ake yi ana sakewa.
Can Dinah ta tsallaka ta dauko wayar
acan kuryar gado inda Nasrin ta wurga ta, tana
dubawa sunan Dr. Jalo ta gani.
Ta zabura ta mikawa Nasrin ta ce, "ke
mutuminki ne, Dr.Jalo ne yake kira, ba
Malaika bace."
"
"ko jikina dukka kunne ne ba zan
yardaba, ba wani Dr.Jalo." Nasrin ta fada yayin
data juyar da kanta gefe ta ki kallon inda wayar
take.
Dinah ta dungura mata wayar wajen
2 idonta tana kalla kuwa sunansa ta gani, sai ta
karɓa da sauri ta danna, ta ci sa'a bata katse ba.
.
Rigijigafji! Wani kaya sai amale! Zo
kaga ladabi a wajen Nasrin da nutsuwa. Ta
koma gefe ta sami kujera ta zauna ta na
magana kamar tana gaban sarkin Kano. Da
turanci suke magana kuma cikin rada. Dinah ta
gama kasa kunnuwanta iya kasawa amma ta
kasa jiyo abinda take fada, har suka yi sallama
suka kasha wayar.
103 Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Nasrin da Dinah suka dau ihu suka
rungume juna har sai da Zainab ta fito daga
kicin da gudu ta zaci gobara ce ta tashi a ɗakin,
sai ta iske su suna rawa 'kerewa'a tsakar daki
Ta tabbaye su suka shaida mata Dr.jalo ne ya
kira a waya.
Haushi ya kamata ta yi tsaki ta fice, ta
tabbatar basu da matsala a duniya shiyasa suke
wannan taɓarar.
Har dare basu daina murna ba sai da
Dinah ta tashi tafiya suka fito daga cikin dakin,
bayan sun ki fitowa su ci abinci, Zainab da
Salis sun gaji da kira har sun ci abincinsu.
Sai a lokacin suka zauna suka ci nasu
abincin Zainab tana bawa mijinta labarin
shiriritar da suke yi, ya sha dariya.
Ya fada a bayyane "yarinta mai dadi .
Nasrin ta raka Dina wajen tsaleliyar motarta,ta
shiga ta tafi.
Jama'a ga tambaya? Ina Malaika? Ta zo
taga yadda matan Abuja suke matsa sitiyarın
tsala-tsalan motoci.
104 | Jamila Umar Tanko (UT)
DA MA NI CE... 1
BABI NA SHIDA
RANAR ASABAR...
ASIBITIN NASSARAWA KANO
alaika ta yi tagumi akan gadon
Asibiti ta zurawa Ahmad ido
tana kallo, yana ta numfasawa
sama-sama. Hankalinta a tashe yake matuka
dan bata taɓa ganin ya galabaita haka ba, ta je
wajen Ma'aikatan jinya ‘Nurses'ya kai sau
goma tana nuna musu numfashin ɗanta yake
yi, tun Nurse tana bata baki har ta shiga tsuye
ta, ta balbale ta da fada ta ce ai ba laifinsu ba
ne laifin mijinta ne an ce ya je ya siyo allurai
tunda ya fita wajen awanni uku bai dawo ba.
Malaika ta dawo kan gadonta ta zauna tana
kallon matan da mazansu suke ta yi musu
hidima, ana ta ajiye kayan shayi da kayan
marmari na itatuwa, ita kan lokarta wayam
babu ko pure water.
105 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Ta dauko wayarta a hankali ta danno
lambar Shamaki amma ba zata iya kira ba
saboda babu ko sisi a cikin wayar. Ta yi masa
‘pleasecall me'ya fi a kirga bai kira ta ba.
Ta ji ta tsane shi, ta tsani rayuwarta,ta fara
tunanin mafita dan ba zata dauwama a cikin
wannan rayuwa a haka ba. Ta jawo Ahmad ta
rungume shi numfasawa yake sama-sama yana
kuka amma ba'a jin muryar saboda ya
galabaita, kashin kirjinsa sai a lissafe sutsaf
saboda rama.
Wayarta ce ta haukara, babu tantama ta
san Shamaki ne, sai da ta ja aji sannan ta mika
hannu ta dauka a fusace, tana dubawa sunan
Nasrin ta gani maimakon Shamaki. Sai ta sake
gwale ido ta duba yayin da annuri ya sauka a
fuskarta. Ta danna da sauri gami da kiran
sunan Nasrin cikin fara'a.
Nasrin ta yi juyi ta yi mika akan
lintsimemen gadonta ta ce, "Daman na faɗa
miki idan ba'a week end ba ne ba mu da
lokaci, na kira ki mu yi hira."
66
106 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Dadi ya rufe Malaika yayin da Ahmad
ya fara mika yana kara saboda azabar da
kasusuwansa ke yi masa.
Malaika tana ta faman girgiza shi.
Nasrin ta ce, "Jaririnki kuka yake yi ne?"
Malaika ta shagwagwgwaɓe ta rusa kuka
ta ce "Nasrin muna cikin wani hali yanzu haka
ma muna kan gadon Asibiti, da tsakar dare
muka taho ba shiri yaro ya sankare kamar
gawa.
"
Nasrin ta tashi zaune a gigice ta ce,
"subhanallahi. Amma yanzu yaya jikin, likitoci
sun taru akansa sun ceto rayuwasa ko?"
Malaika ta fashe da kuka ta ce, "sanda
muka zo aka yi masa wata allura sai aka rubuta
wasu alluran aka ce Shamaki ya je ya siyo,
tunda asuba Shamaki ya fita bai dawo ba, ya
bar ni da yaro yana ta suma.Ma'aikatan lafiya
suna ta zagina wai zamu kashe danmu da
kanmu, saboda mun ki kawo magani da allurai,
ya tafi ya yi zamansa ya ki daukar wayata.
Daman ai na fada miki, ni kadai nasan irin
bala'ih da nake ciki. Yanzu kin ga mata sun fi
ashirin ne a cikin dakin nan da nake kwance
107 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
amma kowacce mijinta ya kawo mata abinci da
kayan shayi, mu tun abincin jiya ne a cikinmu,
yaro ya kasa kama nono ma ko ya kama babu
ruwa a ciki." Ta fashe da kuka.
Nasrin ta dafe kirji ta sunkuyar da kai a
hankali saboda tashin hankali ta fada cikin
sanyin murya "gaskiya Shamaki mugu ne, baya
kyautawa."
Malaika da Ahamad suna ta kuka a
kunne Nasrin, ta zabura ta mike tsaye ta fito
daga cikin bargo saboda damuwa.
Ta ce "ki goya shi ki je wajen likita ya
sake rubuta miki wata takardar maganin, ki je
ofishin nan da na yi hira da ke, ki ce a nuna
miki Dr.Gumel sai kice ni na aiko ki, zai baki
kudi ki je ki siyo maganin da abinci. Zan yi
masa waya kafin ki karasa dan yanzu idan nace
zan turo miki kati ki siyar wani ɓata lokacin
"
ne."
Malaika tana rawar jiki tana amsawa da
"Toh Toh."
Bayan sun kashe waya Malaika ta tashi
ta goya ɗanta zata fice.
108 Jamila Umar Tanko (JUT),
DA MA NI CE... 1
MetronLuba ta taɓo Metron Aisha ta
nuna Malaika da yatsa ta ce, "kin ga matar can
ta goya dan zata gudu."
Aisha ta yi murmushi ta ce, “rabu da ita
daman ba ta zo da komai ba daga ita sai kayan
jikinta, badan ma da gaske mun ga yaron bashi
da lafiya ba da sai in ce 'yan danfara ne.Kamar
bata da gaskiya ta yi ta kallon mutane, kin san
saboda ita na fasa kirga kudin adashen nan da
na karɓo. Sai kallona take tana kallon kudin
tana ajiyar zuciya tama manta marar lafiya ne a
hannunta."
وو Su ka kyalkyale da dariya suka tafa.
Malaika har ta je baranda ta tuna bata karɓi
takardar magani ba, sai ta dawo wajen
Ma'aikatan jinya.
Tana isa wajensu a gigice ta ce, “mijina
bai dawo ba ku sake rubuta min wani maganin
in je in siyo."
Aisha ta harare ta ta ce, “mijinki ya kasa
siyowa sai ke ce za ki iya kenan?"
Luba ta ce "ke dai rubuta mata kawai mu
ga gudun ruwanta."
109 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA'NI CE... 1
Aisha ta rubuta ta dankwafawa Malaika
akan tebur a gabanta, ta yi gatsine ta ce,
“daman kina da kudin siye kika bar ɗanki cikin
wahala tun jiya?"
Malaika ta dauki takardar a sanyaye ta
juya baya har zata tafi ta gaba zata iya daurewa
ba sai ta mayar da marta ni zata ji daidai.
Sai ta juyo a fusace dubi Aisha ta ce,
"Na girmi wulakanci, kada ku ganni a nan a
yashe, ba ku san da wacce ku ke maganaba .66.
Aisha ta zabura zata yi magana, sai Luba
ta danne hannuta. Malaika ta yi gatsine gami
da hararar Aisha sama da kasa ta juya ta tafi.
Tana fita ta nufi ofishin Dr.Gumel anan
ta yi sallama ta tura kofa ta shiga, sai ta ci karo
da mutumin nan data yiwa wankin babban
bargo. Ya ɗaga ido ya dube cikin fushi da
takaici a take suka shaida junansu.
Ya yi mata tsawa yace, "menene kuma?
Kin zo ne dan ki sake zagina ne kuma?"
.
Malaika ta karaso gaban kujerarsa a
sanyaye ta ce "Nasrin ce ta ce in zo wajen
Dr.Gumel in karɓi kudi."
110 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Ya yi tsaki ya harare ta ya ce, "wallahi
da nasan ke zan bawa kudi da ba zan yiwa
Nasrin alkawarin zan baki ba. Sai dai ta tura ki
wani wajen wani. Marar kunya kawai, har yau
na tuna cin zarafin da kika yi min raina sai ya
ɓaci, amma na yi miki uzuri.'
"
Malaika ta yi fiki-fiki da ido tana ta juya
takardar da take hannunta kamar wata mumina.
Yagama cashe mata sannan ya zaro naira
dubu goma ya dora akan teburin ganbansa ya
tura gabanta a fusace. Ta sa hannu da sauri ta
kwashe ta damke gam, ta ji duminsu.
Sannan ta
juya za ta fita.
rare shi sama da kasa ta
YaceYace, “dan haka ki kiyayi duniya ki
daina wulakanta mutane, ba ki san in da za'a
sake haduwa ba kuma mutumin nan da kika
wulakanta kuma ya yi miki amfani kamar
yadda na yi miki amfani yau."
Ta juyo da sauri a fusace ta harare shi ta
ce "Malam, ya isa haka, more bakin ya isa ko
dan ka ji na yi shiru."
"
Ya zabura ya mike tsaye a fusace, ya
daki tebur da karfi yace, "yau ma rashin kunyar
111 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
za kiyi min? Bari in sa security su kama min
ke, kuma kudin nan dana baki sai kin dawo da
shi."
Ta na jin ya fadi haka sai ta bude kofa ta
fice da gudu.
Dariya ta kama Dr.Gumel ya yi ta
Kyalkyalawa shi kadai.
Yace, "wannan shegiyar yarinyar mijinta
yana hakuri, ko waye shi yana shan wahala.
Kuma da hankalinta ba hauka ba ce iskanci ne
kawai.
Malaika ta fito daga cikin asibiti ta
tsallaka babban titi ta shiga babban kemist din
dake tsallaken mai suna 'Mumtaz' ta je ta siyo
magunguna da allurai a kan naira dubu shida
da dari tara. Ta sayo kayan shayi madara,
konfiles, siga, milo da biredi har da kwalin
Juice, itama dan ta jera kowa ya zo ya ga
sama saman lokarta da kayan dadi kamar sauran.
Ta karaso cikin dakin ta isa wajen
gadonta ta sauke Ahmad ta kwantar sannan ta
jera kayan dadi, tana jerawa ta na juyowa tana
kallon 'yan dakin da suke yi mata gani-gani,
112 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
ko tayin abinci basu yi mataba sai dai a
junansu dan sun ga alamar bata da komai.
Ta gama sannan ta dauki ledar allurai da
magungunan ta je bakin teburin Ma'aikata ta
ajiye a gabansu ta ce "gashi na siyo.”
"
da kai.
Aisha ta harare ta sama da kasa ta kawar
Luba ta ce, "Aisha ta na magana, hakuri
za kiyi ki yi aikinki kada ki biye ta."
"
Aisha ta zabura tana magana cikin fushi
ta ce "wallahi bazan je kan ɗanta ba sai dai in a
abakin aikina.'
Luba ta tashi da sauri ta dauki ledar ta ce
da Malaika ta zo su je, dan taga alamar
Malaika na marmar da baki tana so ta furta
bakar magana, ta san fada za'a tayar gagarumi,
dan kowaccensu gwana ce wajen tsiwa.
Luba ta tsaya ta duba Ahmad yadda ya
kamata ta yi masa allura ta kara masa ruwa, har
numfashin kuwa ya fara daidaita dan dai har
yanzu bacci yake mai kama da na mutuwa.
Suna cikin wannanhali sai ga Shamaki a
gigice ya shigo wando a ɗage, hula a bayan
keya. Daga gani ya sha wahala ba ‘yar kaɗan
113 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
ba. Ya yi baki ya yi datti yana ta gumi da huci da alama bayan gudu akan babur ma ya yi
gudu da kafa.Yana ta rawar jiki da rawar baki,
dan ya ga irin kallon da Malaika ta yi masa na
tara saura kwata.
Ya mikawa Luba ledar magani ta karɓa
ta duba ta ce "ai irinsu muka yi masa yanzu sai
dai bata ɓaci ba ku ajiye saboda nan gaba."
Shamaki ya yi ajiyar zuciya yace
"Alhamdulillahi da aka samu aka yi masa kafin
in dawo. Ina can ina ta nema dakyar na samo
kudin.
"
Malaika dai ta ɓata rai ko kallonsa bata
yi ba, luba ta yi gaggawar matsawa dan kada
shafe .
_ Malaika ta dawo gefen gado ta zauna
kusa da danta tana kallonsa, Shamaki ya zauna
a kusa da ita yana satar kallonta, ya na fargabar
yi mata magana dan kada ta yayyagashi a cikin
mutane, gashi kuwa 'yan ɗaki sun zuba musu
ido suna kallo dan suna son su ji kwakwaf.
Kowa ya san Shamaki ya ɓatawa Malaika rai,
tunda ya fita bai dawo ba har ta fita ta nemo
kudi ta siyo maganin sannan ya dawo. Daga
114 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
yadda take harararsa kowa ya san haduwar ba
zata yi kyau ba.
"Sannu da kokari Malaika, Allah Ya
saka miki da alkhairi."Shamaki ya fada cikin
rada saboda tsananin tsoro.
Malaika ta harare shi ta yi tsaki.
Sai ya tashi sadan-sadan "bari in je in yi
sallar walha, zan dawo."
yace
Ya fice ba tare da ta bashi amsa ba.
Bayan ya fita ne ya kira ta a waya yace ta fito
baranda su yi magana, ta ce bazata iya barin
ɗanta ba ta fito, babu mai kula da shi. Lallai ta
yi hankali dan haka bai ji haushi ba.
Nasrin ce ta kira Malaika awaya dan ta ji
yadda suka yi da Dr.Gumel. Fara'ar da
Malaika ta ke yi sai da kowa ya yi mamaki dan
tunda ta shigo ɗakin nan bata yi dariya ba,
daga harara sai tsaki.
Malaika ta yi mata godiya ta tabbatar ta
karɓo dubu goma har ta siyo allurai, ruwa da
magunguna an sakawa dan.
Nasrin ta tambaya “har yanzu Shamaki
bai dawo ba kuma bai kira ba?"
115 | Jamila Umar Tanko (JUT)
_
Malaika ta tabbatar mata "har yanzu bai
waiwaye mu ba."
DA MA NI CE... 1
Ran Nasrin ya ɓaci ta gasgata cewar
Shamaki mugu ne shi yake cutar Malaika.
Su ka yi sallama suka kashe waya.
Nasrin ta kira Shamaki a wayarsa bai dauka ba
kasancewar yana Sallah, kuma ma ya saka
wayar a silent tana aljihunsa. Ta kira ta sake
kira bai dauka ba sai daga baya ya ga
missedcalls dinta sannan ya kira ta, itama bata
kusa bata dauka ba.
Ya yi mamakin ganin kiran Nasrin amma
bai yi mamaki da yawa ba, ya san Malaika zata
shaida mata suna asibiti,. Ya san Nasrin jaje ta
kira zata yi masa.
Ya fara zargin ko kudin da Malaika ta
sayi maganin ma Nasrin ce ta aiko mata daman
tun dazu yake ta tunani ya kasa nemo tabbacin
in da kudin nan ya fito. Tabbas ba zai wuce
daga Nasrin ba. In dai haka ne kuwa Malaika
ba zata taɓa ganin kokarinsa ba tunda ga wata
daga haduwa a hanya tana yi mata hidima. Ya
fara ganin laifin Nasrin da sake taɓarɓara masa
gida, dan ba taimakonsa take ba sake saka
116 | Jamila Umar Tanko (JUT)
_ DA MA NICE. T
sha'awar masu kudi take yi a zuciyar
Malaika.Ya fara tunanin yadda zai raba alakar
Nasrin da Malaika.
Bayan magruba Kanwarsa ta zo daga
Muntsira Sadiyalle, sai Malaika ta bar Ahmad
da Sadiyalle ta fito kan baranda inda Shamaki
ya sami lungu ya takure yana ta damunta da
waya.
Ta zo ta tsaya a gabansa kerere ta ce,
"meye wai?"
Ya langwabar da kai yace, "Malaika!
zauna mu yi magana dan Allah, ta fahimta."
Ta zauna a fusace tana turo baki, Shamaki ya
yi gyaran murya yana mammatsa hannu kamar
marar gaskiya yayin da zuciyarsa ke dukan
uku-uku.
Ya ce, "Malaika! Na san na ɓata miki rai
amma ki yi min uzuri. Wallahi ban tashi dą ko
sisi ba ciki da waje, haka na fita na duba gabas
da yamma, kudu da arewa na rasa in da zan
nufa, na so in je Bichi wajen aikina in samu a
ranta min in an yi albashi a dauka na tuna yau
asabar babu kowa a sakateriyar. Na juya zan
shiga B.U.K na tuna bamu da Lacca yau sai
117 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
karfe hudu babu wandazan samu, in takaice
miki har kantin kwari na je na yi bara, ina nuna
katin asibiti, basu bani ba suka zage ni wai an
sami sabuwar danfara kato da ni mutuwar
zuciya ce in je in yi dako ko faskare mana. Na
gasgata sun fadi gaskiya.
Na je kasuwar singa zanyi dako, na ji
kudin da za'a biya ni a yini ma ba zai isa ko
rabin kudin maganin ba. Na so in siyar da
wayata ma na ji anyi min tayin wulakanci,
kudin ba zai sayi magani ba.
Daga karshe naga bani da mafita sai na
je na sami Fatima Giwa wata attajirar matace,
daya daga cikin matan ajinmu a gidanta. Na yi
mata bayani ita ta taimaka min da kudin
magani, ta bani naira dubu goma.
"
Malaika ta harare shi ta ce,"Fatima Giwa
'yar ajinku ko bazawararka?"
Ya girgiza kai yace, “matar aure ce ma
tana auren wani attajiri a Nassarawa GRA, ban
taɓa sanin gidan ba sai yau da ta kama,da naga
bani da mafita, direbanta ma na kira ya bani
shawara in zo zata taimaka min dan mun saba
118 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE...1
da shi. Daman itace take siya min handout ni
kuma nake bata amsa."
"
Malaika ta taɓe baki ta ce, "in tayi tsami
za mu ji, in an yi magana ace ni nake
makalewa masu kudi. Kai yanzu me yasa baka
makalewa talakawan ajin na ku ba su 'yar shila
amma ka Makalewa Giwar, saboda tafi maiko,
da tsoka ko?"
Shamaki ya tabbatar Malaika bata da
tausayi ta juya maganar gaba ɗaya zuwa wani
sashi, sai ya yi shiru bai bata amsa ba.
Aka jima ya ɗago ya dube ta yace, "a ina
kika sami kuɗi kika sayi magunguna da kayan
shayi?"
Ta harare shi ta ce, "a wajen 'yar ajinmu
nima na samu Nasrin Giwa.'
"
Ya daɗe yana kallonta kallo na takaici ya
rasa amsar da zai bata.
Ya ce "rokarta kika yi kika ce na kasa?"
Malaika ta zabura ta mike tsaye ta kama kugu
ta ce "ba ka kasa din ba ne? Da ka fitaka dawo
da wuri ne? Sai in bar dan nawa ya mutu?
Daga yau na sami abin gori nima dagaka ce na
119 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
makalewa Nasrin zan ce kai ma ka makalewa
Fatima Giwa."
Ta juya ta tafi a fusace ta bar shi anan a
zaune yana kallonta, kwalla ta cika masa ido.
Ya girgiza kai ya sunkuyar da idanuwansa kasa
sai hawaye ya surnano. Yana ta girgiza kai
yana tausayin kansa da kansa yana mai
takaicinjarabawar (test) din da ya rasa yau a
makaranta. Yana kuma fargabar ko dansa zai
tashi ko zai rasu, saboda jikin ya tsananta, yana
tunanin halin da ya bar yaransa guda biyu a
gidan makwabta. Ko ana kula da su ko kuwa
an bar su da yunwa? Ya shiga tunanin kudin da
za'a bukata nan gaba a asibiti dan bashi da su,
bai san in da zai tafi nema ba kuma.
Sadiyalle ya gani a tsaye akansa tana
kallonsa cike da tausayi ta ce, “Shamaki kuka
kake yi? Ka yi hakuri komai yana da iyaka.
Allah Yana tare da makurci. 99.
Sai ta rushe da kuka, shima ya fara kuka
har zuwa lokaci mai tsawo babu wanda ya iya
magana a cikinsu.
120 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Shamaki ya mike tsaye ya kalle ta da
jajayen idanuwansa yace "mu je gidan dare ya
dan ki kula da su Aliyu."
Su ka isa wajen Babur dinsa suka hau,
suka tafi. A hanya sadiyalle take bashi labarin
zamanta a gidan mijita. Itace mata ta uku, bata
taɓa haihuwa ba amma tana ganin masifa a
gidan nan, mijin baya tsinana masu komai sai
dai kowacce ta nemo. Ta kara da cewa tana
mamakin yadda Malaika bata godewa Allah da
duk irin kokarin da mijinta yake yi mataba.
Shamaki ya yiwa kanwarsa nasihohi
akan ta ci gaba da hakuri kuma idan ya gama
karatu albashinsa zai karu zai dinga taimaka
mata.
Su ka isa gida yace ta shiga Makwabta ta
ɗauko yaran, tana shiga sai ta iske yaran a
kwance a zaure cikin akuyoyi, matar gidan ta
turo su ta rufe dakinta da yaranta, da alama suñ
sha kuka sannan suka gaji suka yi bacci, yunwa
ce a cikinsu daga gani dan cikin da doron
bayan sun haɗe. Sadiyalle bata ji dadi ba ta
kamo hannunsu ranta a ɓace suka fito suka iske
shamaki a kofar gidan.
121 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DÀ MA NI CE... ↑
Yana ganinsu ya tambaya "ba dai a zaure
kika dauko su ba, dan na ga daga shigar ki kin
fito."
Ta fada masa a halin da ta gansu, sai ya
ji ransa ya ɓaci ya kudiri a niyyar ba zai sake
barin yaransa a gidan makwabta ba. Ya bawa
Sadiyalle Mukullin gidan, yace bari ya je ya
suyo musu abinci, ya hau babur ya tafi. Ita
kuma ta bude gida suka shiga tsakar gida ta
shinfida musu tabarma suka zauna. Ba jimawa
sai ga Shamaki ya siyo musu dafafiyar indomie
da kwai a cikin ledoji. Su ka yi ta ci hannu
baka hannu kwarya, da alama ko abincin safe
ba 'a basu ba balle na rana da na dare.
Shaniakiya fada a bayyane "daman
Uwale bata da mutunci, dan rashin imani ta bar
min yara da yunwa?"
Sadiyalle ta ce "wallahi wani abun ma
saboda kai ake yin kara ake yi, amma ba dan
Malaika ba. Aka bibiya ita ma Malaika tana
yiwa 'ya'yanta rashin mutunci. Kai a ganinka
Malaika zata rike wa Uwale yaranta ta ciyar da
su na yini guda?"
122 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
Shamaki ya gyada kai yace, “da wannan
dan wannan."
Sadiyalle ta ce, "yanzun ma saboda
nauyin kai ka tura su ya sa ta karɓa. Sau nawa
nake jin Malaika tana zagin Uwale ta ce sun yi
zage-zage. Ai rashin kirkinta ne ya jawo aka
yiwa nata haka.'
"
Bayan sun gama ci Sadiyalle da yara
suka shiga ɗaki suka kwanta, Shamaki ya shiga
falo ya kwanta akan doguwar kujera, baccin
gajiya ya kwashe su su dukka basu farka ba sai
da assalatu.
*** *** ***
RANAR LAHADI.. °
.KANO
Tun bayan da suka idar da Sallah
Sadiyalle da Shamaki suka yi ta hidimar gida,
Shara, wanke wanke, dafa abinci da wankin
kayan fitsari.
Sadiyalle ta yi tsaki ta fada a bayyane
"gaskiya Malaika kazama ce, Shamaki kalli
yadda yana da kura su ka yanyame ko ina, datti
kamar babu bil'adama a gidan. Wai me
Malaika take yi ta bar gidanta a haka?"
123 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NICE... 1
Shamaki ya yi tsaki ya harare ta, ya ce,
"dalla Malama ki gyara in da zaki gyara, bana
son yawan magana da cin naman mutum dan
baya kusa. A gabanta za ki iya fadar haka?”
Da alama ya ji haushi dan an caccaki
rabin ransa Malaika. Sai Sadiyalle ta zunɓuro
baki bata kara magana ba, ta turo baki gaba.
Da misalin karfe tara na safe suka gama
shiryawa tsaf, Sadiyalle ta dauko leda ta zubo
kayan sakawar Malaika da na Ahmad, brush,
makilin, soso da sabulu, suka jifgu akan babur
su dukka ga kaya ga yara suka tafi.
Suka isa cikin asibitin, bayan ya nemi
waje a wata inuwa ya tsaya sai suka dunguma
cikin dakin su dukka dauke da filasanabinci a
hannunsu.
Tun daga nesa suka hango Malaika cikin
tashinhankali, ta tsaya a tsakiyar ɗakin ta ɗora
hannu aka kamar maishirin kurma ihu.Sai suka
tsaya cak sannan suka ci gaba da tahowa amma
fa suna karanto
99 "Innalillahi wa'inna ilaihi raju'un.'
124 | Jamila Umar Tanko (JUT)
☐
DA MA NI CE
Tun Shamaki bai karaso ba ya gama fahimtar
abinda ya afku, sai ya saki kayan da yake
hannunsa ya kwaɗa salati a bayyane.
Malaika na ganinsa ta tahoda gudu ta
rirrike shi ta na kururuwa, kukan da yake tafe
da dinbun hawaye ta ce, "Shamaki! Ahmad ya
rasu da asuba.'
"
Sai hawaye ya surnano daga idanuwansa
ya zame hula ya rike a hannu yana tafe yana
sanɗa har ya karasa wajen gawar, ya buɗe a
hankali, ya yin da kirjinsa yake ta faman dukan
uku-uku. Ya dubi Ahmad yaro a mimmike
daga kashi sai fata.
Ya shafa kansa ya fada a bayyane "Kulli
Nafsin za'ikatil maut. Ahand! Allah ya
jikanka ya baka uwar goyo a Aljanna. Mu ma
muna nan tafe, ba mu yi jinkiri ba, haka kai da
ka tafi yanzu baka yi gaggawa ba."
"
Ba Malaika kadai ba, gaba daya 'yan
dakin da ma'aikatan sai da Shamaki ya basu
tausayi, hawaye kawai zaka dinga gani a
idanuwan manya maza da mata. Sun tausayawa
Shamaki da Malaika sun tausayawa Ahmad
yaron ya sha wuya, suna kuma masu tausayin
125 | Jamila Umar Tanko (JUT)
DA MA NI CE... 1
kansu da kansu, suma wataran zasu zama gawa
tabbas.
Nan dai Shamaki ya yi ta maza ya nufi
wajen Ma'aikatan lafiya suka ci gaba da
tattaunawa akan fom din da zai cike da kuma
yadda zai dauki gawar. An ɓata lokaci, daga
karshe ya samo mota tasi aka saka gawar,
Malaika, yara da Sadiyalle suka shiga suka tafi,
bayan an saka ganye a bayan motar shaidar
motar da gawa, duk wanda ya gani sai ya kauce
ya basu waje.
Shamaki ya tsaya a jikin babur dinsa
yana ta bugawa Makwabta da 'yan uwa na can
garin su, 'yan uwansa da 'yan uwan Malaika
waya ya sanar da su anyi rasuwa duk mai hali
ya zo jana'inza. Daga karshe ya hau Babur
dinsa ya biyo su gida. Kafin ya karaso Mata
sun cika gidan ana ta kuka. Malaika kam har
rirrike ta ake yi tana ta kururuwa, mutuwar nan
ta sshige ta an tausaya mata, ta sha jigila da
yaron nan tunda ta haife shi bata hutaba.
Daidai lokacin Nasrin ta kira wayar
Malaika dan ta tambayi mai jiki, wayar a
hannu Sadiyalle sai ta shaida mata Malaika ba
126 | Jamila Umar Tanko (JUT)
NI CE... 1
zata iya amsa wayaba saboda danta ya rasu ko
binne shi ba'ayi ba. Kafin ma Sadiyalle ta
fadawa Nasrin haka kuruwar kukan Malaika ta
tabbatar mata da haka. Nasrin mai tausayi sai
ta ji hankalinta ya tashi, tausayi ya lullɓe ta ta
fara zubar da hawaye, ta kashe wayaba tare da
ta ce wa Sadiyalle komai ba.
DA MA
Ta shaidawa Zainab yayarta halin da
Malaika ta ke ciki sai jikin Zainab ya yi sanyi
dan ita neman haihuwar ma take bata samu ba,
sai yanzu ne take da karamin ciki.
Nasrin ta bugawa kawar Dinah waya ta
shaida mata abinda ya sami Malaika, duk da
Dinah bata sansu ba amma ta ji tausayinta, ta
yiwa Nasrin gaisuwa ta ce ta yiwa Malaika
idan sun yi waya. Haka Nasrin ta kasance yini
guda cikin sanyin jiki mutuwar ta shige ta.
Aka binne Ahmad aka ci gaba da zaman
makoki, Sai da daddare bayan komai ya lafa
sannan Nasrin ta sake kiran Malaika ta yi mata
gaisuwa gami da yi mata wa'azi akan dangana.
Malaika tana ta kuka abin tausayi har sai da
Nasrin