Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
da tsawa yanxu hakama saida bilti takaita asibiti daga can muke Ya subhanallah,"...yaa mata wani abu ko?Alhj ya tambya cikin son ya sani fuskansa a dame. Kai tsaye tace eh tsawa ya daka mata yarinyar ta suma.But doc told me its bcos she is asthmatic tanada matsalar fitar numfashi,Wai tsawar da ya daka mata ne yasa numfashinta ya dauƙe Yanzu haka cemishi nakeyi kawai ya sassauta mata sannn ya kula kar yarinyar ta kasa zama damu bayan ita amanace agare mu kuma surkuwarmu ce fa Dan dariya tayi Alhjn shima yana dariya yace Yes of couse!! ure right amma yaji ki da kyau ko? Ajiyar zcy ta sauƙe "Eh to amma....yace kawai kyale maganan ni zanji dashi muje kawai inga yanayin jikin yarinyar... daga nan suka Dunguma. sama sukayi suka samu har bilti ta rarrasheta ta samu ta zauna ƙusa da ita a rakube tayi shiru sai hawayen dake sauƙa akan kuncinta ahankli suna zubowa Tanajin motsin ɓude kofar ta tashi tsaye da dan banzan sauri tay baya zata gudu Ta boye abayan bilti,a nitse bilti ta riƙo ta ta zaunar da ita agefenta,tana cewa dawonan ina kuma zakije... sallama su alhj sukayi yanata kallon yadda ta zauna a takure kanta na jikin bilti,duk tsorone fall cike acikin zcyrta,zama matarsa tayi kusa da ita daf tana mata murmushi mai sanyi,kanta ta shafa ahankli "mama na karkiji tsoronmu kinji?My little Ozoza,shafa kyakkwan fuskarta tayi..with sincere adoration tace 'ure a beautiful girl did u knw dat?darling kaganta fa..chokolate goddess ..kyawawa aibasa kuka ,toh me kike so inje a siyo miki..zaki sha alawa mai dadin tsiyan nan ko?wani sabuwar kuka mai sanyi wasimé ta sakar mata tare da girgiza kanta sideways cikin sanyin yanayi da alaman batason komi .."alhj Qasimu ya tsuguna agabanta cikin sassauto da muryan sa ƙasa shima"toh me kike so a kawo miki ƴata?kifadamin koma miyene Ni Zan kawo miki..kanta ta kife tsaknkanun cinyarta ta sake kukan datake dannewa dagaske gwanin ban tausayi, cikin shehsheka mai zafi tace"Nide ka kaini wajen innono na dan Allah.. murmushi yy iya abunda kike so kenan?Cikin kukan ta gyada kanta da sauri tanajan majina.matarshi ce ta matso kusa daf da ita shima tashi yy ya zauna daf da ita yanamai dage kanta dakansa har sanda suka hade idanunsu waje guda dashi"kallonta ya shigayi itama tana kallansa,idanunta duj sunyi jajur tsoro duk ya kama zcyrta sosai ya nakasata.sosai tausayin ta ya kama zcyarshi, muryansa dauƙe da salon lallami wanda ya fi na da yace "kinaji ko?kwarjinin sa yasa ta gyada kanta a ladabce Yace"nida kaina zan kaiki Wajen Anono inhar zakiyi duk abunda zamu ce kiyi agidan nan...Ga matata nan,ga kuma bilti akwai ɗana dahiru agidan nan karkiji tsoronsa,shi yawan kukane kawai bayaso amma yanada dadin zama zaki saba dashi sosai,kedai kizauna da mu kiyi musu biyayya..musamman ma dahiru..nikuma sai inga ko kincancaci in kaiki wajen anononki!! shiru tay kamar bata fahimce shi ba sabida magana yay mata a nitse kamar yana magana da wata babba wacce ta mallaki hanklin kanta.Haka ma matarsa ta sako baki tana mai ƙara lallabarta hardai ta samu nitsuwar zuci sosai tayi shiruu tanajinsu sosai da sosai ,sun dade a dakin suna kkrin shawo kanta tazauna din ,maganganunsu kuwa sosai yy tasiri a zcyrta halinka da yaro tadauka dagsken suke intayi abunda sukace din dagske zasu kaita wajen anono,daga nan bata ƙara wani fitina ba. Fannin tej kuwa tunda ya shiga dakinsa ya sauƙa akan tebirin karatunsa yama manta da cewa wani abu ya afku dazu,halayyarsa ne shashantar da abu cikin sauƙi,he is so self absorbed nd discplined in harkan gabansa ya taso mai kusan mancewa da komi yakeyi a duniyar nan shiyasa zakaga kamar babu abunda yake iya shiga ransa bare ya damesa. A ranar bai fito ba sai washe gari da sassafe,7am ya dawo daga wajen motsa jiki ya samu kowa ya hallara wajen abun ƙari kamar yadda aka saba hanklinsa ne ya kwanta sosai da baiga wasime anan din ba,waje ya samu ya durkusa adan gefe ya gaida iyayensa cikin ladabi da biyayya sannan ya haura sama yakimtsa kansa ya dawo cikin shigarsa ta kananan kaya,a nitse yanemi seat ya zauna ya fara cin abinsa kominsa a nitse faten wake ne da miyan dage dage na manyan manyan kifin tuna,iyayensa dake zaune awajen basu wani takuramai da wani magana ba harsaida suka tabbata yaci abincinsa ya koshi. hamdala yy zai miƙe tsaye kenan mahaifinshi yay gyaran murya snn ya kirawo sa. dawowa falon yy ya nufi inda suke zaune ya same su duk dama Tafiya yake kamar baxai karaso ba dan yanajin ance "son i want to talk to you"..yasan doguwar nasihace ke jiransa, atake yaji kamar ciwon kai yakamasa. fuskansa adan takune ya zauna dan yagama sanin akan meye ne za'a yi maganan bai wuce akan wacan yarinyar ba da baison fitinarta.. idanunshi a kankance ya zauna tare da nitsewa, kansa na ƙasa can dan ma karsu fahimce rashin intrest dinsa akan topic din,as xpected nasiha iyayen nasa suka dinga masa akan yabi wasimé ahankli yarinyace,wani bin saiyaji kamar ma wasiyya ake bashi akanta,shidai tunda suka fara maganan su yana shiru yana sauraran su bai tanka ba har suka kammala snn yace musu yaji,daga nan yay musu sallama ya tashi ya fita. Haka rayuwar tasu ta kasance harna tsawon kwanaki goma amma babu abunda ya sauya a fannin wasimé don sosai ta kasance acikin yanayin zazzabi da damuwar da ta cusa ma ranta da tsoran taher datakeyi..ji take kamr komi ya cirke mata musammn shegen sanyin a c wanda bawai ta saba da shi bane inyana kadata cikin bacci sai taji ta daban wanda hakan yasaka tafiye yin fitsarin kwance,kullum ta farka ta dinga rakube rakube kenan tana bobboye jikinta dan kunya,gashi ba su fara barinta tanayin komi ba,bilti ne take tsaftace ta fes.kusan ako wani rana zatayi mata wanka ta wanke mata kayan datayi fitsarin ta shanya su a rana,ahankli har wasimé ta zo ta fara samun sauƙin jikinta., saidai tsoron taheer shaf yanahata motsawa daga cikin dakin kullum tana kumshe kamar wata amarya,haryau gani take kamar inta fito zata ci karo da shi wanda a yanzu bata sani ba shi harkan karatunsa kawai yakeyi. kwance tashe ba wuya bayan wata guda wasime ta fara sabawa da bilti ta kuma soma sake ranta da kadan kadan tana dan saukowa tana biyota su fito har kitchen tana tsaye agefe haka har bilti zata kammala ayyukanta subi su dawo daki tare. Yau asabar antashi da haddari sosai,karfe 6 saura wasimé ta farka a bacci duk ta jiƙe jikinta da fitsari,kamar zata saki kuka take kallon sket dinta, Ganin bilti bata shigo ba yasata saurin dirowa ƙasa cikin sauri ta wuce bathrum ta cire kayan jikintan duka snn ta dora sabon zaninta a kirji.,dauko bucket tayi da omo ta tattaro kayan datayi fitsarin bata tsaya koina ba sai bakin famfo dake can waje,lokcin koina shiru babu wani mahaluki a tsakar gidan. a hnkli take takawa tamkar wacce bataso aji karar sautin tafiyarta harta isa bakin famfo,aje bucket din tay da sauri abakin tap din sann ta kunna ruwa ya fara zuba shaaaa ta tara acikin bokiti,dan kadan ta saka omo acikin ruwan sann ta kada yay kumfa sosai,a nitse take tsoma kayan tana shafawa a hankli saida tafi awa abakin wajen tana abu guda,wani motsi ta faraji ata bayanta,haka kawai taji ta raxana da motsin duk tsoronta gamuwarta da taher ne,cikin sauri ta tsane hannunta tana dago kanta kuwa sukayi ido hudu da tolu. ajiyar zcyane ya kufce mata as usual tagansa ne ayayin da yake sanda tare da wata yarinyar daya kwana da ita a dakinsa. baida kunya sai famar shafa kugunta yakeyi yana lallashe bakinsa ,halinka da yaro wasime sai ta zuba musu ido tana ta kallonsu bata dauƙe kanta akansu ba har suka bace ma ganinta"yarinyar ce ta soma hankara ta nuna ma tolu wasime..yana kallonta tana kallonshi ,acikin sauri tolu ya tura yarinyar waje ya rufe kofar gidan snn ya dawo ciki cikin gaggawa,bakin famfon ya nufa inda wasimen take durkufe tana shafa kayanta dan tsawon lokacin nan bata taɓa magana da ma'aikatan gidan ba sabida tsokanrta da sukeyi sonyi akan yawan kukan datayi farkon xuwanta.. ya dade akanta yana tsaye amma kota kulasa,sai juye juye take duk yarasa yadda zai tambayeta yaji kota fahimce abunda ta gani ynzu,tsoronsa karfa ta je ta tona masa asiri,ta gabanta ya dawo inda zai kalle fuskarta da kyau, tsantsar kyaun halittar fatarta ne ya soma dauke masa hankli haƙika shi kansa Bai taɓa ganin baƙin fata mai kyau irin na wasime ba,babu dandanin tabo ajikinta gashi sai sheƙi fuskarta yakeyi, gyaran murya yy da ascent dinsu na yarbawa yace"Iya rigimou,.tanajinshi ta basar sanda taja masa aji can snn ta Dago kai ta wani kallesa.."washe bakinsa taga yanayi yace.."kai yarinya meya kawoka nan wajen dis hearly morning,bilti nko?..bata wani fahimce mai yace ba dai ta dauke kanta snn ta amsashi 'Nima bansani ba wanki nakeyi"snn tacigaba da abunda takeyi. Durkusawa yasoyi agabanta yaga tayi maza tabar wankin ta miƙe tsaye tana hararsa "nika tafi wanki fa nakeyi"..da kallo yabita snn ya miƙe tsayen shima yana mamkinta aransa yace Ashe tana magana har haka? "Take ya sa sigar wasa ayanayin sa"ahhh ahh now..comon.. we r friends now..nidakai abokin junane yana fada yana dariya,batako motsa ba ta dada gyara zaman dorin zaninta ta yamutsa fuskarta. "Ina da kawaye sose,she bi u see one of them ba?ko bakigan kawata ba..yanzin nan tafita woje..yanayi yana nuna bakin gate da yatsarsa kamar Solubiyu. ,inda yatsar yy pointing ta duba snn ta murguda bakinta ahnkli tana turo bakinta gaba,tace ni banga kowa ba kuma niba kawarka bace. Tsaye ya miƙe cikin rada Yace Okay naa, tunda kai ba kawata ba ne dont tell anybody say u see my friend een kinji?..karki ce ma bilti komi kinaji ko? shiru tayi tanamai zubamai idanu,suna cikin haka saiga kwarfkwaf ƙarar tofar da khaki dagata kofar malam musa mai gadi,daga can ya wara idanunshi daya kallesu ganin wasime a tsaye a gaban tolu da dorin kirji,a hujajan yace kaiiiiiii Menake gani haka? Share pls Na kudine Its 300# please subcribe via *0152983148* Mohd surayya sule GTB,nd send ur evidence to 08060712446 Or mtn Pin. 7/25/22, 19:19 - Kawata: *FITAR RANA...* _......faduwarsa_ BISMILLAHIRRAHMANIRAHEEM. No 7 Da uban sauri malam musa ya doshi hanyar bakin famfon yanamai kwallara ma tolu ƙira kamar wnda ya kama barawon daya dade yana nema,wajen da suke tsaye ya dosa yana jefa kafafunsa cikin gaggawa tamkar wani babban almari ya hasasho. tunkafun ya tsaya yafara azazzala wa wasimé masifa yana cewa: "ke yar bilti me kikeyi anan?maza wuce kiyi gida, ahhhhhh kagane mini shashashar ƴa.wani rau rau da idanunta tayi kamar wacce zata fashe mishi da kuka ta zumburo ƙaramin bakinta gaba jin yace mata shashasha aranta kanbu?"bzaki wuce kiyi gida ba..adan tsomare ta tsaya snn ta amsa "nifa wanki nakeyi ai bangama ba.Cikin yanayin tsawa da hantara Malam musa yace"Ke yimin shiru awajen wani wanki ke kika iya?,ki wuce ki bar nan wajen nacemiki. na tabbata bilti batada masaniya akan fitowarki, ahaka ne ake wankin kinfito ba kaya ajikinki..? kallon kanta ta shigayi jin yace babu kaya ajikinta bacin ga zani ta dora a kirjinta wani tsaki taja acikin zcyarta ta zumburo bakinta ta haɗe ranta sosai,ganin ya zare mata ido taja tay tsinin baki,batace uffan ba cike da saiɓi ta dauki bokitinta da sauran kayanta ta barsu a wajen suna tsaye suna kallonta harta bace maganin su..," Tolu daya tsaya galala yana kallon musa cikin yanayin mamaki yace .."musa!na why u kon dey shout ontop dis small girl metayi maka?Tolu ya tambayeshi a mamakance. malam musa dake tuƙa masa wani tuwon harara bai tsaya amsa shi ba ya shiga nunasa da yar yatsa ransa a mugun bace sabida a duniya babu wanda malam musa yake bala'in dreaming samu arayuwarshi kamar bilti,ya ɗade yana kaunarta acikin zcyarsa amma haryau babu wanda ya fahimce shi sabida ko a ido bilti ba sa'arsa bane bare ma a shekaru.. Iya inda zaka ganosa Daga zaran Abu ya shafi bilti sai kaga ransa ya harzuka ya baci,hararar tolu yakeyi kamar zai haɗiyeshi,yace "Kai wallhy ka shiga taitayinka..katon banza katon wofi kawai.. kai mai kakeyi anan din? tolu zaiyi magana ya datse sa da wani irin kallon baraxana ...tolu zaka fara halin naka ko? girgiza kai tolu yay cikin dago abunda musa yake nufi snn yaja wata doguwar sautin ohhhhhh ya dora hannu a kugu Hararsa shima yay,snn ya soma cewa "musa "musa, musa,wato saboda kamaida ni dan iska,harni zaka..so u think i came to toast dis cunkuli girl.?u dey mad? U no dey reason..oloshi Kaci ubanka.. malam musa bai kyalesa ya karasa zagin ba yace"Eh mana,zuwa kayi ka ruɗeta danta soma shiga dakinki,yo me za'a fasa wai kunu awani gida.. tolu waye baisanka ba, har kananan yara irinta kana kwamushe su da jarabarka hakane ko ba haka ba?ka amsa ni jarababbe! "tsabar haushi tolu bai tsaya amsawar ba yakai hannu zai doke hancinsa da sauri malam musa yaja da baya .yana huci yace "Sai nace maka abunda ya kawoni nan kenan? cike da izgilanci malam musa ya amsa"..i dontu kiya wat bring u por hiya...toh dai ahir dinka da yarnan...Wannan tafi karfinka ta gidace wallahy kayarda naga kadorata akan cinyarka ko kana matseta nida kaina saina tona maka asiri! duk abunda kake aikatawa agidan nan saina fadawa oga taheer. Wani ihu tolu yasaka game da dora hannunsa akansa.."Ah ahhh now musa haba!!Wannan wani irin wasa ne kake yimini haka aah ahh na, Kaima kasan bana son wannan yarinya..i no wan toast her na cry cry girl she bi..inda kaganni anan akwei babban dalili daya kawoni..,hannunshi ya kama sigar lallami ya soma jansa suka nufi ta bakin gate Yana cewa..'u seee baa Inkanaso infada maka guluma kazo muje room dina,i sweara gwad I get shicken nd juice for u i knw say my man go chop am she bi?... wara idanu malam musa yay jin ance kaza tuni miyau dinsa ya kawo, da gaske kakeyi akwai kaza da jus dakinka?wani hamma ya doka tunkan ma tolu ya amsa,dan malam musa baƙaramin maitar kwadayi Allah ya zuba masa ba ,shi weak point dinsa kenan kahadasa da kayan kwamulashe shiyasa tunda tolu yagane hakan ya samu lakarsa yana sheƙe ayarsa da yanmata son ransa agidan..haka suka wuce dakin tare sunata surutai sauran kazar dayay amfani dashi ya lallabi yarinyarsa jiya ya bawa musa badon yaso ba musa kuwa yazauna ya cinye tasssss yabar masa ledar awajen yay gaba. Kafin nan suna cikin daki wasime ta salalo cikin sanda ta cigaba da wankinta,daga cikin gida kuwa har bakwai shaura snn bilti ta shigo dakinta dubata,da bata ganta ba yasata yiyuwa waje cikin sauri.tasan dai babu inda wasime take iya zuwa acikin gidan sabida tsoron taheer Hangenta datayi Tana durƙufe agaban tap tana ta shafa kayanta sai abun ya bata mamaki,cikin sauri ta ƙaraso har ta tsaya akanta bata hanƙara ba sabida zuciyarta yay nitso sosai acikin tunanin kawayenta na kauye. "Wasime mekikeyi anan? Barin wankin tay ta juyo adan razane,ganin bilti yasata sauke ajiyan zcya Har ƙasa ta rusuna cike da biyayya tace "ina kwana bilti?amshe bokitin da kayan dake hannunta bilti tay snn tace lpya lau tanayi tana dan dudduba kayan adabarance, taga dai ba laifi sun dan fita,kanta na can ƙasa.. bilti ta dubeta tace"ke kikayi wankin ne?a hnkli ta gyada kai snn tace eh..amma dai kinsan bakida lpya kika fito nan sassafe kina taba ruwa ko? ashe dai bakiso akaiki wajen anononki"...da sauri ta dago kanta ta kalli biltin cikin langwabe wuya,tace "ahhh inaso...dama ai ita tacemin ina yin aikina kuma naga acan kauyen mu ina yin wanki.. ki duba aina iya ko..shine nace...bilti ta ce to ya isa haka abar labarin muje ciki kawai gashi duk kin jike jikinki..batayi musu ba ta wuce ciki bilti ta nufi inda clothline yake ta karasa shanya mata kayan sann ta shigo gidan itama samunta tay harta cire jikakken zanin jikinta ta ratayasa ajikin kofa da daga ita sai yar panties dinta tana zaune abakin gado,bathrum bilti ta shiga sann ta dauko dan karamin towel daidai size dinta ta bata dakanta ta dorashi a kirjinta. Hakama wajen wanka taganta da axamanta tana tayata yin komi Da wasa wasa kwana biyun nan bilti ta soma fahimtar cewa da akwai home traininig sosai ajikin wasimé duk da kasancewarta yar karama amma da alama ta iya abubuwa dakanta. Fahimtar hakan yasa ta fara kyaleta da wasu abubuwan kamar share room dinta,dan wanke wanken da yay shaura saita bata ta wanke hartazo ta soma sabawa sosai wani abunma basai angaya mata ba. Agidan bilti became her best friend nd mother Dashike bakasafai ake cin karo da Alhj qasimu da matarsa ba,bare ma ajega dansu dahiru dayanzu baiyason ma shigowa gidan sai can cikin dare,he is alwys occupy da karatunshi. Rayuwarshi Daga school sai hospital barinma da ake hada musu harda military training a school din nasu yanzu. Hanklin wasimé na kwance, saidai fitsarin kwancen datakeyi ne yafi daga mata hankli,wani bin kunya takeji sosai acikin ranta musamman in matar gidan ne taxo dubata ta tsinceta a haka to ranar wuni zatayi tana jin nauyinta a kirji. Tasha kokawa bilti damuwarta akan fitsarin datakeyin amma haryau basu fahimce cewa Sanyin A.cn ne yake sakata acikin wann yanayin ba. Gata ta kasance yarinyace mai balain son tsafta,haka zata lailaya gadonta ta share dakinsun fess,kuma tasowa datayi acikin fulani yasa take da wannan alhininsu na yawan jin kunya gata da kawaici sosai..in bilti ta fito wanka haka take sulalewa tayi waje ta tsaya a bakin ƙofa harse ta kammala saka kayan snn ita zakaga ta shigo. Amma Saboda fitsarin kwancen nan yasaka duka wani kuzarinta ya gushe agidan,kallon kanta take kamar wata kazama. kunyar bilti takeji aboye har cikin kokon ranta tanajin nauyi shiyasa kawai ta yanke hukuncin wanke kayan fitsarinta dakanta Basai an wanke mata ba. Duk shiyasaka bata son fitowa bare ta samu kyakkywar fahimtar juna tsakaninta da surakunanta gani take kamar izuwa ynzu duk sun san tana tsula fitsarin kwance,abun nasaka taji kunyar kanta bakadan ba. Washe gari jumu'a da alaman yau babu kowa a gidan,bilti ce kawai a kitchen alhj qasimu da matarsa sun tafi ikko dansu basa wani zama. Kirjinta na mata ciwo yau haka ta farka a bacci wani iska mai sanyin gaske ne yake kadawa yana ratsata har cikin kasusuwanta tanajinshi ,mikewa zaune tay akan gadonta snn ta kama handle din windown ta leka kadan ganin gari ya rufa,lekewa ta dadayi taga wani bakin haddarine a sama Cikin sauri ta ja windown ta rufe sabida wani iska mai ƙarfi daya busota hancinta.Tana kammala rufe windown ta sauƙa kasa ta tattara inda tayi fitsari snn ta nufo waje. Ko takalmi bata saka a kafafunta ba tashiga saukowa ahnkli cikin sanɗa zatayi waje,kwata kwata batason bilti taji motsinta a sanyin nan tasan bazata taba kyaleta ta fita ba,ita kuma batason tazauna da kayan fitsari a daki mostly shitake fara kawarwa snn tayi alwala duk hanata da bilti takeyi amma batajin magana. Yauma babu motsin kowa a waje ita kadai Tana durkufe agaban tap tana wankinta as usual tanata shafawa kamar wacce batada jini ajikinta,gabanta ne taji ya fadi,barin wankin tayi a hnkli snn ta juyo tana dago kai kuwa suka hade idanuwansu waje guda da wani kywkkwan saurayi wanda tunda take arayuwanta bata taɓa ganin mai irin kamanninshi ba. Its 300# ka subcribe via 0152983148 Mohd surayya sule GTB send ur evidence to 08060712446 Or mtn Pin. 7/25/22, 19:19 - Kawata: *FITAR RANA...* _......faduwarsa_ BISMILLAHIRRAHMANIRAHEEM. No.8 ACikin sauri tabar wankin ta miƙe tsaye tare da ja da baya tana mai tsura masa fararen idanuwanta tanata kallonshi shima kallonta yakeyi tun daga can nesa yana tahowa cikin takunshi mai sanyi daya gama burgeta. kyakkwar fuskarshi dauke take da wata iriyar murmushi mai matukar daukar rai,hadadde dan gaye,sumewan tsaye wasime tayi..shikuwa aransa cewa yake..wow ive seen an African queen."dan kuwa babu abunda yay mugun tafiya da imanin sa sama da shiny luminious dark skin dinta,wanda baiya bukatar ado ko wani kwalliya..he has neva seen a black beauty like this one. har ya iso gabanta kwakwlnsa bata samu cikakkiyar nitsuwa,kallon junansu kawai suke basu kifta idanunsu.kunya da fargaba duk ya kama zcyar wasime,kyaunsa da gayunsa sosai ya tafi da ita, gashi duk tajiƙe jikinta da ruwa kamar wata yar bola,gayen ya kalleta snn ya kalle cikin bucket dinta,wani murmushi ne ya kufce mishi,miƙa mata hannunshi dayasha ado da diamond wristwach da saphire ring dark red in colour yay..yana murmushi mai taushi cikin murya mai sanyi yace "hey,hello beautiful Angel..,shiru tay tanamai sunkuyar dakanta ƙasa. ganin bata motsa ba ya dauki bukitin kayantan Ya fara jera matasu akan clothline.."..Kyakkyawa baki maganane?kanta ya shafa kadan...ure so damn beautiful. ina mum dinki kika fito cikin sanyin safiyar nan kina wanki?u shud be on ur bed by now!!ina mama?kanta ta sunkuyar kasa sosai muryanta kasa kasa tana jin kunya kunya ahankli tace "tana cikin gida"..yace shine ke kika fito waje?tace ehm "dama wanki nakeyi" Dan dariya yy yace "I seee"...what a beautiful voice u got,yana furta hakan ta sauƙe broad smiles a bazata..setin zcyrshi ya capke irin"ohh my gosh wat a smile, u will definately kill me kina kasheni fa...kanta ta sauƙe kasa dan kwata kwata ita bata fahimtar meyake cewa sosai da sosai,tsinta kawai takeyi dan ita bawani iya turanci tayi sosai ba dan zamansu a jos ne ma yasatake dan iya gamutsawa kadan kadan but not all the time takeji,saheeb yana murmushi ya aje empty bucket din a ƙasa snn ya dan nuna chest dinshi da yatsa yace"Ahhm! sunana Doc saheeb..ni likita ne.."Kefa beauty?.meye sunanki mai shegen dadin nan?i know ur name most be special.Mayun idanunshi ya zuba akanta yana sauraron ta,dan kadan ta dago kanta tanajin nauyi nauyin shi a kunyace sosai tace "Emm Ni sunana "wasimé... Murmushi yy yace "wow"yana mai jinjina dadin sunan har cikin zcyarshi yana wani lumshe idanunsa yace "uhm dats so unique!..ke yar uwan Tej ne ko?ive been coming here amma bantaɓa ganinki ba ya akayi hakan to..budan baki tay kamar zata bashi amsa kirjinta ya buga da wani irin ƙarfi a tsorace ta juya ta kalli bayanta taga ashema biltice ke tahowa. amma abayanta kuma sai taga wani abu kamar inuwar mutum wanda tabbas tasan babu makawa shine.Wani hadiyar yawu tayi abazata dan ta dade kuwa bataganshi ba, atake ta zamto tamkar wata kurma tayi shiru bata ƙara kuma dago idanuwanta sama ba, bilti tana isowa daf suka hau gaisawa da saheeb din dake shi yana da son wasa da raha take ya shiga gaya ma bilti dk yadda sukayi da wasime. Yace"Bilti dama wannan yarki ce?she is so damn cute...murmushi kawai bilti tay batace mai komi ba tajanye hannun wasime suka tsaya tare da ita agefe itakam tasan gogan na lura dasu kuma zai iyayin ƙorafi akan yanayin da wasimé ta fito, lura da iyayensa sun riga sun dora masa nauyin jagorantar gidan kafin su dawo daga tafyarsu" ..Daga can baya baya taher din ya tsaya,bai ɓata lokcinshi ya iso garesu ba dan baison ma ransa ya ɓaci,kallonsu kawai yake daga can nesa da idanunshi da suka riga suka kankance da masifa, duk abunda suke fada yanaji daga inda yake amma yanayinsa kwata kwata bai nuna hakan ba. wayarsa yasaka agaba yana latsawa sosai.da kyar ma yake daga idanuwansa sama barema ace ya musu wani kyakkwan kallo.muryan sa ciki ciki kuma a matse yace "guy cmon lets go in,saheeb yace toh am coming"..ya kalli bilti "bari naje ciki pls a cup of coffee. Cikin sauri bilti ta riko hannun wasime tana kkrin janta ciki,ta amsa masa da cewa 'toh za'a kawo insha Allahu..gefen fuskan wasimén yadan shafa daxai wuce snn ya wuce din yy ciki,lkcin tej har ya isa bakin kofa da naturenshi na fushi fushi ya bude ya shiga saheeb na biye dashi abaya. Kallonta bilti tayi snn ta karkada kai "toh Zo mu wuce ciki,kefa bakijin magana wasime ai saida nace miki kidena fitowa wanki anan amma kikayi banza"toh wuce muje ciki. tsadaf tsadaf ta bar jikin tap din bayan ta kulle ,bilti ta cigaba da mata fada sabida sanyi sam Batason ciwonta ya tashi ko wani abu yazo ya sameta,Harta gama surutun Wasimé bata ce mata uffan ba tana famar juya hoton wancan kyakywan mutumin acikin kwayar idanunta,aranta tace dagaji yana da hankli. Nannauyar ajiyar zcya ne ya kufce mata snn ta wuce bayi tay wanka ta doro alwala tazo ta sauya kaya,riga da zaninta tasaka na abc koriya da fari fari sosai ya mata kyau,kitchen ta nifa ta samu bilti ta kammala musu abun kari.da kallo daya bilti ta bita snn ta mika mata wani abu acikin kofi tace.."zauna acan kisha ruwan zafi ne...inkin gama zaki tayani kai abinci,babu gardama tace toh.akan plastic

Chapter 5 of 15