tayi asarar gudan jininka?" Idanunshi ne yayi jajjur domin bai tab'a tsammanin renin hankalin Nady ya kai har kan mahaifiyarshi ba sai yanzu. Kalaman mai martaba ne ya ke yawo a kanshi. *Ba zaka gane ni'imar da Allah yayi maka da samun mace daga kyakkyawar nasaba ba, sai ranar da ya dace ta rufa maka asiri, zaka gane ba kowacce mace bace zata boye gaskiyar ta baka gaskiyar ta dauki laifinka ba, Ina baka shawara akwai lokutan da zaka so ka ji me yasa na ce haka, don nasan zaka zo domin tambaya ta*
A hankali yake sauke ajiyar zuciya yana jin fadar da Mai Babbar daki take mishi har ta gama sannan ya ce mata. "Allah ya huci zuciyarki. Zan koma massalacin ayi isha da ni!" "Allah ya tsare. Amma daga yau fadar ya kare ka zauna lafiya da matarka ga Abdulhafiz yana zaune da Matarshi lafiya amma kai ka gagara yin abin arziki, ta samu cikin ka saka ya zube don Allah ka kula da rayuwar ta." Gyada kai yayi ya fita a gidan, babban zauren ya nufa anan ya samu Alhaji Mamman Abba yayari, zaune shi ɗaya sai dogarai da suke tsaye a kofar. Yana shiga ya zauna shiru tunda yayi sallama. "Yarima Faris!" D'ago kai yayi kafin ya sauke kai kasa. "An yi maka wani abu ne?" Girgiza kai yayi yana cigaba da kallon kasa. "Ko kai da iyalinka ne?" Duk da baya son ya fada amma kuma sai ta ga kamar Abbansa ne a gabanshi. "Mahaifinka ya gaya min bayan dawowarsa daga inda kake ya gaya min bai ji dadin auren da ka yi ba, na ce ya bika da addu'a ya ce yana yi, amma shi matar ce bata mishi ba. Tabbas ya hango wani amma kuma ya fika gaskiya. Wannan kujeran da kai ya dace, sannan duk wanda za a bawa babu wanda zai iya rike shi da adalci kamar kai, amma kuma." Ya sauke ajiyar zuciya mai dan nauyi ya ce mishi. "Matarka ba zata iya rayuwa da wata mace ba, abu daya nake so daga gare ka gobe za ayi zaman fada zan mika bukatata, Please ka min alfarman karba idan ka ji."
"Me yasa?"
"Saboda ta haka kawai zan iya samun nutsuwa."
"Ni rabin rayuwans a wajen kasar nan nayi taya xan iya fuskantar kalubalen al'umma?"
"Zaka iya idan ka samu right woman a gefenka zaka iya Faris zaka iya na rantse zaka iya sai dai a yadda idanun mai Babbar daki ya rufe bana jin zata bari wata mace ta shiga tsakaninta da samun biyar buƙatarta wanda tana yi ne domin kai."
Abinda ya sa ya fadi haka ko kwana biyu da suka wuce Mai Babbar daki ta kira Alhaji Mamman Abba yayari ta tuna mishi kada ya sakankance akan kujeran koda yau Allah yayi ikonsa akan Attahiru Shehu Yayari tow fa Salmanu Faris yana raye, bawa Salmanu Faris mulki ba abu ne mai wuya ba, amma yana bukatar wata Sarautar gargajiya kafin a bashi na jaha bakiɗaya. Don haka Alhaji Mamman Abba yayari ya shirya wani taro na musamman gobe asalin garinsu Mahaifiyar Mai Martaba Hajiya Maryam garin farin kasa........
*ina mata yan gayu ina mata yan yayi! Tow ku matso nesa ta zo kusa collaboration Tangaza_Perfume tare da Anum∆Luxury Perfume sun zo muku da kayan kamshi gida da na jiki kai ba iya nan ba hatta turaren kaya irinsu.*
Mamoul all colors are back in stock. Mamoul turaren turara kaya. Ga kamshi ga kama kaya da gida. Available in;
MAMAOUL MADINA,
MAMAOUL MARYAM,
MAMOUL BADAR &
MAMAOUL SABAYA. Each one 3500
*New Drop!*
*Nassem Oil – 100ml*
Rich, elegant & long-lasting.
This premium fragrance oil is everything your collection needs — and it’s only *₦8,000!*
*Luxury in a bottle.*
| Own Your Scent, Own the Room*
*Mosuf 50ml Body Spray*
Smooth. Fresh. Long-lasting.
Only *₦5000!*
✨💥
Smell amazing, every single day.
*DM to order!*
*Storm for Him & Her – ₦4,500* each
Fresh, fierce, and made to turn heads.
Whether it’s *Storm for Him* or *Storm for Her*, you’re getting bold confidence in a bottle — just *₦4,500!*
A perfect 50ml to carry your essence wherever you go. Subtle. Powerful. Unforgettable.
Now available: ₦2,300 per piece | ₦27,600 per dozen.
Available Just DM
08130269641
[7/26, 10:02 Safiya] Ramlat Manga41: ROYAL POLITICS 🔥
_An yanka ta tashi_
Ramlat A Manga
Mai_Dambu
TOP-NOTCH SEASON 4
Sadaukarwa ga Auntyna RUKAYYA GOMBE 🥰🤩😍
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/HYpizDjKAkJB4QClSeLTvw
Dakata hajia💃💃💃💃💃 kin Dade kina Neman inda Zaki sai amintattun jaka, da takalma, sarkoki,masu kyau da quality cikin farashi Mai sauki❓
Ina marabtarku zuwa cikin wannan gida tare da kasancewa da juna,wannan gidan na RUMIEE UNIQUE BAG'S GALLARY na budeshi ne saboda na Baku damar siyan jaka,da takalma na Yara Dana manya masu kyau da quality da Kuma saukin kudi cikin aminci daga wajena.masu siyan daya da masu sari duk Muna mataba daku
Muna Kano Muna Tura kaya kowanne state da makotan Nigeria cikin yardar Allah
14
Matawalle or Wali
Hakimin Garin Farin ƙasa.
Shi dai bai ce kome akan zamansu da Nady ba, amma tun wancan case din farko dayawa a cikin gidan sarautar sun san yadda yake rayuwa, sannan sun san yadda take gudanar da rayuwarsu. Haka yasa a gefe guda akewa Mai Babbar daki dariya Musamman Kilishi da da mai bi mata, a duk lokacin da zasu ga Nady tow abin dariya ce a gare su, ba shakka ko shi Alhaji Mamman Abba yayari Uwargidansa Hajiya Barra'u ta gaya masa cewa gaskiya yayi wani abu akan Al'amuran Salmanun Faris, domin magana na zuwa yana tafiya a kunnenta.
"Idan Allah ya kai mu gobe kazo Fada don Allah." D'ago kai yayi ya sake murmushi don ji yake kamar mai martaba ne a gabanshi. "In sha Allah!" Ya fada a hankali, "ka ci abinci kuwa?" Wannan shine lokacin farko da wani ya tambaye shi ya ci abinci bayan Faruq, girgiza kai yayi yana faɗin. "Zan saka mr Brandy ya girka min kafin na koma." "Ko zaka raka ni unguwa ne, idan ba zan takura ka ba?" Murmushi yayi ya ce mishi. "Tow Baba babu takuri."
Kiran sallah isha ya dakatar da hiransu, suka fita massalacin, gwanin ban sha'awa yadda suka jera Alhaji Mamman Abba yayari yana zoyalarshi, shu Kuma sai murmushi yake tayi yana sosa kanshi. "Lokacin kana Yaro kafin ka b'ace, ka sha zuwa wurina da dokinka, ranar da aka yi rashin sa'a dokinka ya mutu kai ta kuka a kofar Fada, a lokacin ni dasu Attahiru da Junaid da Saddam mun tafi wani aiki a garin Farin ƙasa. Ai ko muna dawowa muka samu labarin abinda ya faru ga dokin a gabanka kana sharban kuka." Murmushi yayi har lokacin bai yi magana ba. "Bayan mun saka a tafi da dokin kace kai ba za yarda dokin ba, sai dai a binne, tun daga lokacin Junaidu ya ce, yana maka kallon" kabbaran da aka yi yasa shi kara sauri. Tare da rikon hannun Faris lokacin da suka isa an fara karatun sallah. Haka suka bi sawun baya, bayan an idar suna addu'a, Alhaji Nafi'u ya karaso inda suke. Ko ya manta massalaci suke ya ce. "Mamman Abba yayari shi wannan dan naku bai san line din da zai na tsayawa ba ne?" Kallonshi Alhaji Mamman Abba yayari yayi bai ce kome ba. Zai kara magana Alhaji Mamman Abba yayari ya ce mishi. "Muna masallaci ne kuma dakin Allah ne." Shiru yayi har suka gama addu'a wani mutum ya mike yana niman taimakon bayin Allah su taimaka mishi kudin da za ayi wa yarshi aiki " ciro waya Faris yayi ya kira Faruq. "Na'am!" Ya ce daga bayansa. Juyawa yayi mishi alama da idanu. Nufar mutumin yayi ya ce mishi. "Muje daga waje!" "Tow!" Mutumin ya fada yana bin Faruq. "Nawa ne kuɗin!" Mika mishi takardan yayi, ya amsa sannan ya ce mishi. "Shi kenan!" Ya saka hannu a aljuhunsa ya ciro kuɗin ya bashi wanda yake hannunsa ya ce mishi. "Kana da account?" "Eh" amsar number account din yayi ya tura mishi dubu dari uku, don ana niman dubu dari biyu da shida, kuma a hannunsa ya bashi dubu dari. Zubewa kasa yayi zai yi godiya ya d'ago shi yana faɗin. "Gashi can wanda ya baka ba ni ba ne? Jeka Allah ya bashi lafiya ayi fatan a yi aikin cikin nasara." "Allahumma Amin!" Ya fada yana takewa su Faris baya.
Wurin motar Faruq suka nufa Alhaji Nafi'u ya kai hannunsa ya dafa kafad'arshi. Juyawa yayi ya kalli hannun ya wani haɗe rai ya ce mishi. "Sauke!" Ba musu ya sauke, kallonshi yayi ya ce mishi. "Kana da matsala da ni ne?" "Eh tow babu! Amma maganar gaskiya waye ya baka izinin amso kayan Saddam Ba tare da kayi shawara da ni ba." "Nafi'u wannan danku ne fa, akan me zaka saka shi a gaba da irin wannan maganar!" "Faruq kai Baba Mamman motar bari na zo!"
"Tow Yallabai!" Shiga motar suka yi, Faruq wurin zaman drive. Alhaji Mamman Abba yayari a baya, gyara mishi necktie dinsa yake a hankali ya wani tsuke mishi wuya sai da ya fara tari. "Wayyo Allah sannu!" Da sauri ya ja da baya. Sak lokaci guda ya juye mishi Attahiru Shehu Yayari, shi ne ya tab'a mishi irin wannan abin. "Sannu n gyara maka ne." Ya sake matsawa gaban Alhaji Nafi'u ya kai hannu zai tab'a rigarshi. "Kada ka sake ka tab'a ni!" Rike rigar yayi ya wani haɗe botirin rigar da karfi sai da Alhaji Nafi'u ya ji amai ya zo mishi. "Sannu Baba Nafi'u ana motsa jiki. Batun iyalin Saddam T Jatau na dauki responsible dinsu. Yatsa ka nuna musu zamu samu matsala. Ni ba Attahiru Shehu Yayari ba ne sannan ni Ba Junaid Gobir bane, kawai kayi harkan gabanka nayi nawa, ka sake ka shiga harkar akwai matsala." Daga haka ya juya wurin motar ya shiga gaba yana mishi kashedi.
Sai yanzu ya ji kamar fitsarin da yake ji, yana zuba a jikinsa, da sauri ya kira Rilwanu Abubakar Yayari tare da Salama.
-++-
"Baba Mamman ina zamu je?"
"Gidan Malam Junaid Gobir!" Sai lokacin Faruq ya kalli Faris, bai ce mishi kome ba amma kuma yasan sun yi kuskure kin shiga maganar Malam Junaid din. Gidan suka isa, kiran wayar Malam Junaid Alhaji Mamman yayi bayan sun gaisa ya ce mishi. "Gamu a kofar gidanka!" "Tow ku shigo mana!" Buɗe musu get aka yi suka shigo, sannan suka shiga da motar. Malam Junaid yana tsaye, "sannunku da zuwa." Ya fada yana kallonsu. "Sannu ya mai jikin?" "Suna asibiti da Asma'u!" "Allah ya bata lafiya!" Suka shiga parlourn baki da yake harabar gidan. Fita yayi ya shiga cikin gidan wurin Maluma aka shiryo abinci a manyan tire, Iram da ita kanta Maluma. Idanunta ya sauka akan Faris da yake zaune yayi irin zaman raƙumin nan, a gaban Abbansu. Ajiye abincin tayi ta sake fita ya kawo wasu kayan, idanunta yana kanshi. Ta ajiye Malam Junaid ya ce mata. "Ki tawo da Hajja zasu gaisa."
"Tow Abba!" Ta fada tana kallon Faris da bai san tana yi ba, can kuwa sai gasu tare da Hajja, tana mita. "Yarinyar nan anya zaki ga Ma'aikin Allah? Don rashin mutunci kai na zaki tsaya kerere kamar Mamar maza ki ce nazo na gaisa da baki idan naso Junaidu yarka ba zata kashe ni ba, gara ayi auren na wuce inda nafi wayo wannan yarinyar idan ba aure ka mata ba ka shiga uku yarinya sai rashin kunya take fesawa kamar wacce aka yi mata hakila da bunsuru." Ba iya Malam Junaid da Atta Alhaji Mamman da su Faris sai da suka dara. "Na dai gaya maka ka shiga tsakanina da yarka." Daga haka ta juya ga Alhaji Mamman Abba yayari, "Wa nake gani kamar Mamman dilu!" Murmushi yayi ya ce. "Hajja Abu, me wanka da zinari." Murmushi tayi tana faɗin. "Masha Allah, Ashe kana nan?" "Eh Hajja mun zo cin abincin ne ma!" Ya fada yana dariya, sun gaisa sosai, sannan ta fita abincin ne a gabansu tuwon dawa ce jar dawa tayi kyau ta sha kanwa, sai miyar kubewa wanda ya ji tantakwashi kore shar, ga miyar stew a gefe sai pepper chicken, tashi Malam Junaid yayi ya basu wuri. Cikin gidan ya nufa ya samu Maluma tana faman hada kunun aya. A wani babban jug da kananun cup dinsa, ta saka a ture tana biye da shi.. har parlourn bakin ta mika mishi, yana shiga Faruq ya mike tare da amsa ya ajiye. Sai da suka ci sosai. Shi kanshi Salman din sai yaji ya samu nutsuwa sosai. Wanke hannu suka yi, Alhaji Mamman ya ce musu. "Ku dan bani wuri!" "Tow!" Suka fito waje, tare da shiga mota suka zauna.
Kallon Malam Junaid yayi ya ce mishi. "Na jajjanta maka abinda ya faru ya yarinyar da jiki?" "Alhamdulillahi, ni yanzu tsorona kada wani abu ya biyo baya, domin kamar akwai abinda ya faru a can don nasan ba haka take ba, sannan maganar aurenta da Matawalle don Allah ka janye, ba zan boye maka ba, ina cikin tsaka me wuya."
"Ba kome dama ban kai ga sanarwa ba, magana nazo da shi, Yaron nan ina son na bashi mukaminsa, kamar yadda Uwarsa ta bukata tow amma babban damuwata shine kafin nan mutanen fada ba zasu yarda ba, shine nake son na.nad'a shi Matawalle hakimin Garin Farin ƙasa." Shiru Malam Junaid yayi tare da rufe bakinsa ga samu ga kwanan yunwa. Amma sai ya danne haka a ransa ya ce mishi. "Kana tsammanin mutanen Fada zasu amshi haka?" Gyara zama yayi ya ce mishi. "Zasu amsa kai, sannan naso ya auri yarinyar nan ba don kome ba. Sai don ya samu nutsuwa domin karfin hali ne da hakuri ya saka bai nuna gazawar iyalinsa ba, amma lamarin yana buƙatar wani abu sosai ka fahimce ni."
"Na fahimta! Allah yasa a dace." "Amin Ya Allah, ina son kafin a gama tsayar da magana xan je naga halin da yake ciki ne!" Inji Alhaji Mamman Abba yayari. "Allah ya kai mu!"
Haka suka yi ta tattauna har suka gama sannan suka yi musu sai da safe. Ya dawo cikin gidan ya zauna Hajiya Turai ta shigo ta zauna tana faɗin. "Ka janye maganar auren Iram da wancan tsohon kwanon ko sai na fitar da videon irin watsarwa da Ikhlas tayi a Dubai?" "Na amince !" "Waye ya zo na ga iram ta ce ya mata!" "Nan ne kuma baki isa ba duk abinda zaki yi sai ki amma batun wanda yazo baki da hurumi a kai!" Tab'e baki tayi tana faɗin. "Kai ka sani sai ka ji da yarka karuwa wacce ta bar gabanka ta je tayi abinda take so!"
Sam bai ji zafin abin da ya faru ba, sai dai ya san idan Ikhlas taji abinda ya faru zata ga kamar don abin da ya same ta yasa aka juya auren zuwa kanta wanda shi bai yi haka don barazanar Turai ba, yana da makasudinsa nayi haka
+---+
Alhaji Nafi'u
Shafa wuyarshi yayi yana kallon kanshi. "Ka kashe min Attahiru ka kashe min Attahiru!"
"Kashe Attahiru ba zai samu ba, dole sai dai idan za a dawo da shi gida, idan ba haka ba ba zai tab'a mutuwa ba." "Inji Salama, domin shi ya yarda da cewa matukar Attahiru Shehu Yayari yana wata duniya ba zai mutu ba. "Zai mutu mana, zai mutu mana ku nimo min kayan Junaidu ku kawo min mutuwa fa sai ya mutu."
***
Koda suka isa gida kai tsaye ya wuce dakinsa, ya rufe ya bar key a jikinsa. Yasan zata biyo shi. Amma yayi banza da ita domin yana son ta takura mishi. Haka yasa tayi ta buga kofar amma yaki bude mata.
Washi gari bayan ya karya sai dai ba karya abincin jiya ya tashi kansa.
Cikin farar yadin menless ya shirya ya nufi fada, ba karamin ado ya cab'a ba, tunda ya isa ya zauna kanshi a kasa Faruq yana bayansa, "gyara kintsi!" Duk suka zube sai da Alhaji Mamman Abba yayari ya shigo, ya zauna suka mike kowa ya zauna, aka fara gudanar da fada da abubuwan da ake kafin Alhaji Kabir Hammud Yayari galadiman Zanzabira ya bude takarda da yake nuna bukatar niman Izinin bawa Salmanu Faris sarautar Matawalle hakimin Garin Farin ƙasa.
"Akan me za a bashi sarauta har biyu? Wato don an bawa Ahmad Rilwani Yayari,Ci garin zanzabira hakimin kudu?"
"Eh tow me ye a cikin? Shima sai a bashi Matawalle tayi mishi kadin, a bashi Walin Zanzabira, likita ne kuma ɗan kasuwa ne uwa uba mai tausayin talakawa da matasa idan aka ce ba za a bashi anyi kuskure, tunda aka bawa wanda bai da amfani ma balle wanda yake taimakawa al'umma, a saka rana ayi nadin Sarautar." Hannu Alhaji Mamman Abba yayari yayi tare da tura sakon ga gwamnatin Zanzabiran.
Kafin a tashi a fadar sakon approved ya dawo daga Mai girma Gwamna Musharraf, da wannan labarin ya isa cikin gidan dangane da bada Sarautar da aka yi kuma ayi bikin bada Sarautar nan da wasu kwanaki..
***
Ikhlas
Bana ce rayuwata tana gari ba, amma tunda na dawo na samu nutsuwa domin babu tashin hankali. Sannan ina samun kulawa sai dai yadda abin ta faru shine maganata da In-in-ina a cikinsa idan ina son nayi magana mai tsawo sai na sha wahala, haka yasa Abba ya ce a daina min magana a bar ni kawai.
Kwanana goma aka sallame ni, muka dawo gida a lokacin ne na samu labarin an fasa auren Iram da ni za ayi, a yadda Abba yake rarrsshina yasa nayi ta kame zuciyata ni ko Matawallen ya bani don nasan ba tsoho bane akan mai martaba da za a yi ta cewa saboda kwadayi na aure shi kuma taya za ayi wannan auren bayan ba matansa hudu. Haka yasa na dami kaina, sannan a haka na koma makaranta domin mun gama attachments da muke yi, koda na dawo nayi sanyi, sai yasa bana shiga kome sai karatu.
Satina biyu
Ina zaune ni daya a kasar bishiya. Wayata tayi ƙara, dubawa nayi naga sako ne.
*Naji ana shirin miki aure da wani ko? Tow ki sani ba zan tab'a kyale kowaye ba! Ki gayawa iyayenki kin na biya sadakina kuma ina kallonki*
#Dracula
Sake wayar nayi tare da rike wuyata da naji kamar an shake min shi na fara niman numfashi. Yadda nake kokari kama kwace kaina, yasa wasu yan department dinmu suka hango ni, koda suka iso na zube a wurin sumammiya. Haka aka dauke ni sai asibitin makaranta.
Sai da na kwashe awa uku sannan na farka, Abba na gani zaune yana kallona ya shafa kaina. "Sannu kin ji ya jikin?" A hankali na ce mishi. "Da sauki sosai!" "Allah ya baki lafiya!"
"Amin Ya Allah!" Na faɗa.
"Zainab akwai wani da yake razanaki ne?" Zuwa mishi idanu nayi kafin na ce mishi. "A'a Abba!" "Amma ance an ga kamar an shake ki ne kina ta niman numfashi."
"Abba babu! Kasan wuyar akwai ciwo har yanzu!" Tuni na fara In-in-ina, ganin zan ta marin kaina yasa shi rike hannuna. "Ya isa na fahimta."
Gyada kaina nayi hawaye na zuba min.
"Wannan shine ƙaddararki, ki amshe shi da zuciyarki Allah zai kawo miki mafita, idan kika ga magana zai baki wahala ga wannan ki rubuta min kome zan karanta ba zan gaji da karanta rubutunki ba kin ji!" Hawaye ne ya zuba min na amshi jotter din wanda aka mishi ado da hoton Snow white. Murmushi nayi hawaye na zuba min.
"Na gode sosai Abba!"
Cire min ruwan aka yi muka tafi gida da shi.
***
Juma'a
Aka tashi da bikin nadin Sarautar Salmanu Faris, har zuwa yau babu shiri a tsakaninshi da Nady, amma kuma maganar gaskiya ta kashe kudi me sunan kudi domin ranar yau hidimar da ake ba karamin hidima aka yi ba.
Wannan abun ya batawa Alhaji Nafi'u rai, ya saka Musharraf yayi ta mishi fada da cin mutuncin kamar zai dake shi. Haka ya bar gidan, bai ce mishi kome ba.
A ranar da aka yi nadin Sarautar, abu biyu ya samu mai Babbar daki murnan bawa Faris sarauta,na biyu kuma sabon rasuwar mai martaba.
Wannan abun ya matukar girgixa kowa, amma Alhaji Rilwanu Abubakar Yayari da Alhaji Nafi'u sun ji farin ciki. Kafin a kai ga an labarin ya bazu ko ina aka fara taya Alhaji Rilwanu Abubakar Yayari murna zai zama sabon sarki. Wannan rasuwar ta daki Salmanu Faris domin yana shirin tafiya kenan visar ce take da matsala
Mafarin
A wannan duniyar kome yana da farko kuma yana da sanadinsa. Sannan duk wata gwagwarmaya tana buƙatar sadaukarwa mai girma ko karama.
Asalin masarautar Zanzabira, masu rike da ita wasu kabilu ne masu suna Yazuwa, kabilun Yazuwa sun ki amsar Muslunci har ta janyo aka yake su, wanda sanadin haka aka bawa Alhaji Muhammad Inuwa Yayari, bafulatani ne kuma dalibin Mujaddadi Shehu Usmanu danfodiyo, wanda haka ya sa masarautar ya kafu a tunanin fulanin Yayari. Shekaru yana tafiya ana mulki cikin adalci wanda bakiɗaya zuriar Yayari ke rike da wannan muƙamin.
Malam Yunus Gobir shima wani babban muridin malami ne wanda yayi zama na tsawon shekaru talatin a kasar Saudiyya, domin haka dawa'a ya kawo shi har zuwa Zanzabira daga yakinsa na Nijar. Dayawa suna danganta shi da Sharifi ne amma dayawa sun fi bashi cewa bagobiri ne, kasancewar sunanshi yana amfani da Gobir. A lokacin da yazo ya isa har fada domin bayyana kanshi a matsayin malami da ya fito daga yankin Nijar har zuwa kasar larabawa. Haka yasa aka amshe shi hannu bibbiyu.
Malam Yusuf shima ya kara kafa babbar majalisar ilimin addini muslunci a Zanzabira har zuri'arsa suka gado ilimin tare da kara karfafa kansu a matsayin wanda addini yake zagaye da su, amma manoma ne domin ko zuwansa an ganshi da Rakumai kusan garke biyar shanu ma haka,da sauran kananun dabbobin.
A gefe guda akwai Zuriar Shaiba, wand sunan asalin mai tarihin Khalid Shaiba, shi ɗan kasuwa ne daga wannan kurmin zuwa wancan, shima ya kafa nashi zuriar, domin attajiri ne na gaske.
Daga nan aka cigaba Jatau, Jatau babban mai ajiyar zanzabira ne domin su wani abu na ya danganci ajiyar da sauransu shine akan gaba,har ya kafa nashi Zuriar.
Ana yasan musu kirari da cewa.
*Idan mulki kake kake takama da shi, tow kuwa ka nime zuri'ar Yayari, idan ilimi kake ji da shi baka kai gidan Goburawa ba, idan arziki kake ji da shi tow ba na dayan gidan Shaiba,haka idan amana da rikon gaskiya ne ba za a kuma samun irin gidan Jatau ba!* Wannan kirarin.wani mawakin falsafa ne yayi musu.a wani karni da ya shude.
Wannan hadin ya kawo wani irin amana da yarda da juna. Musamman Sarkin lokacin da ya yarda da waɗannan mutane ukun haka yasa suka bawa Gidan Yayari kariya.
*ina mata yan gayu ina mata yan yayi! Tow ku matso nesa ta zo kusa collaboration Tangaza_Perfume tare da Anum∆Luxury Perfume sun zo muku da kayan kamshi gida da na jiki kai ba iya nan ba hatta turaren kaya irinsu.*
Mamoul all colors are back in stock. Mamoul turaren turara kaya. Ga kamshi ga kama kaya da gida. Available in;
MAMAOUL MADINA,
MAMAOUL MARYAM,
MAMOUL BADAR &
MAMAOUL SABAYA. Each one 3500
*New Drop!*
*Nassem Oil – 100ml*
Rich, elegant & long-lasting.
This premium fragrance oil is everything your collection needs — and it’s only *₦8,000!*
*Luxury in a bottle.*
| Own Your Scent, Own the Room*
*Mosuf 50ml Body Spray*
Smooth. Fresh. Long-lasting.
Only *₦5000!*
✨💥
Smell amazing, every single day.
*DM to order!*
*Storm for Him & Her – ₦4,500* each
Fresh, fierce, and made to turn heads.
Whether it’s *Storm for Him* or *Storm for Her*, you’re getting bold confidence in a bottle — just *₦4,500!*
A perfect 50ml to carry your essence wherever you go. Subtle. Powerful. Unforgettable.
Now available: ₦2,300 per piece | ₦27,600 per dozen.
Available Just DM
08130269641
Top_notch season 4 ROYAL POLITICS is not free, pay N500 to get a complete access to the book.
*Marubutan TopNotch Writers sun sake zuwa muku da sabon labarai masu ƙayatarwa a tafiyarsu ta Season Four:*
*MAI_DAMBU kuwa ta faso muku ne da labarin da ya haɗa da Sarauta, Siyasa da kuma Soyayya, duka a littafin ROYAL POLITICS: An yanka ta tashi.*
*AZIZAT kuma ta tattaro muku rikitacciyar soyayya ne da ya hawo jirgin JayKay ya dira a Kitchen ɗin Ziyada. CHEF ZEEY: Love in the Kitchen*
*Account Details:*
*5921536136*
*RAMLAT MANGA ABDULRAHMAN*
*Moniepoint MFB*
*POSTING*
*Ɗaya: 500*
*Biyu: 1000*
*Uku: 1500*
*DOCUMENT (da zaran an gama posting zai koma)*
*Ɗaya: 1k*
*Biyu: 2k*
*Uku: 3k*
domin tura shaidar biya ko Ƙarin bayani, ku tuntuɓi:
*08130269641*
Ko
*08137311900*
Ko kuma
*09063467258*
[7/26, 10:02 Safiya] Ramlat Manga41: ROYAL POLITICS
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 13