Ya yi mana yatsu wani ya fi wani girma
dan mu san ba daidai kowa ya ke ba, wani ya fi
wani. Dan haka dan na raɓi mai kudi dan in
sami danshin inuwa ban yi laifi ba."
Shamaki ya damke hannu ya ji tamkar
zai kai mata naushi, sai ya fasa saboda tsantsar
takaici. Ya rasa amsar da zai bata, kwalla ta
cika masa ido ya yi tsaye yana hangenta tana
zaune a falo, ta dora kafa daya kan daya tana
girgizawa.
Yace "Malaika! ki je ki nemo maganin
jahilci dan wannan ciwon yana damunki. Sau
biyu ina sayo miki fom din makarantar matan
aure sakandire ta ya ki da jahilci kin ki shiga.
Na siyo miki na islamiyya kin ki zuwa. Kin
gwammace kina ta yawo a gari kina kallon
masu ilmi kina sha'awa."
Ta murguda baki ta ce, “ka je ka nemo
maganin talauci dan talauci na damunka kai
kuma.
"
26 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Yace "na godewa Allah a yadda ya bar
ni dan na fi wasu, da yawa a jikina suke cin
abinci. Ko a haka na dauwama Allah Ya yi min
komai da Ya bani imanin sanin Sa da yarda
dakaddara. A koda yaushe bakya taɓa kallon
na kasa da ke sai wadanda suka fi ki dan haka
ba zaki taɓa godewa Allah ba. Kin fi wasu,
wasu kuma sun fiki."
Ta ce "ko a layin nan ma kowa ya fi mu.
Yanzu baka jiyo karar Jannareto a gidan Alh.
Ayuba ba? Toda shi suke kwana da shi suke
yini mu kuwa fa ko injin ba mu da shi. Gidan
haya daki biyu kanana."
"A'uzubillahi minal shaidanir Rahim.
Innalillahi wa'inna ilaihi 2 raju'un. Allah Ya sa
fada a lokacin da ya yi
a gaban mahalaccinsa,
dan abin na ta ya shallake tunanin mai hankali.
Malaika ta murguda baki ta ce, "a kanka,
ki gane. Shamaki
saranda ya mika
ya
wuya
dan ni ba shaidan ba ce.'
Shamaki ya fada cikin sanyin jiki "zo
kiyiwa Kasim tsarki, ga ruwan wanka nan na
dora kiyi musu. Ni zan karasa dafa abincin."
"
27 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Malaika ta girgiza kai ta ce, "wallahi a
gajiye na dawo ga yunwa bazan iya ba, ai na
sha cewa ka dauko min masu aiki ka ki. Ni ba
baiwa bace, gidan kowa da masu aiki."
Yace "Sai dai in auro mai kular min da
yara tunda kin gaza.'
"
Ta zabura ta dire Ahmad a kasa akan
leda a fusace, “garaka yi auren ma da ka
taimaka min dan kana yin aure fitazan yi. Haka
kawai da me zan ji da talaucin ko da fada da
kishiya?"
Shamaki ya shiga kicin da sauri ya gyara
murfin tukunyar da take bori, ya fito da sauri
ya dauko Kasim akan fo zai je bandaki ya yi
masa tsarki, yayin da Aliyu ya calla ihu ya yar
da taɓarya ya rike ido barkono ya fallatso masa
a ido. Yara ukun gaba daya kuka suke yi.
Shamaki ya zama kamar zautacce ya yi nan da
gudu ya lallashi wannan ya dawo ya lallashi
wancan.
Malaika na zaune lambar tana ta kiran
wayar Nasrin bata dauka ba, sai sake kira ta ke,
gami da tura sakonni tana mai gabatar da kanta
dan ta gane mai kira, duk da haka bata amsa ba
28 Jamila Umar Tanko (JUT).
DA MA NI CE….. 1
alhali kuma wayar tana shiga. Ranta idan ya yi
dubu ya ɓaci, ta rasa in da zata saką ranta.
DA MA NI CE... 1
BABI NA BIYU
BAYANKWANAKI UKU.... KANO
a misalin karfe takwas da rabi na
dare, Shamaki da matarsa ☐ Malaika suna zaune a falo, yana
karatatun jarabawa yayin da ita kuma take cin
soyayyen kifi tana kallon talabijin, yara sun yi
bacci.
Wayarta ce a caji take ta ɗau kara, da gangan
ta ki ta dauka dan ko tantama babu ta san
Saude mai siyar da atamfofi ceke kira, dan wata
ya kare bata biya bashin da ta dauka ba.
Shamaki ya kalle ta, ya juya ya kalli wayar, ya
sake juyawa ya kalli matarsa.
Malaika ta sha kunu ta ce, “Saude ce mai
kayan siyarwa, ban biyata bashin dana dauka
ba dan kudin da ka bani na kashe sai wani
watan zan biya."
30 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE...1
Ya dauko wayar ya
karanta sunan mai kiran a
Abdul Nasrin. "
duba sunan ya
bayyane 'Nasrin
Bai rufe bakinsa ba ta zabura ta kwaće
wayar ta mike tsaye a gigice har da dukawa
sannan ta danna.
"Nasrin ta yi murmushi ta ce, "Kawata Malaika
nice. Yi hakuri na ga sakonninki mu na ta aiki
dare da rana sai yau da rana na dawo Abuja.
Na kira in shaida miki yau za'a saka hirarmu
da ke a labaran NTA na karfe tara, na faďa
miki ne dan ki gani.
"
Lah kawata, Nasrin kece?"
Malaika ta dinga tsalle tana murna tana
godiya. Nasrin ta kashe waya, yayin da
Shamaki ya rasa abinda su ke nufi, sai da ta
wayar masa da kai sannan ya fahimta. Amma a
zatonsa tatsuniya take ba gaskiya ba ne dan
haka bai ce da ita komai ba, sai da aka fara
labarai ya ga matarsa tsumu-tsumu cikin
tsumma tana bayanai ga kyamusasshen ɗansa
akan cinyarta yana kyallara ido sannan ya
tabbatar da gaske take. Sai ya fara salati yana
hada ta da Allah ya isa, ta cuce shi.
31 | Jamila Umar Tanko (JUT)
... 1
Bakinta baya mutuwa kuwa, sai kare
kanta take har ma tana shaida masa in ya ga
dama ya sake ta ta koma aikin jarida. Kan kace
kwabo jama'a da dama sun ganta ana ta
kiransu a waya ana sanar da su an ga Malaika.
Murna take tana adarwa, ana ta taya ta murna.
Yayin da shima 'yan uwa da abokai suke
kiransa suna neman karin bayani, ya ma kashe
wayarsa dan takaici.
Suka yi ta musanyan yawu shi da ita, kai
kace wuta zata fito daga bakunansu su kona
junanansu. Sai dif aka dauke wuta ma,amma a
haka cikin duhu suka ci gaba da yagar juna.
Yau sai da ya ji a ransa da zai iya sakinta
da ba zata kwana a gidansa ba, to Allah Ya
hada shi da wani masifaffan ciwo wai shi So.
Yana sonta a ransa, da kuma babu yadda zai yi
da yara idan idan ta tafi ta barshi da su,
mahaifiyarsa ta tsufa babu mai rike masa su.
Ga aiki ga karatu ba zai iya zama da su ba da
sai ya raine su har su girma.
Ya ga da gaske Malaika hada kaya take
zata tafi gidansu, ya shiga lallashi yana bata
baki akan shi bai ce zai sake ta ba amma bata
32 Jamila Umar Tanko (JUT).
DA MA NI CE... 1
kyauta masaba ne, tamkar bara take tana
neman taimako alhali shi kuma bai gaza ba.
Gashi yanzu ta jawo masa gori a wajen abokai,
waɗanda basu santa ba zasu ga sunansa raɗai
an rubuta kowa ya san matarsa ce.
-
Ta ce ita kawai ta gaji da zaman ne.
kawai gara ta tafi, yanzu gashi ko gama
nunawa ba'ayi ba aka dauke wuta, basu da
injin da zasu kunna su ga haske. Sai da ya yi
mata alkawarin Janareto wani watan, sannan ta
hakura ta fasa tafiya.
Yana kwance yana hawaye cikin dare ya
ma kasa karatun jarabarwar da yake da ita gobe
da sassafe.
Asuba ta gari!
33 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE...
BABINAUKU:
ABUJA
Kwannan
arfe huɗu da rabi na yamma, Nasrin ta
jawo wayarta cike da sanyin jiki ta kira
lamba mai matukar
muhimmanci a wajenta. Bayan tsawon watanni
biyu cur tana kiran lambar bata cin sa'a dan
ba’a ɗauka kuma tana shiga, sai yau aka amsa
mata. Ta ji farin ciki tamkar an jefa ta a gidan
aljanna dan murna. Cikin zumudi ta yi salama,
sautin wata kamilalliyar murya ce ta daki
kunnenta.
Ta gaishe shi cikin ladabi, ya amsa cikin
mutuntawa gami da ambaton sunanta 'Nasrin'.
Ta tambaya cike da mamaki "Dr.Jalo,
daman kana da lambata amma na sha kira baka
dauka?"
Jalo ya yi sanyayyiyar dariya, yace, “tun ranar
da muka yi musanyan lamba na ajiye ta da
sunanki a wayata, amma ban cika amsa wayaba.
34 | Jamila Umar Tanko (JUT) () xTacos![]
DA MA NI CE... 1
ne, ban ma cika bude wayar ba ma a rufe take
yawanci."
Ta lumshe ido ta ce, "sannu da
kokari.Aiki ya yi maka yawa ko? Kana wanne
gari ne?"
Bai amsa mata ba sai ya yi shiru, nan da
nan ta canja tambaya ta ga alamar ba shi da
niyyar amsa mata.
Ta lumshe ido, ta ce, "rubuce-rubucenka
suna birge ni ina so in shahara in kware in
zama kamar ka a harkar rubutu.
99
Ya yi murmushi yace, "ko? Allah Ya sa
ki fi ni ma."
Ta kyalkyale da dariya ta ce, “anya
kuwa? Ban isa in kamo kaba ma, ranka ya
dade."
Ya yi sauri ya katse hirar yace, “to na ji dadi da
kiran da kika yi min kuma na gode Allah Ya
bar zumunci. Sai mun yi magana wani
lokacin."
Bai jira amsarta ba ya katse waya, yayin
da Nasrin ta sankare a zaune nanike da waya a
jikin kunnuwanta.Can da aka jima ta ajiye
wayar cikin sanyin jiki, hakika ta ji ba dadi a
35 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
zuciyarta, amma da ta tuna babbar sa'ar data ci
ta samu ma ya amsa wayar yau, sai ta godewa
Allah.
zuwa wai mahaukaci ya hau kura.
Ta jawo 'konfiyutarta' ta budo hotonsa a
'facebook ta daɗe tana kallon hotunansa shi da
wani yaro dan kimanin shekaru hudu,
kyakykyawan yaro da alama dai dansa ne dan
suna kama kuma da shakuwar da suka yi. Ta
daɗe ta na kallo kuma tana karanta rubutunsa
(posts), hakika wannan bawa, Ubangijinsa
Allah Ya cika shi da tsantsar basira da
cikakken ilimi. Kalamansa yana nunawa tabbas
tsantsar masani ne haka babu kalmar da bata da
amfani a cikin rubutunsa. Idan kana biye da shi
lallai zaka karu ta fannin addini balle a
zamantakewa, haka idan kana da ra'ayin siyasa
zaka ginu akan adawa mai maʼana da tsari,
babu gaba babu cin mutunci.
と
'Mu je
Ta shiga cikin sharshin da jama'a suke
rubutawa a kasan rubutunsa (comments). Da
alama yawancin abokansa na facebook sun san
shi a zahiri dan ta lura su kan tsokane shi shima
ya tsokane su, suna kiransa da Dakta ko likita.
36 Jamila Umar Tanko (JUT)
,
DA MA NI CE...
Daga nan ta tambatar da cewa da cikakken
likita take tare, lallai dole Jalo ya yi tsada a
waya ma balle a ido biyu. Ta ji ya daɗa kwanta
mata a rai ba dan su yi soyayya ba tana
sha'awar yin mu'amula da shi dan ta karu a
harkar rubutunta na jarida.
Ta nemo shi a ɓangaren watsappsda
lambarsa, sai kuwa ta ci sa'a ta same shi da
wannan lambar da suke magana.
"Madalla da social Network".Nasrin ta
faɗa a bayyane, yayin da take tsalle a kan
gado.
Wuyanta ya kage sai ta kwanta akan filo
ta yi ruf da ciki ta ci gaba da kallonsa a hoto,
sai dai taga ya ɗaɗe rabonsa da hawa watsapp
tun watan jiya. Ko meye dalili? Oho!
Data leka ‘instagram'ma ta haɗu da shi
acan, amma fa mutumin akwai ruwan turanci,
irin turancin da wata kalmar sai ka koma ka
binciki ma'anar a dictionary.. Sai ga rubutunsa
da larabci ma da yake ita ma gwanar larabci ce
sai da ta karance tsaf, Ko a ina ya na magana
ne akan ci gaban arewa, yana kira da musulmai
37 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE 1
su haɗa kawunansu,ya na magana akan a daina
siyasar gaba da dabanci.
Nasrin ta shiga mamaki tana tambayar
kanta da kanta “me ya haɗa likita da rubucerubuce irin wannan? Tsabar kishin ' yarensa da Addininsane ko kuwa menene?"
Bata tsahirta ba sai da ta ji an kira sallar
magriba ta tashi ta shiga bandaki ta yi alwallah
ta fito ta yi salla, bata tashi daga kan abin sallar
ba sai bayan data yi sallar isha'i amma tana
idarwa ta dawo kan laptop ta ci gaba da bibiyar
Dakta Jalo.
Karfe tara saura kwata ta ji ana buga
mata kofar daki sai ta ji ranta ya ɓaci dan za'a
katse mata hanzari, dan haka ta ki amsawa ta
san yayarta ce Zainab zata dame ta akan ta fito
ta ci abinci ita kuwa ba abincin dare take ci
yanzu ba.
Har yanzu ba'a daina bugawa ba sai ta ji
muryar Dinah babbar kawarta kuma aminiyarta
ce. Ta yi mamaki da jin muryarta a daidai
wannan lokaci, ta yi sauri ta mike ta bude kofa,
suka rungume juna suna murna, bayan sun
shiga cikin ɗakin suka zazzauna a gefen
38 | Jamila Umar Tanko (JUT)
NI CE... 1
gado.Dinah ta kalli laptop taga garjejen hoton
Jalo ya cika allon, 'sceen' din.
DA MA
Ta zazzare ido ta tambaya cike da
mamaki "Nasrin! Waye wannan?"
Nasrin ta harare ta, ta ce, “dube shi da
kyau dai. Ba ki gane shi ba ne? Jalo ne fa,
mutumin da nake nuna miki rubutunsaa jaridu
da facebook.
Me
Dinah ta gyada kai ta ce, “eh na tuno shi.
ya faru kuma?"
Nasrin ta yi dariya ta ce, “ba komai
abokina ne kawai a facebook. Albishirinki!
Yau kuma na ci sa'a ya amsa wayata, kinsan
baya ɗaukar waya ran nan ba muna tare ba
nayi ta kirabai dauka ba."
mamaki.
ah ta yi sororo tana kallonta cike da
Nasrin ta daki kafadarta ta ce, “ke wai
mamakin me kike yi ne wai?"
Dinah ta yi ajiyar zuciya ta ce, "mamaki
kike bani dai, wannan ba halinki ba ne. Yaushe
kika zama marar aji har kike bibiyar mutumin
da baki sani ba haka, har yake ja miki aji."
39 Jamila Umar Tanko (JUT)
CE... 1
Nasrin ta yi dariya ta zungure ta da gefen
hannu ta ce, “ke dalla ki kwantar da hankalinki
ba wani abu ya hada ni da shi ba, nacin da nake
yi masa dan in karu da shi ne kin san zama da
irinsu akwai karuwa musamman ni da nake
bautar kasa a harkar aikin jarida ina so in san
makamar aiki.'
"
DA MA NI
66 Dinah ta harare ta, ta ce, ina joseph
Bawa, ina Mathew Haris na ofis dinku? Ba tare
ku ke ba kuma suna koya miki aiki yadda ya
kamata ba? Ba sai wani a facebook wanda baya
son yin mu'amula da ke ya koya miki ba, ba ki
san ma in da yake ba. Ko ya fada miki?"
Nasrin ta ɓata fuska da alama ta yi fushi.
Dinah ta zabura ta mike gami da jan
hannunta ta ce, “tashi ni ki raka ni zan tafi, tare
da sweetheart dina nake ya kai ni Shoprite na
siyo shafawar nan da nace zan fara
shafawa wanda muka ga tallarsa a settlite.
mans
"
Nasrin ta ja ɗankwali ta ɗaura suka fito
falo suka iske Anty Zainab tana kallon
talabijin. Dina ta duka ta yi mata sallama suka
wuce har sun kai bakin kofar fita daga falo.
40 | Jamila Umar Tanko (JUT)
Gy
DA MA NI CE... 1
Anty Zainab ta ce, “Dinah! kin sami
ladan kawarki da kika fito da ita daga daki, tun
da la'asar ta rufe kanta ta ki ta fito gashi ni
kadai Ogana bai dawo ba sai sha dayan dare."
Dinah da Nasrin suka yi dariya.
Dinah ta ce, "na ga alama bincikenwani
abu aka bata a wajen aiki.
Nasrin ta ce, “kada ki damu bari in raka
ta in dawo. Antimi Zainaba kin ji?"
Suka isa wajen dankareriyar motar,
Adam yana ciki a zaune, bayan ya rage gilashi
wundo sai suka gaisa da Nasrin, kowannensu
cike da fara'a. 00
Nasrin ta yi dariya ta ce, "kuna son
junanku kullum kuna tare a gida da ofis. Wai
me zai hana ayi bikin nan a cikin shekarar nan
daga mun gama bautar kasa."
Adam da Dinah suka kwashe da dariya,
da alama Nasrin ta soso musu in da yake yi
musu kaikayi. Sai suka kalli juna daman kamar
ta yi duba shawarar da suke yi kenan.
Adamyace, “kamar kina duba yanzu fa
maganar da muka gama kenan, amma tare da
aurenku ke da Fu'ad za'a hada.
41 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Nasrin ta yi dariya ta ce, “sai ya koyi zaman Nigeria sannan za mu yi aure." .
"
Adam ya ce, "wallahi Engineer Fu'ad ya
fi ki son zaman kasar nan amma ana bukatarsa
a Embassy Amerika, shiyasa kullum yake bisa.
hanya, shi yake taimakawa Daddy da aiki. To
ke meye damuwarki tunda kin kusa gama
bautar kasarki ba sai ku yi zamanku a can ba?"
Nasrin ta taɓe baki ta ce, “Ba na son
zaman Amerika,a tattakure na daure na yi
shekaru ukun nan inagama karatu na garzayo gida, ni fa babu kasar da na fi son zama irin
kasata Najeriya."
Dinah ta yi murmushi ta ce, "uwar iya yi,
Engr. Fu'ad yana hakuri da ke komai sai kin yi
iya yi."
" 916) 600
sa gilid ive bus. Nasrin ta harare ta ce, "au daman har na
kai ki iya yi?" il refund emey aum sys
denisb usbA
Adam ya yi dariya yace, “za ku zo ɗaya
dai, ai daman kawaye
min kwainane da yawa.
me mSIS SO
ne. Kawai dai
Engr.Fu'ad ya fi ni hakuri ne shiyasa ni ba'ayi
" Iswede adub vs
symsbA
42 | Jamila Umar Tanko (JUT)
8 ននមុន
ม ถอus
pe
A
DA MA NI CE... 1
Su ka yi dariya su dukka, ya ja mota su
ka tafi. Nasrin tana daga musu hannu har suka
fita daga get din gidan.
Nasrin ta dawo gida cike da fara'a ta iske
Yayarta Zainab har yanzu kallo ta ke yi ita
kadai.
Ta fara bawa Zainab labarin yadda suka
yi da Dinah cewar sun kusa yin aure, Adam ya
ce a hada bikinta da fu'ad.
Zainab ta yi farin ciki da jin haka ta yi
mata fatan Allah Ya sa ayi cikin shekarar nan
ta 2011. Nasrin ta taɓe baki ta ce, “ba Amin ba,
sai Fu'ad yagama yawon kasar wajen ya dawo
gida ya zauna tukunna in za'ayi ayi, dan ni ba
zan yi aure a turai ba rayuwar ba dadi."
Zainab ta harare ta ta ce, "iyayenki suna
can kina cewa ba zaki zauna a kasar ba, ke ai
gida ne."
Nasrin ta ce, "na fi sha'awar kasata
Nijeriya."
Ta tashi ta shiga daki tana tafe tana
girgiza ko ba komai ta san ta bada haushi haka
kuwa aka yi Zainab ta bita da harara.
43 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Tana shiga daki ta iske wayoyinta dukka
uku an kirata, kuma da lamba ɗaya ce, tana
dubawa taga Fu'ad ne, bata yi mamaki ba
saboda yanzu ne daman lokacin da ya saba
kiranta amma kuma ya kira da wuri ta san ba
zai wuce maganar da suka yi da Adam ba ne
har ya kyankyasa masa. Ta zauna a gefen gado
tana duba wayoyin sai ya sake kira, nan da nan
ta amsa.
Ta yi fari da ido ta kashe murya ta ce,
"Hallo darling."
Ya lumshe ido yace, "Hi sweet."
Kafin ta gaishe shi cikin zumudi ya fada
"na ji sakonki."
Ta yi dariya ta ce, "ya yi kyau. Ashe har
an kyankyasa maka? Kai! Adam dan tsurku
ne.
"
Fu'ad ya yi dariya yace, “tsurku ko
gaskiya. Kawai dai na lura koda yaushe kina so
ki yi ta tayar min da hankali. Amma yaya muka
yi da ke? Ba cewa aka yi zaki gama bautar
kasa ba ki dawo Amerika mu yi aure ba kiyi
digiri na biyu 'masters ki nemi aiki ba?"
44 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Nasrin ta dafe kai ta ce, "Darlin! Na
dawo daga aiki kaina ya yi min nauyi, ka bari
za muyi maganar da week end ina son hutu
yanzu.
"
Ya yi dariya yace, “ba damuwa gimbiya
yau babu doguwar hira kenan?"
Ta ce "kwarai ina son hutawa.'
Ya ce "sannu kina kokari ma, dan ban
zaci zaki iya ba."
Su ka yi sallama suka kashe waya, ta
tashi ta shiga bandaki, wanka da alwalla ta yi
ta fito, ta yi sallar nafilfili sanna ta saka kayan
bacci ta koma kan gado ta kwanta ta jawo
laptop ta ci gaba da bibiyar Dr. Jalo. Sai kuwa
ta ci sa'a ta gan shi akan layi (online)a
facebook.
Cika
•
Ta da murna cikin
zumudi,hannunta na karkarwa ta rubuta
sallamata tura masa, sai da ya dauki awa guda
sannan ya ba ta amsa ya tura mata
Wa'alaikissalam. Yana amsawa kuma ya fita,
jikinta ya yi sanyi.
Har yanzu tana ta karanta sabon rubutun
da ya turo (post), ya yi magana akan illar
45 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE….. 1
almajiranci da maula a kasar Hausa wanda ya
zama ruwan dare. Abokansa na facebook su
nata ruwan sharhi (comments) sai ita ma ta tura
nata dogon sharshin. Gogan na ta dai bai amsa
musu ba, ya tafi abinsa.
Ta kai karfe dayan dare tana karancekarance akan rubuce -rubucensa sannan ta
kwanta amma ba dan tana jin bacci ba sai dan
kada ta kasa yin sammakon zuwa ofis gobe, da
tunaninsa ta kwana tana mafarkinsa domin
hoton fuskarsa ya dasu a kahon zuciyarta.
Asuba ta gari!
Tana tashi da asuba ta yi sallah ta yi
addu'a Allah Ya bata basira irinta Dr. Jalo
tana so ta kware akan harkar jarida itama.
"DA MA NI CE Jalo." Nasrin ta faɗa a
bayyane yayin da take linke abin sallah.
Bayan ta yi wanka, ta shirya cikin shigar
riga da wando (Suit) sai dan gyale data ɗaura a
kai shimaba yafawa ta yi ba, kamar kullum
46 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE 1
kamar yadda ta saba shigarta. Ko karya
kumalloma yau ba zata yi ba ta dauki mukullin
motarta ta rata yakar Laptop ta fito. Ta iske
yayarta da angonta Salis a falo suna karya
kumallo. Bayan ta gaishe su suka yi mata tayin
abinci.
Ta girgiza kai ta ce, “na makara ina da
shirin da zan aiwatar (program) da sassafe.'
"
Zainab ta kalle ta ta ce,"ai kuwa daga
ganinki bacci bai ishe ki ba, ga idanuwaki sun
kunbura. Wannan wane irin sammako ne haka
har zaki riga mai aikin banki fita?"
Salis ya yi dariya ya ce, "wayar soyayya
ta raba dare tana yi tare da Fu'ad."
Suka kwashe da dariya su dukka yayin
da Nasrin ta kara gaba dan taga alama zasu
ɓata mata lokaci. Kai tsayc ta wuce wajen
taron da 'yan majalissu tarayya zasu yid an
dauko rahotanni, acan zata hadu da abokan
aikinta.
Tabbas taron nan ya caja kai dan ankai
ruwa rana akan banbance-banbancen ra'ayi.
Karfe biyu na rana ta samu ta fito daga
47 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
majillassa (House of reps) ita da abokan aikinta suka nufi gidan NTA dan mika rahotanni.
DA MA NI CE... 1
BABI NA HUDU
.KANO
Zaman Malaika da mijinta ya
faskara kowannensu ra'ayinsa ya
banbanta, Malaika na kan bakarta
na son masu kudi da tsanar talaka, haka
Shamaki ya na ta nuna mata wannan hanyar ba
mai bullewa bace gara ta dawo kan hanya.
Zaman doya da man ja ake a matsayinsa
na mijinta komai ya fada mata bata ji bai isa ya
sakata ba ko ya hana ta ba. Haka bata kula da
yara balle shi kansa. Wani abu dole sai ya yi
magana, wani abu kuwa ya kawar da kai ya
tashi ya yi abinsa da kansa.
Tunda ta sami lambar Nasrin bata taɓa
fashin kiranta ba, a kullum sai ta kira ta sau
biyu ko fiye da haka a rana, sai dai a ki
amsawa amma sai ta kira. Jifa-jifa dai Nasrin
tana amsawa idan bata komai, amma ko Nasrin
49 | Jamila Umar Tanko (JUT)
L
DA MA NI CE... 1
bata fadaba daga yadda take amsa mata itama
ta san ta gallabe ta.
Sai lallaɓa Nasrin Malaika ke ta yi tana
kwantar da kai akan ta yarda su yi kawance,
har ma tana so ta kawo mata ziyara Abuja.
Nasrin ta ce sai ta dauki hutu yanzu kullum a
wajen aiki take yini.
Nasrin ta na ganin kokarin Malaika na
kiranta da take yi a kodayaushe, tana kashe
kudin katin wayarta kullumgashi ba karfi gare
ta ba, sai ta dinga turo mata katin waya na
Dubu daya da dari biyar-biyar jifa-jifa, yayin
da farin ciki ya lullube zuciyar Malaika ta ji ta
kara son Nasrin, ta tabbatar mai kyauta ce
kuma zata karu da ita.
Shamaki ya zuba musu ido yana kallo
kullum aka turo mata katin waya sai ta nuna
masa gami da tsuyuwa ta tsawon awa goma a
ranar, tana kiransa da wanda ya kasa.
50 jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Wata rana Shamaki ya faki idon matarsa ya dauki lambar wayar Nasrin daga cikin
wayarta.
Ya laɓe ya yi ta kira tunda safe ba'a
dauka ba sai cikin dare misalin karfe goma sha
daya na dare ta ga missedcalls dinsa rututu
sannan ta kira da sauri ba tare da ta san mai
kira ba. Aka ci sa'a kuwa Malaika tana bacci,
ya fito falo ya laɓe ya amsa wayar.
Ranta ya ɓaci da ta ji muryar namiji ne
kuma wanda bata sani ba. Ya gabatar mata da
kansa sannan ta tsagaita, tana sauraronsa cike
da mamaki kai tsaye ta zaci halin maza zai
nuna mata, irin cin amanar matansu a bi kawa
a ce ana so. Amma da Shamaki ya fara koro
mata bayanai cikin ilimi da muryar tausayi sai
Nasrin ta dakata ta nutsu tana sauraronsa.
Shamaki yace, "a yanzu haka duk duniya
Matata bata ganin daraja da mutuncin kowa sai
ke, Nasrin ki taimaka min kiyi mata nasiha,
akan ta yarda da kaddara, ta yarda da yadda
Allah Ya ke son ganinta. Ta kula da ni ta kula
da yaranta amma ko da yaushe so take ta ɓalle..
51 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
auren ta fita gari neman kudi. Ita a dole sai ta
yi arziki karfi da ya ji."
Nasrin ta yi shiru ta kasa magana tana
mai tausayin Shamaki, tabbas yana cikin
masifa.
Ta yi ajiyar zuciya sanna ta ce, “Ka yi
hakuri da tambayata Shamaki, watakila ta ɓata
maka rai. An ya matarka bata da taɓin
hankali?"
Nasrin ta tambaya cikin muryar
girmamawa.
Shamaki ya girgiza kai, yace, “ko ɗaya
tana da cikakken hankali. Mace ce dai mai
kwadayi da duban wadɗanda suka fita."
Nasrin ta ce, "bata da ilimin addini da na
boko ne?"
Shamaki ya gyada kai yace, "zan iya
cewa 'Eh' zan iya cewa 'A'a' saboda tana da
shi daidai gwargwado dan tafi wasu da yawa
amma basa yin irin halin da take yi. Kin ga
kenan halinta ne ba jahilci ba."
Nasrin ta yi ajiyar zuciya ta ce, “hakika
na tausaya maka Shamaki kuma duk yadda ka
fada na gasgata bazan musa ba, dan a yini daya
52 Jamila Umar Tanko (JUT)
... 1
nasan Malaika amma na fahimci da yawa daga
cikin halayenta. Ka yi hakuri ka sake yin
hakuri, da yardar Allah zan taimaka maka. Ada
na yi niyyar sake lamba saboda da ita tana
damuna ko in yi blocking dinta, dan ta daina
samuna idan ta kira amma yanzu saboda kai
zan jawo ta a jikina dan in fahimtar da ita
rayuwa, da Izinin Ubangiji zata gyaru."
Shamaki ya yi murmushin jin dadi, ya ce
"Allah Ya saka miki da alkhairi, Allah ya sa ki
fi haka. Wataran zan dauko ta mu je mu gaishe
ki har gida. A wacce unguwa kike a Kano?"
Nasrin ta yi dariya ta ce, "A Abuja nake
zuwana Kano