Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 7
ake yi ana sakewa. Can Dinah ta tsallaka ta dauko wayar acan kuryar gado inda Nasrin ta wurga ta, tana dubawa sunan Dr. Jalo ta gani. Ta zabura ta mikawa Nasrin ta ce, "ke mutuminki ne, Dr.Jalo ne yake kira, ba Malaika bace." " "ko jikina dukka kunne ne ba zan yardaba, ba wani Dr.Jalo." Nasrin ta fada yayin data juyar da kanta gefe ta ki kallon inda wayar take. Dinah ta dungura mata wayar wajen 2 idonta tana kalla kuwa sunansa ta gani, sai ta karɓa da sauri ta danna, ta ci sa'a bata katse ba. . Rigijigafji! Wani kaya sai amale! Zo kaga ladabi a wajen Nasrin da nutsuwa. Ta koma gefe ta sami kujera ta zauna ta na magana kamar tana gaban sarkin Kano. Da turanci suke magana kuma cikin rada. Dinah ta gama kasa kunnuwanta iya kasawa amma ta kasa jiyo abinda take fada, har suka yi sallama suka kasha wayar. 103 Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 Nasrin da Dinah suka dau ihu suka rungume juna har sai da Zainab ta fito daga kicin da gudu ta zaci gobara ce ta tashi a ɗakin, sai ta iske su suna rawa 'kerewa'a tsakar daki Ta tabbaye su suka shaida mata Dr.jalo ne ya kira a waya. Haushi ya kamata ta yi tsaki ta fice, ta tabbatar basu da matsala a duniya shiyasa suke wannan taɓarar. Har dare basu daina murna ba sai da Dinah ta tashi tafiya suka fito daga cikin dakin, bayan sun ki fitowa su ci abinci, Zainab da Salis sun gaji da kira har sun ci abincinsu. Sai a lokacin suka zauna suka ci nasu abincin Zainab tana bawa mijinta labarin shiriritar da suke yi, ya sha dariya. Ya fada a bayyane "yarinta mai dadi . Nasrin ta raka Dina wajen tsaleliyar motarta,ta shiga ta tafi. Jama'a ga tambaya? Ina Malaika? Ta zo taga yadda matan Abuja suke matsa sitiyarın tsala-tsalan motoci. 104 | Jamila Umar Tanko (UT) DA MA NI CE... 1 BABI NA SHIDA RANAR ASABAR... ASIBITIN NASSARAWA KANO alaika ta yi tagumi akan gadon Asibiti ta zurawa Ahmad ido tana kallo, yana ta numfasawa sama-sama. Hankalinta a tashe yake matuka dan bata taɓa ganin ya galabaita haka ba, ta je wajen Ma'aikatan jinya ‘Nurses'ya kai sau goma tana nuna musu numfashin ɗanta yake yi, tun Nurse tana bata baki har ta shiga tsuye ta, ta balbale ta da fada ta ce ai ba laifinsu ba ne laifin mijinta ne an ce ya je ya siyo allurai tunda ya fita wajen awanni uku bai dawo ba. Malaika ta dawo kan gadonta ta zauna tana kallon matan da mazansu suke ta yi musu hidima, ana ta ajiye kayan shayi da kayan marmari na itatuwa, ita kan lokarta wayam babu ko pure water. 105 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 Ta dauko wayarta a hankali ta danno lambar Shamaki amma ba zata iya kira ba saboda babu ko sisi a cikin wayar. Ta yi masa ‘pleasecall me'ya fi a kirga bai kira ta ba. Ta ji ta tsane shi, ta tsani rayuwarta,ta fara tunanin mafita dan ba zata dauwama a cikin wannan rayuwa a haka ba. Ta jawo Ahmad ta rungume shi numfasawa yake sama-sama yana kuka amma ba'a jin muryar saboda ya galabaita, kashin kirjinsa sai a lissafe sutsaf saboda rama. Wayarta ce ta haukara, babu tantama ta san Shamaki ne, sai da ta ja aji sannan ta mika hannu ta dauka a fusace, tana dubawa sunan Nasrin ta gani maimakon Shamaki. Sai ta sake gwale ido ta duba yayin da annuri ya sauka a fuskarta. Ta danna da sauri gami da kiran sunan Nasrin cikin fara'a. Nasrin ta yi juyi ta yi mika akan lintsimemen gadonta ta ce, "Daman na faɗa miki idan ba'a week end ba ne ba mu da lokaci, na kira ki mu yi hira." 66 106 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 Dadi ya rufe Malaika yayin da Ahmad ya fara mika yana kara saboda azabar da kasusuwansa ke yi masa. Malaika tana ta faman girgiza shi. Nasrin ta ce, "Jaririnki kuka yake yi ne?" Malaika ta shagwagwgwaɓe ta rusa kuka ta ce "Nasrin muna cikin wani hali yanzu haka ma muna kan gadon Asibiti, da tsakar dare muka taho ba shiri yaro ya sankare kamar gawa. " Nasrin ta tashi zaune a gigice ta ce, "subhanallahi. Amma yanzu yaya jikin, likitoci sun taru akansa sun ceto rayuwasa ko?" Malaika ta fashe da kuka ta ce, "sanda muka zo aka yi masa wata allura sai aka rubuta wasu alluran aka ce Shamaki ya je ya siyo, tunda asuba Shamaki ya fita bai dawo ba, ya bar ni da yaro yana ta suma.Ma'aikatan lafiya suna ta zagina wai zamu kashe danmu da kanmu, saboda mun ki kawo magani da allurai, ya tafi ya yi zamansa ya ki daukar wayata. Daman ai na fada miki, ni kadai nasan irin bala'ih da nake ciki. Yanzu kin ga mata sun fi ashirin ne a cikin dakin nan da nake kwance 107 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 amma kowacce mijinta ya kawo mata abinci da kayan shayi, mu tun abincin jiya ne a cikinmu, yaro ya kasa kama nono ma ko ya kama babu ruwa a ciki." Ta fashe da kuka. Nasrin ta dafe kirji ta sunkuyar da kai a hankali saboda tashin hankali ta fada cikin sanyin murya "gaskiya Shamaki mugu ne, baya kyautawa." Malaika da Ahamad suna ta kuka a kunne Nasrin, ta zabura ta mike tsaye ta fito daga cikin bargo saboda damuwa. Ta ce "ki goya shi ki je wajen likita ya sake rubuta miki wata takardar maganin, ki je ofishin nan da na yi hira da ke, ki ce a nuna miki Dr.Gumel sai kice ni na aiko ki, zai baki kudi ki je ki siyo maganin da abinci. Zan yi masa waya kafin ki karasa dan yanzu idan nace zan turo miki kati ki siyar wani ɓata lokacin " ne." Malaika tana rawar jiki tana amsawa da "Toh Toh." Bayan sun kashe waya Malaika ta tashi ta goya ɗanta zata fice. 108 Jamila Umar Tanko (JUT), DA MA NI CE... 1 MetronLuba ta taɓo Metron Aisha ta nuna Malaika da yatsa ta ce, "kin ga matar can ta goya dan zata gudu." Aisha ta yi murmushi ta ce, “rabu da ita daman ba ta zo da komai ba daga ita sai kayan jikinta, badan ma da gaske mun ga yaron bashi da lafiya ba da sai in ce 'yan danfara ne.Kamar bata da gaskiya ta yi ta kallon mutane, kin san saboda ita na fasa kirga kudin adashen nan da na karɓo. Sai kallona take tana kallon kudin tana ajiyar zuciya tama manta marar lafiya ne a hannunta." وو Su ka kyalkyale da dariya suka tafa. Malaika har ta je baranda ta tuna bata karɓi takardar magani ba, sai ta dawo wajen Ma'aikatan jinya. Tana isa wajensu a gigice ta ce, “mijina bai dawo ba ku sake rubuta min wani maganin in je in siyo." Aisha ta harare ta ta ce, “mijinki ya kasa siyowa sai ke ce za ki iya kenan?" Luba ta ce "ke dai rubuta mata kawai mu ga gudun ruwanta." 109 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA'NI CE... 1 Aisha ta rubuta ta dankwafawa Malaika akan tebur a gabanta, ta yi gatsine ta ce, “daman kina da kudin siye kika bar ɗanki cikin wahala tun jiya?" Malaika ta dauki takardar a sanyaye ta juya baya har zata tafi ta gaba zata iya daurewa ba sai ta mayar da marta ni zata ji daidai. Sai ta juyo a fusace dubi Aisha ta ce, "Na girmi wulakanci, kada ku ganni a nan a yashe, ba ku san da wacce ku ke maganaba .66. Aisha ta zabura zata yi magana, sai Luba ta danne hannuta. Malaika ta yi gatsine gami da hararar Aisha sama da kasa ta juya ta tafi. Tana fita ta nufi ofishin Dr.Gumel anan ta yi sallama ta tura kofa ta shiga, sai ta ci karo da mutumin nan data yiwa wankin babban bargo. Ya ɗaga ido ya dube cikin fushi da takaici a take suka shaida junansu. Ya yi mata tsawa yace, "menene kuma? Kin zo ne dan ki sake zagina ne kuma?" . Malaika ta karaso gaban kujerarsa a sanyaye ta ce "Nasrin ce ta ce in zo wajen Dr.Gumel in karɓi kudi." 110 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 Ya yi tsaki ya harare ta ya ce, "wallahi da nasan ke zan bawa kudi da ba zan yiwa Nasrin alkawarin zan baki ba. Sai dai ta tura ki wani wajen wani. Marar kunya kawai, har yau na tuna cin zarafin da kika yi min raina sai ya ɓaci, amma na yi miki uzuri.' " Malaika ta yi fiki-fiki da ido tana ta juya takardar da take hannunta kamar wata mumina. Yagama cashe mata sannan ya zaro naira dubu goma ya dora akan teburin ganbansa ya tura gabanta a fusace. Ta sa hannu da sauri ta kwashe ta damke gam, ta ji duminsu. Sannan ta juya za ta fita. rare shi sama da kasa ta YaceYace, “dan haka ki kiyayi duniya ki daina wulakanta mutane, ba ki san in da za'a sake haduwa ba kuma mutumin nan da kika wulakanta kuma ya yi miki amfani kamar yadda na yi miki amfani yau." Ta juyo da sauri a fusace ta harare shi ta ce "Malam, ya isa haka, more bakin ya isa ko dan ka ji na yi shiru." " Ya zabura ya mike tsaye a fusace, ya daki tebur da karfi yace, "yau ma rashin kunyar 111 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 za kiyi min? Bari in sa security su kama min ke, kuma kudin nan dana baki sai kin dawo da shi." Ta na jin ya fadi haka sai ta bude kofa ta fice da gudu. Dariya ta kama Dr.Gumel ya yi ta Kyalkyalawa shi kadai. Yace, "wannan shegiyar yarinyar mijinta yana hakuri, ko waye shi yana shan wahala. Kuma da hankalinta ba hauka ba ce iskanci ne kawai. Malaika ta fito daga cikin asibiti ta tsallaka babban titi ta shiga babban kemist din dake tsallaken mai suna 'Mumtaz' ta je ta siyo magunguna da allurai a kan naira dubu shida da dari tara. Ta sayo kayan shayi madara, konfiles, siga, milo da biredi har da kwalin Juice, itama dan ta jera kowa ya zo ya ga sama saman lokarta da kayan dadi kamar sauran. Ta karaso cikin dakin ta isa wajen gadonta ta sauke Ahmad ta kwantar sannan ta jera kayan dadi, tana jerawa ta na juyowa tana kallon 'yan dakin da suke yi mata gani-gani, 112 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 ko tayin abinci basu yi mataba sai dai a junansu dan sun ga alamar bata da komai. Ta gama sannan ta dauki ledar allurai da magungunan ta je bakin teburin Ma'aikata ta ajiye a gabansu ta ce "gashi na siyo.” " da kai. Aisha ta harare ta sama da kasa ta kawar Luba ta ce, "Aisha ta na magana, hakuri za kiyi ki yi aikinki kada ki biye ta." " Aisha ta zabura tana magana cikin fushi ta ce "wallahi bazan je kan ɗanta ba sai dai in a abakin aikina.' Luba ta tashi da sauri ta dauki ledar ta ce da Malaika ta zo su je, dan taga alamar Malaika na marmar da baki tana so ta furta bakar magana, ta san fada za'a tayar gagarumi, dan kowaccensu gwana ce wajen tsiwa. Luba ta tsaya ta duba Ahmad yadda ya kamata ta yi masa allura ta kara masa ruwa, har numfashin kuwa ya fara daidaita dan dai har yanzu bacci yake mai kama da na mutuwa. Suna cikin wannanhali sai ga Shamaki a gigice ya shigo wando a ɗage, hula a bayan keya. Daga gani ya sha wahala ba ‘yar kaɗan 113 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 ba. Ya yi baki ya yi datti yana ta gumi da huci da alama bayan gudu akan babur ma ya yi gudu da kafa.Yana ta rawar jiki da rawar baki, dan ya ga irin kallon da Malaika ta yi masa na tara saura kwata. Ya mikawa Luba ledar magani ta karɓa ta duba ta ce "ai irinsu muka yi masa yanzu sai dai bata ɓaci ba ku ajiye saboda nan gaba." Shamaki ya yi ajiyar zuciya yace "Alhamdulillahi da aka samu aka yi masa kafin in dawo. Ina can ina ta nema dakyar na samo kudin. " Malaika dai ta ɓata rai ko kallonsa bata yi ba, luba ta yi gaggawar matsawa dan kada shafe . _ Malaika ta dawo gefen gado ta zauna kusa da danta tana kallonsa, Shamaki ya zauna a kusa da ita yana satar kallonta, ya na fargabar yi mata magana dan kada ta yayyagashi a cikin mutane, gashi kuwa 'yan ɗaki sun zuba musu ido suna kallo dan suna son su ji kwakwaf. Kowa ya san Shamaki ya ɓatawa Malaika rai, tunda ya fita bai dawo ba har ta fita ta nemo kudi ta siyo maganin sannan ya dawo. Daga 114 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 yadda take harararsa kowa ya san haduwar ba zata yi kyau ba. "Sannu da kokari Malaika, Allah Ya saka miki da alkhairi."Shamaki ya fada cikin rada saboda tsananin tsoro. Malaika ta harare shi ta yi tsaki. Sai ya tashi sadan-sadan "bari in je in yi sallar walha, zan dawo." yace Ya fice ba tare da ta bashi amsa ba. Bayan ya fita ne ya kira ta a waya yace ta fito baranda su yi magana, ta ce bazata iya barin ɗanta ba ta fito, babu mai kula da shi. Lallai ta yi hankali dan haka bai ji haushi ba. Nasrin ce ta kira Malaika awaya dan ta ji yadda suka yi da Dr.Gumel. Fara'ar da Malaika ta ke yi sai da kowa ya yi mamaki dan tunda ta shigo ɗakin nan bata yi dariya ba, daga harara sai tsaki. Malaika ta yi mata godiya ta tabbatar ta karɓo dubu goma har ta siyo allurai, ruwa da magunguna an sakawa dan. Nasrin ta tambaya “har yanzu Shamaki bai dawo ba kuma bai kira ba?" 115 | Jamila Umar Tanko (JUT) _ Malaika ta tabbatar mata "har yanzu bai waiwaye mu ba." DA MA NI CE... 1 Ran Nasrin ya ɓaci ta gasgata cewar Shamaki mugu ne shi yake cutar Malaika. Su ka yi sallama suka kashe waya. Nasrin ta kira Shamaki a wayarsa bai dauka ba kasancewar yana Sallah, kuma ma ya saka wayar a silent tana aljihunsa. Ta kira ta sake kira bai dauka ba sai daga baya ya ga missedcalls dinta sannan ya kira ta, itama bata kusa bata dauka ba. Ya yi mamakin ganin kiran Nasrin amma bai yi mamaki da yawa ba, ya san Malaika zata shaida mata suna asibiti,. Ya san Nasrin jaje ta kira zata yi masa. Ya fara zargin ko kudin da Malaika ta sayi maganin ma Nasrin ce ta aiko mata daman tun dazu yake ta tunani ya kasa nemo tabbacin in da kudin nan ya fito. Tabbas ba zai wuce daga Nasrin ba. In dai haka ne kuwa Malaika ba zata taɓa ganin kokarinsa ba tunda ga wata daga haduwa a hanya tana yi mata hidima. Ya fara ganin laifin Nasrin da sake taɓarɓara masa gida, dan ba taimakonsa take ba sake saka 116 | Jamila Umar Tanko (JUT) _ DA MA NICE. T sha'awar masu kudi take yi a zuciyar Malaika.Ya fara tunanin yadda zai raba alakar Nasrin da Malaika. Bayan magruba Kanwarsa ta zo daga Muntsira Sadiyalle, sai Malaika ta bar Ahmad da Sadiyalle ta fito kan baranda inda Shamaki ya sami lungu ya takure yana ta damunta da waya. Ta zo ta tsaya a gabansa kerere ta ce, "meye wai?" Ya langwabar da kai yace, "Malaika! zauna mu yi magana dan Allah, ta fahimta." Ta zauna a fusace tana turo baki, Shamaki ya yi gyaran murya yana mammatsa hannu kamar marar gaskiya yayin da zuciyarsa ke dukan uku-uku. Ya ce, "Malaika! Na san na ɓata miki rai amma ki yi min uzuri. Wallahi ban tashi dą ko sisi ba ciki da waje, haka na fita na duba gabas da yamma, kudu da arewa na rasa in da zan nufa, na so in je Bichi wajen aikina in samu a ranta min in an yi albashi a dauka na tuna yau asabar babu kowa a sakateriyar. Na juya zan shiga B.U.K na tuna bamu da Lacca yau sai 117 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 karfe hudu babu wandazan samu, in takaice miki har kantin kwari na je na yi bara, ina nuna katin asibiti, basu bani ba suka zage ni wai an sami sabuwar danfara kato da ni mutuwar zuciya ce in je in yi dako ko faskare mana. Na gasgata sun fadi gaskiya. Na je kasuwar singa zanyi dako, na ji kudin da za'a biya ni a yini ma ba zai isa ko rabin kudin maganin ba. Na so in siyar da wayata ma na ji anyi min tayin wulakanci, kudin ba zai sayi magani ba. Daga karshe naga bani da mafita sai na je na sami Fatima Giwa wata attajirar matace, daya daga cikin matan ajinmu a gidanta. Na yi mata bayani ita ta taimaka min da kudin magani, ta bani naira dubu goma. " Malaika ta harare shi ta ce,"Fatima Giwa 'yar ajinku ko bazawararka?" Ya girgiza kai yace, “matar aure ce ma tana auren wani attajiri a Nassarawa GRA, ban taɓa sanin gidan ba sai yau da ta kama,da naga bani da mafita, direbanta ma na kira ya bani shawara in zo zata taimaka min dan mun saba 118 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE...1 da shi. Daman itace take siya min handout ni kuma nake bata amsa." " Malaika ta taɓe baki ta ce, "in tayi tsami za mu ji, in an yi magana ace ni nake makalewa masu kudi. Kai yanzu me yasa baka makalewa talakawan ajin na ku ba su 'yar shila amma ka Makalewa Giwar, saboda tafi maiko, da tsoka ko?" Shamaki ya tabbatar Malaika bata da tausayi ta juya maganar gaba ɗaya zuwa wani sashi, sai ya yi shiru bai bata amsa ba. Aka jima ya ɗago ya dube ta yace, "a ina kika sami kuɗi kika sayi magunguna da kayan shayi?" Ta harare shi ta ce, "a wajen 'yar ajinmu nima na samu Nasrin Giwa.' " Ya daɗe yana kallonta kallo na takaici ya rasa amsar da zai bata. Ya ce "rokarta kika yi kika ce na kasa?" Malaika ta zabura ta mike tsaye ta kama kugu ta ce "ba ka kasa din ba ne? Da ka fitaka dawo da wuri ne? Sai in bar dan nawa ya mutu? Daga yau na sami abin gori nima dagaka ce na 119 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 makalewa Nasrin zan ce kai ma ka makalewa Fatima Giwa." Ta juya ta tafi a fusace ta bar shi anan a zaune yana kallonta, kwalla ta cika masa ido. Ya girgiza kai ya sunkuyar da idanuwansa kasa sai hawaye ya surnano. Yana ta girgiza kai yana tausayin kansa da kansa yana mai takaicinjarabawar (test) din da ya rasa yau a makaranta. Yana kuma fargabar ko dansa zai tashi ko zai rasu, saboda jikin ya tsananta, yana tunanin halin da ya bar yaransa guda biyu a gidan makwabta. Ko ana kula da su ko kuwa an bar su da yunwa? Ya shiga tunanin kudin da za'a bukata nan gaba a asibiti dan bashi da su, bai san in da zai tafi nema ba kuma. Sadiyalle ya gani a tsaye akansa tana kallonsa cike da tausayi ta ce, “Shamaki kuka kake yi? Ka yi hakuri komai yana da iyaka. Allah Yana tare da makurci. 99. Sai ta rushe da kuka, shima ya fara kuka har zuwa lokaci mai tsawo babu wanda ya iya magana a cikinsu. 120 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 Shamaki ya mike tsaye ya kalle ta da jajayen idanuwansa yace "mu je gidan dare ya dan ki kula da su Aliyu." Su ka isa wajen Babur dinsa suka hau, suka tafi. A hanya sadiyalle take bashi labarin zamanta a gidan mijita. Itace mata ta uku, bata taɓa haihuwa ba amma tana ganin masifa a gidan nan, mijin baya tsinana masu komai sai dai kowacce ta nemo. Ta kara da cewa tana mamakin yadda Malaika bata godewa Allah da duk irin kokarin da mijinta yake yi mataba. Shamaki ya yiwa kanwarsa nasihohi akan ta ci gaba da hakuri kuma idan ya gama karatu albashinsa zai karu zai dinga taimaka mata. Su ka isa gida yace ta shiga Makwabta ta ɗauko yaran, tana shiga sai ta iske yaran a kwance a zaure cikin akuyoyi, matar gidan ta turo su ta rufe dakinta da yaranta, da alama suñ sha kuka sannan suka gaji suka yi bacci, yunwa ce a cikinsu daga gani dan cikin da doron bayan sun haɗe. Sadiyalle bata ji dadi ba ta kamo hannunsu ranta a ɓace suka fito suka iske shamaki a kofar gidan. 121 | Jamila Umar Tanko (JUT) DÀ MA NI CE... ↑ Yana ganinsu ya tambaya "ba dai a zaure kika dauko su ba, dan na ga daga shigar ki kin fito." Ta fada masa a halin da ta gansu, sai ya ji ransa ya ɓaci ya kudiri a niyyar ba zai sake barin yaransa a gidan makwabta ba. Ya bawa Sadiyalle Mukullin gidan, yace bari ya je ya suyo musu abinci, ya hau babur ya tafi. Ita kuma ta bude gida suka shiga tsakar gida ta shinfida musu tabarma suka zauna. Ba jimawa sai ga Shamaki ya siyo musu dafafiyar indomie da kwai a cikin ledoji. Su ka yi ta ci hannu baka hannu kwarya, da alama ko abincin safe ba 'a basu ba balle na rana da na dare. Shaniakiya fada a bayyane "daman Uwale bata da mutunci, dan rashin imani ta bar min yara da yunwa?" Sadiyalle ta ce "wallahi wani abun ma saboda kai ake yin kara ake yi, amma ba dan Malaika ba. Aka bibiya ita ma Malaika tana yiwa 'ya'yanta rashin mutunci. Kai a ganinka Malaika zata rike wa Uwale yaranta ta ciyar da su na yini guda?" 122 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 Shamaki ya gyada kai yace, “da wannan dan wannan." Sadiyalle ta ce, "yanzun ma saboda nauyin kai ka tura su ya sa ta karɓa. Sau nawa nake jin Malaika tana zagin Uwale ta ce sun yi zage-zage. Ai rashin kirkinta ne ya jawo aka yiwa nata haka.' " Bayan sun gama ci Sadiyalle da yara suka shiga ɗaki suka kwanta, Shamaki ya shiga falo ya kwanta akan doguwar kujera, baccin gajiya ya kwashe su su dukka basu farka ba sai da assalatu. *** *** *** RANAR LAHADI.. ° .KANO Tun bayan da suka idar da Sallah Sadiyalle da Shamaki suka yi ta hidimar gida, Shara, wanke wanke, dafa abinci da wankin kayan fitsari. Sadiyalle ta yi tsaki ta fada a bayyane "gaskiya Malaika kazama ce, Shamaki kalli yadda yana da kura su ka yanyame ko ina, datti kamar babu bil'adama a gidan. Wai me Malaika take yi ta bar gidanta a haka?" 123 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NICE... 1 Shamaki ya yi tsaki ya harare ta, ya ce, "dalla Malama ki gyara in da zaki gyara, bana son yawan magana da cin naman mutum dan baya kusa. A gabanta za ki iya fadar haka?” Da alama ya ji haushi dan an caccaki rabin ransa Malaika. Sai Sadiyalle ta zunɓuro baki bata kara magana ba, ta turo baki gaba. Da misalin karfe tara na safe suka gama shiryawa tsaf, Sadiyalle ta dauko leda ta zubo kayan sakawar Malaika da na Ahmad, brush, makilin, soso da sabulu, suka jifgu akan babur su dukka ga kaya ga yara suka tafi. Suka isa cikin asibitin, bayan ya nemi waje a wata inuwa ya tsaya sai suka dunguma cikin dakin su dukka dauke da filasanabinci a hannunsu. Tun daga nesa suka hango Malaika cikin tashinhankali, ta tsaya a tsakiyar ɗakin ta ɗora hannu aka kamar maishirin kurma ihu.Sai suka tsaya cak sannan suka ci gaba da tahowa amma fa suna karanto 99 "Innalillahi wa'inna ilaihi raju'un.' 124 | Jamila Umar Tanko (JUT) ☐ DA MA NI CE Tun Shamaki bai karaso ba ya gama fahimtar abinda ya afku, sai ya saki kayan da yake hannunsa ya kwaɗa salati a bayyane. Malaika na ganinsa ta tahoda gudu ta rirrike shi ta na kururuwa, kukan da yake tafe da dinbun hawaye ta ce, "Shamaki! Ahmad ya rasu da asuba.' " Sai hawaye ya surnano daga idanuwansa ya zame hula ya rike a hannu yana tafe yana sanɗa har ya karasa wajen gawar, ya buɗe a hankali, ya yin da kirjinsa yake ta faman dukan uku-uku. Ya dubi Ahmad yaro a mimmike daga kashi sai fata. Ya shafa kansa ya fada a bayyane "Kulli Nafsin za'ikatil maut. Ahand! Allah ya jikanka ya baka uwar goyo a Aljanna. Mu ma muna nan tafe, ba mu yi jinkiri ba, haka kai da ka tafi yanzu baka yi gaggawa ba." " Ba Malaika kadai ba, gaba daya 'yan dakin da ma'aikatan sai da Shamaki ya basu tausayi, hawaye kawai zaka dinga gani a idanuwan manya maza da mata. Sun tausayawa Shamaki da Malaika sun tausayawa Ahmad yaron ya sha wuya, suna kuma masu tausayin 125 | Jamila Umar Tanko (JUT) DA MA NI CE... 1 kansu da kansu, suma wataran zasu zama gawa tabbas. Nan dai Shamaki ya yi ta maza ya nufi wajen Ma'aikatan lafiya suka ci gaba da tattaunawa akan fom din da zai cike da kuma yadda zai dauki gawar. An ɓata lokaci, daga karshe ya samo mota tasi aka saka gawar, Malaika, yara da Sadiyalle suka shiga suka tafi, bayan an saka ganye a bayan motar shaidar motar da gawa, duk wanda ya gani sai ya kauce ya basu waje. Shamaki ya tsaya a jikin babur dinsa yana ta bugawa Makwabta da 'yan uwa na can garin su, 'yan uwansa da 'yan uwan Malaika waya ya sanar da su anyi rasuwa duk mai hali ya zo jana'inza. Daga karshe ya hau Babur dinsa ya biyo su gida. Kafin ya karaso Mata sun cika gidan ana ta kuka. Malaika kam har rirrike ta ake yi tana ta kururuwa, mutuwar nan ta sshige ta an tausaya mata, ta sha jigila da yaron nan tunda ta haife shi bata hutaba. Daidai lokacin Nasrin ta kira wayar Malaika dan ta tambayi mai jiki, wayar a hannu Sadiyalle sai ta shaida mata Malaika ba 126 | Jamila Umar Tanko (JUT) NI CE... 1 zata iya amsa wayaba saboda danta ya rasu ko binne shi ba'ayi ba. Kafin ma Sadiyalle ta fadawa Nasrin haka kuruwar kukan Malaika ta tabbatar mata da haka. Nasrin mai tausayi sai ta ji hankalinta ya tashi, tausayi ya lullɓe ta ta fara zubar da hawaye, ta kashe wayaba tare da ta ce wa Sadiyalle komai ba. DA MA Ta shaidawa Zainab yayarta halin da Malaika ta ke ciki sai jikin Zainab ya yi sanyi dan ita neman haihuwar ma take bata samu ba, sai yanzu ne take da karamin ciki. Nasrin ta bugawa kawar Dinah waya ta shaida mata abinda ya sami Malaika, duk da Dinah bata sansu ba amma ta ji tausayinta, ta yiwa Nasrin gaisuwa ta ce ta yiwa Malaika idan sun yi waya. Haka Nasrin ta kasance yini guda cikin sanyin jiki mutuwar ta shige ta. Aka binne Ahmad aka ci gaba da zaman makoki, Sai da daddare bayan komai ya lafa sannan Nasrin ta sake kiran Malaika ta yi mata gaisuwa gami da yi mata wa'azi akan dangana. Malaika tana ta kuka abin tausayi har sai da Nasrin

Chapter 5 of 7