kwana biyu kawai na yi, aiki ya
kawo ni, ina bautar kasa a gidan talabijin ta
taraiya NTA."
Shamaki ya kama haɓa yana mamaki
"lallai kuna shan aiki. Allah Ya taimaka,
na gode."
yace,
Nasrin ta ce, "Amin. Sai da safe.'
Suka kashe waya.
"
Shamaki a zaune Cur ya kwana yana
mamakin yadda Malaika ta ke kokarin cusa
kanta a wajen manyan mata irin wadan nan,
53 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
yadda ma Nasrin take magana Hausar ma tana
kwące mata, turancin Amerika take yi, dakyar
in ba girman can ba ce. Lallai Malaika da
karfin hali take, ita da ta taso a kauye Allah ya
rufa mata asiri ta dawo birni da zama amma
tana hangen 'yan Abuja da 'yan kasar waje. Ya
ci gaba da tunanin yadda rayuwarsa da ta
matarsa zata kasance nan gaba, saboda a
kullum kutsa kai ta ke, kuma haduwa da
mayan mata take sake yi, tana sake
taɓarbarewa a koda yaushe. Ya ci gaba da
addu'a Allah Ya sa ta gane.
Gari na wayewa Malaika ta tashi da fushi
tana ta kunzumawa yara asharai KwandoKwando, wani ya yi kashi a kwance, wani ya
yi fitsari, daya kuwa amai ya kelaya mata.
Shamaki yana jinsu yana so ya fito ya taya ta
yana tsoron masifarta.
Ta taho a fusace ta daga labulen falon ta
dube shi sama da kasa ta ce, "sannu hamshaki,
Shamakin Muntsira wanda bai san wahala
ba.Ka zo ka hakimce akan kujera an aura maka
baiwa ko? To ka fito ka kula da yaranka
gaskiya bazan iya ba da rayuwar talaucin nan,
54 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
dan tsiya ko me aiki ma ba zaka iya samar min
ba."
Shamaki ya yi murmushi ya fito tsakar
gida, yace "ina jin ku ai ina so in fito ina tsoron
masifarki."
Ta fusata ta koma ɗaki ta kwanta akan
gado ta ce, "ga su nan sai ka gyara su kayi
musu wanka, kuma na gaji da wankin nafkin
pampers zaka siyo min irin na 'ya'yan kowa su
yini da ita su kwana da ita." aim 162
1
Shamaki ya gyada kai yace, "Cafdijam!
Allah Ya hore."
99
multicl 90cm
Ta zabura ta tashi zaune cikin tsiwa ta
ce, "Daga anyi magana sai kace sai albashini
wani watan. Wai kai nan dan albashi komai sai
an yi albashi. Ni fa gaskiya bazan iya ba. Tam no "
Yana jinta tana ta bala'i, bai kula ta ba,
ya lallashin yaran, nan da nan suka yi shiru
suna wasa da dariya ya wanke su tsaf ya shafa [
musu mai ya ɗora musu koko ya basu suka sha,se
kanana biyu suka yi bacci ya je ya shinfidar da
su sannan shima ya yi wanka zai tafi makaranta
dan yana da lacca karfe sha biyu.
wy 55 | Jamila Umar Tanko (JUT) (TU) 08
DA MA NI CE... 1
Ya tsaya akan Malaika tana ta danna
waya bata kalle shi ba, ya mika mata kuɗi
Naira dari biyu ya ce, “ga wannan a yi cefane a
sayi ruwa."
Ta daga kai ta kalla a shelake, ta ce,
"dubu ce ko dari biyu?"
Bai batakarɓa ba ya ajiye a gabanta ya
fice, yana fita tsakar gida, ya ji ta a guje ta tare gabansa ta ce "wallahi ba in da zaka je sai ka
kara min dari uku, kudin cefanena daga yau
naira dari biyar ne kullum. saboda kowacce
mace kullum sai mijinta ya saka mata katin
waya. Idan da ka ce ba wandazan kira yanzu
ina da manyan da nake magana da su kuma
harkar karuwa ce harda kai. Sannan na gaji da
cin mai da yaji miya zan dinga yi da nama
kamar kowa. Kai hatta da kayan sakawata
canjawazan yi, na gaji da atamfofi kanana,
leshina masu tsada irin na su Nasrin zan fara
sakawa."
"
Ya tsaya yana kallonta, yanajin abinda
take fada tamkar almara, ko mafarki.
56 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE
Ya ja hannunta suka shiga falo suka
zauna ya jima yana kallonta ya yin da ita kuma
take gatsine- gatsine.
Ya fara magana cikin sanyayyaiyar
murya. "Malaika! Shin ada a haka muke, ba a
kauye muke ba gidan kasa da kara? Allah Ya
daukaka mu muka dawo birni har na kama
gidan haya na siminti. Da a kauye ba tallar
goro kike ba ni nake sayar da rake daga baya
na sami aiki har na samu na dawo jami'a? Kika
san babban aikin da zan samu idan nagama
karatun nan? Haba Malaika, Dan Allah ki
nutsu ki yi hakuri na dan lokuta Allah Zai
warware mana. Babban tashin hankalina ma
shine yaran nan musaminan marar lafiyar nan.
Malaika bakya kula da shi kin san yanayin
ciwonsa sai da kula. Ki taimake ni Malaika ki
taimaki yaran nan. Kin ga Aliyu ya isa shiga
makaranta ko Nursery cikin unguwa ina so in
saka shi amma asibiti duk ya cinye kudin.
',
Yanzu kina maganar in saka miki kudi a
waya ki dinga kiran manya. Su waye manya?
Kada son zuciya ya kai ki ga fadawa ga
halaka."
"
57 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Ta zabura ta harare shi sama da kasa ta
ce, "zargina zaka fara kuma? Ni Nasrin nake
nufi da Dr.hala. "
Shamaki ya gyada kai yace, "ba zarginki
zan yi ba, Malaika ban taɓa zarginki ba. Amma
bai kamata ki fi ganinsu da daraja ba fiye da ni,
ni mijinki ne kuma aljanarki tana karkashin
tafin kafata. Ban rage ki da komai ba, bakya
raga min. Abin ya kai ma mun raba shinfida
daga na doso ki sai tsaki da hantara. Menene
laifina? Dan Allah Ya halicce ni a talaka?
Malaika talauci ne laifina?"
Sai hawaye ya surnano daga idanuwansa
yayin da Malaika ta kura masa ido itama
idanuwanta sun cika da kwalla, ta yi sauri ta
mike zata fice daga falon.
Ya jawo hannunta ya ce, "kiyi min
alkawari daga yau kin daina duk abinda kike yi
min. Kiyi min alkawari za ki gyara mu zauna
lafiya. Ni kuma na yi miki alkawarin zan ci
gaba da fada miki gaskiya da samuna da
rashina. Albashin ma duk wata zan dinga kawo
miki shi dukka kina kasaftawa, dubu goma sha
takwas ne albashin."
58 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Malaika ta fisge hannunta ta fice da sauri
ta koma daki ta kwanta.
Ya fito yana goge hawaye da takardunsa
a hannu, ya hau babur dinsa daya ajiye a zaure,
ya tafi. Aliyu ne ya raka shi har kofar gida
yana ta cewa “Baba ka siyo min alewa."
***
Wayar Malaika ce ta hau kara jim kaɗan
bayan fitar maigidanta, tana dubawa taga
sunan Shamaki ne.
Ta ki dauka gami da yin dan siririn tsaki
ta ce,"me zai yi min kuma?"
Ya ci gaba da kira sannan ta dauka a
fusace ta san dai wani abu zai ce ta saya duk a
cikin dari biyu kamar wani kayan gabas.
"
Ta fada a fusace “ina jinka."
Ya yi murmushi yace, “ina cikin
makaranta yanzu zan shiga Lacca nace bari in
kira ki in ji muryarki gimbiyata."
Haushi ya tokare ta, takaici ya baibaye ta
yayin da dacin kunar zuci ya yi ta taso mata a
makoshi.Ta yi tsaki ta kashe waya.
59 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Ta wurgar da wayar gefe ta kwanta tana
takaici, ita fa duk wannan soyayar da zai nuna
mata ba zata wadatar da itaba, ba zata zauna ta
kare a cikin lungu ba bayan ga mata can suna
fantamawa a cikin manyan motoci da manyan
gidaje. Ta tuno yadda ta hango Dr.Hala a cikin
motarta, ta hango Nasrin yarinya kamar furen
fulawa saboda kyau da gayu, ga kamshi. Ta
kalli kanta sama da kasa ta ganta kamar wata
bushashshiyar bishiyar da ta
sanadiyyar fari, wacce ba'a bata ruwa da taki,
hakika wataran faduwa zata yi ta zama
bushssheshan itace daga nan kuwa sai sara a
kwasa akai gida a dafa tuwo ya kone, ya zama
toka.
bushe a
Ta fada abayyane “ba zai yiwu ba
wallahi.'
"
Wayarta ce ta ci gaba da kara ta ma ki
kallon wayar balle ta dauka sai a karo na uku ta
sa hannu ta ɗauka a fusace ta san Shamaki ne,
ta faɗa cikin tsawa bayan ta danna “wai
meye?"
Sai ta ji wata sanyayyiyar murya mai
kama da ta busar sarewa, aka yi mata sallama.
60 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Da sauri Malaika ta cire wayar daga kunnenta
ta duba sunan mai kira.
'Nasrin Abdul Nasir'
Wai! Rigijigafji!! Zo ku ga murna da
ladabi gaba daya ta sauko daga kan gado ta
durkusaa kasa.
a
Malaika ta gaishe da Nasrin. Ta yi mata
kirari gami da addu'oin samun nasara
rayuwarta. Sai Nasrin ta fara mamakin yadda
Malaika ta iya kalamai haka amma bata yiwa
mai gidanta. Ta gasgata Malaika tana da
cikekken hankali babu taɓin hankali haka tana
da ilimi da dubara ba gaɓuwa bace. Ta kudiri
niyyar sai ta nemo daga ina matsalar ta ke. Yar
jarida me neman labarai.
Nasrin tana gyara zama tana juyi a
kujerar ofis dinta ita kaɗai ce, dan yau gaba
daya abokan aikinta sun fita aiki.
Nasrin ta yi murmushi ta ce, "kawata, na
kira in gaishe ki ne kuma in ji lafiyar yaranki
da mai gidanki. Yaya kuma yaro mai sikila?
Ina fatan ya ji sauki.'
99
Malaika ta washe baki ta ce, “lafiya kalau kawata, Allah Ya bar mu tare."
61 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Nasrin ta ce, "amin. Yau fa kira na yi
muyi hira sosai dan ba ni da aikin yi."
Sai Malaika ta dafe kirji, aka yi murmushi ta tashi bazar-bazar ta dawo falo ta
zauna akan kujera aka yi bake-bake, jinta take tamkar da shugaban kasa ta ke magana, ita
kuma ta zama minista.
"lah dan Allah da gaske kike Nasrin? Amman na ji dadi, ashe kina sane da kiran da nake yi miki kullum? Wato aiki ne yake hana ki amsawa. Na zaci wulakanci ne ma dan kin
ganni talaka."
"
Nasrin ta ce, "haba dai ai ke ma ba talaka
bace kyakykyawa dake gashi sunanki mai dadi kuma naga alamar ke jinin sarauta ce ma
'Shamaki'. Ba ni tarihin rayuwarki Malaika."
Dadi ya rufe Malaika, ta yi dariya ta ce,
"Kwarai nice kuwa jinin sarauta.
62 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE...
LABARIN MALAIKA
Sunana Malaika, sunan mijina
Shamaki, sunan garinmu
MUNTSIRA,a cikin karamar
hukumar Bichi.
Mahaifina attajiri ne, mai kudin gaske ga
sarauta amma ya rasu, ni kaɗai ya haifa 'yan
uwansa suka cinye min gado. Na zo na auri
talaka yana ta gana min wahala ni da yarana.
Shine nake so ki kawo min agaji nima in fita
daga wahalar nan. "
Malaika ta fashe da kuka. Sai Nasrin ta
yi shiru hankalinta ya tarhi ta kasa tantance
mai gaskiya a tsakanin mijin da matar..
Nasrin ta ce, "Malaika daina kuka ki
faɗa min abubuwan da mijinki baya yi miki na
hakkin aure.'
"
Malaika ta goge hawayen da daman bai
zubo ba ta ce, "gidan haya nake ɗan karami
63 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE...
mai kunci, daki biyu kanana, idan zafi ya zo ba
iska numfashinmu na cikewa, sai ayi wata ba'a
kawo wutar lantarki ba, muna cikin duhu ba
mu da jannareto, babu ci, babu sha, dari daya
yake ba ni ko naira hamsin kudin cefane kuma
a ciki zan sayi ruwa. Ga yara uku daya ba
lafiya.Kayan jikina a yayyage, kamar almajira,
makawabtana ma basa kawance da ni saboda
duk sun fini."
Nasrin ta girgiza kai cikin damuwa ta ce
"bashi da shi ne ko yana da shi ya ɓoye?"
Malaika ta cije baki ta ce, "yana da shi.
ya ɓoye baya bani sai dai ya kashewa 'yan
matan waje da danginsa."
Nasrin ta dafe kai dan tausayi, ta faɗa a
bayyane "me yasa mazan Hausawa suke da
mugunta ne? Allah sarki Malaika, ki ci gaba da
hakuri. Kin ji? Ita rayuwar aure lada ne kuma
wannan jarabawar itace zata kai ki ga shiga
aljanna, idan kika yi hakuri za ki haye.".
Malaika ta fashe da kuka ta ce, “shiyasa
kika ga ina ta binki rannan da muka haɗu, ko
Allah Zai sanima ki samar min aiki a Abuja in
samu in rike 'ya'yana. Auren nan ya ishe ni
64 Jamila Umar Tanko (JUT)
- DA MA NI CE…..
daman kullum cewa yake zai sake ni ya auro
wata.'
"
Nasrin ta girgiza kai ta ce, “kada ki sake
ki kashe aurenki, aure daraja ne da shi ki zauna
ki rike ‘ya'yanki. Za ki iya sana'a a gida ba sai
kin fito ba, Abuja kuma ta yi nisa, ke da kike
Kano. Aiki a Abuja kuwa sai ka yi karatu mai
zurfi kin ga ke ba kiyi ba."
da
Malaika ta zabura ta ce, “ai na yi karatu
yawa dan nagama sakandire na yi diploma."
Nasrin ta zare ido ta ce, “da gaske, ashe
kawar tawaba sauki? To gaskiya ko koyarwa
ce ya kamata a samo miki anan unguwarku bai
kamata ya tauye ki ba.'
Malaika ta ce, "ni dai gara in zo Abujar
nan in same ki in ma ba aikin ba in kwana biyu
nima in ga gari an ce kamar a turai garin yake,
ban taɓa zuwa ba. Sai dai makwabciyata ce
suke hutu acan idan ta je ta dawo sai ta dinga
yi mana yanga, da jijji da kai. Ina so nima in je
Abujar nan, Nasrin ki taimaka min.”
Nasrin ta girgiza kai ta ce, "kullum ina
fama da aiki amma karshen wani watan za mu
shigo Kano aiki zan neme ki sai mu ga yadda
65 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
za'ayi. Yanzu zan turo miki da katin Naira
dubu uku ki siyar ki rage wata matsalar, amma
dan Allah kawata ki kula da hakkin aure, ki ci
gaba da hakuri watarana Shamaki zai gane
kurensa idan shi ya cuce ki, ai Allah ba
azzalumin sarki ba ne.99
Malaika ta fara shshshekar kukan karya
tana godiya.
Suka kashe waya.
Malaika ta daka tsalle tana rawa tana
murna Aliyu ma ya taho da gudu yana taya ta
suna ta rawa suna murna duk da bai san me
yake faruwa ba, ya san tabbas yau Mamarsa na
cikin farin ciki saɓanin kullum da ta ke cikin
fushi tana kyararsu da zagi.
Ba'a jima ba sai ga sako ya shigo wayar
Malaika tana dubawa taga sakon kati daga
Nasin, sai ta dauki mayafi ta fita wajen mai
sayar da kati na kofar gidansu, anan ta siyar ya
bata kudinta ta shigo gida tana ta fara'a, babu
sauran fushi kuma ayau.
Ta yini tana lissafin abubuwan da zata
saya da kudin nan Naira dubu uku saboda
bukatarta tafi ta dubu talatin ma. Tana son ta yi
66 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
dinkuna, tana son jaka, tana son takalma da
mayafai, tana so ta fara saka tabarau (glasses)
a fuska irin na Nasrin da Dr.Hala, itama ta
zama 'yar gayu kamar su.
.Da misalin karfe huɗu da rabi na
yamma Shamaki ya fito daga cikin masallacin
B.U.K bayan ya idar da sallar laʼasar, sai ya ji
wayarsa na kara ya dauko ya duba lambar,
lamba ce kayatacciya kai kace mai lambar
tsarata ya yi da kansa,daga gani babu tambaya
lambar ta daban ce, musamman daga kamfanin
MTN, sai ya ga kamar ya taba sanin lambar
amma ba zai tuna in da ya san ta ba. Gabansa
na faduwa ya amsa yana mai addu'a ko waye
mai kira Allah Ya sa alkhairi zai fada.
A lokaci guda suka yiwa juna sallama
cikin girmamawa. Shamaki ya yi shiru yana
jiran mai kira ta gabatar da kanta, kuma ta fadi
dalilin kiran.
67 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE...
Ta ce, "sunana Nasrin Abdul Nasir daga
Abuja. Ina fatan ina magana da Shamakin
Malaika?"
Shamaki ya yi mamaki gami da farin ciki
sai ya amsa "Eh nine."
Yana tafe yana magana ya gaggauta
barin jikin masallaci ya koma can gefe ya sami
bishiya da kujerar zama ya zauna suka ci gaba
da Magana, ya tabbatar tunda Nasrin ta kira shi
da akwai wata magana mai muhimmanci. M
✓ Bayan sun gaisa Nasrin ta yi ajiyar
zuciya ta ce "Jiya ka kira ni a da daddare na
fara bacci, shiyasa na kira ka yanzu. Kafin in
shiga cikin irin wannan magana musamman
magana ta maʼaurata ya kamata in dan san
wani abu daga cikin rayuwarku ko da kuwa
kadan ne, ba sai dukka ba.” na 37
Shamaki ya gyada kai yace, "haka ne
Nasrin. Ki saki jikinki mun baki amanar
kanmu,mun yarda da ke ki tambaye ni komai
da kike son sani in Allah Ya yarda zan amsa
miki."
Nasrin ta yi murmushin jin dadi ta ce,
"na gode. Malam Shamaki zan so in ji
68 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
labarinka dana Malaika, da yadda ku ka hadu
har ku ka yi aure.
Shamaki ya ji dadin tambayar nan sai
yace, "Malama labarin da tsayi sai dai in kin
shigo Kano mu zauna saboda kudin wayarki
zai kone da yawa."
Nasrin ta yi dariya ta ce, "kada ka damu
kuɗin wayata zai isa mu yi ta magana daga
yanzu zuwa gobe da safe ba zai kare ba.”
"
Shamaki ya gyaɗa kai ya yi jinjina ya
faɗa a ransa "babban goro sai magogin karfe,
sama ta yiwa yaro nisa sai dai ya ɗaga ido ya
hango ta. Allah Ya yi mana arziki ta hanyar
halal. Amin.'
"
Shamaki ya yi ajiyar zuciya gami da
gyaran murya, yaci gabace, “to ba damuwa
bari ki ji cikekken tarihina da na matata
Malaika.
LABARINSHAMAKI:
Yace "sunana Yusuf Muhammad Yusuf,
sunan garinmu MUNTSIRA garinmu bashi da
nisa da karamar hukumar Bichi, cikin jihar
Kano. Na ci sunan Kakana Yusuf shi kuma
69 | Jamila Umar Tanko (JUT).
CE... 1
yana da lakabi da ake kiransa Shamaki,
Mafarauci ne kuma gwarzo a wajen sana'arsa.
Shiyasa nima ake kirana da Shamaki karami,ko
a makaranta Shamaki Yusuf Shamaki nake
rubutawa.
DA MA NI
Na tashi a maraya mahaifina ya rasu tun
ba'a yaye ni ba kuma nine ɗansu na fari,
mahaifiyata ce kadai ke da rai, ana yaye ni sai
Kakana Shamaki ya dauke ni, a wajensa na
girma. Mahaifiyata ta je ta yi wani auren ta
haifi kannena maza biyu, Kasim da Hashimu,
da mace daya 'yar autarmu mai suna Sadiyalle.
Babu abinda Kakana ya iya sai farauta
abinda ya koya min kenan, da girmana na shiga
makaranta boko amma na yi zurfi a karatun
allo, babu wanda ya saka ni a makarantar
boko,da naga abokaina suna zuwa nima abin
yake bani sha'awa na ke binsu. Na gama
firamare na shiga sakandire,daga garinmu da
kafa nake zuwa Bichi makaranta, in je in dawo
babu abinci, babu kudin tara, kayan
makarantata ma a yayyage sai dai idan 'yan
ajinmu sun tausaya min sai su bani tsohon
70 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
nasu, haka takalmana sun fatattake saboda
tafiyar kafa.
Cikin ikon Allah duk wadanda muka
fara karatun tare tun ba'aje ko in ba suka
watsar da karatun a takaice dai a wannan
lokacin ni kaɗai ne nagama sakandire a
kauyenmu. Nima sai na yi kamar zan bari
Malamin ajinmu ya zo har gida yayi min
nasiha dole in koma ba dan ina so ba saboda da
ni ake ji a makarantar ina da kokari sosai.
Kokarin da nake da shi ba irin wanda za'a ce
na daya yake zuwa ba kullum, A' a kokarin da
zan gagari Malamai ina kokarin kure Malam a
aji, idan aka yi jarabawa babu dalibin da yake
samun maki kusa da nawa sai dai can kasa dan
ni a kowacce jarabawa casa'in zuwa casa'in da
tara nake ci a cikin dari. Mutane har gani suke
ko ni ba mutum ba ne ba ma. 29
Nasrin ta gyara zama ta ce, “dakyau
shamaki ina jinka.'
"
Ya yi murmushi ya ci gaba da cewa, "Na fito
da sakamakon jarabawa mai ɗankaren kyawun
gaske. Malamin nan na ajinmu ya yi iya
kokarinsa wajen ganin gwamnati ta dauki
71 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
nauyin karatuna zuwa Jami'a, Ciyaman din
garinmu na wancan lokacin ya ce zai taimaka
min amma basu mayar da hankali ba, sun yi
alkawari ba su cika, ba har aka canja
gwamnati.
Na hakura da maganar karatu na ci gaba
da sayar da rake a kofar gidanmu, sai daga
baya ina ta fadi tashin neman aiki bayan
shekaru sannan na samu aiki a sakateriyar
Bichi, anan nake aiki har yanzu da satifiket
dina na sakandire.'
99
.
Nasrin ta gyada kai ta ce, “da kyau.
Malaika fa? Wacece Malaika?"
LABARIN MALAIKA:
• Yace "Malaika Dahiru Muntsira, garinmu daya
layinsu a bayan layinmu yake,tare muka tashi
mun girme su amma dai dukka an yi wasa tare.
Babanta Malam Dahiru shine mai garin
garinmu Kuma yana da mata huɗu da yara da
yawa, ko a ɗakin su Malaika ma su tara
mahaifiyarsu ta haifa."
Nasrin ta cika da mamaki ta bude baki ta
kasa rufewa dan mamaki.
72 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Ta yi ajiyar zuciya ta ce, "Allah ya jikan
Malam Dahiru."
Shamaki ya zabura, yace, "ai bai rasu ba
yana nan ya dai tsufa, ai ita ‘yar gatace da
uwarta da ubanta a raye."
Sai Nasrin ta zazzare ido tana mamaki
dan ta fara jin banbance-banbance a tsakanin
labarinsu, tabbas akwai makaryaci a cikin su
biyun nan amma dai bari sai taga abinda zai
turewa buzu nadi.
Ta yi gyaran murya ta ce, "Allah
na zaci ya rasu ne, Allah ya kara girma."
Shamaki yace,"Amin. To kasancewar
mu a kauye, dan sarki da talaka duk talawa ne
kowa na yakin neman abinda zai ci, suma a
gidansu akwai tsabar gero da masara ammafa
mahadin dahuwa kowacce ita zata nema da
yaranta. Haka muka taso kuma muna jin daɗin
rayuwarmu kamar kowa, Allah ya jarrabe ni da
son Malaika itama tana sona sosai har ma fiye
da yadda nake sonta. Ban taɓa yin budurwa ba
a rayuwata sai Malaika ita kadai na taɓa ji ina
so har a cikin raina, haka itama ni kadai take
kulawa. Mahaifinsu yana tilastawa 'ya'yansa
sarki ai
73 | Jamila Umar Tanko (JUT)
_ DA MA NI CE... 1
mata da maza su yi makarantar firamare
kasancewarsa mai gari dole sai an ga yaransa suna zuwa makaranta sannan 'yan gari zasu
yarda su bar nasu 'ya'yan su je, dan haka
Malaika ta gama firamre tas, ni na je na sami
babanta na bashi shawara ta tafi sakandire ni
zan dinga yi mata siyayyar makaranta da yake
Makaranta kwana ta ci.
Ya amince Malaika ma bataso na
lallashe ta, dan bata son ɓacin raina aka kaita
makarantar kwana ta garin 'Dan zabuwa' nan
kusa da garinmu.Garin kwaki, Kanzo, maggi,
man gyada, gishiri sune dai siyayyar nake siya
mata, idan ya kare ta yi min wasika wani
Malamin makarantarsu ya kawo min in siya in
bashi ya kai mata. Idan kuma ranar ziyara ta zo
wato bisiting ni nake je mata, kawayenta kakaf
sun san Malaika da Shamaki, dan soyayya ma
haka ta mayar da sunanta a makaranta ba'a
kiranta da Malaika Dahiru. A garinmu kowa ya
san soyayyata da ita, samarin da suke sonta da
yawa mun sha tare ni dambe a hanya suna
ganin a dalilna ta ki su, haka itama ta sha
74 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
dambe da 'yan matan da suke matukar sona
bana kula su.
Ina sana'ar Rake bana tsinanawa kaina
komai a jikin Malaika nake karewa, dangina
suna ta zagina hatta mahaifiyata sai da ta fara
jin zafin haka takan kira ni ta yi min fada, ina
tabbatar mata wani abin ma karyar 'yan gari ne
ba ayi ba.
Sai da na zamar da Malaika abar
kwatance a cikin kawayenta, ni ne dinkunan
sallarta, ni ne ankon bikin kawaye da danginta,
ni ne kudin kashewarta, ni na bata jarin da take
sayar da wainar fulawa da awara a kofar
gidansu idan tadawo hutu. Malaika tana da
kokari matuka kuma na yi kokarin koyar da ita
abubuwa da yawa idan an yi hutu, hatta turanci
ni nake koya mata. Har ya zamanto ta fi
kawayenta iya turanci, sai ayi ta mamaki idan
aka ji tana turanci.
Tana matukar jin maganata kasancewar
tana da tsiwa da taurin kai dan wani lokaci sai
mahaifiyarta ta kira ni a kawo min kararta in yi
mata fada sannan ta bar abinda ta ke yi. Tana
aji hudu na sakandire Mahaifinta yace ta isa
75 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
aure za'a cire ta in zo in aura idan kuma bana
so zai yi mata miji, dan ya ji na fara rokarsa
ya bar ta, ta kamala sakandire. akan
A dole na fito aka yi aure daman na daɗe
ina taron kayan auren. Dakin kasa guda daya
jal Kakana yaba ni,anan muka zauna shi kuma
da matarsa suna cikin daki daya. A haka muke
zaune ban dade da yin aure ba na sami aiki a
Bichi ake biyana albashi daga nan rayuwarmu
ta dinga ci gaba. Mun fi karfin ci da sha da
sutura sannan a hankali na yaɓe gidan kasarmu
da siminti, na cire katagar kara na yi Katanga
ta bulon kasa, muka ci gaba da zama na
soyayya har Allah Ya ba mu haihuwa yaronmu
na farko Aliyu, muka haifi na biyu na saka
masa sunan kanina Kasim.
A lokacin ne abokina yaba ni shawara
muka je muka zana jarabawar Jamb, muka cike
B.U.K. Abokina ya SO in karanci
Likitanci(Medicine) na ki amincewa saboda shi
ya san zan iya amma ni ina ganin ba ni da
damar da zan jure karatun likita saboda ga
iyali, ga aikina, zan fito in je neman abinda zan
ci dole. Na cike kos din Biochemistry, Allah
76 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
cikin ikonsa ranar jarabawar Jambmuka je
muka zana kuma na ci da yawa, abokin na
kuwa bai ci ba.
Nan da nan da gudu suka ba ni abinda na
zaɓa daman sakamakona na sakandire ya yi
kyau. Na nemi izini daga wajen aikinmu suka
bar ni na tafi da albashina (inserɓice) ko da
yaushe da babur dina nake zuwa daga Bichi
zuwa Kano, in yi lacca in koma, da na ga da
wahala sai na yi adashi na hada da rance na zo
na kama mana gida anan Kano,a unguwar
Dorayi akan Naira dubu talatin da biyar haya a
shekara.
Na dauko iyali muka dawo yanzu haka
muna cikin shekara ta biyu kenan, anan aka
haifi dan autan danmu Ahmad, kuma Allah Ya
yi shi yana da sikila. Gashi dai ana ta faman
zirga-zirgar zuwa asibiti.'
Nasrin ta yi shiru tana mamaki wannan
labari mai kama da almara, ta ji talauci tsantsa
dan ita bata san irin wannanrayuwar ba.
Ta yi ajiyar zuciya ta ce, “idan na lura
Malaika na sonka kuma tana yi maka biyaya
ko? Menene laifinta yanzu?"
77 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Ya yi dariya yace, "Jama'a da yawa tun a
garinmu suna ta maganar cewa Malaika tana yi
musu kallon banza, dan ta auri miji yana yi
mata hidima, da na fara aiki ta fara miya da
nama sai abin ya karu har 'yan uwana da 'yan
uwanta suka shiga layi suna ta jin haushi wai
Malaika na wulakanta su in an je gidan sai taga
ḍama ta kalli mutum, in dai ba da kai zata karu
ba bata kawance da kai. Ni dai ban gani ba dan
bata yi a