ta
zo ta durkusa ta gaishe ni alhali ni da
kafafuwana nake takawa. Abokaina suka dinga sha'awar wannan soyayya ta mu suka d: Ingab
ni goyon baya akan in aure ta tana sona kuma
wannan ta tabbata mace ta gari."
Nasrin ta girgiza kai cikė da tausayi ta
ce, "Allah sarki. Soyayya ba karya ba ce.'
"
Jalo ya yi murmushi ya ce, “haka ne
amma za ki sha mamaki nan gaba. Ni dai ina ta
tsoro saboda bana son kai kaina gidan masu
hannu da shuni. Na fi son in koma garinmu in
auro 'yar dangina zata fi yi min biyayya ina
tsoron irin matan nan da aka hadu da su a
Bariki.
26 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Duk halinda nake ciki sai da na shaidawa
Mamana tun ranar farkon haduwarmu da
Rayyana.
'
Na dinga jan abin dan ina so in gama
tantancewa da gaske ina tsoron masu kudi
saboda ni dan talaka ne.
Da gaske tana so na a yadda ta nuna
min ba matsala kuma a shirye take ta yi min
biyayya. Ban ɓoye mataba na shaida mata bana
son auren masu kudi dan ina da nawa ra'ayin
ina da tsare-tsaren da nake so gidana ya
kasance.
Ta nuna min zata yi min biyayya kuma
lahirarta take nema.
Nasrin ta yi kabbara ta ji Payyana ta
burge ta ta sha yabonta.
Jalo "
ya ci gaba da cewa Haka abokina
sulaiman ya dinga karanto min kyawawan
halin Mahaifanta da ita kanta. Har sai da na ji
na gamsu da ita zuciyata ta nutsu.
Ashekarar nagama makaranta na barta a
label2, ina gamawa na fito da aikina aka dauke
ni kyarwa a makarantar kasancewar
sakamakona ya fi na sauran dalibai kyau.
27 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Sai aka fara shirye-shiryen aure dan a
lokacin an sanni a gidansu haka nima kowa ya
ji labarinta a dangina.
Amma abu daya na lura Babanta kamar
baya son auren duk da an shaide shi da kirki
amma ni kamar baya sona ya yi ta wahalar da
mu dakyar dai ya fara kula ni akan bukatata ta
neman auren 'yarsa. Tashin farko ma yace in je
in kawo masa gwaji na kanjamau amma bai ce
mu je mu yi tare da 'yarsa ba, saboda ina sonta
na je na yin na kawo masa. Sai yace in dauko
biro da takarda na dauko na mika masa, yace
sai na rubuta a alkawari na saka hannu akan a
lallai-lallai zan bar ‘yarsa ta kammala karatu
sannan ta ci gaba da karatu bayan ta hada digii
na biyu kuma zata yi aikin gwamnati.
Tun daga nan na tabbatar gidana ba zai
yi karko ba, da farko na ki na rubuta saboda
ina ganin in har baban matata ya shiga juya
gidana akwai matsala sai da jama'a suka taru
suka dinga bani hakuri suna nuna min ba
komai ba ne harkar manya kuma 'yan boko
haka take. Na ga shi matansa uku babu wacce
ta yi degree balle mai aikin gwamnati kuma
28 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
iyayensu basa shiga harkar gidansa, yana da cikakken iko akan iyalansa. Dole na rubuta ya saka hannu nima na saka."
Allah."
Nasrin ta yi ajiyar zuciya ta ce, “ikon
Jalo ya yi murmushi ya ce, "Hmmm! Ai kadan
kika ji ma.Aka yi aure cikin girma daman su ne
masu karfi su suka dauki kusan dawainiyar
auren gaba daya haka na yi iya yina, na samo
hayar Babban gidan da zata iya zama aka cika
mata da kaya amma ni kayan daki ba shine aka
burge ni ba fatana ta yi biyayyar aure."
"
Nasrin ta yi murmushi ta ce, "Allah
sarki, ka ji masu arziki masu yi dan Allah.'
"
Jale ya yi murmushi ya ci gaba da cewa
"sun so su bani gidan zama a Lagos, na ce
masu zan nemi gidan haya.Na hada lefe daidai
karfina da gaba daya abinda al'ada ta tanada
. amma a Bauchi aka yi bikin, dangina daga
'Yalleman suka ciko mota-mota suka je biki
haka Mahaifiyata itama da tawagarta suka taho
daga Lagos.
7
An yi biki komai a wadace kuma
Mahaifin Rayyana ne ya dauki nauyin komai,
29 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
aka shirya mata gida a Bauchi ba tare da sanina
ba ma dan ba'a shawarce ni ba. Anan aka kai
Amarya aka watse aka bar Ango aka ce
saimunyi sati biyu za mu dawo Lagos, saboda
danginta su gama zuwa ganin daki. Daga nan
na tabbatar ba ni da 'yanci sai abinda Hajiya da
Alhaji suka tsara min. Aka biya mana 'Yankari
Game reserɓe'dan mu je mu huta, ni dai ina
biye da su ba ni da cewa. "
Nasrin ta gyara zama ta ce, “Ikon Allah.
Abinda ka ke gudu kuma shi yake shirin
afkuwa ko? Ina gidan da ka kama mata na
Lagos?"
Jalo Ya cije baki ya yi shiru na dan
lokaci sannan ya ci gaba da cewa, "gidana na
'Lagos Island' ma an cika shi da kaya kafin ma
a taho bikin.”
"Yaya aka yi to?" Nasrin ta tambaya
cikin zumudi.
Ya ci gaba da magana ya ce, “muka
dawo gidanmu na Lagos na ci gaba da aikina
itama tana karatunta. Amma fa tun ba'a je ko
ina ba na fara fuskantar matsala."
30 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Nasrin ta ce "Allah sarki. Wacce irin
matsala kuma?"
Ya ci gaba da cewa, "Bayan mun tare an yi.
farin ciki na amarci kamar na watanni biyu
kafin halayar gaskiya suka fara bayyana.
Matsala ta farko da muka fara samun damuwa
itace yawan zargina, ba damar in je aiki sai ta
kira ta ce ta ji muryar Mace a kusa da ni haka
idan na dawo gida ta dinga binciken wayata
dan taga sako ko kiran da bata gamsu ba ta yi
masifa, ban isa in fita unguwa ba sai ta ce
zance na je amma duk na ɗauke shi a matsayin
so kuma halinsu na mata.
Abu dai ya yi ta gaba-gaba na tantance
Rayyana ta raina ni bata ganin darajata balle tr
‘yan uwana talakawa idan suka zo, haka abin
ya gangaro kan abokaina, dan ta zagin abokina
akan idonsa ma ba komai ba ne. Bata dafa min
abnci sai dai in fita in saya tamkar ban yi aure
ba amma ana ta bani shawara ana bani hakuri
an ce idan ta haihu zata bari.
Bayan shekara da yin aurenmu Allah Ya
bata haihuwar da namiji, sai na ga rashin
mutunci kamar ana kara mata, ta kai ta kawo
31 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2 m
babu abokina da yake iya zuwa gidana saboda
tsoron rashin mutuncinta. A 'yan uwana kuwa
karwata ceFatima kaɗai ta taɓa zuwa gidana ta
yi min kwanaki amma bata ji da dadi ba, suka
rabu baram-baram ta koma garin da take aure.
Kullum na kira surukata zan gaishe ta sai ta
balbale ni da faɗa ta ce ta gaji da halayyata ina
wahalar da 'yarta, ba taga amfanin auren nan
ba dan bani da hakuri. Ba sa ganin laifin 'yarsu
ko kaɗan kullum karana take kaiwa tana ɓata
ni.
Na yi takaici da da-na-sa-ni ban yi auren
nan ba saboda ko daya bata taɓa nuna min
halayenta na gaskiya a waje ba, da duk son da
nake yi mata da ban aure ta bo.
Allah cikin ikonsa wata rana wata
matsalarsu ta haɗo ta da Mamarta da yayanta
suka zo suka same ta a falo suka yi mata tatas,
sai a lokacin mahaifiyarta ta yabe ni cewar ba
dan uwa uwa ba ce da bazata iya da halin
'yartaba, dan albasa ba ta yi halin ruwa ba.
Yayanta uwa daya, uba daya yace, “da
ace matar da zan aura mai irin halinki ce ko na
yini daya ba zan iya zama da itaba saboda
32 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
rashin jin maganarki da rashin mutuncinki. Jalo
ya yi hakuri da ya iya shekaru da ke.'
"
Ina jin haka sai na dafe kai nace
“innalillahi wa'inna ilaihi raju'un. Allah Ka
canja min halin kunci da nake ciki na zama da
matar nan.
Muka ci gaba da rayuwa a haka watarana
na sami wata harka ni da abokaina, ta karamar
kwangila na fita tunda safe ban dawo gida ba
sai karfe tara na dare, na shigo na same ta ta
cika ta batse gaba daya ita a rayuwarta
mummunan zato take yi min a tunaninta wajen
'yan mata nake zuwa saboda taga na fita da
abokina Yahya shi kuma baiyi aure ba kuma
tana ganinsa da ‘yan mata a jami’a. Ita da take
da auren ma ina ganinta da maza'yan ajinsu kuma tana karɓar Note dinsu ta zo gida da su
amma ni bana zarginta. Na yi mata sallama ta
ki ta amsa buɗar bakinta ke da wuya sai ta yi min addua wai 'Allah ya sa in yi hatsari motata
ta yi kwarankwatsa da ni.' Kalmar 'Innalillahi
wa'inna ilaihi raju'un.' Na ambata na shige
daki na barta.
33 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Haka na ci gaba da zama da ita cikin
rashin ‘yanci da fargaba, ina ta takatsantsan
dan kada in ɓata mata rai a ce nayi laifi. Idan
tana fushi da ni sai ta huce akan ɗana guda
ɗaya wanda na ke matukar ji da shi, dan ta
fahimci raina yana matukar ɓaci idan ta taɓa
masa, sai take hucewa akansa.
Watarana tana fushi da ni sai kuwa ta
tunkuɗe shi ya fadi akan tiles da ya zo da
tsautsayi sai ya karye, muka sha faman zaman
asibiti na kashe kudi sosai amma ta fadawa
iyayenta wai faɗowa ya yi daga kan gado.
Haka har rana irin ta yau ban faɗawa kowa
cewar ita ta karya shi ba."
Nasrin ta yi tagumi babu abirda take sai
girgiza kai tana salati a bayyane saboda tashin
hankalin da take zuka a cikin kunnenta.
Ya ci gaba da Magana cikin marainiyar
murya "Babu wacce ban tuna ba daga cikin
jifgin 'yan matan da suka so ni a garinmu
Yelleman da na Lagos, na yi da na sanin barin
"yan kauye masu tarbiyya nana faɗowa 'yar
birni Amma daga baya na saddakar da cewa
Allah ne bai so ba amma na tabbata har yanzu
34 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2 2
da yawansu suna can suna sona duk da sun yi
aure kasancewarwasu dangina ne mu kan haɗu
a wata hidimar suna mutunta ni sosai."
Nasrin ta ce "Kwarai kuwa komai sai
Allah Ya yarda za ayi."
Jalo ya gyada kai ya ce, "Tabbas haka
ne. Wata rana Rayyana ta tsare ni ta ce Babanta
yace baya so ta dinga yin tuki da kanta saboda
tana da ciwon ido dan haka duk abinda nake yi
na bari na dinga zuwa ina kai taunguwa. Na
amsa masa da to. Haka kuma aka yi ko me
nake yi sai na bari na zo na kaita unguwa wata
unguwar ma kirkiro ta take yi da gangan dan ta
wahalar da ni, ban damu ba saboda bana son tashin hankali ko kadan.'
و,
Nasrin ta bude baki dan mamaki ta ce
"abin har ya kai haka? Sun zamar da kai direba
ma kenan?"
Jalo ya gyada kai ya ce, "Direba ma ai
yana da 'yanci bawansu na zama. Rayanna bata
zaman lafiya da makwabta ko kadan duk sun
ɓata, gashi ni kuma da son mutane karfi da yaji
ta sa nake ja da baya da jama'a. Gashi ko
dayaushe tana yi min gaba sai muyi sati bata yi
35 Jamilu Umar Tanko JUT
1
DAMA NI CE...2
min Magana. Gaba daya bana jin dadin
rayuwata bana samun walwala a kowanne
ɓangare, babu in da zan shiga in ji sanyi a
raina. "
Hawaye ya cikawa Jalo ido haka ma
Nasrin suka yi shiru na dan lokaci kowanne
yana takaici.
Nasrin ta rike baki zuciyarta cike da
ɓacin rai ta ce "subhanalla! Wannan bata da
ilimin addini amma ko tana da ilimin ma bata
amfani da shi."
Jalo ya yi murmushi yace, “ke kenan da
kika san za'a mutu za'a koma ga Ubangiji ai
ita ko salla ma sai ta ga dama.
"
Nasrin ta dafe keya ta ce, "wayyo Allah
mata mun shiga uku."
Ya ci gaba da cewa, "bata dade da yaye
Hisham ba ta kara samun cikin na biyu. A
lokacin na sami tallafi daga gwamnati
tafi London karatu a
UniversityofBedfordshireLuton Campusanan
na yi PHD shekaru uku.
(schoolership) na '
Ina zuwa Najeriya akai-akai in gansu
suma idan suka yi hutu suna zuwa wajena acan
36 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
London dan a lokacin ta gama karatunta har ta fara aiki.
Babu abinda ke tsakani::mu a can
London din ma sai fada saboda Allah Ya yi
mata mummunan zargi, duk in da na shiga ta
dinga kira na a waya ta ji ko ina tare da wata,
idan kuma ban amsa wayarta ba sai ta yi ta turo
sakonni na zagi tana kira na mazinaci. Alhali
Ubangijina shine shaidata ban taɓa yin zina ba
tunda nake a rayuwata."
"
Nasrin ta ji kwalla ta cika mata ido ta ce
"Allah sarki.”
Ya sharce kwalla ya ci gaba da cewa
"Idan na zo Najeriya daga London ɓacin rai ne,
idan na ce su zo da fada za'a rabu; idan basu zo
ba a waya zagi ne, idan na ki amsa wayarta ta
yi ta turo sakonni munana.
Da na ga ɓacin ranta ya na kokarin ya
taɓa karatuna na share ta na daina kula
damuwarta na ci gaba da karatuna dan in fito
da sakamako mai kyau. Amma duk da haka sai
ta je ta huce akan mahaifiyata da kannena duk
da ma Mahaifiyata tana ɓoye min amma wasu daga cikin kannena suna kira su fada min a
37 |Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
ya
boyc. Idan raina ya yi dubu sai ya ɓaci sai na
kira Mahaifiyarta na shaida mata, bab kara
haka zata bi bayan ‘yarta karara. Na zaci dan
ita Mace ce, sai na faɗawa Babanta abin
bani tsoro dan shima karara ya bi bayan 'yarsa,
ni ma suke bawa laifi wai bana kulawa da ita
na fi kula da kannena da mahaifiyata. Tun daga
nan na yi alkawarin na dai fada musu komai
kawai dai zan yi addu'a Allah Ya zaɓa mana
abinda ya fi alkhairi amma bana son yin saki
saboda darajar yarana.
Ina can na ji an ce an bawa mahaifinta
Minister dan haka sun kaura sun koma Abuja.
Ba izinina Rayyana ta rufe gida ta kwashi yara
ta canja aiki ta canjawa yara makaranta ba tare
da ta faɗawa Mahaifiyata ba ta bi iyayenta, sai
da kannena suka je gidan suka ganshi a datse,
kwana da kwanaki da na kira na tambaye ta
take fada min hukuncin data yanke.
Na rabu da suna ci gaba da karatuna har
Allah Ya sa na kammala na fito da sakamako
mai kyau na zama cikakken Dakta. Na so in yi
zamana acan in fara aiki dan Jami'ar sun so su
rike ni na ji ina kishin bayar da ilimin da na
38 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
samu a turawa, ina kishin kasata Najeriya
yadda gwamnati ta biya min PAR BAUER ta biya min ya kamata su more ni, ina so in zauna kusa da Mahaifiyata
da 'yan uwana dan in taimake su suna cikin
wahala. Haka zan so ina kusa da deman taimake su suna cikin yarana in kula
da tarbiyyarsu dan ban yarda da tarbiyyar
Rayyana ba daga ita har iyayenta.
"
JellA
Nasrin ta langwaɓar da kai dan tausayi ta
ce, Allah sarki.” shuvanagh nim i
STS BA
bududs.
Ya ci gaba da cewa "Na kunso kudina da
yawa na zo na biya kudin gidana da nake hay
daman sun yi min magana idan ina so in saya,
duk da gida na da tsada aLagos sun yi min ragi
sosai kuma duk da haka ban gama biyansu ba
amma na biya su fiye da rabi. Mun i da su zan
dinga biyansu a hankali har in gama. Gidan
wata Allaja ce mai kirki wacce take sona da
alkhairi, mijinta ya rasu ya barta da dukiya mai
80
yawa.
stsWIBVox ab adsy to i 2014.I
Na je Abuja na zauna da waliyinta da
Waliyina aka yi Magana sosai akan yadda
zaman auren zai kasance, na shaida musu a
tambayi Can Rayyana in har ta gaji da War la gaji da auren ta bani yarana in sauwake mata, ni ban fadi abubuwan
39 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
da take yi min ba amma mahaifinta ya
zakalkale yana ta zano sharri wanda ban san an
yi ba. Gaba daya wajen suka ga laifina bana sc:
in yi masa musu ko in karyata shi sai da
yagama fadar nasa sannan na kalli Rayyana
nace ta rantse idan haka aka yi, da yake bata
tsoron Allah ta rantse dan haka na bar ta da
Allah.
Na gyara Zama na fara karanto
abubuwan da suke yi min daga nan kawunan
waliyanmu ya kulle suka rasa mai gaskiya a
cikinmu kin san manya sai suka ce abar zancen
kuma a cire maganar rabuwa a sulhunta. Ni dai
ina kan bakana ko ta biyo ni Lagos mu zauna
ko ta bani yarana in tafi da su, Ta rantse ita ca
Mahaifiyarta ba za'a ba ni yara ba sai dai nima
in dawo Abuja a ba ni wani aikin mai kyau. A
lokacin ne na fada musu karara bazan iya yin
aiki a karkashinsu ba yanzu, na fi son in koma
Lagos in ci gaba da koyarwata.
Nan dai suka nuna basa son saki kuma
aka amince zata dawo Lagos nan da watanni
uku idan yara suka yi jarabawar canja aji. Aka
bani hakuri na amince na dawo Lagos na zauna
40 |Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
ni kadai har tsawon watanni biyar sannan ta dawo."
Tausayinsa ya kama Nasrin sai hawaye
ne kawai ke fita daga idanuwanta, tana ta
faman girgiza kai. Ta jawo Computer ta ta
kunna ta nemo hotonsa a Facebook ta zuba
masa ido tana kallon kyawu ido da hanci kamar
balarabe, ga ililmi ga nutsuwa amma Rayyana
take wulakanta wannan kadarar.
Ta ce "Allah sarki, yi hakuri dan uwana
jarabawa ce kowa da irin tasa kai kuma irin
taka kenan."
Jalo ya daga robar ruwa ya sha ya ci
gaba da cewa "haka ne sosai kuwa. Na yarda
da kaddara mai kyau da marar kyau.
Rayyana ta dawo da sababbin salo na
rashin kunya, bata raga min duk da bana daga
ido in kalle ta amma bata kyale ni ba. Zargina
take ina bin mata a jami'a dan haka ma bana
kusantarta kullum addu'arta Allah Ya
ragargaza ni a mota a hanyata ta zuwa wajen
.
Nasrin ta dafe kai ta runtse ido ta ce,
"Wa'iyyazu billah."
41 Jamilu Umar Tanko JUT
NDAMA NI CE...2
Jalo ya girgiza kai yace, “kadan ma kika
ji daga cikin mugayen jafa'in da take jawo
min. Kullum ta ce min ina takama da kyau da
ilimi sai na yi rugu-rugu, kyawun ya disashe a
kwabo ma babu mai dauka ta."
99
Nasirin ta gyara zama ta ce, "amma
wannan ba kaunarka take yi ba. Subhanallah!"
Jalo yace, "na dade da gane haka bata
kauna ta ko kadan.'
99
Nasrin ta ce, “meyasa ta dage sai da ta
aureka? Kuma sun fi ka kudi balle ace kwadayi
ne.
"
Jalo yace, "ina ga saboda kyawuna take
sona, ko ilimi, kuma tana son auren talaka ta
taka shi ta yi abinda take so ni kuma na ki:
binta in yi wasu abubuwan. Duk abinda shari'a
ta hana bana yi.
Koda yaushe Rayyana addu'arta a gare
ni kenan Allah Ya kwace aikin nawa ma taga
yadda zanyi takama. Dan haka zaman gidana
ya fara gagarata kullum daga wajen aiki sai
gidanmu wajen Mamana ita ke dafa min abinci,
tana mai lallashina da bani baki akan in yi
42 Jamilu Umar Tanko JUT
MAMAN
DAMA NI CE...2
hakuri in daina damuwa. Allah Yana tare da mai hakuri⠀⠀⠀⠀⠀880
ht
Yarana suna sona basa bacci sai na dawo
haka zaá mumu viyi was wasa da tsalle-tsalle, zan kai su
makaranata in ɗauko su. BBB R (BO suals
A haka muke har watarana and de mana hakamuke harwatara штаби
Allah ya aiko slide oqush Seb Ed yajaikums da hatsarin mota ni, ita,yaranmu
,direbana da kanwarta.'
"BYD ORAMA BY
Nasrin ta firgita ta mike tsaye gami da
dafe kirji ta ce, "hatsari fa ka ce Yaya Jalo?"
Ya surnano da hawaye yace, "hatsari
*****
muka yi kanwata.” solst ou slud sisw
Nasrin ta langwaɓe kai ta koma ta zauna
ta jingina da bango ta ce "Allah Ya sa ya zo
muku da sauki.' BIE
headmet
gashi
66 Jalo ya ci gaba da cewa amma yau
shi baki sanni baba
baadhi baki t:ɓa ganina ol ba amma kin yi min adaddu'a. Ya Allah ina rokonKa da ka 8082262 Tube 90
61 162006.
amsawa Nasrin bukatunta na duniya da lahira Asobi sebel
6 Sai Nasrin ta zare ido ta cika da mamaki Rosli ina nols exp
BOUL BWSIE J dub zuciyarta cike tambayoyi masu dinbin
har ma bata san ta in da zata faraba. greet of overand U16 Bawa b
60 Bbat cl6x sbaids
43 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
"Dakta Jalo ban fahimce kaba, kana
nufin kunyi hatsari har ka ji mummunan ciwo
matarka bata yi maka saanu ba?”
Bai bata amsa ba sai ya kashe waya da
alama baya son maganar.
Nasrin ta sake kiransa, wayar tana shiga
amma bai dauka ba, data dame shi da kira sai
ya kashe wayar gaba daya.
*** *** ***
Nasrin ta fito falo a gigice gami da yaye
wata hula data tuma a kanta ta wurgar a kan
kujera saboda gumin da ya keto mata.
Kamar daga sama ta ji murya ana
tambayarta "lafiya?"
Ta daga ido ta dubi mai Magana, Zainab
ce, sannan ta sassauta ta ɓoye damuwarta
amsar ita ce "babu komai, ina jin zafi ne?"
Zainab ta daga ido ta kalli Ac dake
kunne sanyi ya cika falon sai itama nasrin ta
dubi AC suka kurawa juna ido. Nasrin ta juya
da sauri ta shiga daki ta rufe ba tare da tasan
abinda zata faɗa ba.
44 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2 YEARS
Zainab ta faca a bayyane "Allah Ya baki lafiya toh."
Nasrin ba ta ma san har karfe ɗaya na
dare ya yi ba sai da ta duba agogo, dan haka ta kwanta zuciyarta cike da damuwa.
Asuba ta gari!
*** *** ***
a
Da safe ma ta gwada kiran Jalo bata
shiga ba har yanzu bai kunna waya ba.
Labarinsa ya na ta yi mata zagaye kwakwalwa tana so ta ji ci gaban wannan abin tausayi. Tana mai matukar son ya karɓi
bukatarta shine ya yarda ya so ta ya ga yadda ake kula da miji. Ta ji tana son Jalo amma tana tsoro ko zai sake yarda ya auri yar masu kudi saboda ya sha wuya a baya.
Ta na kallo ana ta kiranta daga ofis amma ta ki amsawa ta san ana matukar
bukatarta amma ko ta je ta san ba zata moru ba damuwa ta buwaye ta.
45 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Ta ga kiran Shamaki da Malaika ma ta ki
amsawa dan ta san wata damuwa zasu kara iza
mata.
Dinah ceke ta kiranta ta ki ta amsa sai da
ta ga kiran ya yi yawa sannan ta amsa wayar. A
tunaninta hakuri dina zata bata dan ta ɓatamata rai jiya sai ta ji akasin haka.
Dina ta balbale ta da fada akan maganar
Fu'ad daga nan ta tabbatar Fu'ad ya yada ta
har ma ya kara da sharri dan wasu abubuwan
ma ba'ayi ba.
Ba ta da lokacin sauraren wadannan
maganganun dan haka ta kashe wayarta ba tare
da ta cewa Dina uffan ba.
Dina ta fusata ta ci gaba da kira Nasrin ta
ki ta amsa, ta fito falo ta gaishe da Zainab ta
iske ta tana cin kwadon zogale ta zauna suka ci
tare ba tare da suna yin hira ba. Da suka gama
Nasrin ta fita farfajiyar gidan tana shawagi
hakika huhunta yana bukatar iska mai sanyi
dan ya cushe da takaici.
Ta gaji da shawagi ta shigo falo suka hau
kallon kallo da zainab har ta shige daki bas u y
46 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Magana ba, da alama Zainab ta gaji da ɓata
yawun bakinta wajen tambayarta.
Nasrin tana shiga daki ta iske kira rututu
amma na Dr.Jalo dana Mahaifiyarta ta fi
damuwa da kira. Ta fara kiran Mummy sun
jima suna Magana da alama Zainab ta kai
kararta haka Fu'ad. Hankalin mahaifiyarsu a
tashe tana zargin Nasrin bata da lafiya dan
haka ta umarce ta ta bar bautar kasar ta dawo
Amerika ta yi jinyarta.
Nasrin ta yi amfani da duk wata kalma ta
turanci da ta Hausa da ta sani wacce za ta iya
gamsar da Mahaifiyarta wajen ba ta hakuri
amma Mahaifiyarta ta ki amincewa, daga
karshe ma kashe wayarta gaba daya.
Nasrin ta gigice ta fito falo a fusace ta
sami Zainab a kicin tana mai nuna ɓacin ranta
akan abinda ta yi mata gashi ta jawo an ce ta
bar bautar kasa ta koma gida.
Zainab ta fada cikin isa da gadara ba tare
da tsoro ba, ta ce Eh ta fada dan tana kaunarta
ba zata zauna ta zuba mata ido ba ta je ta kashe
kanta saboda damuwa, tunda ta ki fada mata
gaskiya ai dole ta fadawa wacce ta haife ta.
47 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Nasrin ta koma daki a fusace hawaye
yana zuba abin mamaki tana shiga kiran Jalo
yana shigowa.
Ta mika hannu da sauri ta amsa gami da
yi masa sallama sannan ta gaishe shi.
Ya sake neman gafarar ta dan ya kasha
mata waya jiya.
Ta yi murmushin karfin hali ta ce ba
damuwa' tana fatan yau zai daure ya karasa
bata labarinsa har karshe. Ya yi mata
alkawarin hakan, ta sami kujera ta zauna ta ci
gaba da sauraronsa.
CI GABAN LABARIN JALO
Jalo ya ce, "Wata rana Mahaifiyata ta
tafi garinmu Yalleman da niyyar ganin gida sai
ciwo ya kwantar da ita acan. Ina zaune aka yi
min waya mahaifiyata bata da lafiya sosai ko
wanka ma sai anyi mata.
$Y
Hankalina ya tashi na yi magana da
abokina Saifullahi a Kano nace ya tanadar min
direban ofishinsu idan na zo Kano a jirgi sai
direban ya zo ya kai ni Yelleman. Rayyana ta
48 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
ce itama zata je amma da alama taṇa so ta tsaya
bikin kawarta a Kano dan na san dai ba
Mahaifiyata take son ta dubaba, ta fake da
haka. Nan da nan na amince, a lokacin
kanwarta Salima ta zo wajenta hutu. Muka
tsayar da ranar da zamutafi, mu ka dunguma
mu biyar ni, Rayyana Salima, da yarana biyu
muka hau jirgi zuwa Kano kafin mu iso
direban Saifullahi ya zo yana jiranmu, ya so
ma ya kaimu gida mu ci abinci kamar yadda
abokina ya umarce da ya yi, na ki nace gara mu
wuce Yelleman kawai dan hankali ya tashi
sosai Mamana kawai nake so in ga yadda jikin
yake. Sai dai a waya na kira Saifullah na bashi
hakuri."
Nasrin ta ji gabanta yana ta dukan ukuuku dan fargabar abinda zai faɗa nan gaba.
Fadi take "Allah ya kawo da sauki.
Allah ya yi muku afuwa."
_ Jalo Jalo ya ci gaba da labara, “Ahanyarmu ta
Yalleman ne Allah ya aiko mana da
mummunan hadari."
Nasrin ta runtse ido ta takure jikinta tana
ta salati yayin