gabana, in na tambaye ta ta ce karya
ne. Na yi faɗa da jama'a da yawa akan sukar
Malaika a gabana. Abin nata bai giga ba sai da
muka kauro Birni inda ta hadu da wayayyu,
masu arziki sannan halinta ya fito fili karara,
dan a kauye kowa babu, balle ta sami mai kudi
ko 'yar gayun da zata makalewa.
Idan dare ya yi sai taga kowa a unguwar
yana kunna Inji, sannan ta lura ashe sai a haske
ake rayuwa, taga kullum matan birni idan zasu
fita kwalliya suke ci ba'a saka koɗadiyar
atamfa ta ce itama sai ta yi haka, taga wasu
motarsu suke shiga akai su unguwa ba kamar a
kauye ba da sayyada ko da acaɓa ake fita, nan
ma ta ce itama sai ta yi haka. Ta ga ana zuwa
78 | Jamila Umar Tanko (JUT)
CE...
Dubai da Saudia ayi sayayya itama ta fara
DA MA NI
sha'awar haka.
Akwai wasu masu arziki a kusa da mu a
gidan ta tare nan take ganin kayan kyalkyalin
duniya, kafin aka yi faɗa kaca-kaca ta daina
shiga. Ta koma gidan wasu masu kudi a
tsallaken titinmu nan ma aka yi fada ta daina
shiga, ni kuma ta zo ta sauke min kwandon
masifa sai na yi kudi da karfin tsiya dan adaina
yi mata gori.
Tun daga nan nake yi mata nasihaamma
tamkarzugata nake yi, yanzu data hadu da ke
abin ya ci tura ta sake barkalewa.Nasrin ki
taimaka ki nunawa Malaika yadda rayuwa
take, na tabbatar ke kanki a danginku akwai
talakawa dole wani ya fi wani.
"
***
Nasrin ta yi shiru tana tunani ta rasa
abinda zata ce, bayanansa kamar da kamshin
gaskiya na Malaika ma ta gasgata dan in har
karya take yi ba zata dinga sharɓar kuka haka
ba. Me yasa Malaika zata yi mata karya? Ko
79 jamila Umar Tanko (JUT).
DA MA NI CE... 1
me yasa Shamaki zai yi mata karya? Dole a
cikinsu akwai makaryaci.
Nasrin ta gyada kai ta ce, “tabbas uwa
ɗaya uba ɗaya ma dole a sami wani ya fi wani
arziki, Shamaki ka ci gaba da hakuri. Kenan
yanzu albashinka na can kauye da shi kadai ka
ke cin abinci?"
zama
Ya gyada kai yace "Eh! Naira dubu sha
takwas ne kacal kafin wata ya zagayo sai na ci
bashi na bawa Malaika, gashi na koma
makaranta siyan Handout, da yawa ma 'yan
matan ajinmu da nake koyawa karatu su suka
dauki nauyina ni kuma na
bawansu, assignment da aattendance dinsu nine
dan ba zuwa suke yi ba kullum, to a haka muke
rayuwar gashi an hana Acaɓa a Kano balle in
yi da babur dina, amma na kan fita wajen gari
in yi acaɓa ma wataran. Ni dai fatana in
kyautatawa Malaika kada ta tafi ta bar ni."
Nasrin ta cika da mamaki ga shamaki ma
yana kokarin kece mata da kuka kamar yadda
Malaika ta yi mata.
Ta yi tagumi ta yi shiru tana saurarensa
wani abu take ji yana yi mata yawo a cikin
80 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
kwakwalwarta. Ta yi ajiyar zuciya ta
ce,“kenan kai dalibi ne a B.U.K ba Malami
ba?"
alhali
Shamaki ya fara mamakin tambayar nan
ya fada mata komai.
Ya gyaɗa kai, yace,"ai na faɗa miki in
da nake aiki, anan kuma karatu nake."
Nasrin ta gyara zama ta yatsune fuska ta
ce "ka fara tunanin kara aure ne ya sa Matarka
da rashin samun zaman lafiya a kishi
junanku?"
Shamaki ya yi dariya ya ce, "Aure? Ina
ta kaina auren me? Ko kadan bana taɓa
sha'war yiwa Malaika kishiya. Ina son Malaika
har cikin raina bana son ɓacin ranta, ta kasa
yarda. Da ina da kudin da ya kai cikin duniyar
nan, da zan juyewa Malaika dan ta yi farin
ciki."
Sai Nasrin ta ji gabanta ya faɗi ta faɗa
cikin firgici "Shamaki ka tabbatar abinda yake
rankaka ke fada min?".
Ya yi dariya yace, "Baiwar Allah baki
san ni ba, ban san ki ba amma na kwashe
sirrina kacokan na faɗa miki. Wallahi ban da
81 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
ke duk duniya ban taɓa irin wannan hirar da
kowa ba dan ke ma na san zaki taimake ni ki
fahimtar da ita. Kin ga yanzu ina Laɓel3,
karatu ya yi nisa saura shekara daya in gama,
gidana ba nutsuwa ina tunanin yara bana iya
zama a makaranta in yini ina karatu, ba dan ma
kwakwalwar mai dauka da wuri ba ce da
tayaya zan din ga hayewa jarabawa, kuma ban
taɓa samun carryoɓer ba, babu kuma dalibin
daya fi ni ci a department dinmu."
Nasrin ta gyada kai ta ce, “dakyau
Shamaki na jinjina maka, in Allah Ya so zan
taimaka maka cikin dabara zan fahimtar da
matarka ba tare da ta san mun taɓa magana da
kai ba."
Ya ce "na ji dadi na gode."
Nasrin ta ce,“tambayata ta karshe itace
shekarun Malaika nawa? Naka nawa?"
Ya yi murmushi ya ce, "Shekarun
Malaika ashirin da shida, ni kuma talatin da
biyu. Ke fa shekarunki nawa?"
Nasrin ta yi dariya, ta ce, “ni saʼar
Malaika ce shekaruna ashirin da biyar, gobe ne
Birthday dina. Na gode sai anjima."
82 Jamila Umȧr Tanko (JUT)
DA MA NI CE..
Nasrin ta kashe waya tabar Shamaki a
zaune yana ta murmushin jin dadi shi kadai. Ji
yake tamkar matsalarsa ta zo karshe, gyara ya
zo Malaikarsa zata shiryu. Ya yiwa Nasrin
addu'a Allah Ya bata dama da ikon shawo kan
Malaika. Dan tunkarar Malaika da zunmar
gyara abu ne mai wuya dan bata jin Magana.
Ya isa gida da murna ya iske Malaika
cikin farin ciki, hatta cimar gidan ta canza
abinci da kaza ta yi musu, sai ya ji gabansa ya
fadi ya tambayi in da ta sami kudi ta sayi kaza,
ko zakka makwabcinsu ya yi musu daman ya
saba basu?
sai
Malaika ta ce kawai ya ci ba sai ya tambaya ba.
Shamaki ya girgiza kai ya ce ba zai ci ba
ya sani.Ta gyara zama ta yi fari da ido ta
dauko wayarta ta bude sakon Nasrin ta nuna
masa. Ya kalla ya dubaba tare da ya gane ba.
Ta yi masa bayani kati ta turo mata na Naira
dubu uku.
Sai ya ji jikinsa ya yi sanyi ya fara tunani
aransa “anya Nasrin gyara zata yi ko kuwa ɓata
min mata take? Na fara nadamar labarina dana
83 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
kwashe na faɗa mata ɗazu. Ashe ta turowa
matata kati sannan ta kira ta ji ta bakina.'
"
Sai ya shiga zulumi yana mai tsananin
takaici, yaga dakyar ya nemo Naira ɗari biyu
ya bayar a yi cefane,yanzu ta zo ta turo mata da
dubu uku. Yanzu ta ina Malaika zata ga
mutuncinsa? Ta ina zata ji maganarsa? Ta ina
zai hanata ta hanu ? Me yasa ba zata yi
sha'awar ziyartar Nasrin a Abuja ba? Shiyasa
ta fi sha'awar saki maimakon zama da shi dan
ta koma ta zauna da Nasrin.
"Malaika kada in kara ganin kin kira
Nasrin balle ki roke ta kati." Shamaki ya fada a
fusace.
Malaiaka ta zabura ta taşhi tsaye cikin
tsiwa ta ce "Lallai ma, au haka zaka ce? Bakin
ciki ne abin dan kaga na sami mai taimaka
min? Wallahi baka kaunata saboda baka
kaunar ci gabana. Babu mai raba ni da Nasrin
Aminiyata."
Sai ya fusata ya kai mata hannu kamar
zai mare ta, ya fasa.Tayi tsalle ta faɗa kan
kujera tana makerketa ta zaci dukanta zai yi.
84 | Jamila Umar Tanko (JUT)
CE... 1
Ya fice daga gidan a fusace, Malaika ta
tashi tsaye ta tsaya a falo ta kama Rugu ta rasa
abinda yake yi mata dadi zuciyar ta na tafasa
ga tukikin masifa ya taso mata amma babu
abokin fafatawa.
DA MA NI
Tsaki take tana kwafa tana fadin "cafdi
jam! Ashe za'ayi ta yau a gidan nan. Daman ka
mare ni da ka mari aurenka wallahi. Nasrin
kuwa bazan rabu da itaba sai dai ka mutu.
Shamaki bai shigo gida ba sai da daddare
bayan Sallar isha'i, ya shigo da fara'a ya iske
yara sun yi bacci sai Malaika a zaune a tsakar
gida tana cin tsire.
Ya yi sallama bata amsa ba, ya yi dariya
yace, "kaga madam an sami kudi ana ta cin
dadi bayan kaza ma kuma tsire ake ci, ai dadin
zai yi yawa a rage na gobe mana. Ke kaɗai za
ki ci dan rashin imani sai da kika bari yara sun
yi bacci, ni bana nan?"
Ta yi kamar ba da ita yake ba ta dinga
kai tsoka lunkuma-lunkuma bakinta. Ya ga da
gaskę cinyewa zata yi ya zabura ya kai hannu
zai dauki yanka ɗaya, ta dɗauke namanta da
85 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
sauri ta juya baya ta cinye tas ta wurgar da
takarda, ya zaci wasa ne.
Ya ce ta dauko masa abincinsa na ɗazu
zai ci. Ta harare shi ta ce "ai ka yiwa kanka
wallahi mun cinye tas ka je ka nemi abincinka.
Tunda kai ba'ayi maka gwaninta, kamar wacce
ta samo kudin haram har da kin ci kuma
wallahi duk ran da ka dake ni ka daki aurenka."
Shamaki ya zauna ya yi shiru yana
kallonta yunwa yake ji ta gaske kuwa, dan tun
kokon safe ne a cikinsa gashi ba shi da ko sisi.
Bashi da karfin yin magana ma balle fada,
sannan ba ya son ma a kara tayar da zancen
dan daga baya da ya huce sai ya ga bai kyauta
ba kamata yayi ya yiwa Nasrin kyakyawan
zato tunda taimakawa ta yi.
Ya yi ta karanto istigfari a cikin
zuciyarsa. Duk abinda Malaika take fada masa
kalma daya yake faɗa yana ta nanatawa kamar
karatu "yi hakuri, yi hakuri, bazan sake ba."
Har sai da Malaika ta ji ya fara bata
tausayi sannan ta daina tsigale shi. Ya tashi ya
fitą kofar gida ya je wajen mai shayi da biredi
na kan kwanar gidansu anan ya ci bashi ya cika
86 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
cikinsa ya dawo gida. A ranar dai Malaika bata
kula shi ba, baya ta juya masa ya gaji da
magiya ya rabu da ita.
Asuba ta gari!
***
Shamaki ya shiga cikin matsananciyar
rayuwa, ko inaba dadi, can garinsu yana kula
da mahaifiyarsa wacce bata da komai tana
neman taimako, kannensa gaba daya babu mai
shi babu wanda ya yi karatu a jikinsa ma suke
nema, 'ya'yansa abin tausayi ya kamata an
saka su a makaranta amma suna zaune a gida,
ga marar lafiya kuwa wani lokaci sai dai a
hakura a zuba masa ido yana ta kuka babu
kudin magani, Malaika abar kaunarsa ta tsane
shi ta juya masa baya, ya manta rabon da ta
masa hira mai dadi.
Baya gushewa da yin tsayuwar dare da
addu'a yana kuka yana faɗawa Allah. Ya na
nemawa Malaika gafara da shiriya dan baya
fatan Allah Ya kamata da laifin kin yiwa miji
biyayya da butulcin da take yiwa Ubangiji.
87 | Jamila Umar. Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Malaika kuwa ga ni take kamar duk
rashin gata da rashin sa'a akanta ya kare, gani
take tamkar ta rako mata duniya. Idan ta tsaya
a titi ta hango mace ta na kotsewa a cikin mota
mai kyau ta gani ta fada sai ta ji ta tsani kanta.
Dan haka itama rayuwar ta yi mata kunci bata
walwala ko kaɗan.
Al'amarin Nasrin kuwa ta shiga rudani
matsalar Malaika da Shamaki ta tsaye mata a
rai, ta shiga aikin tunanin tantance waye mugu
a cikinsu kuma waye ya yi mata karya, a haka
dai kowa ya nuna mata shine abin tausayi
dayan ke cutarsa.
To Allah Shine Masanin badini da Zahiri.
88 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
BABI NA BIYAR
ABUJA:
Da misalin karfe goma na dare
Nasrin tana sanye da kayan
bacci tana kwance akan gadonta
tana ta danna Computer ta har yanzu dai tana
biye da Dr.Jalo mutuminta, ta ga ya yi
sababbin rubutu ya turo. Tana ta bibiyarsa a
hankali tana karantawa sai ta ci karo da wani
rubutunsa wanda ta ke neman karin bayani
akai, yadda ya yi rubutun ma kai kace da
Shamaki da Malaika yake, ma'auratan da suka
kasa fahimtar juna. Sai ta je ta yi comment a
kasan posts dinsa. Bai bawa kowa amsa ba,
dan ta iske dariruwan mutane da suka tofa
albarkacin bakinsu, mata da maza suna ta
mahawara. Gogan naka bai tanka ba shi dai ya
zuba bayanai ya kara gaba, ya bar mutane da
hayagaga.
.
Ta dubi lokacin da ya turo sakon, a ranar
ne da safe.Ta dauko wayartą zata kira shi sai ta
89 | Jamila Umar Tanko (JUT) 1
DA MA NI CE... 1
kalli agogo ta ga dare ne bai kamata ta kira mai aure da daddare ba dan ta tabbatar yana da
mata kada ta hada su fada.Ta dubo cikin
hotunansa ta ga ya sake 'profilepicture' dinsa, tabbas ya yi kyau matuka kamar ka kira shi ya
amsa. Idanuwan nan dara-dara, hanci doɗar,
hakora a jere reras gwanin ban sha'awa ya saka
wani farin gilashi wanda ya yi masa kyau, kana
ganinsa kaga cikekken likita, likitan da yasan
abinda yake yi. Ta dade tana kallon hoton nan
a ranta tana mamakin yadda ta sami mutumin
da yake birge ta.
Dr.Jalo ne kaɗai mutumin data taɓa
haduwa da shi take binsa ya ke ja mata aji.
Shima babban abinda ya birge ta shine
tunaninsa da fasaharsa lallai duk wanda Allah
ya bawa fasahar rubutu ko ta magana lallai ya
godewa Allah, ba kowa ne yake samu ba kuma
ba'a saya a kasuwa, haka ba'a koyo a
makaranata.
"DA MA NI CE Dr.Jalo! Dr.Jalo." Ta
fada abayyane a lokacin da ta ci gaba da
kallonsa.
90 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Tana cikin wannan hali sai gashi ya hau
facebook. Ta zabura ta bishi ta 'inbod' ta
masa magana. Salama ce da gaisuwa ta tura
masa, nan da nan ya amsa mata. Sai ta yi
mamaki. Daga nan da kwarin guiwarta ta tura
masa jinjina da yabo akan rubuce-rubucensa.
Sai bai bata amsa ba kuma tana ganinsa
'online.' Ta sake tura masa cewar tana so su
dinga gaisawa ya dinga bata shawarwari.
Bayan ta jima da tura sakon bai bata amsa ba
ma sai ya sauka daga facebook din ma. Ta san
kuwa ba zai dawo a yau ba, ko ya dawo ba zai
bata amsa ba.
Ta ji kwallar takaici ta surnano mata ta fara
tsanar kanta da kanta ma da ta ke jawowa kanta
wulakanci, tana mamakin masu wulakanta
mutane dan sunga mutane suna sonsu. A
sanadiyyar Allah Ya yi musu wata baiwa,
tabbas ita bata da wulakanci tun ma bata fara
hulda da mutane haka ba, yanzu data fara
harkar rahotannin nan ana nuna ta a talabijin ta
samu masoya da yawa da suke turo mata da
sakonni ta waya ko ta Email dinta. Tana kula
91 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
kowa yadda ya kamata shiyasa kula Malaika har sukasaba. ma ta tsaya ta
Ta fara ji a ranta ba zata kara kula
Dr.Jalo ba bare ya sake yi mata wulakanci, eh
yana da kyau, yana da ilimi, yana da kamun kai
, yana da aji, watakila attajiri ne ko dan gidan
attajiri. Sai aka yi yaya kuma? Da me ya fita?
Koda ace ya tara duk wadannan abubuwan da
aka zano Nasrin tana da linkin nasa.Ta fara
tunanin kai zuciyarta nesa ta manta da matsalar
mutumin da bata sani ba.
** *** ***
Washe gari da safe ta shirya zata fita
wajen aiki ta jawo computer ta zata kashe saita
iske amsar Dr.Jalo da asuba ya turo mata.
Ta ji dadi a ranta harda rufe ido da
budewa dan ta gasgata ba mafarki take yi ba
ido biyu ne.Ya tabbatar mata yana farin cikin
haduwa da ita kuma kada ta damu a shirye
yake ya bata shawara koma wacce iri
ce.Hannunta na rawa ta rubuta masa godiya da
92 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
nuna farincikinta. Baya kan layi amma ta san
idan ya dawo zai gani.
Ta fito falo tana walwala har sai da Salis
da Zainab suka fahimce ta, yau tare da su ta
karya kumallo saɓanin idan ta fito da fushi bata
tsayawa ta ci abinci.
Zainab ta harare ta, ta ce kin yi chats
ko? Kin ji wani abu mai dadi dan nasan baki da
abokai sai a socoalNetwork kullum kina kan
computer, haka kawakenki mutanen ɓoye ne
duk anan ku ke haduwa."
999
Salis da Nasrin suka kwashe da dariya.
Nasrin ta ce, "ka ji wai muatanen ɓoye
kamar wasu aljanu."
Da suka gama cin abinci Salis da Nasrin kowa
ya dauki jakar laptop dinsa ya fita, Zainab ta
rako su har wajen motocinsu kowannesu ya shi
tsaleliyar motarsa ya nufi wajen aiki.
Sai yamma kuma ko da magriba, Zainab
ita kadai ta ke yini kuma bata sha'awar 'yan
aiki saboda matsalarsu ta ishe ta.
Nasrin ta isa ofis, basu zauna ba yau,
suka fita da motar ofis dauko rahotanni, acan ta
yini basu dawo ofis ba sai da yamma likis
93 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE イ
wayarta ma a ofis ta bari a caji, ta zo ta iske
missedcalls Malaika babu adadi bata damu ta
kira ba dan ta san kiran kawai take yi dan bata
da abinyi. Kullum sai ta kira ta ta ishe ta da
surutu marar maʼana. Dan haka ba zata kira ta
ba itama sai ranar da bata da abinyi, sai su
haɗu su yi ta hirar rashin abin yi. Kafin ta tafi
gida ta bankaɗo Facebook dinta sai kuwa taga
mutuminta yau 'yan siyasa ya ragargaza ya
kawo musu misalai da manyan 'yan siyarsar
kasashen da suka ci gaba wadanda suka san
darajar bil'adama. Ya kawo misalai da 'Nafsin
Mandela' da 'General Muhammad Buhari' zo
kaga ruwan yabo da jinjina da ake yi masa.
Nasrin ma ta shiga ta zankada turanci irin na su
na gwanaye, ta yabi gwaninta Dr.Jalo, ta yaba
masa akan fadar gaskiya komai ɗacinta.
Tana shiga cikin inboddinta sai taga ya
turo mata da sakon gaisuwa, daga nan dadi ya
kusa tafiya da ita dan ji ta yi ta yi 'luuuu'
kamar zata shide dakyar ta dawo daidai. Ta
godewa Allah da Ya sa wannan hazikin bawan
ya san da ita. Nan take ta bashi amsa tana mai
94 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
tabbatar masa tana nan lafiya cikin koshin
lafiya tare da tambayarsa lafiyarsa shima.
Tana turawa ta tashi rataya jakar laptop
dinta ta fito daga ofis tana tafe tana rangwada,
tafiyar ma yau sai da ta canja ta. Har sai da
abokan aikinta suka fahimci yau nishadi take
ji, masu gadi sun sha kyauta tunda daga
reception take kyautar kudihar zuwa get. Ita a
ranta sadaka take yi, da neman yarda Allah, Ya
kara dorata akan miskilin hazikin nan,
gwaninta Dr.Jalo.
Ta iske yayarta Zainab a kicin bayan sun
gaisa ta shiga daki ta yi wanka ta fito sanye da
riga shimi da wando iya guiwa (Three Kuarter)
za ta tayata abinda zata iya yi dan ita bata son
aiki musamman na kicin, dan bata sababa.
Nasrin ta na ta yiwa Zainab tsiya saboda
bata daukar kuku da masu aiki, sai bayan
kwana bibibiyu wata inyamura take zuwa ta
kalkale mata gidan ta tafi ba zata dawo ba sai
bayan wata kwana biyun kuma kullum, ita ke
yin girki da kanta. Dan haka ne bata son ta yi
aiki gwamnati alhali har masters gare ta.
95 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Zainab dai murmushi take tana aikinta Nasrin
tana ta ɓaɓatun ta ita kadai.
Nasrin ta yi fari ta zauna akan wata
kujerar roba ta ce, "Antimi in baki labari?"
Zainab ta ce, "Engr.Fu'ad zai zo ko?".
Nasrin ta yi tsaki ta ce, “caf! wannan da
zuwansa da rashin zuwansa ma duk daya. Wai
fushi yake yi da ni,mutum ne mai yawan fushi
da daukar magana. Ke ni ba zan iya ba.
99
Zainab ta ce, “ke dai na rasa mai Fu'ad
ya yi miki bakya sonsa."
99
Nasrin ta ce, "kana son mace amma
bazaka lallashe ta ba. Shi fa baya lallashi kuma
baya bada hakuri sai dai a bashi, ya cika son
kansa.
"
Zainab ta girgiza kai ta ce, "a'a haka ba
zai yiwu ba aure ai dan lallashi ne da tausasa
harshe, baʼace mace ce kadai zata yiwa namiji
ba haka ba'a ce namiji shi kadai zai lallashi
mace ba itama sai ta lallashe shi."
Nasrin ta bata hannu suka tafa ta ce, "ina
sonki saboda fahimtar nan tata ki Antimi.
Labarin mutanen da suka san abinda suke zan
baki, irin mutanen da suka yi karanci a
96 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
kasarmu, irin mutanen da ya kamata su mulke
mu, wadanda Allah Ya yi musu baiwa ta iya
tsara magana a rubuce."
Zainab ta gyara tsayuwa ta ajiye cinyar kazar
da take wankewa.
Ta ce, "wannan wanene, daga Amerika
yake shima? A ina kika sanshi,ko a gidan
talabijin dinku?"
Nasrin ta yi murmushi ta ce, “Ban taɓa
ganinsa ba rubutunsa nake a gani a facebook
kawai. Dr.Jalo sunansa, Dinah ta san shi, mu yi
ta yi masa magana ya ki amsawa saboda jan
aji. Amma yanzu kin ga yana kula ni har ma in
tambaye shi abu ya ban amsa.
"
Zainab ta harare ta, ta yi tsaki ta juya ta
ci gaba da aikinta.
Nasrin ta ce "au Dr.Jalon
tsaki?"
kike yiwa
Zainab ta ce “ke wallahi haushi kike ba ni.
Daman har yanzu baki rabu da bibiyarsa ba. Ni
da na karanta wani post dinsa bai birge ni ba,
kawai dai ya iya turanci ina ga a turai ya yi
makaranta.'
"
97 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Nasrin ta mike ta fice daga kicin din
cikin fushi, Zainab ta biyo ta tana kwala kira,
Nasrin ta ki dawowa dan ta yi fushi, Zainab ta
sha dariya ita kaɗai.
Nasarin na shiga daki ta mayar da kofa
ta rufe ta ci gaba da karatun rubutun
mutuminta. Har yanzu dai bai hau ba. Ta
ɗauko wayarta ta kira lambarsa, a kila-wakala
take, zai dauka ko ba zai dauka ba. Sai gashi
kuwa bai dauka ba. Bata ji dadi ba ta ji jikinta
ya yi sanyi sai ta fara daina ganin laifin Zainab
gaskiya ne mutumin da bai ma san tana yi ba
har ta tsaya tana ɓatawa kanta rai.
Bugun kofar da ake yi mata ta ɓaci, sai
yi ake yi ana sakewa. Ta san Zainab ce sai bata
amsa ba amma daga baya ta jiyo muryar
Zainab da kuma ta kawarta Dina. Dan haka ta
taso ta buɗe. Ita da Dina su ka yi tsalle suka
rungume juna suna murna. Dinah ta ce, "kin
huce? Aka ce fushi kike yi. Waya taɓa min
ke?"
Nasrin ta zunɓuro baki ta koma gefen
gado ta zauna.
98 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Zainab tana ta dariya ta ce "wai dan na
kushe wani abokinta a facebook take fushi. Ni
da na ji tana yabonsa na zaci ma ta sanshi, ko
cewa ya yi yana sonta. Saikawaina ji ta ce bata
taɓa ganiusa ba haushi ya kama ni."
"
Dinah ta tsaya akanta tana harara ta ce
"wannan dan wulakancin kika ci gaba da
kulawa? Wallahi ke abin haushi ne da ke.
"
Nasrin ta ce, “ke ma ki biyewa Anti
Zainab ki ci gaba da ɓata min rai. Ni fa ban ce
wani wani abu ba fada mata zan yi in ce ya
rage girman kai fa, yanzu yana ba ni amsa."
Zainab ta yi gatsine ta yi zumɗe da baki
ta ce "Ayyah kanwata yi hakuri, na zaci
wulakancin ya yi miki kuma. Yi hakuri my
sweetsister.
"
Gaba daya suka yi dariya, zainab ta fice.
Dina ta zauna a kusa da Nasrin suka ci gaba da
Kallon rubutun Jalo a Facebook, gaba daya
suka hada kai suka rungumo Computer suna
karantawa a tare suna shewa, suna tafa hannu
suna jinjina.
Suna fadin "Allah Ya taimaki likitan
likitocin Naija."
99 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Dinah ta ce, "gaskiya ya birge ni gashi
yaro bai fi shekaru talatin da biyar ba. A wanne
gari yake ne?"
Nasrin ta taɓe baki ta ce, “inazan sani ni
da ba kula ni yake yi ba? Amma mu duba
profile dinsa. 66
Suka dukufa suna ta bincike akansa sai
bayanai suka nuna shi likita ne, mazaunin
Lagos yana da mace daya da yara biyu maza.
Matar tasa ma 'yar gidan Minister lafiya ce,
sunanta Rayyana Abbas sun san sunan
Babanta. Nan da nan suka koma neman
Rayyana Abbas a Facebook, sai kuwa suka
bankado ta.
Tubarkallah! Masha Allah!! 'yar gayu
ce matuka sai dai bata da kyau,baka ce kirin
gajera mai kiba, amma akwai ilimi da kudi. Ita
kuma cikekkiyar lauya ce.
Dinah da Nasrin suka yi shiru suna
kallon juna suna mamaki.
Nasrin ta ce, "shege ai dole ya ja aji ya
san yagama zabar mace. Ita kuwa ta yi sa'ar
miji mai kwanya, sai ta godewa Allah kuma ta
kula da shi dan idan ta yi sakaci mahara zasu
100 | Jamila Umar Tanko (JUT)
_ DA MA NI CE... 1
kawo mata farmaki saboda mijinta kadara ne.
Kin ji muryarsa kuwa . • • • Hmmmm, ba
magana ke guy din ya hadu daga kafa zuwa
tsakar kai.'
"
Suka sheke da dariya suka tafa hannu.
Dina ta ce, "Nasrin kina son likitan nan ko?"
Nasrin ta yi fari, ta dagaido sama tana tunani ta
ce "not really but...."
Dina ta katse ta, ta bangaji kafadarta ta ce "but
me? Kawai ki fada min gaskiya kawata. Ina
zaki ajiye Engr.Fu'ad?"
Nasrin ta ce, "maganar gaskiya Dr.Jalo
yana burge ni amma ba don kyansa ba, dan in
karu da iliminsa kin san ni da son aikin jarida,
bayan haka ina son mutum mai aji. Duk ya
hada."
Dina ta ce, “idan na kula kina son alaka
da shi ta kurkusa bata nesa ba."
Suka yi dariya suka tafa.
.99
Nasrin ta ce, “ke muyi wata hirar mu
share wannan da ma bai san abinda muke yi ba.
Allah Ya bamu maza na gari muma.
Dinah ta ce "da dai ya fi."
101 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Wayar Nasrin ceke kara Dinah ta miko mata
da sauri, Nasrin ta na dubawa taga sunan
Malaika, sai ta yi tsaki ta ajiye wayar a gefe.
Dinah ta ce, "wacece Malaika?"
Nasrin ta yi dariya ta ce, "sabuwar kawa na yi
a Kano idan na baki labarinta zaki yi kwana
uku kina dariya dan nasan halinki abu kadan
ma dariyar awoyi ki ke yi kina yi."
Dina ta tuntsire da dariya ta ce,"dan
Allah ba ni labarin Malaika."
"
dauka.
Malaika ce ta ci gaba da kira, Nasrin ta ki
Dina ta ce "ki dauka dan Allah ki saka
min ita a hand'sfree mu ci dariya."
Nasrin ta ce, “dan Allah rabu da itaba
zan dauka ba, surutu zata yi ta yi. Ke! zama ki
santa. Ina wacce aka taɓa nunawa a labaraihar
kika kira ni kina ta shan dariyar turancinta, sati
byu da suka wuce? To itace fa. "
Dinah ta yi tsalle ta dire tana ta dariya ta
ce "Wallahi sai kin dauki wayarta, in ba zaki
dauka ba ki bani lambarta ni in kirata mu
gaisa."
102 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Nasrin ta hana ta, wayar dai har yanzu
kara take yi, kira