bakin kofar tana zazaxxare idanuwanta waje kamar wadda taci kudin aika.
Bilti ta dada murmusa ido ta kalleta da kyau snn tace"wai me zakiyi da safen nan?kinma yi sallah kuwa?
Girgiza kanta tayi cikin zumburo baki tace
'Nifa banyi ba tukun,ince wanka zanyi kafin ya iso!.
Cikeda sakalci ta karashe mgann tana wasa da yatsun hannunta.
Tashi bilti tayi ta zauna
"Kinci kaniyarki wasimé.
Kizo nan marar kunya kawai,da sassafen nan ne zaki tashi ko gaida ubangijinki bakiyi ba zaki ce wai zakiyi wankan jiran wani saheeb?Shi saheeb din ne yace miki asubanci zaiyi.Yanzu halama yana can yana baccinsa kuma bazai karaso ba sai can wajen karfe goma...ki wuce kije kiyi alola kizo kiyi sallah.Inba haka ba babu inda zakije.
Batasan sanda tafara bubbuga kafafunta akasa ba...murya kamar mai shirin yin kuka tace
Haba bilti,haba bilti
"ÆŠan wankan ma?kaiiii bilti..warin fitsari fa nakeyi,..yanzu da kike cewa bazaizo ba inyay batan kai yay asubanci yazo faaa, basai kawai na saka sabuwar atamfata da matar Qasimu ta siya min in bishi ba?
Tsaye bilti ta miƙe sann ta capko hannayenta gameda buge mata baki
"Kewai meyasa bakida kunya?kina kirar sunayen mutane gatsau babu respect ko?uban waye kikaji yanace mata matar Qasimu?ehhh
Hannu ta dora akan fuskarta cikin muryan kuka dik tabi ta firgita
Amma bakin dai bai mutu ba"yo ni ai bansan sunanta ba..mezance mata!
Bilti ta dungureta
"Kice mata "mama" mana!Ita sa'arki ne? toh Wallh zamu saka kafar wando daya dake agidan nan inbaki shiga taitayinki ba wasime
Wani Zirrr hawayenta suka zubo kasa batace komi taja tayi shiru
Kije kiyi alwala kixo kiyi sallah,ahankli tace Toh snn ta ja kafafunta kamar mai ciwon aljanu ta shige cikin bayi ta kulle kofar da dan karfi ,kada kai bilti tayi snn ta bar wajen..sharp sharp wasime tayi alwala ta fito ta samu babu bilti
Dan haka batayi sallahn ba kawai ta shafa'a ta bude jakarta tahau fidda sabbin kayanta na dinkin sallah waje..
da akwai takalmin kwas kwas ma da jaka da aka siya mata,ita duk sanda ta debo su tana kalla sai ta dada shafasu..
Lallai matar Qasimun nan akwaita da kokari
Ai bilti tariga ta gayamata cewa itace tayi mata dinkin sallahn ta har kalaloli biyar,masu dan karan kyau.,tsadarsu ma bai dameta kamar yawansu ba.
Yatsarta ta cusa a bakinta tana ciza cikeda da tunanin zuci mai yawa
"Wayyoo Inaga yanzu tana can ƙauyensu cikin kawayenta su hansatutu da indodo da kuluwa dasu yar ficcika?,aiko da anga wankar cakarewa da caku gaye,wannan irin kaya masu hegen kyau haka?yo Kaff kauyensu tasan baza a yi mai irinsa ba,yau farinciki fall ranta..Ta shafasu ta dada shafasu fuskarta cikke da murmushin jin dadi,yau duk ta rasa wani irin ma kwalliya yakamata tayi ma fuskarta dake tana tsantsar natural beauty mai daukar hankli so bata saba da yin kwalliya ba" ..saidai fa yau din na daban ne acikin zcyarta.
Yaune ranar da zata soma ganin garin kaduna
..sosai ta zaƙu ta kuma saka komi a ranta,musmm sabawa datayi da irin labaran da saheeb yake bata akan inside town da yadda abubuwan nishadi na yara ke gudana..yau gashi Allah yay itama zata leƙa taje tagani da idanuwanta
Jin motsin bude kofa yasata firgita a firgit ta kama sallahn ƙarya kanta babu ko dankwali...
Wani galala bilti ta tsaya tana kallanta,cikin sauƙe ajiyan zuciya harta ƙaraso ta tsaya a gefenta bata hankara ba.
"Kunnenta taja saida tayi ƙara."ni zaki maida shashasha wasime?wai meye ya shiga jikinki ne yau kiketa wann haukar rawan jikin?Wato ina wasa dake ko?Toh bari inje in ƙira taheer infada masa bakyason sallah kinga sai ya hanaki fitar mai gaba daya inga ta tsiyar ko..
Wani ragab ta fado ƙasa ta kamo kafafun bilti
"Bilti dan Allah karki ƙira wancan mayen !!namiki alkwari,na rantse miki bazan ƙara ba..Nifa Yanzu zan yi sallar. wallahi kitsaya ma zaki gani..Bilti da mamaki yacikata tace"wasimé Kikace mene?waye Maye kuma?Au,maye kika ƙira taher din dashi?
.....bakinta ta kama agurguje kuma a tsorace da alaman bata masan hakan ya futa daga bakinta ba,atake tayi wani lagwas fuska kalar tausayi,kada kai kawai bilti tayi tace ehhhhh
Lallai kam,wasimé ina ganin saina farsa bakinki..duk sanda taheer ya riƙe ki wallh bana cewa komi.
Na kudine if u want to read pls Subcribe,its 300# kacal pay urs
Via *0152983148*
Mohd sule surayya
GTB
Or contact me 08060712446
7/25/22, 19:19 - Kawata: FITAR RANA 12
Bilti tana ficewa a dakin wasimé tabi ƙofar da wani irin tsoratacen kallo nannauyar ajiyar zuciya ce ta kufce mata jin ko ina ajikinta yana sacewa gabobinta duk sunyi sanyi da feelings na mummunan fargaban za'a hanata jin dadi...
Tsillin Hawayen tsoro da fargaban za'a iya rushe mata farincikinta da zumudinta na tafiya yawo tare da saheeb dinta shiya shiga cirke mata zcya,ahankli ta runtse idanuwanta snn ta fashe da wata kufulallen kuka harda shesheka.
Idanunta a rufe suke gam gam hawaye sharkaf akan kumatunta tashiga yarfa kafa da hannu cikin kuka sosai tace.."Yo nifa wallhi bansan na fadi haka ba"...yanzu sai yaji haushi na ko?dan kawai nace mishi maye yo
Inhi ba maye bane ai maganar baxata darashi ba...
kuka ta cigaba dayi cike da fargaba aranta tamkar wanda akacemata har ankai maganan kunnen taheer, ahakan da kyar ta iya kwantar da hanklinta snn taje tayi wanka.
Bayan ta shafa mai Wani zugummm tayi ta neme waje ta zauna agefen gadon su snn ta rabza wata uban tagumi.
Duk abun duniya ya isheta,haka take sumtimes tana da muguwar anxiety Allah ya zuba mata tsoron taher bakadan ba,har cikin ƙashin jikinta take jin matsanacin tsoron TEJ tasan kuma in yace bazataje koina ba tofa shikenan ya wuce mata kenan har abadaa,ga bilti ma shiru batako leko tace mata tazo tay break fast ba...tasan hala itama fushi tay da ita.
Jiki a sanyaye ta tashi,Sabbin kayantan ta hau sakawa golden atmfa wax ce mai kyau yar dubu goma kalar golden yellow an mata peplum blouse da 4pieces skirt wanda yay mata cas cas
Dan kwalin kawai ta kifa akanta bata tsayayin wani kwalliya ba, kajol dinta ta shafa da dan man baki kawai ta sauƙo.
A hankli take tafiya kamar wanda ruwa ya kwasota, Hanyar Kitchen ta nufa direct tana takawa ahankli cikin sanda yadda
Ko motsinta ba aji harta sauƙo,samu tayi bilti na waya ga tarin wanke wanke agabanta ,a gefe taja tsaya tay shiru kamar wata mareniya tana kare mata kallo.
Bilti tana kammala wayar ta juyo suka haɗe ido cikin sauri tayi saurin kauda kanta gameda mayar da idanuwanta can ƙasa ta cigaba da kallan tiles batace uffan ba. Babu yabo babu fallasa Bilti tace
"Hm wasimé harkin fito ?To ki taho kixauna acan ga abincinki akan table dama ynzu nake shirin zuwa ƙirarki kar abincinki ya huce...
Caraf ta dago kai da muryan kuka sosai cikin kukunin daya gama shake mata wuya tace"Wallhi ƙarya kikeyi"Babu ƙirana da zakizoyi.Makaryciya kawai...
A mugun raxane bilti ta aje plate din dake hannunta snn ta juyo ta kalleta sai taga kuma tana sauƙe hawaye sosai.
Æata ranta tay sosai itama cikin daka mata tsawa tace"Wasime
nice yau kuma nakoma makaryaciyan ki?Ke
Añya na taɓa dukanki kuwa?to wallh kinyi na karshe kiƙara wani rashin da'ar anan zakiga abunda zan miki maza Tattara abincinki kiɓacemin anan tunda ke bakiji.
Jikinta na bari ta karaso kan table dib dan Æata taba ganin bilti ta bata ranta har haka ba sai gaba daya abun ya É“ata tsoro,kuka takeyi awajen rungume da bangon wajen kamar wani anbugeta.
shareta bilti tay kamar bata wajen ta cigaba da wanke wankenta kamr bata sanda ita ba while a zahirance Xcuyarta cike yake da tunani kala kala akan sauyawar halayyar wasime,ita dai tasan datazo ba hakan take ba sam sam.
Bataso ta ayyana abun aranta ne kawai, amma zcyarta yana lazimin cewa a sanadin tarayyarta da saheeb ne halayyarta yake kkrin sauyawa.
Sau babu adadi tana dan lura da cewa kamr saheeb ne yake cusama wasime wasu tambadadun ra'ayoyi da manya manyan maganganu wanda baidace ace tana furtawa ba.
After like 10mins sai ga sallama a kofar kitchen din,saheeb din ne ya shigo yana mai furta "salama alaikum" tundaga bakin kofar waje
Yana murmushi
Wa alaikisalam
Bilti ta amsa da sakin fuska,but ganin har ya maida kallonsa akan wasime data kama bango tana rabza uban kuka yasata dauke kanta akansu ta cigaba da abunda ke gabanta.
Gabaki daya wasime ta susuce tayi wani fayau idanunta har sun soma haurawa sabida tsabar kukan banza..arayuwa dan tayi kuka akan komi bakomi bane,ita sam kuka baiya mata wuya shiyasa ma bata gajiya da yinshi inta fara.
..'har gabanta saheeb ya matso snn ya tsuguna yana kallonta Sheshheka mai zafi takey Tanajan numfashinta sama sama da kyar,yana kaiwa daidai tsayinta ta wani jaa ajiyar zgiya snn ta rungumesa ta saka sabon kuka mai cike da sakalci da shagwaba
Rarrashinta ya shigayi yana dan mulmula mata bayanta,kwayar idanunshi atake suka nuna alamar baiji dadin tsintar a wannan yanayi ba,Yace"toh kiyi shiru mana wai waya taɓaki ne? Bata amsashi ba ya dauketa cak ya rabata da ƙasa tare da jijjjigata snn yace "meye?...idanunta tahau mutsukawa tana share hawayen cikin zafin sheshheka tayi nuni da bilti...
Dan shiru yay yanakan jijjigata, can snn ya kalli biltin yace bilti kunyi fada da mutuniyarki ce?
Bilti Tana kan wanke wankenta batare da ta juyo ba tace mishi"..
Eh,bataji ne..rashin kunyarta yafarayin yawa.
Dan Murmushi yay snn ya Sauƙeta a kasa ya riko hannayenta anashi yana dan murzawa a memakon ya tuhumeta saiya nuna mata shima baiji dadi ba,can ya dubi biltin yace..."toh ayi mana afuwa bilti..insha Allahu bazata ƙara ba.
Suna cikin hakan saiga sassanyar sallamar taheer akansu,,a nitse ya shigo jikinshi sanye da wata dark brown jallabiya mai guntun hannu,wani mummunan haɗe rai saheeb yay ya dauƙe idanunsa akansa basuce ma junansu uffan ba kowa ya hade rai yana shan qamshi
,saheeb ya miƙe tsaye tare da tura wasime ahnkli"Beauty na Jeki kibata hakuri saita shiryaki inkin gama sai kizo kisameni a mota mutafi ko?"
..kallonshi ta dingayi tana sake boyayyr ajiyar zcya kafun ta gyada masa kai,murmushi yy ya shafa kanta baice ma kowa komi ba yasa kansa yay waje.
Taɓe baki taheer yay yana shirin dauke kansa daga bakin kofar kenan yaji dirar tsiririyar muryanta a raƙube a gefenshi ta tsaya kusa da inda yake,cike da tsoronsa ayanayinta tace..."Ina kwana? kanta na kallan ƙasa..shiru yy abunshi,ya dade yana kallonta kamar wanda ya mance wani abu ajikinta can snn ya amsa gaisuwar ciki ciki snn ya wuce gaba ya samu bilti
A hkli,kuma a cikin nitsuwa yace
Bilti,juyowa tayi ta kallesa sai suka haɗe ido kowannen su yana sakar murmushi,ajyar zcya taga ya sauƙe snn yace
"pls can u see me in my room before i leave!da akwai abunda nakeso mudan tattauna akai ne nd ive got jist 30 mint to get ready..
Dan murmushi tay
Sannan tace insha Allah
Zanzo.Baice uffan ba yay nodding head dinsa snn ya juya ya fita tare da haurawa sama can dakinsa cikin gaggawa.
Wasimé data gama kallonsu har suka kammala maganan su taga babu wanda ya kulata wani shiru tayi ganin bilti ta bala'in shareta batace mata uffan ba haryanzu.
Cikin rasa nayi da tunani irinna yara ta juya ta tafi daki batare da tabada hkrin ba,tana shiga gaban madubi ta soma nufa ta caɓa dan karamin kwalliyarta ta kammala sako kayanta tsaf snn ta fito..balaifi tay kyau abunta.
Ahnkli take tafiya tana waige waige sabida fargaban datakeji acikin ranta sosai,koda ta sauƙo saida tayi tsayuwar mintina biyar abakin ƙofar kitchen manne da bango cikin rasa abunyi,duk tinaninta yadda zata soma budan baki tabawa bilti hakuri.
Aganinta Itafa simple magana tafada batasan abun zaikai har haka ba.
Daga ce mata tay ƙarya shine zata hau dokin zuciya..kai biltin nan akwaita da fadin rai..kai duka yan binni ma haka suke..abu kadan kayi saisuyi ta fushi dakai.
Maganganun zuci shaff ya ciƙe zcyarta har bilti ta kammala ayyukanta ta fito zata wajen Tej, taci karo da wasime a wajen a rakuɓe wadda batama hankara da isowarta ba tsabar tayi nisan nitso acikin tunani...
Kai kawai bilti ta girgza bayan ta gama kallanta
Tabi ta haÉ—e rai batare da ta tsaya ba.tana tafiyarta cikin nitsuwa tace "ke kuma me kikeyi anan? Bajiranki yakeyi awaje ba...
A firgit ta farfado daga tafken tunanin data fada cikin i i na ta shiga cewa
.."Em..emm..innmm..
Dama..dama...sai kuma
Tayi shiru....take idanunta suka cikka da ruwa,muryanta yaa sauya launi ixuwa na nadaman abunda tayi"..
Gani tay bilti zata wuce acikin rashin kulawa da yanaayinta a hanzarce Tayi sauri taje ta rungomota ta baya ta manne da ita
Wani Sassanyar kuka ta saki tanamai runtse idanunta sosai wanda ya saka biltin jin gwiwonta suna kakkabewa a lokaci guda jikinta saiyay sanyi
cikin shashheka mai zafi tace"Toh kiyi hkri mana"..
Ainasan fushi kikay kika fita a dakin kuma ƙi kirana inzo inci abinci saida nazo zaki wani cemin ga abinci
yo ai Wanke wanken ma duk kin kama kinayi sabida yau duk kintsane ni...
Jawota bilti tayi ta gabanta tahau share mata hawayenta cikin sauƙe ajiyar xuciya,batare da ta sake fuskanta ba tace 'toh naji ynzu kibar wann kukan kije yawon sallanki kidawo tukuna zamuyi magana saiki gayamin matsakarki, kinga ynzu taher yana nan kar ya zo ya riskemu anan da wannan maganan,
aikinsan dukan tsiya kawai zaimiki inyaji kina fetsa rashin kunya.."..mai bakin cema babba makaryaciya kawai oya maza jeki.
Da dan wasa tay mata maganan ynzu,wanda hakan yasaka ta sake ranta kadan snn tace
"to ai hikenan zanje din,hee mun dawo.
shafa kanta bilti tay babu yabo babu fallasa snn tace to maza a kula.
Ina fatan baki manta ababen dana fada miki jiya ba? Tinkan ta gyada kai bilti ta ja kunnuwanta
"Wasime ki girmama babba, banda taɓe taben kayan mutane,bana son kwadayi,banda yawan kallo sann inba ai dake ba karki sake ki tsoma musu baki acikin zancen su.
Asshhhh toh naji bilti
Saina dawo..
Daga nan sukayi sallama ta fita ta same saheeb a mota,bilti kuma ta haura sama dakin taheer domin amsa kirarsa
******
A hankli take kwankwasa kofar tsawon mintina bataji an amsa ba,sai can daga baya kafun talura ta gane cewa kofar a bude take"dan turawa kadan tayi ta leka ciji
Da mamaki ta ci karo dashi cikin wani irin zulmammen yanayin ziriya shikadai yana jeka ka dawo da alama ransa ya dagule sosai da tunani
Wajen windownsa ya kara nufa ya yaye curtain din yana leƙawa kadan kadan,daga ganin hakan bilti ta dagoshi,hala fitarsu wasimé ne bai masa ba..dan tabe baki tayi batare da ta kara tunanin wani abu ba tay gyaran murya snn ya juyo a farge.
"Bilti!...
Yana hade ido da ita ya ambace sunanta adan razane da alaman baisan da shigowarta ba.
Da yanayin damuwa a fusknta tace
"Taheer lpya kuwa?
Ko akwai wata matsala ce
Dakewa yay atake yana kkrin basarwa,
yace"Lapiya kalau me kika gani"?batace mishi uffan ba,shima sai ya share zancen yace Taho ki zauna gaba yy ya zauna abakin gadonsa ita kuma yabar mata kan kujera
Babu musu bilti ta isa wajen ta samu zama acikin yanayina nitsuwa,sasanyar idanuwanta ta zuba akanshi da alaman tana sauraran sa.
Boyayyar ajiyar zcya ya sauke gameda sauke gwauron numfashi.
Batare da bata lokaci ba ya Miƙe ya nufi gaban table dinsa ya doko wasu files ya mika mata snn ya soma dora mata da bayanai batara dajin ko dardar acikin ransa ba
"Bilti tamkar uwa ta biyu ce agareshi zai iya cewa ma ita tarbiyantar dashi dan tun usuli yafi samun lokcinta fiye dana asalin mahaifyarsa.
Atakaice dai tafiya ne na dan kwana biyu ta kamasa, duk dama bai tabbatar da cewa iya kwanakin da aka kayyada masa akan zai gama ayyukan ya dawo ba kenan.
Tafiyar ta gaggawace data zame su dole suyishi dan oder ne daga babban offishin babban jami'i mai kulawa dasu,taheer is one of the best medical student nd a brave soldier kusan kowa na son hada harkokinsa da shi sabida sam shi babu ruwansa da shirme careernsa kawai yake chasing and nothing more to add to that.
Cike da kulawa bilti tay masa adduar fatan samun nasara da kuma rokon Allah ya dawo dashi akan lokaci.
"Bilti nasan basai na fada miki ba amma dan Allah ki dada kulawa da gidan nan...bana son inji ance wasu sunzo bana nan.
Tace karka damu zam kula, shiru yy...can snn ya sace kallon windown yana dauƙe idanuwan su sukayi karo da na bilti wani Kunya yaji ta lullubeshi.
Murmushin manya ta saki aranta
"Taheer dama kunyi magana da saheeb akan lokacin da zai dawo da wasime ne?
Kansa ya dago sama kamar dama jira yake a sako topic din snn ya cabe,bayabo ba fallasa yace yes"5 mukayi da shi akan zasu dawo"idan bai dawo alokcin ba ki kirasa ko ki aiki tolu yaje har gidansu yace nina aikosa .
Bilti tace toh insha Allah zasu ma dawo akan lokci.Da akwai wani abune bayan haka?
Aranshi yanata so ya bada dokar cewa kar abar wasime ta kara fita da saheeb amma baisan yadda xai saka kalman ba.
"Kudade kawai ya ciro ajikinshi yan dubu dubu guda goma bai ma kirga su ba ya damka ma bilti a hannu..a ladabce yace
Gashi inda wani abunda zaku bukata.
Amsa tayi cikin godiya tare da fahimtar duk wani saƙon dake boye acikin kwayar idanunshi musamman ma game da wasime...
Sallama sukayi tafita snn shikuma ya cigaba da kammala shirinsa ƙarfe 11:30am ya nufi offishin ogansa inda zasu tashi tare da motocin tawagar yin tafiyarsun....
Access fee is 300 via
0152983148 mohd sule surayya Gtb. 08060712446
7/25/22, 19:19 - Kawata: FITAR RANA 13
A fannin su wasimé kuwa tunda ta zamu shiga cikin hadaddiyar hummer jeep din saheeb ta ƙasa aje duwaiwakanta waje guda
Tayi juyi nan tayi juyi can
Komi ma acikin motar ya gama tafiya da imaninta dan kuwa bata taɓa tunanin zata shiga irin wannan babban motar ba.
Shikuwa saheeb baƙaramin dadi yakeji ganinta a kusa dashi ba dan komi nata na burgeshi hatta kayan data saka yau saida yaji aransa inama ace ƙanwarsa ce ita da yanajin duk fadin duniya babu wanda zai kaita gaye da kwalliya da kuma saka tsadaddun kaya..ko ayanzun ma ya qudira aransa cewa he might sumhow take responsibility of her needs,fitinar taheer ne kawai bai shirya fuskanta yanzu ba dan sosai yasan abokin nasa da iya nuna iko akan iyakarsa.
10:40am dot suka iso bakin kofar gate din wani katafaren gida mai tsayin gatanga da babban gate da aka ƙawatashi sosai da bishiyoyin ƙawata muhalli da kuma furanni.
wannan shine babban guest house din da mahaifinshi ya mallaka masa acikin Wata kerarriyar estate da ake cewa millenium zone B inda ma bakasafai zakaga middle class anan ba duk dai gidajen masu hannu da shuni ne a layin irinsu.
security ne baja baja a bakin kofar gidan wanda suna ganin dosowar motarsa suka tashi tsaye suka tsatsaya,ganin mutane tsatsaye da bindigogi yasaka wasime ta koma kan seat dinta taxauna a hnkli snn ta nitsu ta cigaba da kalle kalle.
Gate daddaya daddaya har sau uku aka bude musu kafin suka iske asalin harabar main house din Komi na gidan bugun girma ne masha Allah baki a bude wasime take lekowa da fuskrta waje zcyarta kamar zai diro yay tsalle waje tsabar mamakin datakeji acikin aranta,gani tay kamar wani aljanan duniya aka kawota,ganin ababen duniya da idanuwanta basu taɓa cin karo da shi ba hakan yasa taji kamar ta zauce dan murna, kallan sa tay da wasashen hakwara.
Snn Tace"Nan ne gidan naku?Yana murmushi yace "eh mana...toh sauƙo muje ciki.
batagama rufe baki ba taga harya bude side dinshi ya fito yayo ta side dinta,Bude mata kofar motar yy snn ya riƙo hannayenta tare da taimaka mata ahankli harta samu ta sauƙa, idanuwanta ta gwalo waje cikin tsananin rudewar girma da kyaun muhallin,a yanayin kauyanci da yarinta Tace
"Wayyo Allah na..
Ji katoton gida.....
Ahe anan kake zama yo shiyasa mana bakason daÉ—ewa a gidanmu
Dariya ne ya kufce masa ganin yadda tayi maganan with so much ignorant sai kalle kalle takeyi abunta, jawo hannunta yy suka nufi ciki.
A bakin kofar wani katafaren palo suka tsaya snn ya danna door bell, after like 4mints mai aiki tafito sanye da blue uniform tazo ta bude mai kofa tana dan murmushi,"ure welcome sir.Babu yabo babu fallasa yace "thank u susan."Cikin sauri wasime tace ma mai aikin ina kwana anty?Murmishi mai aikin tay saidai Kafunta amsa saheeb ya wani hade ransa tare da cewa wasime"wayace miki ki gaisheta toh? ido kawai ta tsura masa cikin rasa mezatace tuno da cewa bilti ta gargade ta akan ta rika gaishe da babba...
Yace "wann Mai aiki nace u dont have to greet her kinji?..ai itace zata gaishe ki bake zaki gaisheta ba.."da wutsiyar ido wasime ta dan sace kallon mai aikin ganin ta babba wuce sa'arta,abun saiya kuma dore mata kai yo shawarar wa zataji kenan na bilti ne kona saheeb?,mai aikin bataji dadin hakan dayay ba amma tasan bata isa ta nuna ba, murmushi tay ta gaida wasimen kawai ta wuce ta tafi tabarsu a tsaye awajen.
"Beauty Karki ƙara gaishe da kowa saina umarce ki
Kanta ta gyada mishi a hankl hade da binshi cikin wata ƙerarrayiyar royal falo daya shige dasu ciki mai niimtaccen sanyin A.c da kuma dadin turarrukan wuta masu sanyin qamshi tana biye dashi abaya har suka iske gaban wasu lumtsa lumtsan cushions milk colour da gold wanda girman su da yawansu kawai yakai acike manyan faluka uku harma ayi ƙari dasu,ga wani babban tv plasma mai girman iya dungu to dungu.
Akan daya daga ckin lumtsatsun kujerar ya dorata ta zauna,"snn ya zauna agefenta yana mai kallon cikin kwayar idanunta dasuke matukar kawatar dashi cikin wani sanyin yanayi mai rikitarwa.
Shikadai yabarwa kansa sirrin irin tunanin da zucyarsa takeyi akan wasime..danji yake kamar asalin itace matarsa in the future!
Har wani Imagining yakeyi inda ace wasime fara sol ce toh da tuni baki da idanun mutane sun kasheta har lahira,ahaka ma gani yake kamar bakar fatan da Allah ya bata ne kawai yake dan protecting dinta daga samun too much attention na mutane.
Ya dade yana kallonta ayayinda taji kirjinta na bugawa da dan karfi sabida fargaba da kuma nauyin idanunshi daya zubosu duka acikin nata yana mata wani irin mayyar kallo..a dan takure cikin sanyin murya tace.."Yaa s..aheeb..saheeb
Baisamu damar amsawa ba ya lumshe idanunsa yanajin sautin muryanta har cikin zcyarshi da duka ilahirin jikinshi
Muryanta a sarkafe tace "uhm uhmm to ina su innarkan suke ne?..
Kace...Gefen fuskarta ya shafa cikin katse mata sauran maganan snn yy dan murmushi muryansa kasa kasa kamr maijin bacci yace" hey relax they are coming okay?
So nake kidan zauna dani
Dada Mikewa zaune yay yana kallonta tay saurin sauke kanta can kasa bata ƙara dagowa ba.
,ko inje in dauko miki su ne?..da sauri ta dago kanta ayanayin fargaba "tace eh
Mikewa tsaye yy
"Zaki iya zama anan ke kadai kijirani?.kafun ta amsa harya rusuno kasa agabanta cikin marairace fuska..."i dont wanna leave u alone cuty, wani jawota jikinshi yy game da kwantar da ita akan faffadan kirjinshi kamshin turarensa duk ya cika mata hanyar fitar numfashi,a hnkli ya shiga shafa bayanta cikin wani irin yanayn nuna so da shakuwa,matseta yy gam ajikinshi yana catching breath dinsa haka ya dinga cuddling nata akan kirjinshin har jikinta yay sanyi..wani lumui fuskanta yy tana famar zazzare idanunta waje
Nannauyar Ajiyar zcya kawai ta dinga sauƙewa
Tanajin wani bambabra kwai,haka kawai ta soma jin tsoro tsoronsa acikin ranta kkri takey domin ta kwace kanta ajikinshi saiga sautukan takun takalmi bana mutum daya ba,numfashi taja hade dayin kasa kasa da idanuwanta ayayinda saheeb din ya maida kallonsa inda sautin takalman ke fitowa.
Jim kadan Wasu zugan yara yara da yan mata guda biyu suka bayyana
Yara yaran sukayo kanshi da gudu cikin murnan ganinshi" yeeyyyyyyyyyy
He is back...da faraa sosai akan fuskrsa ya tarbesu suma wasu su dale bayansa wasu suna cakulinshi dariya yakeyi sosai"..
Yan mata biyun suka tsaya kikam agefe kamar yadda wasime ta ɓata shiru awajen,dukansu kallanta suka tsaya yi barin ma budurwansa zee baby da bata gane waye wasimen ba.
Dayar kuma ƙanwarsa ce anisa dayake mutuwar kauna arayuwansa,anisa tana kama da saheeb sosai dan haka takeda kyaun fuska itama na daidai misali,wani hadadden off shulder pink flowery gown ta saka na kamfanin milano da pink glittery cover shoes na prada maidan tudu kanta yasha gyara da gel dan bata dora masa dankwali ba, but still she look bit older than her real age saboda tanada jikin girma sosai.
Zee budurwnsa data kasa hkri tace
"Babe waye kuma wannan?daga ina kasamo ta..hmm sannu sarkin kwashe kwashe
Tunkafin ya amsa tambayar zee din, anisa ta isaga wasimé,
agabanta ta durkusa Ahnkli tana mai dago kanta sama, hade ido sukay snn shiru yabiyo baya, dan shiru anisa tay snn ta canko abun tace "wow,Wasimé right?..
kece wasimen da yaa yake ban labari?
A dan rude wasime ta gyada kanta jin ankira sunanta,cike da sakin fuska anisa ta juya ta kalli saheeb snn tace..
"wowww bro she is soo cute...melanin goddess..gaskiyane yau na yarda dakai akwai bakake kyaywawa a duniya, comn check this girl out.arrghhh she is damnn...dariya sosai
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 15