da aiki, sun jikatu matuƙa sunyi laushi, kuka da roƙo babu kalar da basuyi ba, hakama kawunansu sun bama Daddy Imran haƙuri amma yace idan suka bar aikin nan Boarding fa babu fashi. Da ga ƙarshe dai suka zagaye suka kira Aunty Ummie a waya suna mata kuka suka sanar mata. Dama kwana biyu bata leƙo gidan ba saboda aiki. Aunty Mommy kuwa basa ƙasar ita da mijinta sai a satin nan zasu dawo. Ita ko Aunty Mimi ciki gareta tsoho haihuwa ko yau ko gobe shiyyasa Mammah ta hanata zuwa gidan.
     Alhamdullahi zuwan Aunty Ummi da suke kira da Big Mah-mah ne ya cecesu a hannun Daddy Imran. Dan bayan an sako massalacin juma'a yazo gidan gaida Mammah ta tareshi da daɗin baki da ban haƙuri har ya haƙura masu aiki su dawo gobe. Amma duk da haka da sharaɗin daga yanzu kullum dasu za'a dinga shiga kitchen yin girki. Da wannan ALLAH ya ƙwacesu. Masu aiki suka dawo, su kuma suka samu sauƙi. A cikin satin ma suka koma zuwa islamiyya dan suspension ɗin ta ya ƙare, sai kuma karatun da akayi basa nan ya sakasu a gaba. Sati ya zagayo suka koma boko ma, amma duk da haka sai da akai zama da Hajiya ta kafa sharaɗin babu su ba yarinyar ta, dole kuma a raba musu wajen zama sannan case ɗin ya mutu. Dan an dai gane ƴarta na kalle-kallen banza a waya da gaske kamar yanda su Nimrah ɗin suka faɗa......

        >>>>><<<<<<

    Yau ta kasance juma'a, dan haka an tashesu da wuri. Sai dai shiru babu drivern su babu alamarsa. Sun san maybe ya fara zuwa ɗaukar su Abees kafin yazo nan, duk da kuwa a kulum su yake fara zuwa ya ɗauka kafin su ƙarasa makarantar su Abees ɗin saboda suna rigansu tashi. Tun suna kallon agogo har suka sare, ga mafi yawan ɗalibai duk sun wuce anzo an ɗaukesu. Makarantar su nada doka kuma ma tilas zuwa ake ɗaukar kowane ɗalibi bawai buɗe musu gate ake su fito ba kawai.
     Sun gaji ga Ruky na ciwon mara, dan ita in zatai period ba ƙaramin jikata take ba. Ganin ta fara kuka hankalin Nimrah ya tashi. Ofishin Principal ta nufa amma ta tasar baya nan wai sun shiga meeting da malamai. Da gudu ta dawo wajen Ruky, ta sameta durƙushe azaba ta isheta, bata son suje clinic ɗin cikin makaranta dan an riga an tashi. Idannunta na cika da ƙwalla itama ta kamata ta miƙar. “Tashi muje wajen security ko zai taimaka ya barmu mu fita kawai, amma shima Baba Driver bai ƙyauta mana ba”. Da ƙyar da ƙyar Ruky ta iya miƙewa suka isa gate ɗin, cikin sa'a suna isowa sai ga motar Yaya Ammar na isowa. Ajiyar zuciya Nimrah ta sauke, dai-dai Mu'azz na fitowa daga motar, ya ƙaraso inda suke da sassarfa yana faɗin, “Lafiya kuwa? Miya sami Ruƙayyan?”.
        “Yaya ciwon mara, muyi sauri mu tafi kasan idan ya fara tsanani sai suma. Amma Yaya driver fa?”.
      Sai da ya buɗe musu suka shiga yake bata amsa yana reverse. “Baba driver accident yayi, yanzu haka ma yana asibiti”.
     “Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, badai da su Aheel ba?”.
     “A'a bada su ba, shi kaɗai ne yaje ɗakko motar Ummie (Aunty Lailah suke cema Ummie, Shariffa Ammie) daga wajen wanki”.
        “Ya rabbi, ya jikin nasa?”.
    “Gaskiya yaji jiki sosai, dan har yanzu ma ba'a bari an gashi ba. Motar kuwa tama tashi aiki, dan babbar mota ce ta haye shi”.
      Gaba ɗaya jikin Nimrah ya ƙara sanyi, ita kanta Ruky dake fama da kanta hankalinta ya sake tashi, a haka suka iso gida ciwon marar ya ƙara tsanani, dole ma sai Mu'azz ɗaukarta yayi. Gaba ɗaya hankalin ƴan gidan a tashe yake da hanlin da baba driver ke a ciki, dan mazan gidan duk suna can. Ganin hanlin da Ruky ke ciki kuma duk sai suka maida hankali a kanta. Babu bata lokaci aka kira family doctor ɗin su, da yake ya san matsalarta yana zuwa allurai yay mata....

     Basu sami ganin Baba Driver ba sai ranar Lahadi da yamma. Gaba ɗaya gidan suka shirya suka je suka duba shi. Yaji jiki kam kwari da gaske, amma Alhamdullah yana samun dukkan kulawar data dace. Ga matarsa an ɗakko tana jiyyarsa. Komai na asibitin Kuma su Yaya Ja'afar ne suka biya.
Received at 6:57 PMSosai matar ke godiya akan yanda suka bama al'amarin mijinta muhimmanci, inda wasu ne ko'a jikinsu, ƙilama suce sai an biyasu motar miliyoyin kuɗin data tashi aiki. Amma su bata motar suke ba ta lafiyarsa sukeyi.
        Shima Baba Driver kallonsu kawai yake yana hawaye, dan baya iya magana har yanzu. Su duka sun ɗauka yana kuka ne kawai akan halin da yake ciki. Dan haka Mammah tai masa nasihar haƙuri da tawakkali akan ƙaddara. Kusan awar su ɗaya suka koma gida suna sake jimanta al'amarin. Satin baba driver biyu ya fara samun sauƙi, zuwa yanzu kuma Mu'azz ke jigilar kai su Nimrah makaranta da ɗakkosu kullum. A haka kwanakin tafiyar Mammah da Yaya Ammar suka cika zuwa Egypt ganin likita. A tare suka mata rakiya airport cike da kewa, dan Ruky da Nimrah harda kukan su. Ƙarshe Uncles ɗin nasu suka koma lallashinsu da tabbatar musu ai sati biyu kawai zatai ta dawo. Haka suka dawo gida. Tafiyar Mammah da Yaya Ammar da kwanaki biyar al'amarin karatun Mu'azz ya taso, dole su Yaya Ma'aruff suka fara batun neman driver, dan su basu da isasshen lokaci, wani lokacin ma da ƙyar suke ƙulla sati uku a ƙasar. Ammar yana fama da aikinsa, ga Bilal ma baya ƙasar, ko yana nan aikinsa shima ya ishesa, bazasu so kuma matansu kullum na gantalin kai yara makaranta da ɗakkosu ba, balle Biebah da bata da magana yanzu sai ta project ɗinta. Sunata tunanin ina zasu samu sabon driver mai amana kamar Baba amma sun rasa makama.
    Shawarar kota hanyar Baban za'abi Yaya Ma'aruff ya bayar, dan haka suka amince da hakan. Bayan sun taso kasuwa suka nufi gidansa dake can wani ƙaramin ƙauye, sai dai atanan yankin babban birnin yake. Sun sameshi jikinsa Alhamdullah, sai dai ƙafa data samu nakasa sosai har yanzu anata fama. Sun sake jajanta masa da ajiye masa alkairin da basa gajiyawa wajen yi masa sannan suka sanar masa abinda ya kawosu. Cewar suna son ya sama musu wani drivern mai amana kamar shi dan sun yarda da shi. Da farko shiru yayi idanunsa na cika da ƙwalla. Sai da Ja'afar ya ce,
       “Baba wannan ai ba abin kuka bane. Mun yarda da kai ne da amanar ka shiyyasa muka sake biyowa ta kanka, kuma in ma ALLAH ya baka lafiya muna maraba da dawowarka cikinmu”.
    Hawaye Baba ya share, “Na sani ku mutanen arziƙi ne masu tarin alkairi, har abada kuma bazan manta da tarayyata da ku ba. Amma mizai hana ku cigaba da kai yaran makaranta da kanku?”.
        “Baba bazai yiwu ba, kasan yanda uziriri sukai mana yawa dai, idan muka ce mune zamu kaisu za'aita samun matsala. Ga boko ga islamiyya, ga cefanen gida kai Mammah anguwa da iyalanmu”.
        Baba yay shiru zuciyarsa na kai-kawo, dan yasan bazasu fahimci mi yake nufi ba daman kai tsaye, shi kuma tsoro bazai barshi fitowa ya buɗe musu komai ba kai tsaye, sai kawai yace to su bashi lokaci zai kira a waya. Cikin gamsuwa sukai musu sallama suka tafi. Cikin damuwa matarsa ta ce, “Wai miyasa kake ta musu kwana-kwana malam? Mutanen nan mutanen kirki ne, banyi zaton zasu zo da damuwa kanada damar musu maganinta ka kasa ba”.
       “Ba kasawa nai ba Tabawa, kawai ina duba al'amarin ne dai kawai, kin san yanda rayuwa ta lalace yanzu ba kowa ke raɓarka da ƙyaƙyƙyawar zuciya ba. Ko ni ɗin ma alkairin su da hukuncin UBANGIJI ne ya sauya ni daga dalilin raɓarsu”.
    Cikin rashin fahimta ta ce, “Kamar ya? Ban gane ba malam!”.
    Murmushi kawai yayi bai sake cewa komai ba ya barta da wasi-wasi. Awa ɗaya ba'ayi da tafiyar su Yaya Ma'aruff ba Baba Driver yayi baƙo. Kasancewar matarsa tasan mutum ya saba zuwa wajensa bata kawo komai a ranta ba ta shiga ciki gida ayyukanta ta basu waje. Dan yana jiyyar a ɗakin soro ne...
             “Rabe! Kana ganin taurin kanka zai cigaba da baka nasara ko? Halin da kake ciki bai zame maka aya ba kenan?”.
      Murmurshi Baba Driver yayi mai ciwo, idanunsa cike da ƙwalla ya ce, “Ba darasi ne ban ɗauka ba Ari, ina tausayin bayin ALLAHn nan ne. Wlhy mutanen nan munanen kirki ne su da mahaifiyarsu.
Sannan ya kamata mu yarda ba laifinsu bane akan abinda ya faru baya, shima kansa wanda ake son azabtar da su ta dalilinsa mufa sani rayukanmu ya jajirce wajen karewa, ALLAH ne ya ƙaddara za'a tarwatsa mu a ƙauyukanmu har mu watse irin haka. Hasalima mutanen nan dake munana shi a garemu sune silar faruwar komai akan waɗan can abubuw......”
        “Rabe! Kana nufin wuyanka yayi kaurin bijirema su Oga Dagger ko? Amma kasan minene hukuncin yin hakan a gareka ko? Karka manta kana cikin ƴantattun da aka bama damar zuwa su rayu a cikin mutane har suyi aure su hayyafa cikin ƴanci. Baku san wahala da azabar da mu dake cikin jeji kullum a ɓoye muke sha ba. Mutanen nan da kake ƙoƙarin karewa ance maka kaje kai musu wani abu ne? Information ɗin abinda ke gudana a rayuwarsu kawai akace ka dinga kawowa. Musamman ita wannan yarinyar Nimrah, amma taurin kai yasa ka zauna kana kawowa mutane ƙauli da ba'adi, gashi nan har sai da ka jama kanka zaman guri ɗaya, da da ƙarar kwana ma yanzu wani labarin ake ba naka ba. Ni dai yanzu ga saƙo, Oga Mole da Oga Dagger sunce gobe zasu turo sabon driver ka turashi ga mutanen nan ya maye gurbin ka, zaɓi ya rage naka kayi koka

Please Login or Register in order to submit comment