Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 7
ta yi kamar itama ta barke da kuka. 127 Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 Da yake Malaika 'yar dangice jama'a daga Muntsira suka yi ta diddikowa suna zuwa gaisuwa, haka dangin Shamaki da abokansa na Bichi da na BUK suka yi ta zuwa matansu da Mazansu. Anan ne Malaika ta ga Fatima Giwa. Duk da an yi mata mutuwa amma sai da ta jinjina kyau da kudi irin na Fatima, farar shuwa kal. Ta kawo musu buhunhunan shinakafa biyu da Kudi naira dubu goma. Malaika ta dauko kwaraɓɓiyar wayarta ta karɓi lambar Fatima Giwa abin takaici kowa ya gane, bata karɓi lambar wayar kowa ba sai ta mai kudi.. *** *** *** Bayan kwanaki bakwai sannan kowa ya watse aka bar Malaika da Shamaki sai sauran yaransu guda biyu, su kaɗai jugum, sai a lokacin mutuwar ta dawo musu sabuwa fil. Malaika bata da aiki sai kuka Shamaki yana ta lallashinta. Yana ta lallaɓata duk wani abu da zai kwantar mata da hankali shi yake yi. Sun sassami kudi amma duk ya tattara ya damka 128 Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 mata dan ta ji sanyi a ranta dan ya san ita masoyiyarsu ce. Vayayi sanyi kalau da alama ta fara saduda da kyalkyalin duniya. Ba'ataɓa yi mata mutuwar da ta ji a jikinta ba sai wannan karon, kasancewar Uwa da uba da wasu kakaninta duk suna raye haka 'yan gidansu wajen su talatin suna nan da rai, da wayonta babu wanda ya taɓa mutuwa. Haka shima Shamaki bayan Mahaifinsa da yamutu yana karami bai san shi ba. Kakansa da 'yan uwansa duk suna raye dan haka sai yanzu aka fara yi masa mutuwa. Sun yi kuka sun gaji Ahmad ya tafi ba zai dawo ba. Allah ya kyautata karshenmu. shi ba. Mahaifiyarsa, vidid net Malaika jikinta Nasrin ta yi kokarinzumunci danmullum sai ta kira Malaika kala ta yi mata ta'aziyya jumata taʼaziva idan Shamaki na kusa ta ce a bashi shima. Malaik ta mika masa shima ta yi masa taʼaziyya. Ta yi mata alkawarin idan aiki ya yi sauki zata shigo Kano ta yi mata ta'azivya azıyya. melicu sist UCH IV: Malaika ta ji dadi kwarai da wannan kulawa ta sharariyar mai kudi da take yi mata. 62800s at out a omum stop det oM Schuede ennem a ovadonat 129 | Jamila Umar Tanko (JUT) Us | 020 DA MA NI CE... BABI NA BAKWAI RANAR ASABAR. .ABUJA au asabar ce, da misalin karfe goma sha daya na safe, Nasrin tana zaune a falo da kofin shayi a hannunta. Dakyar take kurɓar shayin saboda yanayin zazzaɓin da take ciki. Ita kadai ce a gidan daga ita sai wayarta da take karancekarance a facebook. Ta ci karo da sababbin rubutun Dr.Jalo tana ta bibiya amma bata yi niyyar tofa albarkacin bakinta ba. Kamar daga sama ta gan shi ya hau (online) bata yi masa magana ba dan bata shirya kwasar takaicin shariya ba, ta kanta take yi yau. Sai ta zaci mafarki take da taga ya yi mata sallam. Ta amsa, ya sake gaishe ta. Nan da nan ta gyara zama ta ji sanyin da take ji ya fara gushewa dan har zufa ta fara feso mata. Ta cika da murna a take ta amsa masa. Ya tambaye ta menene tambayarta? Me take so ta 130 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 koya daga gare shi da take cewa tana so ta zama kamar sa? Nasrin ta kaikaice ta yabe shi, ta koɗa shi, ta jinjina masa, sannan ta ce yana birge ta ne haka kawai. Da alama ya ji dadin kalamanta shima sai ya yi mata godiya data sami dama takebiye da shi. Ta nemi ya fada mata mafita game da wata matsalar aure dan taga rannan ya yi magana akantaɓarɓarewar auren Bahaushe. A takaice ta bashi labarin Malaika, sannan ta bashi labarin Shamaki kamar yadda suka bata. Ta shaida masa ta yi hira da mijin ba tare da matar ta sani ba haka ta yi hira da matar ba tare da mijin ya sani ba, kowannensu abinda ya faɗa daban ne ta rasa mai gaskiya a cikinsu. Dr.Jalo ya yi murmushi ya rubuto mata bayanai a tsare daki-daki, ya jero matsaloli ya jero mafita. Daga bayanansa ta fara samun mafitar matsalolin auren Shamaki da Malaika. Ta ji dadi sosai ta yiwa Dakta godiya daya bata dama da lokacinsa yau. Shima ya yi godiya ya sauka. 131 Jamila Umar Tanko (JUT) CE... 1 Sai Nasrin ta nemi zazzaɓi ta rasa, ta ware ragas, ta yi tsalle ta dire tana ta rawar murna ita kadai a cikin falo.Hakika mahakurci shine mawadaci. Ta jwo wayarta da karfin gwiwarta ta kira DA MA NI wayar Malaika. Malaika ta amsa amma tana ta magana kasa-kasa cikin rada, da alama ba ita kaɗai bace a in da take tana tare da mutane Malaika ta shaida mata ta fito unguwa ne sai ta koma gida zata kira ta. Nasrin ta kashe waya tana kashewa ta kira wayar Shamaki da karfin guiwarta tana, murna ta samo masa mafita, Shamaki na ganin kiran Nasrin sai ya ji ransa ya ɓaci, yayi jagejage da garin fulawa yana kicin yana kwaɓin danwake, yara suna ta kuka suna jin yunwa. Malaika ta fita unguwa bada izininsa ba. Gaba daya yana zargin Nasrin dasake ɓata masa Mata, dan ta turo mata katin dubu uku jiya shi ta siyar ta sami kudin hawa A-daidai-ta-sahu ta shiga gari. Ya na kallon wayar ya ki dauka sai a karo biyu data sake kira, ya dauka a fusace 132 Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 yana huci, Nasrin ta yi sallama sai ta ji ya ja dogon tsaki ya katse. Ta cika da mamaki bata tunanin hakan yake nufi dan haka ta sake kira, ya dauka tana gaishe shi sai ya yi mata tsawa “Menene kuma? Kawar ta ki bata nan. Ya kashe wayarsa ma gaba ɗaya. Nasrin ta sankare a zaune tana ta mamaki da takaicin abinda Shamaki ya yi mata, lallai ya wulakanta ta, ba'a taɓa yi mata irin abinda ya yi mataba a yau, ta fuskanci haushinta yake ji. Ta shiga zulumi shin ko dan bata zo musu gaisuwar mutuwa bane? To su a suwa da za zasu kullace ta dan bata zo gaisuwa ba? Yaushe suka santa ma da zai zama laifi? Gaisuwar data yi musu a waya ma ai ta isa. Kai! Ba wannan ba ne. Anya Shamaki bai fara kishi badan ya gaMalaika tana yawan zancenta da nemanta a waya?Dole da daya daga cikin wadannan abubuwan da ta zaiyano a ranta. . Nasrin ta damu da wannan yankwanawa da Shamaki ya yi mata,gashi shi ba kowan kowa ba. Amma ta kudiri niyyar ko ya kira ta ba zata sake ɗauka ba, itama har abada ba zata 133 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... sake kiransa ba. A fusace ta goge lambarsa tana ta faman hucin takaici, ta rasa wanda zata faɗawa wannan mummunan labarin, ta ji sanyi a ranta. Ta jawo wayarta a sanyaye ta kira lambar Jalo, cike da fargaba kada ta sake haduwa da wulakanci irin wanda Shamaki ya yi mata. Tana kira ta ji Mace kamila ta amsa, sai gabanta ya fadi ta yi kamar ta katse wayar sai ta daure, ta san dai matarsa ce tabbas. Cikin ladabi Nasrin ta gaishe ta sannan ta shiga in-ina wajen gabatar da kanta. Matar ta yi murmushi ta ce, “bari akai masa wayar. Ga Jalon can." " Tana jin karar tafiyar matar har ta isa in da yake ta mika masa wayar, sai Nasrin ta shiga kogin mamaki gami da jinjina ga wannan mace ta gari marar kishi. Hakika ilimi ya yi a rayuwa rashin ilimi ke sa mata yin taɓargaza da sunan wai kishi. Haka kawai sai su binciki lambar mace a wayar mijinsu su kira suna zaginta, shima miji a tutsiye shi ayi ta rigima. Dr.Jalo ya karɓi waya bayan ya duba sunan mai kiran. Ta ji kamar a dakile baya 134 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 walwala a yadda yake amsa gaisuwar, dan haka sai ta shiga damuwa. Nasrin ta ce, "na kira in gaishe ka ne kawai, sorry ban san kana gida ba ina fatan banyi laifi ba, uban gidana?" Ya yi dan murmushi ya girgiza kai ' yace "ko kaɗan bakiyi laifiba, za ki iya kira kowanne lokaci.' " Nasrin ta lumshe ido ta ce,"haba dai kowanne lokaci, ai ko Madam bata damuwa idan taga kiran ya yi yawa zata zargi wani abu.' " Ya girgiza kai yace, "Madam babu ruwanta. " Nasrin ta gyada kai ta ce, "amma ina jinjina ga wannan gwarzuwar Mace ta gari, ta fahimci mijinta yadda ya kainata." Ya yi murmushi ya ce, "da Mamata kika yi magana yanzu ba da Madam ba.” وو Sai Nasrin ta sake tsunduma cikin sabon kogin mamaki tana linkaya. Ta tambaya a cikin zuciyarta "Me yasa mahaifiyarsa ta dauki wayarsa ta amsa sannan 135 Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... ↑ kuma bashi ya zo ya karɓa ita ta tafi ta kai masa? Lallai dan gata ne, ya cika sarauta." " Nasrin ta yi ajiayar zuciya ta ce "daman maganar ma'auratan nan ne nake so in baka labarin yadda muka yi, na kira su ɗazu zan basu shawara kamar yadda kace in basu sai aka sami matsala.' " Yace "mu koma online mu yi bayani na fi kaunar rubutu (chats)." Sai ta amsa masa cikin ladabi, suka . Nasrin da Jalo sun dauki awanni biyu cur suna hira a rubuce,idan ta fadi matsala sai ya faca mata mafita. Har ta gangaro matsalarta da wanda zata aura Fu'ad, ta fada masa halayɩnsa wanda take ganin aure da shi ba zai yiwu ba, yana da yawan fushi sai ya yi wata guda cur yana yi mata gaba. Jalo ya bata shawarwarin yadda zata bi ta gyara shi. Tabbas ya shaida mata Shamaki ya fara jin haushinta yana zargin kudin da take bawa matarsa yana kara jawowa ta raina shi. "Meye mafita?" Nasrin ta tambaya 136 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 Jalo ya bata karfin guiwa ta ci gaba da jajaircewa zata sami lada. Kada ta yi fushi kuma kada ta gajiya. Wayar Nasrin ceke ta ruri tana dubawa taga Malaika ce ta tabbatar ta dawo daga unguwa sai ta amsa da sauri. Da yake da computer take hirar da Jalo, tana waya tana bashi amsa. "Innalillahi wa'inna ilaihi rajun." Nasrin ta faɗa a lokacin da ta ji Malaika na kuka kamar ranta zai fita. Nasrin ta tambaya "yaya aka yi?" Malaika ta shaida mata Shamaki ya sake ta har yayi mata watsi da kaya. Sai ta ji jiri ya fara daukarta ga Jalo a Computer yana ta jero zancen mafita, nan kuma aure ya taɓarbare.Sai ta kurawa rubutun Jalo ido babu abinda zata iya yi a yanzu. Nasrin ta katse waya tana ta huci ta sake gasgatawa Shamaki mugun bawa ne shi yake cutar da Malaika, tabbas shine makaryaci, labarin duk da ya bata karya ne. Yana da kudi yake ɓoyewa yake bin karuwai.Duk da ta goge 137 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NICE lambarsa dazu, amma ta na da ita ala 'dailledcalls' da ta kira shi dazun. woorisjej Nasrin ta kira wayarsa a fusace daman da haushin wulakancin da yayi mata ɗazu sai ta hada ta cashe masa.assislaM syst ☐ yana Shima ya amsa a fusace tashuciny ace "menene kuma? Ai ta faru ta kare, sai ta kaura Abuja wajenki ta zauna, saboda ke ta ki zaman aure ta raina mijinta. 92; aires Nasrin ta fusata ta ce, "baka da adalci, baka san darajar aure ba.. Me ya kawo maganar saki?" siit is inT TEMES Yace "au har ta kira ta fada miki na sake 99 ta? To ni ban sakin matata ba idan burinki kenan." ayed sb fetsw stem iyey isd st Bol Sai Nasrin ta yi kasake ta kasa gane kan wannan matsala. Ta kashe wayarta ta koma ga Dr. Jalo ta iske ya sauka baya kusa. Nasrin tá sulale ta kwanta tana mai tsananin damuwalda shiga rudani. Mafita daya itace ta fita daga harkar Malaika da Shamaki kawai. Daman bata sansu ba balle matsalarsu ta zame mata matsale. Bata da hawan jini samma da nalama agog et ab oluⱭ.iswi aid exsy swayed by 138 | Jamila Umar Tanko (JUT)) oxosT U slime | TEI DA MA NI CE... 1 Shamaki da da Malaika zasu saka mata. Toh wai me ya yi zafi ido zai ci wuta? *** *** *** Da daddare misalin karfe goma da rabi na dare taga Dr.Jalo a facebook ta gaishe shi ya amsa amma sai ta ji ya ambace ta dawani suna wanda ya bata mamaki. Nasrin Abdul Nasir (kueen), bata yi mamaki mai yawa ba dan dai bata rubuta wannan sunan akan Username dinta ba. Ta tabbatar ya yi bincike akanta, yau ya gano kowacece Nasrin kuma me yasa take ta bibiyar rubutunsa tana so su saba. Sai yanzu ya gane da wa yake magana ashe da cikakiyar ‘yar jarida yake magana, wacce take daya daga cikin mata 'yan jaridar da suke burge shi wadanda suka san makamar aiki. Dr.Jalo ya jero mata waɗannan manyan kalamai na jinjina. Sai ta ji tamkar a mafarki take ganin wadannan kalamai nasa, ta tabbatar yanzu ta zama mutum sosai a wajensa tun da andzadad ng joint enou 139 jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 har ya damu ya bincika ya san ko ita wacece, lallai ta sami shiga. Ta yi masa godiya, sun kai karfe sha biyu na dare suna ta magana a facebook, . sannan suka yi sallma kowa ya sauka, bata damu da kwanciya da wuri ba saboda gobe lahadi babu aiki. Tana duba wayarta ashe Malaika ta kikkira ta da yawa, bata ji ba saboda ta saka wayar a silent tun da yamma da suka ɓata mata rai. Tana gani ta yi tsaki ta turo baki kafin ta ankara Malaika ta sake kiranta. Nasrin ta danna a fusace tana jira ta ji abinda Malaika zata ce,sannan ta yi mata wankin babban bargo. Malaika tana ta kuka har yanzu ta ce "Nasrin! Ki taimake ni ina cikin wani hali. Shamaki ya kore ni kuma ya bani kwana daya in kwashe kayana, na je gidanmu ana ta zagi ana cewa basu da inda zasu saka ni da kayana, sai dai in san na yi. Ki taimake ni ki bani adireshinki in taho a Abuja wajenki tunda bani da goyo kuma ya kwace 'ya'yansa.' " Nasrin ta ji tamkar Malaika ta caka mata wuka a kahon zuci na takaici, ga hausshin 140 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... Shamaki gami da tausayin Malaika, ga haushin jin danyen hukunci da Malaika ta yanke na zuwa wajenta. "Ta zo wajena Abuja ta zauna akan me? Meye hadinna da ita?" Nasrin ta faɗa a cikin zuciyarta. Nasrin ta dakatar da ita, ta ce, "in takaice miki mijinki yana zargina da kashe muku aure gani yake ni nake zuga ki saboda ina turo miki katin waya, dan haka Malaika kada ki sake nemana a waya balle kice za ki zo gidanmu.Ki je iyayenki da iyayansa su yi muku sulhu ku zauna lafiya, babu in da zaki je ki zauna ki yi daraja wanda ya wuce gidan mijinki, ki rungumi 'ya'yanki dan babu mai rike miki su ki ga daidai idan bake da kanki ba. Dan Allah Malaika ki cire ni daga cikin mutanen da kika taɓa sani a rayuwa, matsalar gidanki ta dame ni ta tsaye min a rai, gashi ta jawo min zargi da wulakanci daga Shamaki.' " Nasrin ta tsiyayo da hawaye ta katse wayar, tana katsewa ta yi sauri ta goge lambar Malaika daga cikin wayarta. Ta kashe wayar 141 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... gaba ɗaya ma dan taga Malaika tana ta sake kiranta. Ta rubutawa Dr.Jalo sako ta ce, “daga karshe wannan auren da muke kokarin ceto rayuwarsa Allah ya yi masa cikawa a yau da yamma. " Ta rufe computer ta, ta kwanta cikin gagarumin ɓacin rai. DA MA NI CE... 1 BABINA TAKWAS RANAR TALATA ABUJA • au Dr. Jalo da Nasrin sun daɗe suna a facebook kasancewar ta ga wadansu sakonninda abokansa su na tura masa suna yi masasannu da jiki. Ta tabbatar bashi da lafiya, dan haka ta damu tana ta tura masa sakonninfatan samun lafya cikin gaggawa. Ya yi mata godiya saboda kulawarta ya nuna ya ji dadi. Amma ta matsa ya faɗa mata abinda ya ke damunsa, sai bai ce mata komai ba ya ma canja hirar. Gudun kada ta ɓata masa rai sai ta bar zancen, dan taga alamar baya son yawan tambaya. Daga nan ta shaida masa tana yawan zazzaɓi da ciwon kai kwanan nan. Ta tambaye shi wanne irin magani ya kamata ta sha dan ta warke? Ya jima bai ba ta amsa ba, daga baya yace ta je asibiti mana. Ta ce tana so ta je amma aiki ke hanata zuwa, kasancewar 143 Jamila Untar Tanko (JUT) DA MA NI CE 1. zazzabin dare ne kafin safe ya sauka sai ta manta ta fita ofis. 4 ХАТ АЙШАЯ Sai yau yau ya tabbatar mata shi ba likitan asibiti ba ne likitan karatu ne kawai. Nasrin ta yi mamaki matuka dan ya yi mata kama da cikakken likita mai farɗe mutum ya dinke. Sai ta ji ta rage mamakin yadda ya zama kwararren marubuči, rubutu masu masu mama'ana ' ashe likitan karatu nesanlods sbainnolsa p2ebsw ST Yashaida mata ya karanci English Litraturëb yana koyarwa a jami ar Lagos. Nasrin ta ji dadi kwarai da ta fara sanin wani abu nasa bodsa syibog stem by Y swaggsy SY BUGSY sbstas y mamaki da ta ji yace ta bashi 2010 2: bride sisu karanta 16 FT 8260 sted tarihiin rayuwarta yana so ya sani.Ta sakon nan daya daya tura tura,, yaya fi sau biyar dan ta tabbatar haka din yake nufi nufi dan kada ta fara zuba alhali bai ce ba. Ta gasgatanewer haka yake sys nufis sai ta gyára zama. Ta rubuta ta tura masa ta ce idan bazai damu bazatakira is shi bidsvess su yı new ida magana a waya, zai fi dadiidan suka yi magana baki da baki, ta shaida masa kada ya damu bata biyan kudin katin waya.Nan da nann yay bata izinin, żata iya kira ba damuwa. Farin ciki ya woman swusstened 144 Jamila Umar Tanko (JUT) (TU) of DA MA NI CE... 1 rufe ta kafin ta kira shi sai da ta kira Dinah ta bata labarin yadda suka yi da Dr.Jalo, ta tabbatar mata yanzu ma zata.kira shi su yi labari. Dinah ta yi mamaki ta kuma ta taya ta murna ta tabbatar mata ita ma ba zata yi bacci ba har sai sun gama wayar, tana jiran ta kira ta fada mata yadda suka yi, Nasrin ta yi mata alkawari zata kira k ta fada mata komai. Dinah ta yi mata alkawarin zata dauki jarbi mai dubu ta taya ta da addu'a Allah Ya sa atattauna abubuwa masu alkhairi. Maganar Dina ta bawa Nasrin dariya kwarai, dan haka ta yi ta dariya ta kashe waya. Ta fada abayyane "Dina shakiyiyar yarinya ce wallahi." Ayaw Gab Nasrin ta tashi ta buce firij ta dauko lemon kwali da kofi ta dawo kan gado ta zauna ta nutsu sannan ta kira lambar Jalo, bayan da ta b karanto kula'uzai ta tottofa a kowacce 5 kusurwa ta dakin, ta na neman Allah ya tsare ta da ɓata masa rai ko ta faɗamasa abinda zai sa ya janye daga gare ta. 145 Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 Data buga bai dauka ba har ta katse sai a karo na biyu aka dauka, maimakon ta ji muryarsa sai ta ji muryar matar nan data dauka ran nan, wacce yace mahaifiyarsa ce. Nasrin ta zabura ta dukar da kai ta gaishe ta, cikin fara'a ta amsa gami da cewa ki kira nan da mintina goma idan yagama abinda yake yi. Nasrin ta amsa cikin ladabi sannan suka kashe wayar. Sai mamaki ya hana Nasrin rufe bakinta, ta duba agogo taga karfe goma shaɗaya da minti goma sha daya na dare amma Jalo yana tare da mahaifiyarsa. "Ina matarsa ne? Ko irin mutanen nan ne masu son uwa, har yanzu yana nanike da ita? Daga gani baya ɓoyewa Mahaifiyarsa komai dan wayarsa ma yawanci a wajenta ta ke.' Nasrin ta ke tambayar zuciyarta. " Tana cikin mamaki sai ta ji kira, tana dubawa ta ga shine ta ki amsawa, sai bayan data katse sannan ta kira saboda bata so ta ci masa kudin waya. Tana kira sai ta ga ya katse kiranta, sannan ya kira ta. Ta amsa cikin ladabi ta gaishe shi. 146 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 Yace “me yasa za ki kira ni? Ai ni ya kamata in kona katin wayata ba ke ba. Kada ki damu nima katin wayar zai isa mu kwana, mu yini muna hira bai kare ba." likita.'" " Nasrin ta yi dariya ta ce, “na gode kwarai Ya yi dariya ya girgiza kai yace, “kada ki gode min ki godewa Allah da Ya hada mu, gashi muna ta zumunci muna karuwa da juna. Yau ma na ga rahotanninki a gidan shugaban kasa (Billa), a labarai aka nuna, sannu kina kokari fa har kin fi wasu tsofaffin maʼaikatan sanin makamar aiki." Nasrin ta yi dariya ta sosa goshi ta ce, "haba dai muna ta koyo dai, ai ku ne gwanayen magana. Da ma zan iya ganinka in yi hira da kai ka wanke mana 'yan kudu da suke yiwa 'yan arewa gani-gani." 99 Ya yi dariya yace,“rufa min asiri ni asu wa?" Ta yi dariya ta ce, "kai kuwa kai ne komai, amma sannu a hankali zan sanka, na yi alkawari sai na haska ka a duniya, gaba daya 147 Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 sai an sanka. Kuna da amfani a cikin al'umma." Ya yi murmushi ya canja hira,yace, "Nasrin, ba ni labarinki. Ina so in san ko ke wacece?" Ta gyara zama ta yi farfari da ido ta yi gyaran murya. LABARIN NASRIN: Ta ce "Sunana Nasrin Mahaifina kuma sunansa Abdul Nasir, sunan mahaifiayata kuma Hajja Khadija. Gaba dayansu daga tsatso daya suka fito 'yan uwan juna ne kakanninsu ɗaya, jikokin wani shahararren sarki ne mai karfin mulki a arewacin Najeriya. Dan haka jinin sarauta ne. A daki daya aka rike su, da suka kammala karatun sakandire sai aka daura musu aure daman su na son junansu, aka tura su karatu America, acan suka zauna. Bayan sun kammala karatun jami'a ma basu dawo ba suka fara aiki acan. Haihuwarsu ta farko aka haifi yayata Zainab wacce nake gidanta anan Abuja,nice ta 148 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE biyu sannan aka haifi dan autanmu Nafi'u yana can tare da su shima ya shiga Jami'a. In takaice maka dai Mahaifina shine ambasadan Amerika da yake wakiltar Nigeriya.” Dr.Jalo ya yi ajiyar zuciya yace, "da kyau. An daɗe ana neman ilimi a duniya ashe?" Nasrin ta yi dariya, ta ce "gidansu gaba daya 'yan boko ne abin mamaki kuma duk sai da suka sauke ku'rani tun kafin a saka su a makarantar firamare ma, dan haka hafizai ne, mu ma haka suka yi mana. Akwai wasu ustazan larabawa a Amerika su suka koyar da mu tun muna kanana." Jalo yace, ni kwarai." "masha Allah amma sun birge Nasrin ta yi ajiyar zuciya ta sa hannu ta jawo kofi ta tsiyayi lemo ta kora ta ci gaba da cewa, "A Amerika muka yi firamare, muka yi sakandire da jami'a. Amma ni ina yawan zuwa Najeriya akai-akaiduk hutu, wajen kakannina.Amma na fi zuwa a lokacin da Zainab ta yi aure a Najeriya. Yanzu haka bautar kasa ce ta kawo ni. Idan na kammala 149 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 zan koma Amerika sai in yi masters da PHDdina, dan ina so in zama Dakta a fanni jarida. La so in zama kamar ka. Suka yi dariya su dukka. " Ya ce "in sha Allah Nasrin sai kin fi ni ma dan irin karatuna da naki ma ba daya ba ne, mu da mu ka gama karatu a Najeriya kasar da ake yawan yin yajin aiki, ga wahala. Ku kuwa karatunku babu wata damuwa, kun yi kun kare cikin nutsuwa. 99 Nasrin ta yi dariya ta ce,"abin ai a kwakwalwa ne, ga shi kuwa a wajenka mu ke koyo." Ya ce "kin gama zayyano min karatu amma ban ji kin ambaci aure ba. Ina labarin Fu'ad?" Nasrin ta yi dariya ta rufe ido da hannunta ta ce "Fu'ad dan gidan Yayan Babana ne, A gidanmu aka rike shi, dan haka gidanmu daya, yana can tare da Baba a Amerika, yana aiki a karkashinsa. 99 Ta ji muryar mace tana yi masa magana cikin yaren fulatanci, shima ya bada amsa cikin harshen Fulatanci, sanna ya dawo kan Nasrin. 150 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE S " Ya yi dariya yace, "sorry! Muna magana da ke na juya ina magana da Mamata. Ta ce min in je in kwanta haka dare ya yi.”be iam os Nasrin ta yi mamaki ta juya da sauri ta kalli agogo, karfe goma sha biyu saura mintina biyar. end men ofbud 3d stTa ce "Allah sarki da gaskiyar Mama dare ya yi." new Jalo yace, “to za gobe." ayaw sismios ad cams iguaz et ab cust mu yi magana sosai que fabi at six stas Nasrin ta yi dariya ta ce, "na gode, Allah Ya tashe mu lafiya." To adeown) sy loosd Su ka kashe waya. Gaba dayansu suka kwanta cikin farin ciki da tunani muryoyin juna, da alama muryar Nasrin ta yi matukar tafiya da hankalinsa, haka itama muryarsa tana burge ta matuka. st husYana ta nanata labarinta yana juya shi a ransa. Ya tabbatar Nasrin ba karamar 'yar hutu bace, ko ba'a faɗa maka ba daga ganin suffarta da maganarta ba tashin nan bace. imen st danis 90 st Ita kuma tana tamamakin yadda Mahaifiyarsa take tare da shia koda yaushenA" "saspason nojsw s saitisl 151 | Jamila Umar Tanko (JUT) on muslims SI DA MA NI CE... 1 "Ina matarsa da yaransa ne? Ban taɓa jin muryar yara a cikin gidan ba. Ko irin uwar nan ce mai saka ido akan 'yayansu su hana su zaman lafiya da matansu? Ko kuwa matar ce ta yi tafiya kasar waje kasancewar ‘ya'yan masu kudin nan haka suke basa kula da mazansu? Oho!" Nasrin na ta tambayar kanta da kanta ba tare da ta sami amsa ba. Ta ma manta ta yiwa Dinahalkawarin zata kira ta idan sun kammala waya da Jalo, haka ita ma Dina tuni ta yar da carbi gefe, bacci ya kwashe ta. Asuba ta gari! Nasrin ta dan makaraam mata yi sauri ta shirya ta fito falo, ta iske Salis ya riga ta fita.Zainab kaɗai ta iske a falo, bayan sun gaisa Zainab ta nemi da Nasrin ta zauna ta ci abinci. Nasrin ta duba agogo ta girgiza kai ta ce "Antimi,yau na makara sosai na san saina amsa laifina a wajen manajana." 152 Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE T Zainab ta harare ta ce, "kin kwana kina hira da kawaye ko in ce da Mutanen ɓoye su Jalo ko?" Nasrin bata amsa mataba, ta fice da sauri tana saɓa jakar Lap-top a kafaɗa. Zainab ta bita da kallo cike da tausayi, saboda wahalar da take sha akan aikin nan data ɗorawa kanta, dan ba dan kudi take yi ba saidan sha'awa da neman suna. *** *** Nasrin bata dawo gida ba sai da yamma likis karfe biyar na yamma. Tafiya take tana jefa kafa dakyar saboda gajiya ga yunwa. Banda lemon kwalba guda daya babu abinda ta saka a cikin cikinta yau. Burinta ta ganta a kwance akan gadonta kawai, amma yau ta kudiri niyyar cin abinci da yawa dan

Chapter 6 of 7