da hawaye ya fara kwaranya
49 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
daga idanuwansu su dukka. Lokaci mai tsayi
suna kuka sannan ya yi ta maza ya ci gaba da
magana cikin sheshshekar kuka. >
"Hatsarin ya faru ne da yamma ranar
5/10/2006 a wani kauye da ake kira Dingare,
kusa da Yelleman."
"Ya salam" In ji Nasrin yayin data mike
da sauri ta je ta fada akan gado ta danna kanta
a cikin filo ta fara kuka amma wayar tana
nanike a kunnenta.
Jalo ya share hawaye ya ci gaba da cewa
"bayan an taimaka ana cire mu a mota sai na ji
tsoron kar motar ta kama da wuta dan an fara
cire da Salima,sai Hisham, Umar da direba.
Sai ni da Rayyana ne a cikin motar, na hango
ta tana ta motsu-mutsu, nace ta taka bayana ta
yi sauri ta fita, data taka ni sai na ji kamar ba'a
taka ni ba, nan da nan na razana na ce a raina
'ba dai Lakata ce (Spinal cord) ba ne ya tabu.
Nasrin ta tashi zaune tana juyi akan gado
"
zuciyata cike da tashin hankali hawaye ya yi
mata kawanya, duk da bata so ya gane kuka
take amma sai da ya gane.
50 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Ta zabura ta ce, "in sha Allahu ma
lakarka ba ce ta taɓu ba."
"
Ya yi murmushin karfin hali yace,
"Nasrin kin manta labari nake baki? Abinda ná
ke fada ya dade da faruwa ai. Koma meye ki
bari in kai karshen labarin mana."
Ta amsa a gigice "to ina jinka."
Ya ci gaba da cewa "Da aka daga motar
na yi iya kokarina in fita na kasa sai da aka ciré
ni. Na ji kamar an raba ni gida biyu ‘innalillahi
wa inna ilaihi raju'un' shi kadai na ke Ambato.
Abu kamar wasa sai gamu a asibitin Hadeja, da
suka duba ni suka ce ya fi karfinsu sai aka tura
mu asibitin Aminu Kano, satina uku anan
suka tabbatar mana da cewa abin ya fi
karfinsu.
"
Nasrin ta fasa kuka ta ce "Innalillahi
wa'inna ilaihi rajun. Dakta me ke nan?"
Ya surnano da hawaye ya ci gaba da
cewa "Mahaifiyata ta na jin labarin na yi
hatsari sai ta mike ta nemi ciwonta ta rasa ta
bazamo asibiti wajena, a cikinsu ni kadai ne na
ji ciwo ana tsaye akaina."
51 Jamilu Umar Tanko JUT.
DAMA NI CE...2
Jalo ya kasa ci gaba da labarinsa saboda
kuka ya kashe waya. Ta yi ta kira bai dauka ba,
haka ta kwana bata rintsa ba.
*** *** ***
Kwananta biyu tana zagaye a cikin gida
cike da damuwa Jalo bai kunna wayaba sai a
rana ta uku da sassafe ta kiransa. Ta cika da
mamaki jikinta na rawa ta amsa. Ya bata
hakuri ya ce ta yi masa uzuri rashin caji ne ya
same shi ba da gangan ya kashe wayar ba.
Ta yi mamaki yadda caji zai gagare shi
har tsawon kwanaki biyu kamar wani dɗan
karkara.
ya
Tambayar da ta yi masa ita ta bashi
mamaki ta ce ya faɗa mata in da yake gata nan
zata zo. Kafin ya bata amsa ta dinga yi masa
magiya har sai da yaya ji hankalinsa tashi. Ta
ce ya turo mata cikakken adireshinsa. Sun ajiye
wayaba dadewa ta ji sako ya shigo tana
dubawa ta ga adireshinsa ya turo mata, tana
karantawa ta ji hankalinta ya yi mummunan
52 Jamilu Umar Tanko JUT
by DAMA NI CE...2
tashi ta firgita ainun. Ta fara tunanini ta in da
zata fara wannan bulaguro.
Kamar da wasa ta fita a gigice ta fadawa
Zainab cewar zata je Bidda dubiya.
Zainab ta shiga jero mata tambayoyin
data kasa amsawa. Amsa daya ta fada mata ita
ce wajen Jalo zata je ya yi hatsarin mota.
Ta koma daki ta hada karamar jakar
kayanta ta fito, Zainab ta yi tagumi tana
kallonta ta zo ta wuce ta, direba ya kaita tasha
ta shiga motar haya.
DAMA NI CE...2
l of si
BABINAGOMASHADAYAW ME SE
_BIDDA w donics
niyovi diunt,sand, onoj
ali
N
asrin bata tsaya a ko inaba sai a
in da Jalo ya fada mata. Ba zatoCS
ba tsammani Jalovaya jiyo
muryarta a kofar dakinsus oli simsynd
Ya gigice ya ma rasa vad yadda zai fadawa
Mahaifiyarsa sai ya cika da mamaki da ya ji Mama ta ambaci sunan Nasrin radai. Ashe tana
.
biye da su tana Hankalin jin hirarNasrin dwaya yasuke yi yi a matukar tashi a
lokacin da ta ga mutuminta a cikin wannan
hali, bata taɓa zaton abin har ya kai haka ba.
Nasrin a durkushe a gaban Jalo yana kallonta tana kallonsa cike da Mamaki. Kanta ya daure
ta kasa gane abinda yake damun Jalo gashi dai a zaune sanɓal amma baya iya tashi. Bayan ta yi sallar azahar ta ce ya bata
labarinsa tana so ta san komai. Mama ta tashi
ta fice ta je karkashin bishiya ita da wata mata
da suka saba suna hira.
54 Jamilu Umar Tanko JUT TULT a list 2
DAMA NI CE...2
*** *** ***
CI GABAN LABARIN JALO
Ya yi shiru na dan lokaci yana tunani sannan ya bude baki dakyar ya fara Magana cikin marainiyar murya ya ci gaba cewa, "Na fada miki ina asibiti a Kano sun yi iya yinsu abu ya fi krfinsu.Nan da nan labari ya cika
garin Yelleman kasancewar ni mai jama'a ne, sai Gwamnan Jiharmu na wancan lokacin ya ji labari, ya aiko aka tabbatar masa da jikina sai
ya ce a dauke ni a fita da ni turai, kasar
Germany. Miliyoyin Naira aka ba mu.
Rayyana da Yayanta Bashar su ne suka
raka nican,kudin gaba daya a hannunsu aka damka.'
"
Nasrin ta mike tsaye tana kai kawo a
tsakar daki fadi take "Allah Ya saka sami
lafiya."
Kuka ya ci karfin Jalo na dan lokaci ya
kasa magana sannan ya ci gaba da cewa "Jinya
ta Spinalcode mutum baya iya tsayar da bayan
55 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
gida da fitsari haka nake fama sai dai kawai in
ji ni na ɓaci.'
"
Yana fadar haka Nasrin ta sulale ta
zauna ta dora hannu aka ta fasa kuka ta ce
"Dakta yanzu lakarka (Spinal cord) ce ta taɓu?
Lahaula wala kuwwata illabillah. Mai rai ya
shiga uku."
Su duka sun jima suna kuka kafin a sami
wanda ya iya ci gaba da magana a cikinsu
Jalo yace, "watarana a asibitin muna
zaune da ita na shaida mata jikina ya ɓaci ko
zata taimaka ta gyara ni? Ta kalle ni sama da
kasa sai ta ja Jakarta ta fice ta bar ni a zaune,
da aka jima sai ga ma'aikatan jinya mata su
biyu sun shigo. Suka tambaye ni wai matar da
ta fito daga ɗakin nan ta ce su zo ina da
damuwa. Na fada musu su gyara ni jikina ya
ɓaci, bayan sun saka safar hannu suka gyara ni
sai suke tambayata waccan matar wacece? Na
shaida musu matata ce, sai mamaki ya bayyana
a fuskokinsu suka yi Allah wadai da ita, bata
damu ba ita.
Ita da Dan uwanta Bashar siyayyarsu ce
a gabansu suna zagaya gari da makudan
56 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
miliyoyi a aljihun su, ni ina kwance a asibiti.
Masifa goma da ashirin. Ga faca da tsawa da take yi min kullum sai na roke ta data harhada
kayanta ta koma Najeriya bazan iya ci gaba da zama da ita a haka ba, ta bar ni in ji da ciwo da kaddarar data same ni. Daman haka take so ta
kaɗa kai ta yi tafiyarta, yayanta yana ta kwashe mata albarka.
Da ni da Bashar muka ci gaba da zama a kasar Germany, ana ta jinya amma jikin dai yana nan yadda yake, aka sake yi min aiki a karo na biyu ba'ayi nasara ba."
Kuka ya ci karfin Jalo ya kasa ci gaba da magana sai su dukka suka fashe da kuka.
Ya daure ya ci gaba da cewa “Duk da facakar daBashar yake yi a kasar waje da kudin jinya amma ya yi kokari, baya kyama ta, kullum shi yake gyara min jikina ya goge ni, ya fesa min turare ya canja min kayan jikina. Tun da Rayyana ta koma
Nijeriyako flashing a waya bata taba yi min ba,
balle kira a waya ta ji lafiyata, har muka koma Nijeriya.
57 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Bashar a ranar yace zai wuce gidansu
Abuja ba zai zauna da ni ba, na yi zaton
kaunata da yake yi a kasar waje ta gaskiya ashe
saboda kudi ne. Na yi kuka na share hawaye na
ci gaba da zuba ido in ga yadda Allah zai yi da
ni.
"
Nasrin ta girgiza kai ta sharce hawaye ta
ce “Allah sarki. Rayuwa da wuya. Allah Ya
baka lafiya."
Jalo ya gyaɗa kai yace, "Amin
nagode.Babu ruwan Rayyana da ni, koda
yaushe tana cikin dakinta tana kallon setlite
bata kula ni. Sai abokina Muhammad ne yake
zuwa ya gyara ni ya bani abinci. Ko sati guda
banyi bana kira Mahaifiyata ina neman
taimakonta akan ta zo ta yi zaman jinyata dan
matata ta kasa.
Mahaifiyata da mijinta sun
Yelleman tun wannan rashin lafiyar bata koma
Lagos ba, bata da karfi kuma gata a karkashin
wani dole sai ya bata izini zata taho, bayan na
fada mata sai da ta dauki tsawon sati uku
sannan ta zo kafin nan Makwabta suka yı
shawara a kai ni Teaching Hospital na lagos
kauro
58 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
don in sami kulawa, sai suka dauke ni suka kai
ni.
Mahaifiyata da kaninaAbubakar suka zo
dagaLagossuka same ni a asibiti,Mama ce take
wuni da ni da daddare sai ta koma gidana ta kwana, kanina yake kwana da ni. Bayan
tsawon watanni biyu Rayyana ta ce ta gaji da dafa abincin da take yi tana kawo mana asibiti
dan bata son warin asibiti, sai kanina yake
zuwa yana dauka ita ta daina zuwa, duk da
haka ta ce ta gaji da dafa abincin. Abin ya kai
sai MaKwabta ne suke kama-kaman kai min
abinci saboda na zauna da su lafiya.
"Innalillahi wa’inna ilaihi raju’un” kawai
nake kira hawaye kuwa idanuwana basu taɓa
bushewa ba, haka mahaifiyata daga ta kalle ni
sai ta runtse ido ta zubar da hawaye dan
tausayi."
Hawaye ya hana Jalo ci gaba da Magana.
Cikin kalaman tausayi Nasrin ta ke
magana "ka yi hakuri Allah Yana sane da
kai....'
"
Kuka ya hana ta ci gabada magana itama.
59 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Jalo ya ci gaba da cewa "Yau da ba
mutuwa da sai in ce na lalace, ko da a ce jinya
ba ibada ba ce da sai in ce nayi hasarar kai. Na
ga wulakanci dukka-dukka watanina shida da
fara jinya sai dai kawai na yanke shawarar yin
hakurida komai don Shi Allah ba Ya kuskure.
Watarana ina zaune a asibiti sai ga
Rayyana ta shigo da tsohon saurayinta wai ya
zo ya gaishe ni, na yi mamakin ganinsu tare.
Ko dan na zama haka shine ta fara nemo
samarinta na baya, ko daman suna tare ni ne
ban sani baoho?
66
Saurayin ya kalle ni a yamutse ya ki
zama ma yace, yanzu Rayyana haka zaki ci
gaba da zama da wannan mijin na ki? Ai bashi
da wani amfani."
"
Sai ran mabaifiyata ya ɓaci ta fusata ta
ce masa"yaro! Da shi da yake kwance da kai
da ke tsaye waye ya san gawar fari? Abin duk
na Allah."
Ya yamutse fuska ya fice.ita kuma
Rayyana ta tashi ta bi shi a bayansa, suka fice
ni da mahaifiyata muka yi kuka har muka
lallashi kanmu.Kin san ya yi mana haka da
60 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
kwana uku, ya yi hatsari ya rasu a take. Rayyan ta sha kuka a gabana babu kunya.”
Nasrin ta rike kai ta ce "wayyo Allah. Allah abin tsoro ne. "
Jalo ya matse hawaye ya ce, "Kullum
muna zaune a waje daya jiki dai yana nan
yadda yake, sai dai ana ta kawo mana labaran
wajen masu maganin gargajiya aka ce ana
warkewa. Ba mu da zaɓi sai muka tafi Bidda
akwai wani kauyen nufawa mai suna Gayko,
cikin kauye kayayau mota ma bata shiga sai
bukkoki. Daga inda muke da in da ake zuwa
ɗauko ruwa tafiya ce mai nisan gaske haka
abinda zaka saya ma ka ci babu, rogo da gyada
muke ci."
Nasrin ta langwaɓe kai ta girgiza kai ta
ce, "Allahu akbar! Allah Ya sa kaffara ne."
Jalo ya ce, “amin. Sai da gorin
makwabta ya yiwa Rayyana yawa sannan ta nemi kauyen da muke ta zo, da jakar kayanta.
Ta tsaya kawai tana kallon yadda muke
rayuwa tabbas na san ba zata iya ba saboda
rayuwar da muke yi ma a Lagos ta raina balle a
nan. A daddafe dai muka yi kwanaki biyu tare
61 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
da ita. Mahaifiyata ceke ta faman dauko ruwa, har wata Mata mai suna Aisha ta fara
tausayawa tsohuwa, sai ta karɓi jarkar ta je ta ciko mata da ruwa ta kawo kofar dakin nan ta
dan ajiye,kafin Mama ta ta kasafta ruwan
cancanawa muke yi Rayyana ta dauke dukka ta
je ta yi wanka da shi.
Sai Mama ta yi mata magana ta ce,
"yanzu ruwan wankan mutane uku kika dauka
ki ka yi wanka da shi dukka? Alhali ke ba
daukowa kike yi ba,ni ba karfi ne da ni balle in
jido, makwabciya ta tausaya min ta ɗauko min
kuma ki ɓata gaba daya."
"
Budar bakin Rayyana ke da wuya sai ta
ce “eh ba zan ɗauki jarka in je in debo ruwa ba
dan a gidanmu ba mu saba dauko ruwa ba.
66
Sai na shiga maganar nace
Rayyanakada kiyiwa Mama rashin kunya, na
san zamanmu anan ba zai yiwu ba, ki dauki
jakar kayanki ki koma in da kika fi wayo."
Nan da nan ta dauki kayanta ko sallama
bata yi manaba ta juya ta yi tafiyarta. Duk da
halinda nake ciki anaba ni albashina kuma a
ciki nake cewa ta ciri kudin abinci dana
62 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
makarantar yara, amma ta ɓoye bata fadawa iyayenta gaskiya ba, nuna musu take bana bata
komai su suke ta aiko mata da kudi suna
tausaya mata."
Nasrin ta girgiza kai ta cė, "Tir da
halinta, bata ci wannan suna ba Rayyana."
Jalo ya ce, "Ga magani ana ta yi amma
abu sai kara muni yake sai aka kai ni
TeachingHospital na Maiduguri, a inda aka yi
min tiyata na mafitsara."
Nasrin ta dube shi cike da tausayi ta ce
"Allah Ya sa anyia sa'a "."
Jalo ya ce, "toh Alhamdulillah kawai
za'ace. Gidan da nake ciki kinsan na ce
ansayar min zan dinga biya a hankali,Mai
gidan Alaja Allah Ya yi mata rasuwa dan haka
yaranta suna son cikon kudinsu da gaggawa ko
su siyarwa wasu, dan haka sai hankalina ya
tashi na cewa Babanta ko zai saya saboda a
ganina zai iya sayawa 'yarsa Rayyana ko
jikokinsa guda biyu da yake matukar so, wato
'ya'yana. Amma sai ya aiko min miliyan
daya, sannan ya je ya biya masu gida cikon
63 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
kudinwanda suke bina, shikenan gidan ya zama
nasa.
"
Nasrin ta buɗe baki tana mamaki ta rasa
me zata ce.
Hawaye yana kwaranya daga idanuwan Jalo ya ci gaba da cewa "abin ya yi min ciwo
sosai saboda mun yi da wani abokina zai bani
miliyan biyar, kuma sannan ya cika musu
kudin da suke bina. Amma ban damu ba dan na
san ko ba komai dai ba zai kori ‘yarsa da
'yayanta daga cikingidan ba."
Nasrin ta cije baki dan takaici ta ce,
"Allah Ya sawake. "
Jalo ya ci gaba da cewa "Ba'a dade da
yin haka ba sai Babanta ya turo min kannensa
suka zo suka duba ni a Asibitin Lagos. Sannan
suka faɗa min wai yau shekarata daya da
watanni biyar da kwanciyata ciwo, ko a kotu
alkali shekara daya yake bawa marar lafiya
idan ba'a warke ba sai a bada karin watanni
biyu, idan mutum bai sami sauki ba kotu tana
raba aure. Haka alwalina ya saka ni a gaba
yace in sake ta saboda sun daɗe suna damunsa
da maganar saki.”
64 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Nasrin ta zazzare ido tana mamaki, ta
sunkuyar da kai kasa sai hawaye ya surnano daga idanuwanta.
Jalo ya surnano da hawaye ya ci gaba da
cewa "ina hawaye na rubuta mata takardar saki daya, ba kukan rabuwa da ita nake yi ba sai
kukan yadda so saboda Allah ya yi karanci, na kuma tausayawa yarana da muka haifa tare. Rayuwarsu abin tausayi kasancewar
Mahaifinsu na zama abin tausayi.".
ni
Nasrin ta runtse ido ta surnano da
hawaye ta dago ta dube shi cike da tausayi ta
ce, "Allah Ya musanya maka da wata mafi
alkhairi. Yanzu ina Rayyana da yaran suke?”
Ya girgiza kai ya ce, "tunda muka rabu
basu taɓa tunanin kawo min yarana na ganni ba, duk da damunsu da suke yi da maganata."
Allahu Akbar!~
***
Nasrin ta mike tsaye ta fito waje a gigice inda ta ci karo da Maman Jalo ta na laɓe tana
65 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
jinsu ta yi kuka har ta gaji. Nasrin ta rungume
ta suka daɗe suna kuka.
Mama ta sharce hawaye ta ce, "mun
gode da kauna amma ki zo ki koma gida da
wuri kada a neme ki."
Nasrin ta girgiza kai ta ce "a gidan
yayata nake amma na faɗa matazan kwana ana
ta ji labarina ta ji labarin Jalo.".
Mama ta yi shiru tana tunanin yadda
rayuwar 'yar gayun nan wacce babu tabo a
jikin ta zata kasance a cikin kauyen nan.Shin
me zasu bata ta ci? A ina zata kwanta ma. Ta
yaya zata iya doguwar tafiya zuwa rafi dauko
ruwa? Yaya zata yi da mahaukata da kutare da
ake taruwa waje daya idan mai magani ya zo
ganin marassa lafiya?"
Nasrin ta katsewa Mama tunanin da take
yi ta ce, “Mama yanzu me za'ayi in taya ku?
Dauko ruwa ko shara?"
Mama ta kalle ta da jajayen idanuwa
wanda ta sha kuka ta ce, "Babu wani aiki
Nasrin, sai dai muna zuwa dauko ruwa, yanzu
zan je in dauko, ki kula da shi har in dawo."
66 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Nasrin ta ce, “mu je tare Mama idan na
ga wajen sai in ci gaba da zuwa ni kadai ke sai
ki huta.'
"
Mama ta dauki jarka daya ta bata ɗaya
suka tafi, Jalo yana zaune daga daki yana jin su
yana mamakin yadda halin Nasrin ya ke. Ya ji
a ransa dama lafiyarsa kalau da ya sami matar
kirki. Amma ya san komai da sanin Allah Ya
ke faruwa.
Sun sha wahala sosai a tafiya haka a
dawowa har kamar Mama ta fi Nasrin kokari
dan Nasrin bata saba ba ta jigata sosai.Sai da
aka taya ta saukewa wuyanta ya kage.
Jalo ya kwalla kiran Nasrin ta shiga
fuskarta cike da murmushi Ya dube ta ya yi
murmushi yace "sannu da aiki. Kada ki damu
ki zo ki tafi gida na gode da kulawarki."
Nasrin ta girgiza kai ta ce "kada ka damu
zan zauna tare da Mama."
"
Ya girgiza kai yace, "za'a neme ki a
gida."
Ta girgiza kai ta ce, "'yan gidanmu sun
san zan zo nan.
"
67 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Ya daɗe yana tunani ya ce mata "ga
wayarki nan tana ta kara a cikin jakarki."
Ta zabura ta dauko ta duba abin mamaki
sai ta ga sunan Malaika, ta kira ta ya fi sau
goma.
Sai da Jalo ya gane ta shiga wani yanayi
na mamaki.
Ya zabura ya tambaya "lafiya kuwa?"
Ta yi ajiyar zuciya ta ce, "wata kawata
ce."
Ta na rufe bakinta sai wayarta ta sake
yin kugi, tana dubawa ta ga sunan, Zainab.
Bata yi mamaki ba dan ta san ya kamata daman
ta neme ta.
Ta danna sannan ta yi sallama, Zainab ta
amsa bayan sun gaisa. Zainab ta tambaye ta ya
bata dawo gida ba har yanzu?
Nasrin ta yi ajiyar zuciya ta ce, “Kada ki
damu Anti Zainab ina cikin koshin lafiya
kamar yadda na fada miki na zo Bidda
dubaDr.Jalo.'
"
Zainab ta zazzare ido ta ce, "Bidda?
Yaushe zaki dawo?"
68 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Nasrin ta yi shiru can ta ce, "zan kwana biyu. Lafiya dai ko?"
Zainab ta ce, "kawarki ce Malaika ta
dawo ina tsoron zuciyarki nace ta zo ta tafi
kafin ki dawo. Ta ce da gaske mijinta ya sake
ta, gata ma ta taho da takardar saki. Ni fa bazan
iya wannan rigima irin ta ku ba, gata da naci.
Nasrin ta yi tsaki ta kashe waya. "
Zainab ta sake kira sai Nasrin ta kalli
Dr.Jalo ya kura mata ido da alama abinda ya ke
tunani ma daban ne ba ya ma gane abinda suke
cewa. Hakika ransa ya sarkafu da son Nasrin
musamman da ya tabbatar da gaske take sonsa.
Ciwo ne bana karau ba da babu abinda zai hana
ya kasance tare da ita. Ya ji kwalla ta cika
masa ido har Nasrin ta fara ganewa ya na cikin
halin damuwa.
22.
Ta yi murmushi ta mike da sauri ta ce
"yi hakuri minti biyu, zan fita in amsa waya.
Ya gyada mata kai ba tare da ya iya
Magana ba.
Tana fita Mahaifiyarsa ta shigo da
katuwar roba wacce zata zuba kayan kazanta
69 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2 m
idan ta gyara masa jikinsa. Ta kara kofa dan
kada Nasrin ta dawo idanuwanta su gane mata.
Tana can gefe tana amsa wayar Zainab
da Malaika. Idan rayukan Nasrin da Zainab ya
yi dubu yau ya ɓaci, saboda Malaika matsala
ce.
Ta dage ita ba zata koma Kano ba anan
Abuja zata zauna, zawarcinta karakaf a gidan
zata yi har sai Allah Ya bata miji ɗan Abuja.
Zancen karatu da aiki ma ta ke yi.
Idan suka takura sai ta tafi sai ta ɗauki
kuka irin na mutuwa ta ce "ko wanke-wanke ne
su bata za ta yi mata, an tsane ta a gidansu.
Nasrin ta yi wani tunani sai ta ce Zainab
ta bawa Malaika waya zata yi mata magana.
Kuka kawai malaika ke rusawa. Nasrin ta
lallashe ta ta ce shiru su yi
magana.Malaika ta tsahirta da kuka tana
sauraron Nasrin.
:
ta yi shiru
Nasrin ta ce "Malaika! Tabbas kina
kaunata kuma bazan guje ki ba. Sannan ban iya
wulakanta dan adam ba. Kin zame min dole
amma baki zama dolen Zainab ba, tunda bana
70 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
gidan ki biyo ni ki zo ki same ni a Bidda tunda
babu nisa da Abuja.'
"
Malaika ta washe baki ta yi dariyar dadi
ta ce "ina ne Bidda? Gidan wa?"
Nasrin ta yi murmushi ta ce, "Minna
ne.Gidan Gwamna ina tare da matarsa acan zan
kwana biyu.
Ki zo kawai."
Malaika ta ji kamar ta yi ihu dan murna.
Nan da nan ta hau godiya. Nasrin ta ce ta bawa
Zainab waya zasu yi magana.
Zainab ta karɓi waya ranta a ɓace dan ta
gaji da lamarin Malaika da Nasrin.
Nasrin ta yi murmushi ta ce, "ki sa
direba ya kai ta tasha yanzu,asaka ta a motar
Bidda yanzu muna waya har ta karaso in da
nake kada kice mata fa a wajen masu magani
muke."
ta kashe waya.
Nan da nandireba ya kai Malaika tasha
da katuwar akwatinta ta shiga mota.Farin ciki
ya cka mata zuci tana tafe a mota tana murna,
kawai hango ta take a gdan Gwamna ta baje,
sannan ta hango ta a motar Gwamna ana yi
Zainab ta amsa sannan
71 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
mata jiniya. Babu abinda take hangowa sai
rayuwarta ta da Shamaki cikin kunci, yanzu
kuma ta hango rayuwarta yadda zata kasance a
cikin ni'ima.Bata san sanda ta kyalkyale da
dariya ba a bayyane. Har mutanen cikin mota
suka juyo suna kallonta, sun fara tunanin ko ta
zare ne.
Suka isa Bidda, Malaika ta kira Nasrin a
waya ta ce gata a tasha, a turo Motar gidan
Gwamna ta dauke ta.
Nasrin ta ji dariya ta turnuke ta ta toshe
baki ta yi dariya sannan ta ce "ki nemi motar
garin Agay, daga nan ki hau Motar Goyko kina
sauka sai ki tarimai acaɓa ki hau ki bashi
wayazan fada masa in da zai kawo.ki."
"
Malaika ta zabura, ta zazzare ido ta
maimaita ta ce "Acaɓa fa kika ce? Cabdijam!
Au har wasu motoci zan shiga nan gaba?”.
Nasrin ta kunshe baki ta kyalkyale da
dariya ta ce, "ga mu nan a lambun Gwamna,
muna tare da matarsa muna ta shan kayan
marmari, sai da magriba za mu koma gidan
Gwamnati. Ki yi sauri."
72 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
"
Malaika ta yi dariya ta amsa"yauwa ga motar can ma na ji ana cewa Agay."
Ta tafi da sauri ta shige, bata daɗe da
shiga ba ta cika suka kama hanya. Tafiya mai
nisan gaske sannan suka isa. Suna Isa ta kira
Nasrin ta sake tuna mata sunan daya garin
wato Goyko. Malaika ta nemi motar Goyko ta
shiga suka tafi, da ta isa ta kira Nasrin ta ce ta
nemi mai acaɓa ta bashi waya zata kwatanta
masa.
Malaika ta zunɓura baki ta ce "Ga dan
acaɓa ma ya zo,ki kwatanta masa.
Malaika ta mikawa dan acaɓa waya ya
karɓa Nasrin ta yi masa bayani sosai nan da
nan ya gane dan garin ba ɓoyayye bane.
Ya dauko Malaika niki-niki da kaya
suka fara tafiya, ashe ma tafiyar da ta yi ma a
baya wasace lungu da sako sai yanzu suka
surkumo.
a
Hankalin Malaika ya tashi kwarai tun
tana hango hango girman lambun Gwamna
zuciyarta har ta fara hango kabarinta. Ta fara
zargin ko siyar da ita Nasrin take shirin yi.
73 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA
Idan ta kalli keyar dan acaɓa nama
dumu-dumu sai taga ya yi mata kama da ɗan
yankan kai, gashi baya jin Hausa dukka
tambayoyin da take yi masa baya ganewa. Ta kwajiɓa turanci ta ce ya tsaya. Su kaɗai a
dokar daji babu gida gaba babu gida a baya. Ya
shaida mata akwai 'yan fashi a hanya idan ya
tsaya zasu fito su kama su ko su kashe su,
musamman suna ganinta da katuwar akwati.
NI CE...2
Idanuwan Malaika kawai zaka dinga
hangowa a bayan acaɓa, kai kace Mujiya aka
jefa a rami. Salati take yi a bayyane tana kiran
sunan Iyayenta na yanka akan su yafe mata
rayuwarta ta zo karshe. Nasrin kuwa tsinuwa
take sha ba adadi yayin da dan acaɓa yake shan
asharai da tofi a keyarsa. Ta tofa masa addu'ar
aljanu ta ga bai ɓace ba, ta tofa masa ta neman
tsari daga azzalumai ta ga bai razana ba.
Aikinsa yake kawai yana shirga gudu fatansa
ya kaita ya karɓi 'yan canjinsa, addu'arsa idan
ya kaita ya samo masu fita ya fito da su riba
biyu kenan.
Malaika ta kira Nasrin a waya, Nasrin ta
amsa da sauri sai ta ji Malaika tana kuka tana
74 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
yi mata bayanin dokar dajin da suke ketawa.
Nasrin ta kwantar mata da hankali akan ba
guduwa zai yi da itaba haka hanyar take. Gonar
tana karshen garin ne.
Malaika ta ji dan sanyi a ranta, suka ci
gaba da tafiya basu iso ba sai da daddare.
Nasrin tana tsaye a farfajiyar gidan tana
jiransu, sai ga idanuwan Malaika