Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 6
ta zauna acan ba zata sake dawowa Najeriya ba kuma zata ci ko Allah Zai sa ta sami asibitin da suka kware akan ɓangaren ciwon. gaba da bincike akan ciwonsaima zata ci Ya yi mata godiya sosai, Malaika ta zo ta ja hannunta suka fito, Mama tana biye da su 99 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 tana kuka tana godiya, ya yin da Jalo ya kece da kuka ya dafe kai ya ji son Nasrin tamkar ya fasa masa kahon zuciya, amma babu yadda zai yi ne. Nasrin ta kwaso kudin Jakarta kakaf ta bawa Maman Jalo kadan ta rage na motarsu, ta ce Mama ta yi mata kokarin neman lambar Account ta turo mata zata taimaka musu da kuG. Ma'aikata suka rugo da gudu suna yi mata allama,nan ma ta tuna da wasu kuɗaden a wani diihun Jakarta ta kwaso ta yi musu rabon dubu-dubu, sai murna ta kama su. Nasrin da suka hau acaɓa suka tafiyayin da kuka ya tokare Nasrin, dadi ya ruftowa Malaika ta shaki iska mai sanyi. A cikin motarsu dagadda zuwa Abuja ne Nasrin ta bude wayarta ta hau facebook anan ta ga rubutun Jalo. Tabbas ya yi rubutu karara akanta suna ne kawai bai ambata ba. Amma ya suffanta ta da mace ta gari kuma duk wanda ya aure ta ya yi dace a duniyarsa da lahira. Daga karshe ya yi mata addu'a Allah Ya bata dukka alkhairan da suke cikin rayuwarta ta duniya da lahira. . 100 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 Nasrin ta tsinci Kanta tana mai murmushi mai hade da hawaye, Malaika tana gefe tana harararta dan ita haushi take bataba tausayi ba. Kafin su shiga Abuja Nasrin ta yiwa Zainab waya ta shaida mata sun kusa shigo Abuja ta aiko direba ya zo ya ɗauke ta a tasha. Dan haka suna sauka suka hango Direba yana jiransu, ya zo da sauri ya ɗauki jakunkunansu ya saka a but suka shiga mota suka nufi gida. : Nasrin ta kula Malaika tana ta fara'a tana yi mata hira dan a shinya, amma Nasrin ta gama harka da ita har abada, tasan itama zata guje ta idan Allahya dora mata larura ta rashin lafiya ko ta talauci. Dan haka Malaika ba abokiyar zama ba é DAMA NI CE...2 BABI NA GOMA SHA BIYU ed climb shansind an olay ABUJA... ediyszust shunda ght be any Suka isa gida, Zainab ta tare su da fara'a tana yi musu tsiya tana kiransu da aminan juna, ayi faɗa a sy hose ab as sy transtil Nasrin ta sha kunu bayan sun gaisa tay wuce cikin dakinta ta yi wanka ta canja kaya ta shirya. fito ta nemi shaya ta iske Malaik sha saboda yunwa take ji, ta yi zubin abinci da karig uku, sai turawa kawai take yi tana ci tanag murmushi tana zare ido. Zainab tata shaidawa Nasrin cewars Dr.Hala ta dawo daga Amerika shekaranjiya, Iyayensu sun bada sako ta kawo musu dan haka ta je ta karɓo musu. Nasrin ta ce gobe zata je ta karbo musu, Insha Allah. Zainab ta sami waje ta zauna a kusa da Nasrin Wacce take lasar romon farfesu ba tare 102| Jamilu Umar Tanko JUT ufust | For K DAMA NI CE...2 da ta iya cin naman kazar ba. Zainab ta shiga jero mata tambayoyi akan in da suka je? Nasrin ta yi shiru ta ki yin magana sai can jimawa sanda ta ga damar bata labari sannan ta fara bata labarin Jalo, hawaye na zuba daga idanuwansu su dukka, daman Zainab uwar tausayi har tafi Nasrin tausayi. Suka sha kuka,Malaika tanazaune a gefe tana kallonsu ta na mamakin yadda masu kudi suke zubar da hawayensu a banza akan talaka. Da Nasrin ta gama abinda take yi a falo cewa Zainab ta nunawa Malaika boskwata(Boy's Quarter) dan batason damu, ta ba zata kara zama daki daya da Malaika ba. Nasrin ta shiga daki ta kulle kanta tabbas ba zata fito ba sai gobe. Bayan ta idar da sallar isha'i ta jawo wayarta ta ga kiran Jalo har sau uku nan da nan ta bi baya ta kira shi. Bayan sun gaisa ta bashi hakuri akan bata kusa da wayar ne a sanda ya kira. Ya tambaye ta gajiyar hanya sannan suka yi sallama suka kashe waya. Ta hau facebook akan computer ta, ta sami lokaci a nutse ta karanta sannan itama ta 103 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 suffanta shi da Miji na gari mai sanin y kamata ta tura masa. Ta kira Dina ta bata labarin abinda ya faru a Jalo da yadda suka iske shi. Sai hankalin Dina ya tashi matuka ta dauki dogon salati da kururuwa. Nasrin ta kasha wayar da sauri tana zubar da hawaye. Ta kwanta ta yi shiru tana tunani, bata san sanda bacci ya dauke ta ba saboda gajiya. Bata farka ba sai da asuba bayan ta idar da sallah ta koma bacci sai karfe goma sha biyu ta tashi ta yi wanka ta shirya ta fito, dauke da mukullin mota zata je gidan Dr.Hala, ta yiwa Zainab sallama ta fice. Sai ga Malaika ta zaro gyale da gudu ta biyo bayan Nasrin tana yi mata magana, Nasrin bata kula ta ba ta shige mota ta kunna sai g Malaika ta daka tsalle ta shige gidan gaba. Ta dubi Nasrin ta yi murmushi ta ce, "Kawata wai har yanzu fushin kike yi min? Dan Allah ki yi hakuri." " Nasrin ta dube ta da gefen ido ta kawar da kai gefe ta ci gaba da tukinta, daMalaika ta ishe ta da magana sai ta kure rediyon motar da karatun kur'ani. Basu tsaya a ko inaba sai a 104 Jamilu Umar Tanko JUT ya DAMA NI CE...2 Asokoro kusa da gidan shugaban kasa, gidan Dr.Hala kenan. Nan fa Malaika ta bude baki tana kallo fuskarta cike da farin ciki.Suka wuce kai tsaye cikin katafaren get din gidan amma ba'a bude masu har sai da aka kira Dr.Hala a waya, ta ji muryar Nasrin sannan ta yarda a bude musu su shigo. Malaika dai bata daina yi da bakinta ba. Tana faman santi tana kiran "Allahu akbar! Allahumma arzukuni. Wayyo arziki.' " Haushi ya rufe Nasrin ko kallonta ba ta yi ba ta fito ta shiga gidan, Malaika tana biye da ita da sauri har suka isa katafaren falo mai kama da aljannar duniya. Nan fa Malaika ta yi ta taɓe-taɓe abubuwan da bata taɓa gani ba. Aka turo 'yar aiki aka ce su shigo daki. Suka wuce zuwa wani katafaren daki wanda girmansa ya kusa kaiwa gidan malaika gaba daya. Setin gado ne da kujeru a gefe ga kayan kallo ga sanyin Ac da kamshi ko ta ina. Sai yanzu Malaika ta gane wacce suka zo gidanta. Ashe wannan hadadiyar matar nan ce 105 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 likita da suka hadu a Kano. Tabbas mafarkin ya fara zama gaske gata, ga hadaddiy dattijuwa. Ta kudiri niyyar ba zata fita daga gidan nan ba sai ta yi mata kwanaki biyu sannan ta nemo mata aikin yi koda na kula da gyaran daki ne. Su ka zazzauna akan luntsumaluntsuman kujeru suka duka suka gaishe ta Ita dai Dr.Hala bata ma gane Malaika ba sai da ta ishe ta da surutu da kwatance sannan ta shaida ta. Haushin Malaika ya na ta nukurkusar Nasrin, sannan ta gyara zama ta fara tambayar Dakta lafiyar iyayenta.Dr.Hala ta fayyacewa Nasrin farin cikinta yadda Mamarta ta karɓe ta.Nasrin ta ji dadi da ta ji haka suka ci gaba da hira. 'Yan hidimar gida suna%. ta sintiri suna jere musu kayan marmari na ci dana sha a gabansu. Dr. Hala ta duba agogo ta zare gilashin dake fuskarta ta ce, “bari in yi alwalla. Ku sha lemo barizan yi sallah.' " Tamike a nutse ta tura kofar katafaren badaki sai kamshi ne yake busowa, Malaika ta 106 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 kama baki tana kallon aljanar duniya, daga nan ta sake gasgatawa kudi ya yi a rayuwa dan haka ko ta hali kaka sai ta nemo shi. Ta damu Nasrin da surutu amma ba ta tanka mataba, lemo ta zuba kaɗan a kofi ta sha ta ci gaba da karatun jarida, yayin da Malaika ta yi goho ta dinga aika kayan dadi zuwa ga birnini tunbinta, Nasrin tana harararta da gefen ido amma bata yi mamaki ba kauyanci da jahilci ne babban ciwon da yake damun Malaika. Dr.Hala na fitowa daga bandaki Nasrin ta shiga don yin alwalla itama. Malaika ta gyara zama tana murna ta sami damar yiwa Dakta Magana son ranta. Malaika ta kalle ta, ta yi mata murmushi ta ce, "sannu ranki ya dade. Ki godewa Allah dan Allah Ya yi miki komai a duniya, DAMA NI CE ke." Dr.Hala ta dube ta ta yi murmushi ta ce,"Hmmm! Malaika! Ni kuwa tun dazu nake kallonku ina cewa a raina DAMA NI CE ku, kar ki yi fatan ki zama ni. Ki tambaye ni me yaşa nace haka?" 107 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 Malaika ta gyara zama ta na murmushi kai ka ce anyi mata albisuir da gidan aljanna saboda tana magana kai tsaye da mai kudi. Malaika ta ce, "Me yasa kika ce haka? Dube ni fa talaka, ba ni da ko sisi ciki da waje, ba ni da gida ko fili balle Motar hawa, ba ni da kayan sakawa sai tsummokare. Allah Yaba ni miji talaka, ga yara sun taso a cikin talauci, iyayena a kauye talakawa ba su da komai...."" Dr.Hala ta yi dariya ta girgiza kai ta ce, "Allah sarki, 'DAMA NI CE'ke. ... Amma bari in nuna miki wani abu da za ki tabbatar da abinda nake nufi. kin gani." " Malaika ta juya da sauri ta kurawa Dakta ido tana kallon abinda ta nuna mata, sai idanuwanta suka hango mataabinda ya gigita ta, Malaika ta kwalla ihu ta tafi a guje ta nufi kofar bandaki wajen Nasrin, suka ci karo da Nasrin tana fitowa. Malaika ta rirrike Nasrin jikinta yana rawa ya yin da hawaye yake zuba daga idanuwanta. Muryarta na karkarwa ta ce, "Nasrin! Zo mu bar gidan nan yau idanuwana sun hango 108 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NICE 2 abinda ban taɓa gani ba. Ashe haka masu kuɗin suke? Gara in koma kauye wallahi bazan zauna a gidan nan ba. Ke dai ki zo mu tafi zan fada miki abinda na gani.' " Nasrin ma ta gigice ta rirrike Malaika tana tambaya ta ce, "meya faru? Me kika gani? Fada min mana." " Malaika tana hawaye tana nuna Dr.Hala hannunta na karkarwa ya yin da Nasrin ta dubi Dr.Hala ba ta ga komai ba, Dakta dai tana sallah amma a zaune akan kujera. Nasrin ta juya ta dubi Malaika, taga har yanzu jikinta rawa yake kuma ta na ja da baya ta ki sakin jiki. Daga nan Malaika ta buɗe ɗaki ta fice da gudu ya yin da Nasrin ta bi ta da gudu tana so ta damko ta amma ina Malaika ta wuce falo uku sannan ta keťa kicin, ta gangara farfajiyar gidan, ta na dankara gudu gami da ihu ta na neman agaji. Nasrin tana biye da ita da gudu itama tana neman agaji tana cewa "a tare-a tare" Nan da nan ma'aikatan gidan da masu gadi suka kawowa Nasrin dauki, aka dinga tsere da Malaika tuni ta yi tsalle ta kama get 109 | Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 tana neman hanyar dira, saboda ta ga halaka. Haka aka damko ta aka sauko da ita, nan take ihun da take yi ya karu kai kace ido ake kwakwale mata. 3 Nasrin ta rasa abinda yake yi mata dadi Malaika ta kunyata kwarai, koma dai me ta gani bai kamata ta tayarwa da kowa hankali haka ba. Tabbas Malaika ta zame mata annoba a rayuwarta, hawayen takaici ne kawai ya ke kwaranya daga idanuwan Nasrin. Tana ta addu'a a zuci Allah ya rabata da Malaika dan ta zame mata barazana a rayuwarta. Dakayar aka samu Malaika ta nutsu ta daina ihu, Nasrin ta kama hannunta suka shiga cikir falo amma fa Malaika ta ki yarda ta koma cikin dakin likita saboda tsoro. Nasrin ta shiga dakin Dr.Hala a sanyaye ta iske ta har yanzu tana salla a zaune akan kujera. Ta shinfida abin sallah ta tayar da ikama. Bayan sun idar sun dade suna ta kwararo addu'oi kowacce tsakaninta da ubangijita take karanto abinda da ya dame tana neman agaji a wajen Rabbil samawati.Bayan sun shafa sai suka kalli juna + 110 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 suka yi murmushi a lokaci guda sannan suka gaisa. Nasrin ta ce, "Mummy Hala kina jina da kawata ta firgita ta fita da gudu ko? Me yake faruwa ne?" Dr.Hala ta kyalkyale da dariya ta ce, "ina Malaikar take?" Nasrin ta nuna da yatsa ta ce,"tana falo ai ba zata shigo ba." Dr.Hala ta ce, “mu je falon in bata labarin rayuwata ko zata daina sha'awata.' " Suka fito falo suka iske Malaika ta yi tagumi, tana ganin Dr.Hala sai ta zabura ta gyara zama ta sake takurewa. Bayan sun zazzauna akan kujera kowaccensu tana kallon Malaika tana dariya, sai Malaika ta zaci sun shiryo wani abu ne da za'a cutar da ita ta fára tunanin ma ko a gidan yankan kai take. ". Dr.Hala ta dubi Malaika ta kira sunanta cikin marainiyar murya ta ce, "Malaika! Na fi sha'awar rayuwarki akan rayuwata shiyasa na ce kada ki yi fatan ki zama ni. Ga kudi ina da shi, ga kyau ina da shi amma bana jin daɗin 111 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 rayuwata. Da za'a kwace komai a bani lafiya kamar ki da na ji dadi, da za'a kwace dukiyata a bani haihuwa kamar ki da na ji dadi, da za'a Kwace dukiyata dukka a ba ni miji kamar ki da na ji dadi." Sai Nasrin da Malaika suka hada ido suka juyo gaba daya suka kalli Dr.Hala a lokaci guda, cike da dimuwa. Hala ta surnano da hawaye ta sunkuyar da kai kasa ba tare da ta kara cewa komai ba. Hankalin Nasrin ya tashi. Ta gyarazama ta fada cikin harshen Turanci ta ce,"Mummy ki bamu tarihin rayuwarki saboda ya zama darasi a rayuwarmu, musamman Malaika da take ganin kamar kudi ya fi komai muhimmanci a rayuwa. LABARIN DAKTA HALA Ta ce,"sunana Hafsat ana kirana da Hala kasancewar Mahaifiyata balarabiya ce yar asalin kasar Turkey, Mahaifina bafillatanin Adamawa ne. Ya je karatu can suka hadu suka yi aure aka haife ni, a wajen haihuwata ta rasu ta barni 112 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 a hannun Mahaifiyarta dan haka a hannun Kakata na girma." Nasrin ta gyara zama ta langwaɓe kai cike da tausayi. Ya yin da Malaika ta fara jiyo harkar Jajayen fata a ta san tabbas Babanta mai kudi ne. Dr.Hala ta ci gaba da cewa "Mahaifina ya dawo kasarsu Najeriya ya yi aure-aurensa amma ya kan zo ya ganni jifa-jifa nima na kan ZO. Na tashi a kasar Turkiya a in da na yi karatuna gaba day daya, na tashi a cikin rashin kwaɓa babu tarbiyya, na hadu da saurayin da nake matukar so mai suna Jaddi tare muka yi karatu a jami'a babu abinda muke yi sai watsewa, na sha yin ciki ina zubarwa ashe kwayayen haihuwar gaba daya aaawa na zubar. Na ashe zama cikakkiyar likita amma babu aure na zaci Jaddi yana so na ne da gaske kuma zai aure ni amma ya ki aurena, kullum yana yi min karyar zai aure ni amma daga karshe na ji labarin ya auri wata a ɓoye. Hakan ya sa na hargitsa na je na cinnawa gidansa wuta ya kone shi da amaryar amma ba su mutu. " 113 | Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 Nasrin da Malaika suka zazzare ido gami da dafe kirji. Nasrin ta tambaya "Me yasa kika aikata wannan danyen aiki?" Dr.Hala ta yi murmushin takaici ta ce, "sharrin zuciya, dan haka aka ɗaure ni na tsawon shekaru dakyar aka samu aka fito da ni bayan na shekara biyar cur a gidan yari. Dan daurin shekaru sha biyar aka yanka min da aka sami canjin Gwamnati na sami alfarma. Na dawo 'yar shaye-shaye saboda bakin cikin rayuwa kullum a buge nake hakan ya sa kowa ya tsane ni, Kakata kadai ke kaunata ko da yaushe tana yawo a gidan rawa (club) tana kamo ri dan acan nake kwana a buge. Watarana nasha na bugu ina tukin mota na yi mummunan hatsari a take kafata ta hagu ta tsinke a take ta fita daga jikina. Yanzu haka bani da kafa sai ta karfe da ita nake amfani." Ta bude musu kafar ta sa hannu ta kwance kafar sai ga kafar karfe a hannunta. Malaika ta daka tsalle ta fado kan Nasrin ta kankame ta tana salati.. cinud teed 114 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 Hankalin Nasrin ya tashi ta fara karanto"Innalillahi wa'inna ilaihi raju'un. Allah Ka sa mu gama da duniya lafiya. Allah Ya sa mu yi kyakykyawan karshe.' " Dr.Hala ta ɓarke da kuka yayin da Nasrin da Malaika ma suka rungume juna suna kuka. Har na wani lokaci. Malaika ta koma kan kujerarta ta zauna ta yi tagumi tana kallon kafar karfen da Dr.Hala ta wurgar a kasa tana ta godewa Allah a zuciyarta da Allah Ya barta da kafafuwanta da hannayenta ba'a gutsiri komai daga jikinta kan ba. Dr.Hala ta ci gaba da cewa "a sanadiyyar wannan bakin cikin ya sa Kakata ta hadiyi zuciyata ta rasu, na zamanto sai ni kadai a gidan daman 'ya'yanta da jikokinta sun tsane ni sai tsanar ta karu suna kirana da wacce ta kasha musu uwa. Hakan ta sa suka kore ni na haɗo na dawo Najeriya garin Babana Babana Adamawa, Alhamdulillahi! Yana nan a raye tare da iyalansa matansa uku da yara ashirin da hudu. 115 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 komawa jami'a na zama Ya yi murna da ganina anan na sake tabbar likita (consultant) na fara aiki a asibiti. Na yiwa kaina faɗa na daina shan komai sannan na koma ga Ubangijina gaba daya na koma bautarsa ina tuba akan Ya yafe min kurakuren dana tafka a baya. Allah mai jikan bayinSa Ya sa na sami nutsuwa sannan ya hore min arziki da hanyoyin daukaka da samun kudi. Na yi tashe a garinmu a babban asibiti saboda na san abinda nake yi, na san makamar aiki har na bude asibiti nawana kaina. Daga baya na shiga harkar siyasa na san manyan gwamnati har na dawo Abuja da zama na kuma sami sukunin tafiya Amerika na karo karatu har Allah ya kawo ni wannan matsayi ina kusa da shugaban kasa." 2 Akt Akbar Nasrin ! Yaya batun ta langwaɓe aure kuma kai da ta haihuwa ce, "Allahu ?" Dr.Hala ta girgioza kai ta ce, "Allah bai sa ina da miji a duniya ba, babu irin kokarin da banyi ba, haka mahaifina da abokan aikina duk mai kaunata sai ya yi kokarin hada ni da wani mu yi aure amma sai Magana ta fara nisa sai su 116 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 fasa. An ce bakin aljani ne, an ce asiri ne amma ni na yarda da cewa daga Allah ne. Yanzu ina da shekaru hamsin da hudu ban taɓa aure ba har na fitar da rai, bana bukatar in yi auren ma. Na riga na nakasa duk sanda aka hango kafar karfe sai su gudu ina zargin wannan ma yana cikin matsalata.' " Nasrin ta dora hannu aka zata fasa ihu ta daure ta sauke hannun, hawaye na zuba daga idanuwanta. Dr.Hala ta matse hawaye ta ce "Malaika! Tun ranar da na fara ganinki na ke fada a raina DA MA NI CE ke kina da yaranki a gidan mijinki. Ni na rasa wannan kuma ya wuce ni har abada, bazan taɓa yin aure ba balle ir haihu. Ba zan taɓa dawowa daidai ba kamar ki tunda na rasa kafata na zama gurguwa. Ba ni da masu gadon uwar dukiyar da na tara saboda Mahaifina ya tsufa lokaci kawai yake jira babu abinda zai yi da dukiyata sai dai yaransa su gada wadanda ba kaunata suke yi ba ko kadan. Ni kadai mahaifiyata ta haifa ta tafi ta bar ni. Amma ina tallafawa marayu da gajiyayyu kuma ina rike su har in aurar." 117 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 Kuka ya ci karfin Dr.Hala har ta kasa ci gaba da magana. Nasrin ta zabura ta je ta dauko kafar ta mikawa Dr.Hala ta ce, “ki mayar da kafarki kada ki damu lilkita na ki mai sauki ne idan kika ji labarin Dr. Jalo. Da Dr.Jalo zai ganki da sai yace'DA MA shine ke, saboda shi baya tafiya, baya iya tsayar da fitsari da bayan gida, ya rasa Lakarsa wanda bana tunanin akwai maganin da za'ayi masa ta dawo dai dai har abada." " Dr.Hala ta tsagaita da kukan ta kuarawa Nasrin ido sanan ta tambaya "waye Dr.Jalo? Nasrin ta ce, "wani abokina ne da muka hadu a facebook kuma Allah Ya jarrabe ni da matukar kaunarsa sai bayan da muka ga juna sannan na tabbatar da yadda yake. Likita me ya kamata ya yi ya sami sauki ko kuma ina ya kamata ya je ayi masa aiki ya warke? Ina son Jalo zan iya salwantar da duk abinda na mallaka da wanda iyayena suka mallaka dan in ceto rayuwarsa. وو Malaika ta zabura ta kalli Nasrin cike da mamaki ta sake gasgata cewar lafiya ta fi 118 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 komai muhimmanci a duniya ba kuɗi ba. Ta. sake yarda babu abinda ya fi soyayyar gaskiya dadi a duniya hakika Nasrin tana kaunar Jalo sona hakika, ba dan kudinsa ba, ba dan kyawunsa ba. Dr.Hala ce ta katse tunanin da Malaika ke yi ta ce, “maganar gaskiya idan Laka ta taɓu sai dai dibaru,shawarar da za ki bashi ita ce kice masa idan ya sami kamar awa guda ya yi kokari ya mike tsaye yana dogara sanduna yana jan kafafuwan tunda kin ce hannayensa suna amfani. Ya kokarta ya shiga bandaki ya sa hannu ya matsa cikinsa da karfi da mararasa ya turo bayan gida da fitsari su fito sai ya koma bayan kamar awa gida ya sake komawa ya yi haka zai yi ta yi. Za ki ga ya daina amfani da katata kuma zai daina zubowa ba tare da ya shirya ba. " Nasrin tana sauraronta tana gyada kai da alama ta fara jin farin ciki a kalla dai zai rage wani abu na alamar samun sauki. Ma'aikata suna ta safa da marwa suna jere musu abinciccika kala-kala akan tebur 119 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NICE...2 amma tashin hankali ya hana gaba dayansu ci. A haka suka yi sallama suka tai. Dr.Hala ta bawa Nasrin sakon daloli da iyayenta suka aiko mata da kayan jarirai na Zainab, ta bawa Malaika atamfa super Holland kyauta. Su na godiya suka tafi suna tafe a mota kowaccensu ta yi jugum babu wacce ta ke iya magana. Haka suka shiga gidan Zainab sokoko babu laka a jikinsu, kallo daya Zainab ta yi musu ta tabbatar suna cikin damuwa amma ta yi zaton fadan suka tafka a hanya. Bayan Nasrin ta zazage sakon a gaban Zainab sai farin ciki ya kama Zainab. Ta tambaya lafiya ta gansu basa walwala. Nasrin ta bata labarin Dr.Hala gaba daya, sai Zainab ta gigice ta daga hannu sama ta na yiwa Allah godiya da Yaba su rai da lafiya da abinda lafiyar zata ci. Gaba dayansu suka yi tagumi ba tare da wani ya iya ci gaba da magana ba har zuwa lokaci mai tsayi. Malaika ta fasa kuka ta ce, “na ko yi darussa, na lura da cewa damuwar masu kudi 120 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 har ta fi ta mu ta talakawa. Wallahi a zatona masu kudi ba su da matsalą ko kadan sai na iske ko da yaushe idanuwansu suna zubar da hawaye har ma suna sha'awar da DA MA su ne mu, tabbas lafiya itace komai. Zan koma gida in zauna in yi hakuri da yadda Allah ya ajiye ni.' Nasrin ta matse hawaye ta ce, “nima zan bar kasar nan jibi in koma gaban iyayena in zauna bazan iya jira har sai na gama bautar kasar ba. Na rasa farin cikin rayuwata Dr.Jalo, na ji gaba daya rayuwata a Najeriya bana jin dadi. Zan koma in da Allah ya ajiye ni in ci gaba da addu'a Allah ya hada ni da farin cikin rayuwa amma kudi ba komai ba ne idan babu farin ciki babu lafiya." Su ka yi tagumi ba tare da sun iya magna ba. Can Nasrin ta mike ta dauki mukullin mota ta shiga daki ta dauko passport dinta da Jakarta ta fito da alama wajen sayen tikiti zata tafi ta fice da sauri. Malaika ta tashi ta tafi tana haɗa kayanta a cikin akawati da alama ta yiwa kanta fada ta ga bala'in da ya fi nata. 121 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 *** Washe gari da safe misalin karfe takwas na safe Malaika ta tashi ta shirya ta fito da akwatinta ta bubbugawa Nasrin kofa, kasancewar Nasrin din ma ba bacci take yi ba tana ta waya da Jalo tunda asubah. Ta shaida masa shawarwarin da Dr.Hala ta bayar, kuma ya yi Amanna. Daga karshe ta yi masa sallama a kan washegari zata bar kasar nan ba zata dawo ba, amma ta yi masa alkawarin yin bincike a game da masu irin larurarsa in har an sami mafita zata ciko a kai shi zata dauki nauyin yi masa aikin. Ya yi mata godiya sosai gami da yi mata fatan alkhairi. Ya nuna matukar damuwarsa da ya rasa ta amma ta ce kada ya damu akwai waya akwai facebook ko da yaushe zasu din ga haduwa. Bugun kofar da Malaika ke yi ta sa ta katse wayar ta je ta bude sai ga Malaika a tsaye 122 Jamilu Umar Tanko JUT DAMA NI CE...2 a bakin kofa da akwatinta da alama ta shirya tafiya gida. Nasrin ta yi mata iso ta shigo ta zauna a sanyaye, bayan sun gaisa sai Malaika ta fara magana cikin marainiyar murya. Ta ce "Nasrin! Na gode da kulawarki. Na gode da jahadin da kika yi akaina har sai da kika ga na fahimci rayuwa. Ina miki fatan ki gama da duniya lafiya ki sami rabauta da aljanna. Na gode da dukka hidimomi da kika dade kina yi min. Na gode da jajircewa da kika yi akan kokarin gyara aurena da Shamaki. Lallai na zalunci kaina, shamaki bai cuce ni ba ni na cuce shi. Idanna fada miki cin mutuncin da na yi masa kafin ya rubuta min takardar saki hakika bana jin har abada zai iya yafe min ya dawo ya ci gaba da zama da ni." Malaika ta rushe da kuka yayin da Nasrin ma hawaye yana surnanowa daga idanuwanta ta kurawa Malaika ido ba tare da ta san abinda zata fada mataba. Sai girgiza kai ta ke tamkar kadangaruwa. Malaika ta ci gaba da cewa, “abinda ya fi tayar min da hankali ma shine yadda iyayena 123 Jamilu Umàr Tanko JUT DAMA NI CE...2 suka tsine min, auren Uwata da Ubana ya rabu a dalilin na zaɓi in taho Abuja akan na ki yin biyayya a maganarsu naki yin zaman aure. Na shiga a uku na lalace, ta inazan fara harhado rugurgujajjiyar rayuwata alhali ta rugurguje?" Nasrin ta taso da sauri ta dafa kafadar Malaika tana lallashi ta ce, “tabbas kin tafka kuskure amma ba ki makara ba tunda iyayenk: suna raye kuma Shamaki yana raye na san ba yi aure ba kuma har yanzu na san yana sonki, zai yi hakuri da ke saboda yaranki da kuma kaunar da yake yi miki.' 99 Malaika ta goge hawaye ta

Chapter 5 of 6