Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 6
ce, "Allah Ya sa hakan, amma tabbas Shamaki ya yi fushin da bai taɓa yi ba, ya yi furuci a gaban kowa furicin da bai taɓa yin irinsa ba. Ya jawowa kansa bala'ai da tsinuwar ubangiji ta tabbabata akansa in har ya kara zama da ni, yace ya hakura da ni in har ya cika dan halas a cikin uwarsa da ubansa. Na shiga uku na lalace Nasrin yayazan yi?" Nasrin ta girgiza kai ta matse hawaye ta ce, "kada ki damu, ki je kiyi ta addu'a, kuma ba da baki za ki fada musu kin shiryu ba 124 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 kamata ya yi su gani da idanuwansu su tabbatar kin canja sai su tausaya miki su yafe miki.' " Malaika ta surnano da hawaye ta ce, "ki yafe min Nasrin na jawo miki zargi da zagi a wajen Shamaki da iyayena. Gaba ɗaya suna zarginki da ke kika hure min kunne har suna kiranki da karuwa mai zaman kanki." Nasrin ta girgiza kai ta ce,"ba komai Malaika na yafe miki, na yafe musu suma kuma In sha Allah za su gane gaskiya." " Nasrin ta dauko kudi naira na dukan Naira dubu ashirin ta bata ta ce ta je ta yi jari, sannan ta dauko mata kaya kala uku masu kyau a cikin nata da take sawa ta bata, da yake kirar jikinsu daya. Malaika ta yi ta godiya matuka sannan suka dingumo suka fito zuwa dakin Zainab suka iske ta a kwance ita kadai. Malaika ta durkusa ta gaishe ta gami da yi mata sallama. Zainab ta yi mata fatan alkhairi sannan suka fito, Narin ta dauki motarta ta kaita tasha ta shiga mota ta zauna, suna dagawa juna hannu suna zubar da hawaye da alama kowannensu tana kukan rabuwa suna kuma kyautata zaton a 125 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 yau wannan rabuwa ta su itace ta karshe ba zasu kara ganin junansu ba.. Allah sarki sabo turken wawa! Bayan mota ta cika direba ya tashi mota suka fara tafiya sai Malaika ta runtse ido hawaye zazzafa ya fara kwaranya daga. idanuwanta, kamar daga sama ta ji an mika mata hankici. Tana daga ido sai ta ga mutumin da ke kusa da ita ne ya tausaya ya bata dan ta goge hawayenta. Amma fa ta yi matukar razana a lokacin da ta yi ido hudu da shi, Shamaki ta gani fuskarsa cike da damuwa. Ya kawar da kai gefe dan baya so 'yan cikin motar su fahimci wani abu. Mamaki mabayyani ne yake kwaranya daga fuskar Malaika ta kasa tantance daga in da ya diro. Shin binta yake yi a baya ne ko kuwa Katari aka yi? Shin daman Shamaki ya taɓa zuwa Abuja ko kuwa biyo ta ya yi kawai? Shin sonta yake yi har yanzu ko kuwa so yake ya damke ta da laifi dan ya fadawa duniya koi ta wacece? " Amsar tambayar tana wajen Shamaki sai dai kash! Ba ta ga fuskar jero masa wadannan tambayoyi ba. 126 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 isa garin Kano. Bai ce mata uffan ba itama haka har suka *** *** *** *** Washegari da daddare Zainab da maigidanta Salis suka kai Nasrin filin jirgi na Abuja tare da rakiyar kawarta Dinah. Tabbas Nasrin ta dage sai ta tafi Amerika amma tana ta kuka kamar an yi mata dole, Zainab da Dinah ma suna taya ta yayin da Salis ya dinga basu hakuri amma sun kasa dainawa. Nasrin tana ji a ranta kamar idan ta tafi mutuwa zata yi ba zata dawo ba, haka Zainab ma tana ganin kamar idan ta zo haihuwa mutuwa zata yi ba zasu sake haduwa ba. Bakin cikin Dinah kuwa shine ga aurenta ya zo. ba za'a hada aurenta da na su Nasrin ba dan gaba daya sun gama ɓaɓewa da Fu'ad an rabu. Babu yadda zasu yi dan jirgi baya jira dole suka saki Nasrin ta wuce ciki ta karɓi (boading pass)na tafiya. Tana tafe tana waiwayensu suna waiwayenta suna dagawa 127 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 juna hannu, yayin da hawayen da yake kwaranya ya yawaita. Allah sarki rabuwa ba mutuwa ba! *** *** *** Nasrin ta shiga cikin Jirgi ta zauna kafin a gama shigowa ta jawo wayarta ta kira Dr.Jalo, tana jin muryarsa sai ta fashe da kuka. Shima kukan yake yana mai yi mata nasiha akan ta zama mai hakuri da tawakkali. Ya shaida mata yadda yake ji idan ya tuna rayuwarsa ta baya a lokacin da yake da lafiya yana takawa kamar kowa dan haka kada ta zamanto mai yiwa Allah butulci dan Ya hada su kuma Ya raba su a sanda Ya so. Ya yi mata fatan alkhairi itama ta yi masa amma ta roke shi da ya bar cikin dajin ya koma gida ko asibiti, bata jin dadi idan ta tuno irin masifar wahalar da ta baro shi a cikin dajin nan. Ya yi mata alkawarin za su koma gida su zauna su jira ranar da Allah (SWA) Zai yanke musu wannan wahala itace ranar da Allah Zai dauki rayuwarsa. Ya na da tabbacin mutuwa ita kadai 128 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 ce hutu a gare shi. Kuka ya hana su ci gaba da yin waya sai ta katse. Ta kira Mahaifiyarta ta shaida mata har ta shiga jirgi idan sun karaso a zo a dauke ta a filin jirgi. Hakika Momi ta yi farin ciki da jin haka ta yi mata fatan Allah Ya kawo ta lafiya. Daga karshe ta kira Dr.Hala ta shaida mata yau zata koma Amerika, tana fatan idan ta shigo kasar zata neme ta. Dr. Hala ta yi alkawarin yin haka ta yi mata addu'a gami da fatan alkahairi. Ta na kashe wayar sai ga kiran Dina, Nasrin ta amsa da sauri, Dina tana Magana cikin lallashi ta ce "Nasrin! Ki yi hakuri idan kin je ku daidaita da Fu'ad ku yi aurenku. Kin ga wanda kike so din ya nakasa ba yadda zai yi ya aure ki, Fu'ad ne kadai ya dace da rayuwarki shine wanda za ki ji dadin zama da shi dan hutu ke ma 'yar hutu." Nasrin ta fusata ta ce, "Dinah, Wai shin kin manta ko waye Fu'ad? Kin manta cin mutunci da rashin kulawar da yake yi min? Kin manta da cewa idan na aure shi bakin ciki zai tula min saboda girman kai da ji da kan da N. 129 Jamilu Umar Tanko JUT 1 DAMA NI CE...2 yake yi min? Kin manta da tulin 'yan matan da yake da su a turawa da bakaken fata amma duk da haka ki ce in aure shi? Ba ruwana da abinda yake da shi in har ba ni da kwanciyar hankali da farin ciki a ransa. Allah shi Ya san dalilin da Ya hada ni da Jalo kuma ya raba mu. Allah Shi yasan dalilin da Ya mayar da Jalo nakasasshen da ba zai iya moruwa ba. Na rasa nutsatstsen saurayi, mai kamala da sanin ya kamata. Na rasa wanda na ke so kuma wanda yake sona. Kawata! Ki yi min addu'a Allah Ya ba mu yadda za muy da ni da Jalo amma ba Fu'ad ba." Dina ta yi kasake tana gasgata maganar Nasrin ba tare da tana da bakin gyarawa ba. Ta yi ajiyar zuciya ta gyada kai ta ce, "haka ne kawata, Allah Ya bawa Jalo lafiya Ya zaɓa miki abinda ya fi alkhairi a rayuwarki. Ina yi miki addu'a Allah ya kai ki gida lafiya ki same su lafiya. Ki gaida Mummy da Daddy dan Allah." Nasrin ta ce "zasu ji. Amin. Na gode. *** *** 130 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE2 Jirgi ya lala sama yayin da Nasri ta rutse ido sai hawaye ya surnano mata, kamar daga sama ta ji an nanika mata hankici a hannunta tana bude ido ta dubi mutumin da ya ke zaune a gefenta ne ya bata, tabbas ta firgita ta gigice a lokacin da suka yi ido hudu da Fu'ad. A Sai ta zazzare ido saboda mamaki gami da fargaba mai tsanani. Da alama yagama jin wayar da duk ta yi da su Jalo, ya gama jin wayar da ta yi da Dinah. Sedeg nen sonsand Ta dube shi sai ya yamutse fuska ya kawar da kai gefe ya sha kunu ransa a ɓace. Lallai dole ransa ya ɓaci da jin irin wadanan munannan kalamai da ta furta akansa.(TUL) Abin tambaya shine caman Fu'ad yana kasar amma bai zo ya neme su ba kuma bai faɗawa kowa yana nan ba? Shin me ya kawo shi kasar, uzurinsa ne ya kawo shi ko bibiyarta yake yi? Rigiji gafji! Wani kaya sai amale! Basu kara cewa juna uffan ba har suka isa kasar Amerika. 131 | Jamilu Umar Tanko JUT Txost rem!! ulims!| DAMA NI CE...2 Kash! Anan zan dakata mu hadu a littafin DAMA NI CE... Kashi na 3 Mu ji yadda zata kasance. *Tsakanin Nasrin da Dr.Jalo *Tsakanin Malaika da Shamaki da Iyayenta. *Tsakanin Nasrin da Fu'ad. *Tsakanin Nasrin da Mahaifiyarta. *Yaya rayuwar kasance nan gaba? kowannensu zata Ku biyo ni ku sha Labari. Ta ku har abada Jamila Umar Tanko. (JUT) DAMA NI CE...2 A DADE ANA YI SAI GASKIYA. Ina makaranta da 'yan kasuwa? Ina masu sayen daidai ko sari? Inamasu neman littattafan JUT gaba daya tun daga kan 'KWANA ASHIRIN DA HUDU' zuwa 'DA MA NI CE' marmaza ku garzayo shagona mai suna 'ADON DAWA BOOKSHOP' da yake layin layin ''yan littatfai littatfai SABON GARI KANO. KASUWAR Farashi cikin sauki. Abubakar akan A tuntubi wannan lamba 08060267571 domin neman karin bayani. Sai kun zo. 133 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2. MATA ADON GARI IN BA KU BABU GARI, IDAN KUN YI YAWA GARI YA BACI. *Idan kina neman shawara akan zamanki na aure. *idan kina da matsaloli ta kowanne ɓangare. *Idan ki na da korafi. *Idan mai gida baya jin daidai. *Idan fatar jikinki tana neman gyara. *Idan ki na so ki rike kamshi na ciki da waje. *Idan abubuwa sun motse ki na so ki ciko. *Idan ki na bushewa. *Idan kina so ki zama marubuciya. *Idan ki na neman shawara akan sana'a dan taimakon kanki da kanki. 134 Jamilu Umar Tanko JUT 1: DAMA NI CE...2 MACE SAI DA GYARA Ka da ki bari ki zama bora, ka da ki bari Oga ya raina ki, ka da ki bari kishiya ta raina ki. Yanzu ba'a kishin fada sai dai a yi kishin gyarada kyautatawa Mai gida. Ga wata dama ta samu JUT ta bude kofar ba da shawarwari da bada gudunmawar abubuwan gyara, a tuntuɓe ni a wannan layi 08037196708. TSARABA: Ki nemi tumatur mai kyau ki raba gida biyu ki goga a fuskarki kafin ki shiga wanka. Ko ki matse tumatur a cikin 'peak milk' sai ki goga a fuska da wuya. Ki bari bushe sannan ki murje tas. Idan kin shiga wanka kada ki wanke fuskar da soso, kada ya 135 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 ki saka ruwan zafi idan za ki wanke fuska da sabulu da ruwan sanyi za ki wanke. Za ki ga yadda fuskar zata din ga gyalli kamar tangaran. Fuska bata son jagwalgwalo da yawan taɓawa. Haka a guji dafke-dafken mayuka daban daban a fuska. Masha Allah! Allah Ya sa mu dace. Amin! An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 6 of 6