hunzalu ina mai shawartarka da ka gaggauta janye gidan gonar nan kafin cikar dakika dari ko Yanzu nan na umarci dakaruna dake kan ganuwa suyi musu ruwan kibau.
Yana gama fadin hakan sai ya juya ya koma can bakin kofar gidan gonar inda sauran yan uwansa masu gadi suke.
Nan take hunzalu ya karaso gaban yarima Huzaifa ya dubeshi cikin tsananin damuwa yace, ya shugabana yanzu menene abinyi?
Kawai sai Huzaifa yace, ku zo mu koma da baya izuwa can cikin duhuwar dajin can.
Ba tare da bata lokaciba suka bi wannan umarni suka shige izuwa cikin duhuwar ciyayi da bishiyoyi wadanda ke nesa kadan da kofar gidan gonar inda ba a iya hangosu.
Da shigar su wannan wuri sai suka sauko daga kan damakansu kowa ya zauna a kasa dirshan cikin alamun karayar zuciya aka yi tsit tamkar babu mai laka a jikinsu.
Tsawon yan dakiku dayansu baice uffan ba kowa yana tunani, a sannane hunzalu ya dubi yarima Huzaifa yace, ya shugabana yanzu kana da wata dabara ne wacce kake ganin zamu iya amfani da ita wajen samun nasarar dauko Luhaira kuma mu fito a raye ba tare da mun fuskanci wata matsala ba?
Lokacin da hunzalu ya zo nan a zancensa sai Huzaifa yayi ajiyar zuciya sannan yace, a rayuwata ban taba samun karayar zuciya ba irin ta yanzu bisa duk abinda nasa a gabana.
Ina da yakinin cewa Allah zai iya bamu nasarar shiga cikin wannan gidan gona bisa taimakonsa, to amma bani da tabbacin cewar da yawan mu bazamu rasa rayuwarmu ba.
Abu na biyu shine, duk a cikinmu babu wanda yasan ainahin dai dai gurin da Luhaira take bare da zarar mun shiga ciki mu wuce kai tsaye izuwa wajen dole sai mun bata lokaci mai yawa wajen gano wajen ko kuwa hunzalu ka san inda aka ajiye Luhaira?
Humzalu ya gyada kai yace,ai kullum ai an sauyawa Luhaira dakin kwana a cikin gidan gonar nan, kuma a kallah dakunan sun fi guda dari uku, sannan kowanne daki tsakaninsa da wank akwai tazara ta a kalla tafiyar rabin saa.
Koda jin wannan batu sai zuciyar yarima Huzaifa ta sake karaya fiye da ko yaushe yaji kamar ya fashe da kuka saboda takaici, kawai sai ya dubi gaba daya dakarun yace, ku tashi muyi kokarin barin garin nan ba zamu iya shiga cikin gidan gonar nan ba har mu iya dauko Luhaira.
Tunda dai Allah ya sa ni da su aljani hurusul Marwas mun sami nasarar ceto rayuwarku ai mun sami gagarumar nasara ta farko.
Koda gama fadin hakan sai kowa ya mike da nufin a hau dawakai abi wata barauniyar hanya wacce zata kutsa dasu izuwa cikin daji.
Kwatsam! Sai suka hango badakaren nan wanda wakilin sarki ya tura can kurkuku domin yaga abinda ke faruwa bisa doki a sukwane ya durfafi kofar gidan gonar. Koda ganin haka sai hankalin su Huzaifa ya sake dugunzuma ainun domin sun san cewa da zarar ya iso bakin kofar gidan gonar ya tambayi labarin su asirinsu ya tonu kenan.
Ba zato ba tsammani sai kuma suka sake hango aljani hurusul Marwas ya sauko daga sama ya sure shi da dokinsa gaba daya yayi sama da su kamar shawo ya suri dantsako kuna dai ya lullubesu da fuka fukansa ya luluka da su izuwa can kololuwar sama.
Kafin kiftawar ido ya bace bat! Bayan yan dakiku sai gashi ya sake bayyana tsulum! A gaban Huzaifa.
Kawai sai ya dubeshi yace, ya shugabana ka yi mini izini ni kadai zan shiga cikin gidan gonar nan na dauko Luhaira cikin ikon Allah batare da asirina ya tonu ba.
Kuma a cikin dakiku kadan zan hattama wannan aiki.
Koda jin wannan batu sai Huzaifa yayi murmushi sannan yace, Yanzu ina kakai wannan badakaren da dokinsa?
Hurusul Marwas najin wannan tambaya sai ya mai da masa da martanin musmushin sannan yace ai tuni nayi aikin namu na aljanu.
Cikin jikinsa na shiga na komar da shi izuwa can wajen wakilin sarki ya shaida masa cewar yaje kurkuku da gidan gona ya tabbatar da babu wata matsala.
Bayan wakilin sarki ya sallameshi ya koma cikin yan uwansa bayi kuma sai na shafeshi na sa masa barci mai nauyi saboda ina tsoro cewar bayan na fita daga jikinsa zai iya dawowa cikin hayyacinsa ya koma wajen wakilin sarki ya sanar da shi ainahin gaskiyar alamari.
Koda aljani hurusul Marwas yazo nan a jawabinsa sai murna ta kama yarima Huzaifa da su Humzalu kuma suka Sam cikakken kwanciyar hankali.
Cikin faraa Huzaifa ya dubi aljani hurusul Marwas yace, tabbas Yanzu ne na dada tabbatarda cewa ni da kai duk muna bukatar juna kuma idan dayanmu baya tare da dayan to babu yadda za'ayi ya sami nasarar cika aikin da yazo yi a kasarnan.
Ya kai hurusul Marwas nayi maka izini maza ka shiga cikin gidan gonar nan ka dauko mini Luhaira.
Hurusul Marwas ya risina yace, an gama ya shugabana.
Kafin ya budi baki yace wani abu tuni aljani hurusul Marwas ya bace bat daga gabansa.
Nan fa tunanin zuci yace fadowa Huzaifa ya tambayi zuciyar sa yana mai cewa, menene dalilin da yasa aljani hurusul Marwas ya kirani da matsayin shugabansa a wannan karon alhalin tun daga lokacin da muka hadu dashi abokina yake kirana dashi?
Amsar da Huzaifa ya kasa baiwa kansa kenan, amma sai ya kudure a cikin ramsa cewar idan suka sami nutsuwa dai ya yi masa wannan tambayar.
Huzaifa na cikin yin wannan tunani ne kawai yaga aljani hurusul Marwas ya sake baiyana tsulum! A gabansa goge da Luhaira gadon bayansa amma ko ina a jikin hurusul Marwas sara ne na takobi sai jinine ke kwarara daga jikinsa.
Da rub da ciki aljani hurusul Marwas ya kife kasa yana numfashi sama sama, ita kuwa Luhaira dake kwance a bayansa, barci take ta faman sharara bata ma san abinda ke faruwa ba.
A dimauce, cikin tsananin firgici yarima Huzaifa ya dauke Luhaira daga kan bayansa. Hurusul Marwas ya shimfide akan ciyawa gefe daya sannan suka taru akan aljani hurusul Marwas suna yi masa magani gami da tofa masa adduoi domin su ceto rayuwarsa.
Sai da lokaci mai dan tsawo ya shafe sannan numfashin aljani hurusu Marwas ya dawo dai dai har ya iya bude idanunsa.
Koda ya tsinci kansa a gabansu Huzaifa kuma yaga Luhaira kwance a cana gefe daya tana ta shara barcinta sai ya yi kabbara cikin tsananin Farin ciki kuma yayi godiya ga Allah, sannan ya mike zaune ya dubi Huzaifa yace, ya shugabana burina na farko ya cika tunda har bukatunka sun biya bisa abinda kazo nema a garin nan.
Ka kubutar da dakarunku wadanda aka tsare a kurkuku sannan kuma ka dauko Luhaira.
Koda jin wannan batu sai Huzaifa yayi murmushi a gareshi yace, a'a gyara maganar ka, ba nine na dauko Luhaira ba kaine, kuma in ba don kai na da babu yadda za'ayi na iya daukota.
Gama fadin hakan ke da wuya sai hankalin kowa ya koma kan Luhaira wacce ke kwance akan ciyawa.
Nan fa su duka suka dimauce bisa ganin irin tsananin kyawun da Allah ya bata domin inda za'a hada kyawun gimbiya Lafirta dana yar uwarta Sazirat a waje guda bazai kai rabin ma Luhaira ba.
A wannan lokaci wata doguwar riga ce fara kal mai shara shara a jikinta, don haka duk surar jikinta a fili take, musamman ma idan iska ta kada rigar.
Cikin gaggawa Huzaifa ya cire alkyabbar jikinsa ya lullubeta da ita sanna ya dubi aljani hurusul Marwas yace, ya kai dan uwana yanzu menene abinyi?
Koda jin wannan tambaya sai hurusul Marwas yayi murmushi yace, babu abinyi face muyi sauri mu bar garin nan mu durfafi birninku na Darul husuf domin muje mu ga halin da ake ciki, walau anci nasarar yakin da ake yi ko ba'a ci ba.
Koda jin wannan batu sai Huzaifa yaji gaba daya hankalinsa ya koma kan birnin Darul Husuf.
Nan take ya sake daukar Luhaira ya dorata a gadon bayan aljani Hurusul Marwas sannan shima ya kama dokinsa ya hau, suma su Humzalu sai suka yi koyi da shi.
Nan take aka ci gaba da tafiya ana karanta wannan addua wacce yarima Huzaifa ya bayar tun da farko.
*wannan shine abinda ya faru ga su Huzaifa, bayan sun sami nasarar debo fursunoninsu daga kurkukun sarki shaaran kuma sun dauko Luhaira daga gidan gonar sa bayan sun sha bakar wahala da bakin gumurzu*
* * * * * *
Al'markin su sarki shaaran kuwa, bayan ya gama sanar da mahaifiyar ukashat duk abinda ya faru da kuma hukuncin da zai dauka na gaba wato neman taimakon dakarun yaki daga sauran kasashen kafirai na nahiyar don aje a yiwa birnin Darul Husuf rubdugu a gama da shi farat daya, sai ta kyalkyale da dariyar Fatin ciki sannan kuma ta tashe da kukan bakin ciki tace, tabbas dana ukashat ya ci amanata a matsayina na mahaifiyarsa, kuma ya bani kunya.
Lallai da hannayena zan kashe shi, amma kuma nayi matukar Farin ciki daka sami nasarar cin wannan birni namu da yaki cikin BAZATO!
Shawarar da zan baka itace, ka gaggauta shirin tafiya izuwa kasashen makwabtaka domin nemo dakarun gudunmawa na yaki amma kafin ka tafi ka bar jiran gari nan a hannuna.
Nayi maka alkawarin cewar kafin ma a sake yin yakin karshe zan kama sarki Uwaisul Karni da duk mukarrabansa sai dai ka dawo ka iskesu a cikin kurkuku a tsare.
Koda jin wannan batu sai sarki shaaran da yarda Sazirat suka kalli junan su sannan suka kalli mahaifiyar ukashat cikin alamun rashin yadda da gamsuwa, kawai sai suka koma gefe daya sukayi dan kuskuks.
Sarki shaaran ya dawo wajena ya dubeta yace, yake matar babban maki yina, kiyi sani cewa na yi shawara da yata Sazirat kuma mun yanke hukuncin cewar zamu bar Miki jiran birnin Darul Husuf a hannunki, amm bisa sharadi guda.
Sharadin kuwa shine, idan har da gaske zaki iya kama sarki uwaisul karni shi da mukarrabansa har ki tsaresu a kurkuku to mu dawo mu iske kan danki ukashat a tsire a jikin ice akan ganuwar garin nan.
Idan kuwa muka dawo muka ga babu wannan kai na Danko, to mun san cewa yaudararmu kikayi don haka zamu shigo cikin birnin ne da karfin tsiya mu sake yakarku kuma mu kashe kowa da komai ko kaza guda daya bazamu barta da rai ba.
Koda jin wannan sharadi sai hankalin mahaifiyar ukashat ya dugunzuma ainun saboda ta san cewa bazata iya kashe danta ba ko kuma ta sa wani ya kashe shi komai tsanar da take yi masa a rayuwarta.
Nan take ta nuna cewa zata cika wannan umarni, amma tan bukatar a bar mata kamar dakaru dubu dari wadanda zasu karta ta sami ikon tafiyar d komai kamar yadda ya kamata, sarki shaaran yayi murmushi yace, shikenan na amince da hakan.
Nan take ya ware dakaru dubu dari aka barsua birnin Darul Husuf sannan sarki shaaran, Sazirat da sauran dakarunsu suka yi shiri suka hau dawakansu suka fice daga cikin birnin suka nausa cikin daji a guje suka durfafi hanyar da zata kaisu birninsu na shumbul.
* * * * * *
Bayan kamar rabin sa'a da bacewar sarki shaaran a cikin daji, sai tawagar su sarki uwaisul karni ta bullo daga wata hanya daban ta durfafi birnin Darul Husuf.
Sarki uwaisul karni ne akan gaba tare da yarima ukashat.
Su da dukkanin dakarun dake biye da su sun yi shigar yaki ne dauke da makamai.
A wanann lokaci rana bata fadi ba amma magriba ta kawo kai.
Kafin a isa inda za'a iya hango kofar birnin sai sarki uwaisul karni ya ja linzamin dokinsa ya tsaya cak! Kuma ya bayar da umarnin a tsaya a wajen a kafa tantuna.
Alamarin da ya baiwa kowa mamaki ke nan, saboda bai kamata a tsaya a daji ba dag da magriba tunda ana dag da shia gari.
Alhamdulillahi, anan zan dakata kuma sai Allah ya kuma ara mana rana irin ta yau zaku jini dauke da ci gaban wannan Littafi.
**DAKARUN MUSULUNCI**
LITTAFI NA BIYAR 5
PART C ✍️ ♥️
NA ABDUL AZIZ SANI MADAKIN GINI
TYPING :-UMAR FAROUQ ZANGO ✍️
POSTING:- Najibullahi Muhammad
Cikin alamun tsananin mamaki ukashat ya dubi sarki yace, ya kai Abbana ina dalilin tsayuwarmu anan?
Ai kamata yayi mu karasa cikin gari da sauri ko don't mu sami jam'in sallar magriba a masallaci.
Saadda sarki uwaisul karni yaji wanann tambaya sai yayi murmunshi sannan ya dubi ukashat yace, hakika kai yaro ne har yanzu ba ka san tuggun yaki ba da sharrin abokan gaba.
Ina son ka sani cewa duk ranar da ka baro gida to idan ka dawo kada ka shiga gari kai tsaye muddin ka san cewa kana da abokin gaba.
Anan zamuyi sallar magriba sannan mu tura kwararren dan leken asiri yaje ya gano mana irin yanayin da birnin mu keciki.
Babu mamaki a bayan ba ma nan anzo an cimu da yaki bamu sani ba, kun ga ke nan za'a iya dana mana tarko muna shiga cikin garin a kamamu ko a hallaka mu.
Lokacin da sarki uwaisul karni yazo nan a jawabinsa sai jikin kowa yayi sanyi aka yi tsit! Har izuwa tsawon yan dakiku sannan ukashat ya sake dubansa yace, ya kai abbana, to wai shin yanzu ta yaya dan leken asirin da zaka tura zai iya gano wani abu idan har an shirya mana wank tuggu?
Koda jin wannan batu sai sarki uwaisul karni ya sake yin murmushi a karo na biyu yace, ya kai dana, ka kyale mai abu da abinsa, sai yau da gobe ta fi karfin wasa.
Akwai abubuwa da dama wadanda zan lura da su, idan har na ga sauyin su na san cewa an kulle kofa da barawo a cikin birnina.
Idan dan leken asirin da zan tura yaje ya dawo akwai tambayoyin da zan yi masa na musamman.
Daga irin amsoshin da zai bani ne zan gane komai.
Yanzu sai mu yi alwala don gabatar da sallah.
Nan take kuwa kowa ya sauka daga kan dokinsa aka gangara bakin wata korama aka yi alwala.
Da lokacin sallah yayi sai sarki uwaisul karni yayi limanci aka gabatar da farilla.
Bayan an idar da sallar kuma anyi adduoi na neman tsari daga dukkan mugun abu da abokan gaba an shafa sai sarki uwaisul karni ya tura wani hadiminsa mai suna SHABBARU.
Ya dubeshi yace, maza ka tafi izuwa dafda kofar birninmu a cikin sanda da labiya kuma ka tabbatar da cewa ba'a ganka ba ko a kamaka sai ka sami wuri ka buya a cikin duhuwa ka zuba ido izuwa kofar birnin har izuwa Tsawon kamar rabin saa, sannan ka dawo nan wajen mu.
Lallai ka lura da duk abubuwan da ke gudana a kofar birnin kada ka mance da komai.
Koda jin wannan batu sai shabbaru ya risina yace, an gama.
Nan take shabbaru ya mike tsaye ya fice daga cikin tantin sarki uwaisul karni ya koma cikin nasa tantin yayi sauyin tufafi ya sa wadamsj korayen tufafi wadanda suka saje da yanayin ciyawa cikin dajin.
Ba tare da ya dauki wani makami ba kawai sai ya fice daga cikin tantin ya falfala da gudu izuwa cikin duhun daji.
Duk da cewar gari ya gauraye da matukar duhu ko tafi hannu mutum baya iya gani amma ko kadan shabbaru bai damu ba sai dada kutsawa yake yi ta cikin koramai, kwazazzabai da duwarwatsu tamkar da rana yake tafiyar ba da daddare ba.
Idan yayi dan gudu na Tsawon yan dakiku a cikin duhuwar ciyawa sai ya tsaya cak! Yayi lambo yana mai kasa kunnuwansa ko zai ji alamar ana biye da shi ko kuma zai ji motsin labewar wasu.
A haka dai yaci gaba da tafiya har ya iso dag da kofar birnin Darul Husuf bai gamu da kowa ba kuma bai ji motsin komai ba.
Da isowarsa dag da birnin sai ya kwanta a cikin duhun ciyawa tamkar lambon maciji ya zubo ido izuwa ga kofar birnin.
Shabbaru bai kawar da idanunsa ba daga kan kofar birnin sai da rabin saa ta cika, sannan ya juyo da baya da gudu ya dawo wajen da su sarki uwaisul karni suka ya da zango.
Da isowarsa yayi inkiya dakaru suka bashi hanya ya shiga cikin sansanin kuma ya wuce kai tsaye izuwa tantin sarki uwaisul karni.
Sarki uwaisul karni na zaune bisa kan sallama rike da casbaha yana lazimi sai yaji muryar shabbaru yana mai yi masa sallama, sarki uwaisul karni ya amsa masa sallamar gami da bashi izinin shigowa.
Shabbaru ya shigo cikin tantin ya durkusa a gabansa bisa gwiwowinsa yana mai sunkui da kansa kas cikin biyayya.
Sai da sarki uwaisul karni ya karasa lazimin da yake yi sannan ya dago kai ya dubi shabbaru yace, shin lokacin da ka je kayi lambo kana kallon kofar birninmu ka jiyo sautin zikirin da aka saba yi a masallaci kullum a irin wannan rana ta yau,v wato jumaa?
Shabbaru ya gyada kai yace, ya shugabana ai nafi rabin saa a kwance cikin ciyawa kuma dag da kofar birnin amma kunnuwana basu ji sautin wani zikiri ba.
Sarki uwaisul karni yayi murmushi gami da ajiyar zuciya yace, shin ka hango hayakin wutar nan da aka saba kunnawa a bayan gidana wacce malamanmu ke jin dumi da ita a duk saadda suka zauna taron karawa juna ilimi bayan sallar magriba?
Shabbaru ya gyada kai yace, ko kadan ban hango wannan hayaki ba.
Koda jin wannan batu sai idanun sarki uwaisul karni suka zazzaro, ya sake duban shabbaru cikin alamun tsananin tashin hankali ya ce, shin ka ga an fito da abinci a cikin kwanon gidan sarauta an kawowa masu gadin kofar gari?
Shabbaru yace, a'a har na baro wajen ban ga ma an bude kofar gari ba.
Koda jin wannan amsa sai nan take idanun sarki uwaisul karni suka ciko da kwalla har hawaye ya zubo masa yayi Salati gami da hailala yace, shikenan abinda nake gudu ya afku.
Tabbas an zub da jinin muminai a cikin birnina kuma an karbe garin daga hannun jamaarmu.
Koda gama fadin hakan sai sarki uwaisul karni ya mike tsaye zumbur a dimauce ya fice daga cikin tantinsa yana mai kwalawa ukashat kira tare da sauran manyan mayakansa.
Nan take kuwa suka rugo da dugu izuwa bakin tantin sarki uwaisul karni, sukayi masa kawanya.
Koda kowa yaga hawaye na zuba a idanun sarki uwaisul karni sai hankali ya tashi.
Ukashat ya matso dag da shi yace, ya abbana shin abin da kake zargine ya tabba?
Sarki uwaisul karni ya girgiza kai yana mai nuna alamun cewa Hakane.
Ai kuwa sai aka barke da hailala, kowa ya kamu da tsananin bakinciki domin da yawa sun san cewa zasu iya komawa su tarar da cewa an kashe makusantansu ko aminansu.
Tsawo yan dakiku ana ta alhini an rasa wanda zaice kala.
Kawai sai ukashat ya zare takobinsa cikin tsananin fishi ya dubi sarki uwaisul karni yace, ya kai abbana ka bani izini na jagoranci dakarunmu da ke nan muje mu yaki abokan gabarmu da ke cikin birninmu domin mu karbi birninmu da karfin tsiya!!!
Koda jin wannan furuci na ukashat, sai hawaye ya zubowa sarki uwaisul karni ya dubeshi cikin alamun tausayawa yace, ai kuna zuwa za ku fada cikin taron abokan gaba.
Babban abin bakin cikin ma shine da dan gari akanci gari.
Tabbas koda mun bi wata hanyar daban akwai mutumin daya JAL wanda zai iya wargatsa mana dukkan shirin mu ya tina mana asiri tunda yafi kowa sanin sirrin da dukkan dakaruna na yaki.
Kodajin haka sai ukashat ya dubi sarki uwaisul karni cikin alamun tsananin damuwa yace, ya kai Abbana wanene wannan mutum wanda yafi kowa sanin sirrin kuma ya zamana cewa shine zai tona mana asirinmu da dukkan shirin mu?
Na rantse da girman Allah duk saadda nayi arba da shi sai na cisge kansa da kaifin takobina domin bai cika musulmi na kwarai ba.
Koda ukashat ya zo nan a jawabinsa sai hawaye ya sake zubowa sarki uwaisul karni yayiwa ukashat wani irin kallo mai nuna tsantsar tausayawa sannan ya juya da sauri ya koma cikin tantinsa.
Al'amarin da yai matukar baiwa kowa mamaki kr nan domin ba a san dalilin da ya sa sarki uwaisul karni ya saka gayawa ukashat ko wane ne wannan munafuki mutum ba kuma gashi bai tsaya an gama tantance matakin da ya kamata dauka ba a yanzu akan wannan gagarumar matsala.
Cikin sanyin jiki yarima ukashat ya bi sarki uwaisul karni cikin tantinsa.
Da shigar sa ciki sai ya iske sarki uwaisul karni zaune bisa wata kujera mai tudu ya hada kai da gwiwa yana kukan bakin ciki irin na manya har ma ana jin shesshekar kukan nasa a fili.
Al'amarin da ya firgita ukashat kenan, kuma ya dugunzuma hankalinsa ainun fiye da ko yaushe, saboda bai taba ganin ranar da sarki uwaisul karni yayi kuka ba haja sai yanzu.
Cikin sauri ukashat ya karasa gaban sarki uwaisul karni ya durkusa bisa gwowinsa sannan ya kama hannunsa da hannayensa biyu suka kurawa juna idanu a lokacin da kowanne nai ke zubar da hawaye yace, ya kai abbana wai shin wane ne wannan maci amanr naka wanda har ka kasa bayyana min shi?
Ka sani cewa bani da wani makiyi a doron kasa sama da wanda ya sa bawayenka mai albarka ya zuba.
Ka gaggauta sanar da ni mi wane ne domin na tafi izuwa cikin birnin darul husuf yanzu na yanko kansa na ajiyeshi a gabanka.
Lokacin da ukashat yazo nan a zancensa sai sarki uwaisul karni ya rungumeshi kuma ya fashe da natsanaicin kuka na bakin ciki kuma ya kasa cewa komai.
Al'amarin da ya kara dagawa yarima ukashat hankali kenan, ajima ya fashe da matsanaicin kukan, sai daga can ya janye jikinsa daga cikin sarki uwaisul karni sannan ya dubeshi yace, ya kai dana hakika ba wani bane wanda ya ci amanar mu ya hada kai da makiyanmu ba face mahaifiyar ka.
Cikin tsananin mamaki da razana ukashat ya dago kai ya dubi sarki uwaisul karni. A lokacin wani zazzafan hawaye ya kara zubowa sarki uwaisul karni, sannan yace tabbas mahaifiyar ka taci amanata, kuma wannan ba komai bane face kin bin umarnin mahaifiyata, tabbas yau na kara tabbatar da cewa duk wanda ya ketare maganar manya to tabbas ba zaiga da kyauba.
Sarki uwaisul karni ya ci gaba da cewa a rayuwata idan akwai wani kuskure da nayi wanda nake nadamarsa to tabbas zai zama shine shine sabawa