Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 7
da Mustapha, amma ban gaya mata nice yarinyar da yake so ba,na dai ce mata, yace yana da yrinyar da zai aura. Waı abin bakın cikın da haushin, sai tasa mani kuka narna rasa da me zanji da marin da nasha, ko tabawar jikin da yayi mani, ko kuwa da bakin cikin kukan da tasakani gaba tanayi mani?. Nan take na tureta na mike abina, tana kirana tana ta magana, amma ban ko tsaya saurarenta ba, da gudunta ta biyoni har bakin motata, dai dai lokacin da nake shirin tashin ta, "Hamida," nayi saurin daga mata hannun "Halimatu nayi iya kar kokarina na kasa, in kinsan har zaki iya da kanki, bisimilla. Ni kam na gama zuwa wajan namiji ya na wulakantani daga yau mani zumuncin namu ya kare in har sai na yi maki abinda kike so, mari! Mari, wai ni Hamida ce namiji ya mareni akan wata." Na ja mota abina nayi gaba, "ina isa gida wajan karfe biyu da rabi na rana, maman na daki, na shiga da katunayen kwalaye biyu na ajiye gabanta, "mama tsaya in dawo, zali nike ji wanka zan danyi in ji sanyi." Nayi gaba zuwa dakına, ni wai duk gudun kada ta gane nayi kuka, bayan na kammala shiryawa, nasa riga da wando, dinkin ganah, na fito zuwa dakin Mamana. Bayani nayi mata cewa na kyautar da na samune yau da na kammala gwajin abincinmu, tayi mani murna, sannan tace in ajiye sai dadday na ya dawo, a haka na dinga hira ta da Mamana. Karara waya naji ta dauki yi da karlin gaske, kamar wacce ke amfani da wayar lantarki? Nayi saurin dauka saboda zuciyata ta bani, cikin mutum biyu, to daya ne wala Mustapha, ko lalimatu. Ina dauka, na kanga a kunena, sai naji anyi sallama, miryar Mustapha naji a kunnena, ban amsa ba, na kife kanwayar nace, "ta 58 tsinke mama," na ajiye kawai, muna fara hira naji ankara bugo wata, nayi saurin dauka. "muryar Mustapha dai na karaji а kunnena. Ban tsaya mayar masa da sallanarsa ba, na ajiye wayar nacewa Manana, "wayar bata da kyau, ta kara tsinkewa" minti biyar tsakani aka Kara bugowa, "muryar dazu dai itace, gudun kada maman ta gane, yasa na gaisa da shi,. Magiyar inyi hakuri ita ya dinga vi a cikin wayar, ni kuwa sai na wayance da cewa bata nan, e, a'a, wai dan dai Mamana ta dauka da gaske wayar nake yi da wani. A haka na ajiye kan wayar, ba tare da na bashi wata kwkwarar amsa daya ba, hakan kuwa yayi dai dai da shigowat Halimatu dakin mamana, tare da sallamarta, kamar gaske na washe mata baki, bayan sun gaisa da Mamana, na mike navi dakina. kamar dai nace zo mu koma dakina kenan. Ina shiga bandaki na shige na kulle, ina jinta, tanata dukan kofa a hankali tana hadani da Allah in bude, ko motsi banyi ba, ta kuwa yi wajan awa daya a haka, ina ji ta gaji ta tafi. Wanda yayi mani dai dai da fitowa da nayi da sauri ta dauki waya da ke ta ihu a dakina, ban tsaya jin ko waye ba na hau masila a waya, "kaga Mustapha bana son wulakanci, wallahi zan gaya ma Daddy in ce kai dan iska ne," "to Hamida in kinga ya dace ki fada ki fada." "kaga wallahi ko ka kyaleni ko kasa in gaya maka maganar da har ka mutu ba zaka manta da ita ba, banda cutata da kaso kayi Allah bai baka sa'a ba, na son ka mayar da ni mai ido daya," nayi saurin kife kan waya, na haye gadona. Kukan me zanyi kuma?, na tambayi kaina, hakan yasa na mike na lito zuwa dakin mama, ina shiga na sameta tayi barci, ni ma sai na dawo nawa dakin, mai makon in kwanta ni kuma, sai nayi alwala nayi sallata raka a hudu, na dinga rokon Allah ya yafe mani akan alkawalin da na kasa cikawa, wanda na dauka sakanina da shi. Bayan na gamane ni ma barci ya daukeni kan abin sallata. ban farka ba, sai shidda da rabi na magariba, hakan vasa na shiga bandaki na Kara watsa ruwa a jikina domin in samu jikina ya dan warware mani. 59 Bayan nayi sallah magariba ne, na fita falo, ni ma kamar yanda muka saba, ina fita Mamana tayi mani maganar idona, da yayi jajir, nan na sanar da ita da cewa ciwo yake kawai, hakan yasa ita kuma tace mani in shirya dadare in je asibiti, na amsa mata da to kawai? Bayan sallah isha ne Daddy ya kirani, fiskarsa a daure yake tambayata, "wai me ke tsakanina da Mustapha?, gaskiya gabana yayi mummunan faduwa, amma sai na dake kamar ban fahimce shi ba. "Daddy wata magana aka gaya maka a kan haka?" "gani nayi wancen lokacin yayi mak kyauta mai yawan gaske, gashi yanzu ma ya kara yin wata shine nike tunanin ko da abinda ke faruwa ne?," "ba komai Daddy dan dai shine babban bako shi yasa." Na samu yabo sosai a wajan iyayena, bayan mun kammala ganin kyaututtukan ne, nace da Mamana zanje asibiti da tace in je Bayan na fito daga Specialist Hospital ne na ga motocin Mustapha a tsaye gefen titi, da hanzarina na kara jan motata sai gida, har muryar Mustapha naji yana kwalla mani kira, amma ban tsaya saurarenshi ba. Bayan na baiwa Mamana magungunan da likita ya bani ne naji karar wayar falonmu, duk da nasan gidan mu gidan jama'a ne, saboda dan milki da mahaifina ke da shi, zamu iya samun waya a kai kai,, amma sai naji wannan wayar kamar tasha ban ban da ta kowa, hakan yasa nayi saurin daukar wayar. Tun daga gaisuwa na gane muryar Mustapha, amma gudun kada Mamana ta gane, sai na tsaya muka gaisa, "lamida ina son magana dake yanzu, yaya zamuyi mu hadu a yanzu?, ni yanz.un haka ina get din gidanku a tsaye in har kin amince, zan shigo yanzu. "Ni yanzu ina da abubuwan yi, saboda haka ina son ayi mani hakuri wani lokaci, ina fatan ka gane?" "karki ajiye wayar, wallahi kika ki saurarata, zan shigo kaina tsaye in samu Daddy inyi mashi bayanin komai .""to shi kenan ina zuwa, "nayi saurin katsi shi. Ina ajiyewa nacewa Mamana Halimatu ce ta bugo mani wai in bayar a kaimata littattafai na da mukayi aiki a satin nan na 60 dauko littattafan Karyata har guda uku, na zo na wuce ta gaban Mamana izuwa kofar fita. Duk harabar gıdan mu, sai da na waiwaiga, amma hanga kowa ba, hakan yasa nayi tattaki zuwa wajan mai gadi domin in tambayeshi, ko munyi bakin mutane a gidan namu Mai gadi ya amsa mani da anyi baki amma suna wajan get fin gidan nan. Ban tsaya jin wani ba'asi daga bakin mai gadi ba, na wuce zuwa wajan get Mustapha ne zaung saman motarsa, ya daga kansa sama, anawa tunanin bulu bulu din samaniya yake kallo, saboda yanayin damana da muke ciki. Har na iso na tsaya bai dawo da kallanshi gareni ba, duk kuwa da uwar sallamar da na rabka, "zuwa nayi in bayar da hakuri akan abinda na aikata na rashin sani ina fatan zaki yafe mani?". "Ba wani laifin da kayi mani, saboda ni na janyo wa kaina da na taka har gidan ka, kaima ya dace in baiwa hakuri. na juva na tafiyata cikin gida, ina jin kiran da yake mani kasan kirane na nadama, mai kuma dauke da miryar dana sani mai yawa. Hakan ni kuma da naji, shi na karayin gaba ban tsava yasa ba, saboda tausayi da Kaunar Mustapha da ya dirrar mani a zuziva a nana ta c. Ban fi minti sha biyar da shiga gida ba. ina zaune gefe Mamana, muna hirar da wani abin ma banajin abinda take fada. saboda hankali na naga Mustapha, Daddy ne ya fito daga sashensa. yace in zo yana kirana. Ban tsaya yin komai ba, na nuli sashin Daddy na, na nawa ne dan mayafin daguwar rigata na rufe kaina dashi, shigar manyan matane ta ruwan tokar boyel, gabana kam ya fadi, amma, han nuna nasan Mustapha ba, halle Daddy ya gane faduwa gaban da nayi. Tsugunawa nayi har Kasa na gaishe da shi. kamar dai na samu Daddy na da hakinsa, sannan na zauna sosai a Kasan kafet nace. "gani Daddy," "ke kinsan wannan" injı Daddy na, tare da nuna mani Mustapha da dan yatsansa. "I na sanshi Daddy, wannan ne wanda ya bani kyauta da na gama makaranta, kuma shine wanda yake son Halimatun gidan Abba (Ghana, shine yanzun yake dan bina, wai in yi mashi hanyar auranta, ni kuma bana son yana zuwa wajena, tunda Halmatu dat 'yar uwata ce shi kenan dama inda na sanshi Daddy." 61 "To kai ka gaya mani gaskiyar zuciyarka, kana son Halimatu ko kuwa?, ni nan da kake gani zan iya auradda Halimatu ga duk wanda naso, kuma a zauna lafiya, saboda haka, kayi magana, in bar da gaske kake. "Yallabai ni bamuyi haka da ita ba, asalima ban san Halimatun ba, ban ma. ...,""Daddy shine fa yace yana sonta zai aureta, shine kuma yanzun zaka ce. .""Daddy ya daga mani hannu, "shikenan, naji, wannan maganar ba lawa bace ba, kun shirya zancen gaskiya, maga yan aike," Daddy ya tashi ya fice abinsa. in Yana fita na fara yi masa masifa, "yanzu Mustapha me kakc nufi ne da kazo har wajan mahaifina?, kasan dai ko kazo wajan iyayena, sai nace ina sonka, zasu aura mani kai ka riga ko sa cewa ni Hamida bana sonka, tunda ba kason abinda nike 11 SO. Tsugunawar da yayi kusa dani ita tasa nayi shiru ba tare da na gama maganata ba, "Dago ki kalleni lamida? ni Mustapha in har da gaske kike baki sona," na dago muka hada ido, ya lumshe mani idon da yasa, naji duk gashin jikina ya tashi. Nayi saurin sunkuyar da kaina," "in har da gaske baki sona, ki tsaya inyi maki wani abu daya, shi zai sa in gane baki kaunata, "me ye shi?" na tambayeshi,' fago ki kalleni so sai sai inji maki abinda zan tabbatar da gaskiyar maganarki. In kuwa har na gane gaskiyar cewa ba ki kaunata, wallahi zan yi maki duk abinda kike so," "to naji kayi mu gani," "me zan ga Mustapha zaiyi mani?" sai naga ya tallabe kumatuna, yana shirin kai bakinsa ga nawa, nayi saurin kwace fiskata, "Kana da hanakli kuwa Yallabai?" na mike zan tafi, ya kira sunana, cikin wata yanayin mirya, baice in juya ba, ni da kaina na juyo na kalleshi, yayi wani murmushin da saura kadan in mayar mashi da amsar nawa murmushin, son Mustapha ya wani karu a zuciyata, hakan yasa na dawo na durkusa gabanshi? "Gani yallabai," na fada, "me kike son inyi maki Hamida kiji dadi a rayuwarki?, ka so Halimatu,ka aurcta, ka aika gidansu, ka cire hotunana daga gidanka," ya dago muka hada ido, "ke bakya sona?, na daga mashi kai. 62 Yayi murmushi mai fitar da sauti, a ya matso da fiskarsa dab da tawa, "naji duk zanyi maki, anma nima sai kin bani amsar tambayata daya, da fada maki sharuddana, in har kinyi mani su, to zan kuwa yi maki duk abinda kike so. Ya janye fiskarshi daga sunkuyowar da yayi" "kin amince da abinda na fada in cigaba da fada maki?" na daga kaina alamar E. Na farko sai kin tabbatar mani da gaskiyar baki sona, har a zuciyarki, nayi murmushi, "ya za'ayi ince bana sonka kana musulmi dan uwana, "ni ba son musulinci ba so na aure nake maki magana," "dan Allah yallabai kabar wannan tamabayar ba yanzun ba, kaga dare nayi. "Ba zanyi maki gardama ba, ko mai kikace inyi zanyi, magana ta biyu, itace ba zan so waccan yarinyar ba, sai dai zan aurela a bisa sharudda uku, ki bani wata daya, anma kafin wata dayan ta cika kema ina son kiyi saurayi. Amma da sharadi ba zaki dinga zance da shi ba, dalilina nace maki kiyi saurayi kuwa, shine ina son in wata daya ta cika na fada maki sharadi na guda uku kika amince da su to tare za'a daura auran mu da 'e da saurayin na ki. Ki sani ba zancan ki tsaya hira da shi, amma ban hanayin hirar waya ba, ki sani ina da mutanen dake kula mani da duk wani taki da zakiyi a garin nan, saboda haka ki kiyaye, ba zancan tsayawa da shi balle ya tsaya kusa da ke, ko ta kai ga taba jikinki, in kuwa na samau daya daga haka, zan iya daukar babban ruatakin da zan iya kashe shi. Na biyu dole ne ki dinga jewa waccan yarinya hira wajena, saboda ni ba zan iya zuwa wajanta ba ni ma, tunda ke zaki zamo madadinta kenan, aınma wani sharadin nawa kuma shine, bana son in kin zo mata hira wajena ki ambaci sunanta ba, sai bayan wata daya, kenan bana son in ji kin ambaci ko sunanta, sai bayan wata daya." "Amma ai yallabai kasan dai makaranta nike yi, kaga ba yarda za'ayi in dinga jewa Halimatu hira, in ka anince yarda ba zanyi hira da kowa ba, kaima kayi hakuri da yin hira da ita," "ni dama ba da ita zanyi ba, da ke, saboda haka ba ruwana, ni dai nasan sai anyi mani abinda nike so zan aure wacce ake son in aura. 63 "yallabai iyayena ba zasu barni in dinga yawan fita ba," "ni ba ruwana, amma ai kin san da haka kikayi mata alkawalin hadata da ni ko? To yanzu ma ki san yarda zakiyi kina zuwan mata hira........" "kullum ko yaya?""ta yiyyu kullum ta yiyyu, sai na nemi son ganinki, saboda haka ki dai shiga saurarata waya in har ina son a zo mani hira. "Ina jiranki gobe," haba gobe kamar ba yau ka zo ba," "ina ruwana, ni dai dole azo mani hira," "a ina zan zo kasan dai ba zan zi gidan ka ba," "aamma ai kina da katin Naicon a hanunki," "gaskiya ba zan dinga zuwa naicon ba, saboda kada in hadu da abukanan Daddy, kaima kasan wajan mayan mutanc ne," "Gobe zan bugo waya in sanar da ke in da zamu hafu sarkín cika alkawali, ni zan tafi na bar mutane suna jiyarana a waje? wallahi kaji tsoron Allah ka daina wahalar da su dan kana da kudi." svital sb ка "Ai kuwa ni a ganina ina kulawa dasu dai dai gwargwado amma duk da haka zan kara kiyayewa na gode, banayi masu haka wallahi, yanzun ma uwargida tace tayi mani fishi, shine muka tahó biko da su, na danyi murmushi "to sai da safe, nasan Diddy na cen ya na jirana in sha jerin tambayoyi.я в вау ла rin Ganin bashi da niyyar tafiya yasa nayi mashi sallamar dole nima na shige cikin gida, ina isa falo, Daddy da mamana suna kallan labaran Karfe tara, hakan yasa na kalli agogon falon 'mu, naga goma saura minti sha takwas, na koma daga gef nima ha zauna, ism Tamilnug 3 06/0 Jikina har rawa yake yi daga zaune saboda zaman jiran tsammanin Daddy ya jefo mani tambayoyi nike yi, amina har'ya shiga sashinshi, bai yi mani magana ba, wanda hakan yayi dài dai da karfe goma da minti sha biyar ha dare АиЯ Mamana ta kalleni, "ina kika j6? "mama Sauráyin Hammatü ne yazo muka gaisa," "wacce irin gaisuwace haka niar dadewaoh "mama shine bai tafi ba shinc ni kuma na Kasa ce masa ya tafi. shine sai yanzun ya tafi?. "Ki dai kiyaye mutuncinki, kullum dai ina gaya maki wallahi in har kika tsaya yaudarar kanki to kin yiwa kanki," ta mike ta nuli nata dakin, nima hakan yasa na kashe talabijin din da sauran yan kayayakin wuta na shege nawa dakin. 64 *** *** Sati biyu kenan da yin yarjejeniyar mu da Mustapha, da motata nike tafe a hankali har na karya ta izuwa ,Amingo stor" domin siyen kayan da Mamana ta aikeni wanda haka yayi dai dai da rabuwata da Mustapha minti ashirin da suka wuce "Amingo na shiga zagayawa domin tsintar kayan da naje siye, ba'afi minti uku da fara daukar kaya siyena ba ina zubawa a dan kwandon da nike zuba kaya, sai naji ance mani, "(sannu, turaran ciki bakar kwalbar mai wahalar gane kala,)" na dan waga gefena kadan. Ba tare da na cigaba da kallansa ba, na danyi murmushi, haba Alhaji sufuyanu, kaine ba'a yi maka kirarin kana wahalar gani ba. sai ni da nike yawo kullum a titi, ina neman dan ilimina, "Hamida kenan, ya gida? Na amsa da lafiya kalau, haka muka cigaba da tafiya ko wannan mu yana daukar abinda yaje siye. Gudun kada yace zai biya mani kudin siyayyar da nayi, vasa. ban karasa siyayya taba, nayi saurin zuwa na biya kudi, amma sai ya zamato na ts ye gefe daya na jira shi, Bayan ya 'iya nasa ne, aka daukar mana kaya zuwa matocin mu, amma sai naga yasa a kawo leda daya mai kaya a ciki wajan tawa mota, hakan yasa na nunawa mai daukar kayan cewa, ba nawa bane, bayan mai daukar kayan ya koma wajansane, sai suka taho tare wands hakan ya tabbata mani da Sufiyanu siya mani kayan yayi. Bayan yar guntuwar mahawarar da ta shiga tsakaninmu. wacce dole ni na hakura ba sifiyanu ba, sai muka tsaya yar hirar wajan minti sha biyar, wanda a wajan hirar ne yake kara dawo da gabatar mani da kanshi a matsayin mai son ya aureni. Banyi mamaki ba, saboda nasan Sufiyanu tsohon masoyinane, tun ina yar aji biyar sakandire, sai dai a lokacin ni ban daukeshi wani masoyi ba na dai mayar dashi abokin wasana ma, tunda in yazo gidan mu ni tsokanarshi muke yi ni da Halimatu. Samun fiska da kumatu da Sufiyanu yayi wajena, shi yasa ya ke sanar dani cewa zaizo a daran karamar wajan takwas na dare. saboda yarjejeniyar da mukayi da Mustapha, ita tasa na amsa masa da ina jiran babban bakona. 65 Amma kafin mu rabu, sai da na dan daure na tambayeshi cewa yayi aure?, ya amsa mani da har yanzu dai yana jiran wacce uyi dai dai da rayuwarshi ne, shi yasa bai yi ba, amma yanzu a shirye yake da yi in har na amince masa. Yar dariya nayi kadan irin tamu ta mata, duk da irin kallan da yake yi mani yana hanani sakewa sosai, wanda irinsa na baro bayan mintuna hamsin da wani abu da suka wuce, wanda Mustapha ya sani a gaba yanayi mani, koma ince yafi na Sufiyanu razana mani jikina. Nasan shigar da nayi yau zata iya janyo mani kallo ga jama'ar gari, to balle masoyana, ba wata shiga bace illa bakar shadda dinkin Good morning momi, da farin mayafi, farin takalmi ga farar jakata ratayc a kafadata. Wanda fashon din 'yankune ne a kunnena da wuya na masu kalar baki da ratsin fari suma, hakan yayi dai dai da bakin jan bakin bakina, da yayi kwance a leban farar mace kamata, wanda bakin kwalli kajal ya dira a dunduniyar tudun idanuwana ya kayata mani fararen idanuwana,gá bakin cikin idon shima yau kamar an tura nani shi. Karin kyan jiki irın na yarda gashin kaina ya kwanta bayana, kitso daya rak akayi mashi, Mustapha ya yaba mani matuka da kwalliyar da nayi duk da dama jama'ar duniya suna cewa kwalliyar yar babbar makaranta, tasha banban da ta yan kanana yaran yan mata. Nayi mumushi tare da yin sallama da Sufiyanu na bude nuwan tukar motata mai duhu, tamkar kayi kallo daya kawai yace mata baka karka tacan yafə mayafin da nayi ya su bace a dai dai lokacin da na záuna matukin direba, zan tashi motata. "Sannu Hamida" haka, naji Sufiyanu ya fada, a dai dai lokacin da yake kada makullan motar da ke hannunsa, ban amsa masa ba, amma nayi murmushi, na ja mayafina tare da ce masa "ina jiran babban bako fa". Wanda hakan yayi dai dai da tashin motata da nayi, nadan jata kadan sannan ya amsa mani da "to karfe takwas fa". Karfe takwas saura minti goma sha uku na dare ina jikin madubi ina kara gyara fiskata, ni nasan ba son Sufiyanu nike ba, 66 amma nayi hakan ne domin in'tursasa zuciyata ta so Sufiyanu dan kawai Mustapha yaga da gaske nike yi, maganar Halimatu. Nasan ban saba ba, amma yan kwanakin nan da nike tare da Mustapha, na dan fara saba iya mayarwa da saurayi amsar tambaya, ko yi masa magana. Hakan yasa banji komai ba da Sufiyanu ya zo, Sufiyanu kam ya samu karbuwa, saboda hirarmu abin sha'awa dashi, muna cikin haka "Aina'u ta shigo, har kasa ta durkusawa ta gaishe da Sufiyanu, sannan tace in zo in dauki waya a cikin gida in ji mamarти. Da annashuwata na fita daga baban falan baki na kusa da shashen Daddy, tare da cewa Sufiyanu, ina zuwa, tun a kofa nayi tsaye chak da na hango Mustapha, tsaye dan nesa da ni kadan, yayi taku uku domin na taho in da yake. Wanda hakan yasa shi kuma ya tsaya, ni kuwa nayi hakane gudun kada Sufiyanu yaji abinda ke faruwa tsakanina da Mustapha, shima yajanye ya barni ba a kowa ba. "Sannu yallabai," waye ciki?", maganar da yayi mani kenan wanda ko sannunt bai amsa mani ba. Wace tambaya ce wannan kuma haka?" "inji naki tambaya, sannan ki dawo mani da ita, nace waya a cikin falan?" "bako nane," "waye kuma haka?" "baka san ko meye bako ba?" "ina sauraranki ki sanar dani ko wayeshi," "bako na, shine mutuman da nike saran zan aura nan da lokacin da za'a daura naka auran kaima," "amma in kinyi tunanin sai da na gaya maki ban amince kiyi hira da kowa ba, kamar yadda ni ma ba zan yi da ita ba. Ya juya ya taka kamar sau uku, tukuna ya tsaya, ba zan hanaki ba, amma kuma duk abinda ya biyo baya akanku kiyi kuka da kanki, "amma yallabai kaine kace in yi saurayi ko?". Bai tsaya ba, balle ya bani wata amsa, ni kuwa hakan tasa na juya zuwa falon da Sufiyanu yake zaman jirana, cikin hirar mu da Sufiyanu ne nayi masa dabara, cikin hikimar cewa jibi zan yi tafiya, saboda haka sai dai a waya zai dinga samuna. Nayi mashi alkawalin buga masa waya kullum mu gaisa da shi, wanda a karshe nace masa gobe yaya na usman zai dawo daga spean saboda haka zai iya samun sako ta waya cewa ya turo da 67 iyayonsa da kayan aure da komai in har aka nemi daga gıda in kawo wanda nake so. Yayi murna kwarai da gaske, wanda na fahimci shi, uciyarsa, fis take tamkar nace ya koma ya turo da mutanc a (faura mana aure dashi a yanzu. Nayi haka ne, gudun kada wani abu marar kyau ya faru a kanshi, saboda ganin yarda Mustapha ya hasala da yawa, Karfc tara da kwata Sufiyanu yayi sallama dani, ni kuwa rakiya har bakin motarsa, abin kuwa sai naga ya bani sha'awa. Wanda zuciyata ta fara amincewa da in aure shi, ko dan hankalinsa da natsuwa da suka gama jikinsa. Halimatu nayiwa waya daga shiga ta gida, na sanar da ita gobe karfe tara na sake ko takwas da rabi, ta zo muyi abincin taryar bako yaya Usman, wanda in mun gama zamu isa filin jirgin Abuja Intel-Air port mu taro shi karfe biyar da rabi na yamma. Ba tantama yaya Usman ne na hango yana saukowa daga jirgi, duk da na samu shekara uku kenan baganshi ba, amma sai gashi ta farat daya na ganeshi. Tun daga nesa nake daga masa hannuwa, har ya hango ni, ganin ba bari isa in da suke yasa, na dinga tsallan mur ıar gashinan zuwa, amma yana tsowa in da zan iya zuwa in taryeshi ban san lokacin da na ruga a guje ba na taryoshi. Yanda yaya ya ware hannuwa, a manufarshi in shiga ya rungumeni, amna saboda gırma da nayi, sai naji na kasa yin haka, sai dai nayi saurin rike hanunwansa duk biyu, ina dariya, amına abinka da zama turai da yaya yayi. Da muka tafi zuwa wajansu Daddy sai da ya rungumeni a gefan kafadarsa, da murnarsa ya durkusa ya gaishe da Daddy, wanda yana zuwa wajan mamarmu, sai naga ya kama hannunta, sannan ya durkusa ya gaishcta, Mamarmu ta amsa tana dariya ta murnar katan danta ya dawo, wanda tuni 'Aina'u ta dare shi dan murna, shi kuwa ya rungumeta yar kanwarsa, ya gaishe da mominsu Halima, sannan Halimatu ta gaishe shi. Dan rashin kunya ta irin wanda ya dan zauna tare da turawa, yasa yaya ya tambayeni, wai har yanzu ba'ayi mana aure ba, ni da Halimatu?, kuma a gabasu Daddy, wanda momi da take ita 68 69 тясесс тai wayayyan kai, ta bashi amsa da ko saurayı bamu da shi. Hakan yasa ni kuma, "momi' Halima tana da wanda zata aura, har sun kusan dai daitawa, ba mamaki a aiko maku da mayan mutane nan da dan wani lokaci. Yayane yace in gaya mashi gaskiya, ni kuwa har da rantsuwa ta, da kara tabbatar masa da gaske nake yi, anan iyayenmu suka zama 'yan kallo, saboda nasan basu san komai ba na game da wani abu na Halimatu. Amma abin mamaki sai na ga yaya Usnan yayi wa Halimatu wani kallo da ban fahimci mai yake nufi ba, hakanan kuma sai naga yasa Halimatu tayi saurin sunkuyar da kanta, kamar wacce bata da gaskiya. Tun daga lokacin sai naga yaya Usman ya dan canja fiska ba kamar farko ba, haka muka shiga mota, amma banga yaya ya canja ba. Daddy da Mamana sashen Daddy suka wuce kai tsaye ni kuwa da Halimatu da yaya cikin gida muka nufa, wanda Halimatu tayi saurin shiga kicin, hakan yasa nima na bi bayanta, domin a tunanina kayan abinci ko sha zata daukowa yaya. Muna kicin ni da lalimatu yaya ya shigo, tambayar da yayi mani itace ta bani mamaki, wai in gaya mashi gaskiya Halimatu na da wani saurayi wanda bashi ba?, na dago da dan hanzarina. "yanzu nan yaya dama kai saurayin Halunatu ne, ni ma na mayar masa da wata tambayar. Ya bani amsa da, "IE mana, yanzun da bata taba gaya maki ba?" "wallahi ban taba ji ba, yayi dan munmushi, "dama ance mata baku da tabbas, kamar yanda kuma kuke ce mana maza bamu da tabhas ya juya ya kalli lalimatu. Yanzun haka kika yi mani Halimatu? "yaya karfa ka zama dan runto da kai saurayin Halimatu ne, nayi imani da ta fada mani," "to zo muje ki gani in nuna maki tabbacin cewa ni babba masoyin Halimatu

Chapter 6 of 7