Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 7
har bata gani sosai saboda yunwa. Ta isa kofar shiga falo, gami da yin sallama sannan ta daga labulen falon ta shiga. Maimakon ta ji muryar Zainab sai ta ji wata murya ta amsa mata. Muryar ta yi mata kama 153 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 da muryar da ta taɓa sani amma bata gasgata ba har sai da ta shigo tsakiyar falon ta kalli mai maganar sosai ta gasgata ba gezau ba ne gaskiya ne, ita din ce kuwa. Malaika Shamaki. ta gani zaune akan luntsumemiyar kujera ta dora kafa daya kan daya tana shan AC ga remote din talabijin a hannunta tana canja tasha yadda take so, ta na karawa kuma tana rage murya. Ta cokalo daurin dankwali gaban goshi, gami da saka wani kwaftareren gilashi baki a fuskarta. Nasrin ta ji wata gagarimar fargaba ta dira a cikin zuciyarta, ta ji tamkar aradu ce ta sauko a kahon kalbinta. Ta ji rugugin takaici ya taso mata. Ta yi kamar ta dora hannu akai ta rafsa ihu. Sai ta tuna da cewa duk sanda bala'i ya diro maka ka lakanci karanta "Innalillahi wa inna ilaihi raju'un.' " Ta fada a lokacin da take kokarin sulalewa, ta sulale ta zauna akan kujera dan kafafuwanta ba zasu iya daukarta ba. Malaika ta taso da sauri cinkin murna zata rungume ta tana fadin "oyoyo ga kawata ta dawo." 154 Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE 1 Jakarlap-top din Nasrin ta sulmiyo daga kafadarta zata fadi kasa. Malaika ta yi sauri ta kama mata. Nasrin ta daga mata hannu alamar kada ta matso kusa da ita. Nasrin ta zauna ta dafe kai tana ta jujjuyawa, sabbabin ciwuka ne suka taso mata, zazzaɓi da ciwon kai suka hadu da yunwa, gajiya da bakin ciki suka cakuɗe mata. Malaika na tsaye akanta tana kallo tana fada a ranta "Tunda na zo bazan tafi ba, ko zaki mutu wallahi, irin wannan daula da na shigo kuma in tafi. Ashe ma na zama sarauniyar wawaye ta shekara. Sai dai idan an raba ni da raina sannan za'a iya raba ni da gidan nan, zama a Abuja daram ba zan koma Kano." " Nasrin ta ci gaba da mamakin ta in da Malaika ta diro, ta shigo gidansu alhali ita bata taɓa faɗa mata sunan unguwar da take a Abuja ba. Ta ma daina amsa wayarta ko ta kira ta, tun ranar da ta goge lambobinsu. Shin Malaika mutum ce ko aljana?Hakika na ɗauko ruwan dafa kaina. Lallai na jajiɓowa kaina masifa. Watakila ma na dauko ajalina da hannuna. 155 Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 Yaya zan yi da wannan natacciyar matar, data nace min? Ina zan kai hakkin auren da ta kaso a dalilina? Ta yaya zan wanke kaina a wajen Shamaki ya yarda ba ni na ce ta fito ta biyo ni Abuja ba? Allah Ka ga zuciyata Ka fitar da ni daga cikin wannan kangin da na shiga. Ka shiga tsakanin na gari da mugu. Ya Allah kada Ka bari Malaika ta cutar da mu tunda da kyakykyawar niyya na karɓe ta." Nasrin take tambayar zuciyarta kuma tana ta addu'a. Suna cikin wannan hali sai ga Zainab ta fito daga kicin da sauri dauke da faranti ta jero abinci kala-kala wanda ta shirya shi na musamman domin bakuwarsu Malaika. Ta sankare a tsaye da ta ga yanayin da Nasrin ta shiga, ta tambaya a gigice, "Nasrin! Lafiya ko jikin ne?" Nasrin ta dago da jajayen idanuwanta, ta dubi Zainaba cikin sanyin jiki ta ce, “ta ina matar nan zo mana gida? Ta yaya ta san gidan nan ta zo, dan ni ban gayyace ta ba?" Zainab ta cika da mamaki ta ce, "Malaikarki ce fa wacce kike ba ni labarinta kullum. Ko ba ki gane ta ba ne? Kin manta 156 | Jamila Umar Tanko (JUT) re DA MA NI CE... 1 wayarki a cikin daki, kina fita na ji ana ta kira na je na dauka, ta ce gata nan zata zo Abuja kun yi za'a bawa direwa waya a fadi kwatance ya kawo ta har gida,na rike waya a hannuna muna ta waya har ta karaso. Da ta isa tasha ta kira, na yiwa direba kwatance ya kawo ta.", Nasrin ta ja dogon tsaki ta harari Zainab ta juya ta harari Malaika sama da kasa, ta tashi ta shige daki a fusace gami da bugo kofa da karfi ta datse, yayin data yi arangama da wata dankareriyar tsohuwar akwatin Malaika a tsakiyar dakinta wato kaurowa ma ta yi gaba daya, babu ranar tafiya tunda ta hankaro kaya haka. Nasrin ta ji wani ɗaci ya taso daga cikin makoshinta har zuwa bakinta, ta fara zaton ɗacin ajali ne ya tunkaro ta gadan-gadan. Sai ta dau salati ta sulale ta zauna a gefen gado ta dafe kai. Malaika ta langwaɓe kai,wai nan ita abar tausayi, ta zare bakin gilashin da yake makare a fuskarta, sai hawaye ya sirnano daga idanuwanta, ta sulale ta zauna akan hannun kujera ta yi tagumi. 157 Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 Hankalin Zainab ya yi matukar tashi,kunya ta kamata, ta tafi kan tebur din cin abinci ta ajiye farantin abinci. Ta taho da sauri ta dafa kafaɗar Malaika tana lallashi, ta kamo hannunta ta kaita kan tebur din cin abinci ta zaunar, tana bata baki akan ta daure ta ci abinci ko kaɗan ne kada ta sa abinda Nasrin ta yi mata a rai ya dame ta. Sai Malaika ta kyallare ido ta hango dankareriyar kaza guda sukutun, bayan kayan ciki, kai da kafafuwan da aka cire ba'a cire komai a jikinta ba, a haka aka gasa ta a gashe tana kamshi. Malaika ta sake kanne daya idon ta kyallaro shinkafa, ta zama koriya ga karas, wake gwangwani, gami da hanta da koda duk an jere a ciki, gefe kuma salad haɗɗade ya ji kwai. Ga lemuna kala-kala da kofi a kusa gaba daya nata ne. Nan da nan ta ji ta fara fita daga cikin hayyacin dan dadi, ta fara tunanin ko jirgin tunanin nan nata da ya saba daukar ta ya kaita duniyar karya ne ya danno. Zainab ta juya baya za ta shiga ɗakinta, sai Malaika ta yi mata gwalo, ta saita masun 158 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE 1 yatsunta ta kaiwa kazar nan hari 'CAK' ta kafa mata hannu. Ta raba cinyar nan da gangar jikin, ba tare da ɓata lokaci ba ta kai mata sara ta cake ta da hakora, ta yaga ta ci gaba da taunawa. Kan kace kwabo dadi ya kaiwa kunnuwanta hari, nan da nansuka dauki zugin dadi 'zuuuu' dan tunda take bata taɓa cin abinci mai dadi irin wannan ba. Ta na ci tana fada tana nanatawa a bayyane tamkar karatu, ta ce, "Nasrin! ko za ki mutu ba zan bar gidan nan ba, sai dai ayi duk wacce za'a yi wallahi. Karen hauka ne ya cije ni da zan koma Dorayi?" Kash! Anan zan dakata. Mu hadu a 'DA MA NI CE. . . .' littafi kashi na 2 Mu ji yadda zata kaya: *Tsakani Malaika da Nasrin 159 Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE.. *Tsakanin Dr.Jalo da Nasrin. *Tsakanin Fu'ad da Nasrin. *Tsakani Shamaki da Nasrin. *Tsakanin Shamaki da Malaika Ta ku JAMILA UMAR TANKO (JUT). An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 7 of 7