a bayan
Babur tana baza su, ita a dole katafaren lambu
take so ta gani da kyawawan mata. Sai ta dinga
hango bukkoki da mutane a dadɗaure kai kace
a lahira take ba a duniya ba. Ta sauko daga
bayan acaɓa sororo da ita jikin babu laka.
Ta ga Nasrin ta koɗe kamar ba itaba,
dukka gayun nan babu ta daura zani daban,
riga daban. Nasrin ta tsaya suna ta magana da
dan acaɓa,falaika tunaninta kw gaba daya
ya bata a gidan yankan kai take an gama
cinikinta.
Nasrin ta bashi kudin aikinsa har ma ta
kara masa sannan ta bashi kudi mai yawa ta cè
ya sayo mata ruwan roba katan, ya sayo musu
biredi (Butter), ta ce ya sayo musu
biskit da duk abinda ya gani mai kyau na ci.
75 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Yana murna ya tafi, ran Malaika a ɓace,
tana tsaye tana yiwa wajen kallon tara saura
kwata. Nasrin ta mika hannu zata karɓi
akwatinta.
Malaika ta goce ta harari Nasrin ta ce
"nan ne lambun Gwamnan?"
Nasrin ta tuntsire da dariya ta ce "ba
wajena kika zo ba? To anan nake zama yanzu,
ke ma anan za ki zauna. Ni kika sani ba Zainab
ba kuma ni kike so ba gida mai kyau ba.
"
Malaika ta harare ta, ta ce, “bazan zauna
a gidan yankan kai ba. 66
Nasrin ta kwashe da dariya ta ce, “nan
wajen marassa lafiya ne asibitin gargajiya ne.”
Malaika ta zabura ta kalle ta, ta ce, "wato
asibitin mahaukata kika kawo ni ko? Daman na
ga alamar kina yi min kallon marar hankali dan
kawai na kashe aurena.
"
Nasrin ta dafa kafadarta sai Malaika ta ja
da baya da sauri dan bata yarda da itaba, gani
take wani abu zata shaka mata irin wanda aka
ce anan shakawa Mutum idan za'a sace shi.
Nasrin ta ce "zo mu shiga ciki ki duba
jikin Dr.Jalo shine bashi da lafiya."
76 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Malaika ta zabura ta zazzare ido ta ce
"wannan dan gayun kyakykyawa da na ga hotonsa a kwamfiyutarki shine ya zo nan? Daman bashi da hankali?”
Nasrin ta ce, “ras yake ya fiki hankali
nesa ba kusa ba. Ai kowanne ciwo ana zuwa
karɓar magani ba sai mahauka ta kaɗai ba.
Malaika ta taɓe baki ta fara bin Nasrin a
baya amma fa sanda take yi a tsorace.
Suka isa kofar daki Nasrin ta yi sallama
sannan suka shiga, suka suka zazzauna akan
tabarma bayan sun gaisa da mahaifiyarsa suka
jira ya idar da salla, a zaune yake yi
kafafuwansa a mike babu sujjada babu ruku’u,
sai dai nuni da hannu. Kwalla ta cikawa Nasrin
ido yayin da mamaki ya hana Malaika rufe
baki.
"Tabbas Jalo ne ga kamar nan. Shikuwa
wanne irin ciwo yake yi haka a mimmike a
zaune haka? Me ya kawo shi nan alhali masu
kudi turai suke zuwa ganin likita?"Malaika ta ke tambayar zuciyarta.
Da ya idar ya juyo ya kalli Nasrin ya yi
murmushi yace “bakuwa muka yi ne?"
77 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Nasrin ta yi dariya ta gyada kai ta ce
"eh! Aminiyata ce, sunanta Malaika daga Kano
ta zo.'
"
Sai ya dubi Malaika ya yi murmushi
yace "Malaika sannunki da zuwa."
Malaika ta yamutse fuska ta yi masa
kallon tara saura kwata. Ta amsa da kyar.
Wannan abu ya yiwa Nasrin ciwo ta kuma
Kudiri aniyyar sai ta koya mata darasi, sai ta
nuna mata talauci da talaka ba abin kyama ba
ne.
Malaika ta yi wuf ta fito ta tsaya a waje
tana hucin bakin ciki, yayin da take jiyo ihun
mahaukata daga cikin bukkoki daban-daban,
ana yare caban-daban. Garin abin :tsoro a
tsakiyar dawa suke gaba da baya babu gari, ga
duhu.
Ta fara tunanin inda za'a kwanta, da inda
za'ayi wanka da bayan gida anan.
Jaloya dubi Nasrin cikin sanyin jiki yace
"Nasrin! Saboda me za kikawo matar mutane
cikin dajin nan? Banda ni babu wanda ta kama
ya shigo nan ya zauna, ke ma dan kin dage zaki
zauna dan babu yadda zanyi da ke ne shiyasa
78 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
na bar ki.Bai dace ba, da ta zo sai kice ta jira a
gida idan ma dare ya yi gobe sai ki je ki same ta."
Nasrin ta sunkuyar da kai kasa ba tare da
tasan abinda zata ce ba.
Mama ta yi murmushi ta dafa kafadar
Nasrin ta ce "Nasrin 'yata! Tana kaunarmu
shiyasa take ganin duk mai kaunarta ya zo ya
zauna tare da mu ko?"
Nasrin ta dago ta dube ta ta yi murmushi
ta ce "Mama! Akwai dalilin da ya sa na kawo
Malaika nan, ba dan komai ba sai dan ta koyi
rayuwa kuma ta kara imani. Bata godewa
Allah da gaba daya ni'imomin da ya yi mata.
Bata son talaka da talauci.'
"
Jalo ya Kurawa Kurawa Nasrin Nasrin ido yana
mamakin yadda take da hankali da zurfin
tunani haka.
Malaika ce take kwallawa Nasrin kira,
dan haka Nasrin ta fito da sauri.
Malaika ta harare ta ta ce, "ɗauko min
akwatina zan koma gida, bazan iya kwana anan
ba."
79 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Nasrin ta ce "babu abin hawa, kuma a
cikin dajin nan ina zaki je ki kwana? Ki tuna
doguwar tafiyar da kika yi ki ka dinga hawa
motoci daban daban, sannan kika hau acaɓa."
Malaika ta yi tsaki ta kama kugu ta daga
murya ranta a ɓace ta ce "Nasrin!Bana ciki da
iskancin banza. Ta yaya zaki kawo ni gidan
mahaukata kice in kwanta?"
Nasrin ta cika da mamaki ganin yadda
Malaika take yi mata magana babu wannan
girmamawar irin na da.
Nasrin tace, "ni na ke yi miki iskancin
Malaika?"
Malaika ta fada a gadarance "Eh! Da ke
nake Nasrin.”
Daga nan Nasrin ta tabbatar ashe ba dan
Allah Malaika ta nace mataba dan kudinta ne
da daular da take ciki, yanzu da ba daula ba
mutuntawa."
"
Nasrin ta ja bakinta ta yi shiru, Malaika
tana ta kai kawo a kofar daki tana zage-zage a
fakaice dai Nasrin take zagi. Sun ci sa'a ma
akwai farin wata da ko tafin hannunsu ba zasu
iya gani ba. Da aka jima sai ga mai acaɓa ya
80 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
cika alkawari ya siyo dukkan abinda ta zayyana masa.
Nasrin ta karɓa ta yi masa godiya ta bashi kyautar kudi mai yawa. Sai Malaika ta daka tsalle ta haye bayan acaɓa ta ce su juya ya mayar da ita in da ya dauko ta.
Nasrin ta ce masa "kada ya dauke ta
marar lafiya ce guduwa take so ta yi.
Kosasshen dan acaɓa ya dakamata tsawa
yace ta sauka daga kan babur dinsa kafin ya
wurgota, a cikin harshen turanci.
Nan da nan ta sauko, ya yiwa Nasrin
sallama ya tafi.
Malaika ta ɗora hannu aka ta fasa kuka
ta na so ta tarawa Nasrin jama'a.
Ma'aikatan gidan suka rugo a guje dan
suna tunani an kawo musu sabon kamu ne. Da
suka karaso suka tambaya, sai Nasrin ta nuna
Malaika ta ce sabuwar marar lafiya ta kawo
tana so ta gudu. Ba'ayi wata-wata ba aka.
damki Malaika aka daure, kamar huhun goro,
sannan aka cicciɓa za'a tafi da ita tana ta ihu
tana tsinewa Nasrin. Dariya ta kama Nasrin ta
toshe baki tana ta tuntsirawa.
81 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Mama ta fito a gigice tana tambaya,
Nasrin ta bata labaria abinda ke faruwa, Mama
ta ce su kwance Malaika lafiyarta kalau, Nasrin -
ma ta yi Magana sannan suka kwance ta, suka
tafi.
Suna juya baya Malaika ta cakumi
Nasrin tana narka mata ashar, Nasrin bata iya
dambe ba, bata ma taɓa yi ba. Mamaki ya hana
Nasrin yin motsi tayi kasake tana kallon ikon
Allah tamkar a mafarki.
Tabbas ta gasgata Malaika ce ta cuci
Shamaki ko tantama babu.
Mama ta shiga tsakaninsu ta raba dakyar,
amma ta kasa sa Malaika ta yi shiru da bakinta
har yanzu zage-zag take yi.
Nasrin ta shiga daki ta zauna a gefe tana
kuka ya yin da Jalo ya kasa magana ya zuba
ido yana kallonsu ba tare da ya san abinda zai
ce ba. Mutum ne mai nutsuwa bai cika son yin
magana ba.
Kukan Nasrin ne yake yi masa ciwo a
cikin zuciya, can da aka jima ya girgiza kai ya
yi Magana cikin sanyayyiyar murya "Nasrin!
Kada kiyi kuka, wannan abu bai isa ya ɓata
82 JamiluUmar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
miki rai ba.Idan kika tuna ni’imomin da Rabbi
Ya yi miki.Babbar ni'ima ita ce da ya baki
lafiya, Ya yi ki musulma, Ya baki ilimin
saninSa kuma kina bauta maSa. Gobe ki ja ta ku koma gida. Kin ji?”
Ta sharce hawaye ta gyaɗa kai.
Mama ta lallaso Malaika dakyar suka
shigo cikin ɗaki suka zazzauna jigum, kowa ya yi tagumi.
Da aka jima Mama ta ce "ga ledojin
purewater can ku sha, abincinmu shayi ne da
garin kwaki ga su can a jakar bacco ku jika ku sha.'
"
gefe.
Malaika ta harari jakar ta kawar da kai
Nasrin ta mika hannu ta jawo ledojin da dan acaba ya yi mata sayayya.
Manyan kifaye ne gassasu masu zafi
yanzu aka sauke daga kan wuta, ga ruwan roba da biredi da butter.
Ta tura gaban Mama ta ce ta raba.
Mama ta dauki kifi daya ta basu ɗaya,
ita da Jalo suka ci daya kuma Nasrin da
83 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Malaika suka ci saboda girmansu sai da kowa
ya koshi sannan ya sha ruwa.
Mama ta fara bayanin wajen kwanciya
yadda za'a yi tsarin, ta ce ba zai yiwu su
cakuɗa a cikin daki daya ba amma Nasrin ta je
ta sami ma'aikata ta faɗa musu su bude mata
ɗaki daya su yi musu shinfida sai su je su
kwanta, dan taga alamar ma'aikatan suna
girmama Nasrin sosai.
Nasrin ta amsa ciki ladabi ta tashi ta
bude Jakar kayanta ta daukozanin gado ta juya
ta kalli Malaika ta ce ta taso su tafi.
Malaika ma ta bude Jakarta taɗauko
zaninta guda daya. Suka yi musu sallama suka
fice, har sun fita bakin kofa Nasrin ta dawo ta
dauki jakar ledar pure water ta fita.
Suka isa wajen maʼaikata Nasrin ta yi
musu bayanai jikinsu na rawa suka amsa mata
saboda tun da safe take yi musu ruwan naira.
Komai ma na musamman aka saka a
dakin, sababbin tabarmi da fitilar kwai sabuwa
an cika ta da kananzir. Bayan ma'aikatan sun
tafi Malaika ta zunɓuro baki ta tambayi Nasrin
bandaki, tana so ta yi alwalla.
84 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Nasrin ta ce ta zagaya baya duk ida taga ya yi mata ta tsugunna kawai. Ga purewateman ta yi alwallar da shi.
Malaika ta daɗe tana hararar Nasrin, ita
kuwa ta yi kamar bata san tana yi ba, ta ci gaba da daddana wayarta. Malaika ta fusata ta dauki ruwa leda 2 ta fice. Ba jimawa ta shigo ta tayar da Sallah.
Abin Mamaki sai ga Jalo a facebook ya
turo Sako (Post) ya yi Magana akan bayin Allah masu kaunar juna saboda Allah, ya haɗa da addu'a Allah Ya sakawa masu kaunar
mutum saboda Allah.
Aka yi ta sharhi da Amin, Amin.
Dadi ya rufe Nasrin tabbas ta san daita yake wannan Magana. Bata san sanda ta fara
murmushi ita kadai ba har da daga hannu sama tana addu'a.
Malaika ta juyo tana harararta tana mamakin yadda har take farin ciki a cikin wannan surkukin dajin.
Nasrin ta zankaɗo sharhi ta tura, tana
mai sake jaddawa cewar Aljannar masu kaunar juna dan Allah daban ce, sai ga Jalo ya tsinci
85 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
kansa yana mai murmushi. Bai ce komai ba
bayan ya karanta sai ya sauka.
Nasrin ta jira ta ga bai dawo ba sai ta
hakura ta rage fitila ta kwanta suka yi kai da
Kafa Malaika tana ta habaici tana tsaki akan an
cuce ta duniya da lahira da aka kawo ta daji
aka jifge, tana addu'a Allah Ya gaggauta yi
mata sakayya.
Nasrin bata kula ta ba dan ta fi kowa
taship hankali bata san yadda bacci zai dauke
nan, babu gado, babu AC. mu dalla
ta banAi kuwa ba ‘a jima ba munsharin
Malaika ya fara tashi da alama daman ta saba
da kauye amma Nasrin ta kasa.
Wayar Nasrin ce ta dauki kara abir ya
razanata kuma ya bata mamaki, tana dubawa ta
ga sunan Jalo, dadi ya rufe ta jikinta na rawa ta
amsa,
ubbe anct
Yana Magana cikin rada yace, "Nasrin !
Ba ki kwanta ba ko? Daman na san ba za ki iya
bacci badan ba ki sababa. Na damu da yawa na
san ba zaki iya ba. Dan Allah ku koma gida
gobe ba dan na gaji da ku ba sai dan kawai bai
ohet sy 9o audeb HallA neb so
86 |Jamilu Umar Tanko JUT Toldot ( | 28 un
DAMA NI CE...2
dace ku cutu ba. Na gode da kara da kaunar da
kika nuna min."
"
Hawaye ne yake kwaranya daga
idanuwansu su dukka, Nasrin ba ta iya magana ba saidai sheshshekar kuka.
safe.
Ya kashe waya bayan ya yi mata sai da
Nasrin ta tashi ta zauna tana rusa kuka
tana addu'a Allah Ya bawa Jalo lafiya.
Malaika ta juyo ta harare ta ta ja tsaki ta
juya keya ta ci gaba da baccinta. Yadda Nasrin
ta ga rana haka ta ga daretana duba agogo tana
soshe-soshe sauro da kwari suna cizonta.
Da asuba ta dauki ruwa ta fita ta yi
alwalla ta zo ta yi ta tashin Malaika ta ki ta
tashi. Nasrin ta yi sallah ta daga hannu sama ta
na ta addu'a amma Jalo kawai ta ke yiwa addu'a akan Allah Ya bashi lafiya, ya gyaru kamar yadda ya ke ada kuma Ya masanya masa da mace ta gari. Kuka ya hana ta ci gaba da addu'a ta yi kuka har ta godewa Allah. Kukanta ne ya tashi Malaika, ta mike a fusace ta dauki ruwa tana gunguni.
87 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Tana mamakin yadda Nasrin ta ke
damun kanta a kan matsalar wani talaka, bayan
Allah Ya yi mata ni'iaomi ta dukiya da lafiya.
Bayan gari ya waye tangararai Nasrin tr
ce da Malaika su zo su dauko ruwa, Malaika ta
harare ta, ta ce ba inda zata je.
Nasrin ta kwallawa garadan ma'aikata
kira, nan da nan suka rugu da gudu, suka duka
suna jiran su ji dalilin kiran. Nasrin ta juya ta dubi Malaika ta ce "ko
ki tashi mu je ko in sa su saka ki a turu in ceke
mahaukaciya ce.'
"
Malaika ta mike cimak a fusace suka
ɗauki jarkoki suka fara tafiya. A hanya suka
hadu da masu zamar jinya da yawa, wasu suna
tafiya wasu kuma sun ɗauko suna dawowa.
Tafiya mai nisan gaske a cikin daji ba
gida gaba babu baya. Haushin Nasrin ya
cikawa Malaika zuciya ta fara tuhumar kanta
akanshishshigi da kwadayinta ne suka ja
matashigowa dajin nan sannan Nasrin in ba neman suna a wajen Jalo ba ta sa wadancan
ma'aikatan su dauko musu ruwan mana sai sun
je da kansu.
88 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Suka isa da kyar bayan sun galabaita, suna isa Nasrin ta zauna ta dafe kirji tana sheshsheka, Malaika ta kudiri niyyar ko zata mutu ko sannu ba zata yi mata ba ita ta jawowa kanta ba wani ba.
Da Nasrin ta huta ta karasa ta ciko
jarkarta sannan Malaika ma ta je ta debo suka
nada gammo amma Nasrin ta kasa ɗorawa
akai, gashi gaba daya abokan tafiyar ta su sun dauka sun tafi.
Malaika ta yi tsaki ta nuna ta da yatsa ta ce, "bazan ɗora miki ba kuwa saboda ke kika
jawo mana wannan jarabar."
Nasrin ta fusata ta buge hannu Malaika
ta ce "kada ki sake nuna ni da hannu."
Malaika ta fusata ta wawuro Nasrin sai
ga Nasrin a kasa saboda bata da kwari, tuwon dawa bai ratsa ta ba.
Malaika ta zauna a ruwan cikin Nasrin ta
danne ta, ta daga hannu zata kai mata naushi,
ta tuna wani abu ta fasa dukan ta, amma ta ja
mata kunne akan kada ta kara marmarin nuna
mata hannu balle ta doke mata hannu.
89 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
a
Mamaki da tsoro ya hana Nasrin yin magana, Malaika ta daga ta ta dauki ruwanta akai ta yi tafiyarta ta bar Nasrin anan tsugunne tana kuka. Sai da ta yi kuka ta gaji Allah ya kawo wasu mata zasu ɗauki ruwa, ta
roke suka dora mata ruwan akai ta tafi,
wuyanta kamar zai ɓalle dakyar ta iso.
Ta iske Malaika har ta shiga wanka wato
ba ba kenan. dan marar lafiya ta dauko ruwan Nasrin ta isa kofar dakin su Jalo ta yi
sallama Mama ta fito, ta sauke mata tana yi
mata godiya. Nasrin ta duka ta gaishe ta
sannan ta shiga ciki ta durkusa a gaban Jalo ta gaishe shi ya amsa cike da fara'a. Yana dauke
da laptop akan cinyarsa yana karatu da alama ya na kan facebook ne. Ta cika da mamaki
ashe daman duk posting din nan da yake a
cikin kungurumin dajin nan yake yi?
Nasrin ta fito ta sake daukar wata jarkar
zata dauko wani ruwan, ta ce Mama su yi
amfani da wannan.
Ma'aikaci daya ya karɓa yace zai dauko
mata dan daga gani ba tambaya ansan
90 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
galabaita ba ta sababa. Duk da a ɓoye ya tafi ba'a yarda su bar mararsa lafiya ba.
Nasrin tana zaune daga karkashin
bishiya tana hango Mama tana faman shiga da
fice dauke da katuwar roba tana tsaftace jikin
ɗanta, sai ta fara kwaranyar da hawaye tana
sake jinjina kaunar Uwa akan ɗanta.
Nan da nan taga Ma'aikaci ya dawo da
jarka cike da ruwa, ta yi masa kyauta har sai da
ya yi mamaki yana ta godiya.
Ta sake kai ruwan bakin kofar ɗakin su
Jalo, Mama ta fito da fara'a tana godiya. Mama
ta diba a bokiti ta je ta yi wanka data fito
sannan Nasrin ta je ta yi wankan itama, gaba
ɗaya tsikar jikinta ta tashi, borin jini ya fito
mata dan bata taɓa wanka a cikin kazanta haka
ba. Ta koma gefe tana ta susa tana kuka ba tare
da ta bari kowa ya sani ba. Tana ta addu'a har
Allah Ya yaye mata.
Ta zo ta dauki jakar kayanta ta koma
ɗakinsu ta iske Malaika ta yi wanka ta canja
kaya tana kwance tana girgiza kafa da alama a
fusace take.
91 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Nasrin bata kula ta ba ta shirya tsaf da
wata atamfa doguwar riga da dan mayafi ta
hada kayanta gaba daya.
Sannan ta juya ta harari Malaika ta ce "in
kin ga dama ki tashi mu tafi.'
"
Malaika ta yi zunbur ta mike har da
murmushin dadi, su na fitowa suka ga mai
maganin yana zagaye daki-ɗaki yana bada
magani, Nasrin ta kalle shi sama da kasa ta
kamanninsa sak na Bokaye ko riga babu a
jikinsa sai fata da gashin kaza a ko ina da a
jikinsa, guru da laya a hannu da kafa, daga shi
har makarbansa abin tsoro. Tabbas babu
alamar musulunci anan, sai tafara tunanin
yadda aka yi Jalo ya yarda ya zo nan neman
maganai da iliminsa da komai. Ta kudiri niyyar
sai ta yiwa jalo magana akan wannan.
Nasrinda Malaika suka nufi dakin Jalo
suka shiga da sallama, abin mamaki sai ga
Malaika tana washe baki ta ji za'a tafi gida, ta
gaishe su da fara'a ta jawo kayanta tana
hadawa.
Nasrin ta mika musu Biredi da butter
Mama da Malaika ne suke ci suna korawa da
92 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
lemo da ruwa. Jalo ya na azumi bai ci ba, Nasrin kuma ta ce ta koshi. Gaba daya hankalinta a tashe yake babu abinda take sai
kallon Jalo tana ganin idan suka rabu yanzu har abada ba zasu kara haduwa ba.
Ya kula da haka sai ya zare farin gilashin
da ke fuskarsa ya dube ta ya yi mata lallausan
murmushi ya ce, "Nasrin! Na san abinda ya ke
damunki. Kada ki damu Ubangijina Yana tare
ta ni, Shi ya ɗora min Shi zai yaye min. Ya fi
ki sona kuma ko dukka duniya zasu taru akaina
bazan ji sauki ba in dai ba Shi Ya so in warke
ba."
Nasrin ta surnano da hawaye ta ce,
“Zamanku anan ne ya fi damuna, kuma yanzu
na ga Mai baku magani sai nagan shi da siffar
Bokaye.'
"
Jalo ya gyada kai yana kallonta yace "Nasrin! Magani kawai yake bani sassake ne
babu wani abu bayan wannan kuma ga Mama
nan ita take kuka idan na ce ba zan zo ba. Kar
ki damu Insha Allah ba zan ɓace hanya ba.' Nasrin ta gyada kai sannan ta langwaɓe kai hawaye na zuba, kuma bakinta yana ta
"
93 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
rawa da alama tana so ta yi wata magana ta
kasa.
yana kallonta
Nasrin ta zura masa ido tana kallo shima
hawaye ke Zuba daga
idanuwansu su dukka. Sai suka juya suka kalli
Mama wacce tashin hankali ya hanata ci gaba
da cin abinci.
Mama ta tashi da sauri ta fice tana
hawaye ta basu waje, amma kuma ta laɓe a
inda zata dinga jiyo abinda zasu ce.
Malaika tana zaune tana cin biredi tana
kallonsu da alama itama tana jin tausayi duk da
bata san ciwon da Jalo yake yi ba, ta ga alama
dai baya iya tashi tsaye.
Can jimawa Nasrin ta sunkuyar da kai
kasa tana tunani, sannan ta sake ɗagowa ta
dube shi cikin sanyayyiyar murya ta ce, “Dr.
Jalo!in tambaye ka wata alfarma zaka yi min?".
Ya dago da sauri ya dube ta cike da
mamaki ya yin da kwakwalwarsa ta kasa tuno
masa alfarmar da zai iya yi mata yana zaune a
cikin kashi da fitsari. S
94 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Nasrin ta dago ta dube shi ta yi magana cikin sanyayyiyar murya ta ce, "Za ka taimake ni ka aure ni?"
Sai ya ji gabansa ya fadi, ya zazzare ido
ya na kallonta.
Ta sake cewa “ina sonka a yadda kake
Jalo."
Sai ta fashe da kuka shima hawaye ya na
zuba daga idanuwansa.
Ya girgiza kai yace, "Nasrin! Ina tunanin
har yanzu baki gane halin da nake ciki ba, ai
babu maganar aure a tare da wanda lakarsa
✓ bata aiki.'
"
Ya ɗaga mata ledar fitsari da take
jikinsa, wato katata.
Ta yi sauri ta sunkuyar da kai kasa ta
fashe da kuka. Yayin da Malaika ta kura ido
tana kallonsa sai yanzu ta gane abinda yake
faruwa.
Nasrin tarusa kuka ta faɗa cikin ɗaga
murya "ina sonka a haka, na yarda zan zauna
da kai a haka. Jalo ban san soyayya ba sai da
na hadu da kai tun ma ban taɓa ganinka ba.
Haka kuma da ka kula ni na ji farin cikin da
95 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
ban taɓa ji ba. Da na same ka da larura babu
abinda ya canja, ina sonka" har yanzu.'
Ya girgiza kai yana kuka ya ce, "Nasrin!
Na gode. Ba zan taɓa mantawa da ke ba a
rayuwata ba. Ke ce mace ta farko da kika taɓa
sona na tsakani da Allah ba dan kyawuna ba,
ba dan kudina ba, ba dan martabata ba. Na fi
bola abin tsantsani amma duk da haka kika ji
kina kaunata.'
"
Kuka ya ci karfinsa yayin da Nasrin ma
kukan take. Mahaifiyar Jalo tana laɓe a bakin
kofa tana rusa kuka dan duk tana jin abinda
suke cewa.
Mamaki ya hana Malaika rufe baki jira
take ta ji Jalo ya amince ta tashi ta rike Nasrin
ta ce baza'ayi wannan taɓargazar a gabnta ba.
Sai Allah Ya sa bai amince ba sai ta ji dadi,
amma tà fara tuhumar Nasrin da ciwon taɓin
hankali tunda take son mai larura kuma talaka
duk da kyau da dukiya da Allah ya yi mata.
Nasrin ta sharce hawaye ta ce, "tun da
nake a rayuwata ban taɓa ganin mutumin da ya
taɓa birge ni irinka ba, a koda yaushe ina cewa
96 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
'DAMA NI CE Jalo, da ma in zama kamar ka, Da ma in kasance tare da kai.. . .”
Ya yi sauri ya katse ta yala magana cikin kuka ya ce, “ni nake sha'awar DA MA
NI ne Nasrin, dama in zama ke, Dama ni ne
nake da lafiya kamar ki. Kada ki yi fatan ki
zama ni.
"
Nasrin ta ce, "Allah Ya na sonka kuma
Allah zai baka ladan tawakkali. Ka yarda in
kasance tare da kai Jalo, na yarda na hakura da
komai na jin dadin rayuwa."
kuka.
Mahaifiyarsa ce ta shigo da sauri tana
Ta rungume Nasrin ta ce, "Nasrin ina
kika shiga tuntuni, baki hadu da Jalo ba? Da
ace mun san ki ada da bai auri Rayyana ba.
'DA MA ke ce' uwar 'ya'yansa mun san zaki
zauna da muda amana, nasan za ki zauna da
mu a cikin kowanne irin hali muke ciki. Mun
gode da kauna, amma Allah bai ga damar ku
zauna tare ba tunda kun hadu a kurarren lokaci
a sanda Jalo ya zama hoto."
"
Su dukka ukun kuka suke yi.
97 Jamilu Umar Tanko JUT
CAMA NI CE...2 SER
Nasrin ta kara kankame Mama ta ce,
"Kada ku hana ni zama da zaɓin rayuwata, ui
na zabe shi a haka zan zauna da shi har lokacia
mutuwata.""
Mama ta girgiza kai ta ce, “mu ma bamu
ki ki ba amma shi kansa Jalo ba zai yardaba,
haka nima ba zan yarda ba balle iyayenki.
Haba Nasrin kada ki makance alhali kina da
idanuwa, kada ki zama kurma alhali kina ji da
kunnuwanki, kada ki haukace da gangan alhali
kina da hankali. Ba kya ganin halin rashin
lafiya da yake ciki?Ba ya bukatar mace yanzu
ma da a rayuwarsa. Mun godewa Allah
Yabashi dama ya yi aure aure ya haifi biyu kafin ya
zama haka. Ni ce ya zame min dole ni uwara,
na kashe aurena dan in zo in zauna da shi. Ina
addı:'a Allah kada Ya dauki raina da wuri dan
in zauna da dana in ci gaba da kula da shi. Ina
addu'a kada Allah Ya dora min ciwon da zan
kasa kula da Jalo."
Jalo ya rike kai ya yi kuka ya gaji, ya
dago ya dube su ya ce, "Allah kada ka fara
kashe Mamana kafin ka dauki raina."
98 Jamilu Umar Tanko JUT
DAMA NI CE...2
Mamaki ya hana Malaika rufe baki da
alama itama ɓurbushin tausayinsu ya rufto
mata. 5
Ta tashi tsaye ta fita da akwatinta ta
dauko jakar Nasrin ta fito da ita sannan ta fita
ta tare Masu acaɓa biyu dan suna ta shigowa da
mararsa lafiya. Ta yi ta kwallawa Nasrin kira ta
zo su tafi, amma Nasrin batagama yin sallam?
batana tare da su Jalo.
ya
h
Nasrin ta durkusa a gaban Jalo takudi.
bata account number sa zata turo masaidi yana Ya girgiza kai yace baya bukat yiwa 'yan siyasa rubutu suna nsa yadda ya kamata. Addu'arta kawai ke bukata shima yana nan yana yi matatan alkhairi ta sami
miji na gari.
Nasrin ta shaida masa gara ta koma
Amerika wan mahaifanta