Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 7
gashi wainar shinkafa da wata irin miya mai dadin gaske, ni kaina nayi mamaki ace kamar Mustapha da yake ba cikakken dan kasa ba, amma ya iya ci waina. Nay sauri na bude jakata na zazzgo fauda na shafa a fisk ta, gudun ka la a gane nayi kuka, yayi sallama ya shigo ya zama kujerar tibirin cin abinci wacce ke kallona. "Alhamdulillahi, mun gama lafiya, sai muyi magana mai kyau bismilla," "na riga na gaya maka komai kenan tun dazu, sai dai tunda ka nemi in karayi maka bayani, zan iya kara yi maka, ni Hamida nazo neman alfarmar a wajanka na ka auri aminiyata Halimatu, Halimatu, aminiyatace, tare mukayi Primary tare mukayi sakandire anan Abuja. Zumuncin da ke tsakanina da Halimatu yasa va koma zumunci na tsakanin iyaye da iyaye, har ya zamana yazu zumuncin iyayen mu yayi karli sosai, ba dan komai ba saboda mahaifin Halimatu dan kasuwa ne, hakan yasa Daddy ya kutsashi a harkar gwamnati, yana kawo kayayyaki daga Kasashen waje.gwamnati na biyanshi. In ba na gaya maka ba, ba zaki taba tunanin ciwa zamunci ne kawai ya hadamu ba, sai dai kace diyar wa da diyar kane, Na daukarwa Halimatu alkawalin zan hada ku kuyi aure, saboda halin da naga tana shiga a kan sonka, in kuma ka karbl wannan taimako 33 da na nema a garcka, zanfi kowa farin ciki a duniya, nagama dai in da tambaya ko kana nerman karin bayani, zaka iya yi a shirye nike in baka amsa duk wata tambayarka." "Naji bukatar ki, Hamida, arnma kuma sai kika same tawa bukatar sabanin taki, saboda nima na samu kaina cikin son auranki yau shekara biyar kenan, tun a lokacin kina yar aji uku. ka Na ganki ne a wajan wani fati nc da aka gaiyaceni naji, kuwa ince dinner,dina ta manyan mutane, ban taba tunanin zanga yara a wajan ba, amma sai kawai na ganki kun shigo tare da mamanki, da aka gama taron nasa aka bincikita mani, sai aka c mani ke yar Haruna masari ce, a lokacin yana a(G.M) awan kamfani ya aiki. *** *** Tun daga lokacin Hamida nasa ake gadinki, duk inda kafark ta taka, to ki tabbatar da yarana suna biye da ke, domin gudun kad wani ya rigani, tun a łokacin baki taba fita daga cikin zuciyata be sai dai naki nuna kai nane a lokacin, saboda ganin ki yariny arama. Duk wata tsarewa da kika ga malamai nayi maki a makarant suce maki (Extra lesson) za suyi maki, nine nan nake biya ar koyar dake, ina son kiyi tunani akaina ni ma ki tuna yarda kil tunani wacca yarinyar zata shiga wani hali nima haka zan iy shiga, yarda kike tunani tausaya mata, kamata yayi nima ki tausay ınani, "Yallabai ka tuna girman alkawari, ba zan taba yarda karya mata alkawari ba, ni dai har yanzu ina nema alfarmark Yallabai Halimatu kykykyawace, ga gashi, fara ce itam makaranta daya mukayi da ita, yanzun haka tare muke zuw makaranta da ita Halimatu ta fini hankali da natsuwa, mahaifin lalimatu y: Daddy kudi, Halimatu. " Nayi shiru, saboda kar hannuna da yayi wanda ke kan tebir ajiyc, ya daga kai yayi m kallan kasan gira. "Duk wannan bata daneni ba, Allah yasa ita aljanace sabe kyau, ni ke nagani, ke kuma nike so, daga yau kada ki karayi m maganar wata 'yarinya, in har ke kinsa bakya sona, ki gaya m 34 gaskiva kawat, in samu wata, mata da yawa a duniya, har sai na Jira An zaba mani Na janyc hannuna, na mike, ban tsaya jin wani karin dogon surutu ba, na rataya jakata, tare da saka takalma na, domin mayafina na akaina na neni hanyar fita, har na kai kofa na juyo Mustapha na zaunc a inda na barshi, ko juyowa bai yi ba. A zuciyata nace tabdijam, yau na hadu da sarkin milki ga takama, ni da ya kamata inyi mashi yarda naga dama, amma shi ke yi mani, na Itabtawa Halimatu ashar a zuciya, nace duk ita ta janyo mani wannan siyar da mutunci, nayi gaba abina. Ni nasan ko da kudi aka hadani ba zan kara hawa wannan abar ba, wacce nasawa suna liptar kasa, na kwammace in tafi a kafa, duk da nasan da tafiya sosai kafin in isa kofar fita. Tafiya nake, amma ko alamar kofar bangani ba,ni sai naji ma tsoro tsoro ya fara kamani, saboda yarda wajen ke amsa takun takalmana na, sunkuya na cire takalmana na rike a hannu, wata zuciyar tace kin zama ba kauya. Kukan wani abu naji a bayana, na tsaya na waiga banga kowa ba, sai na karaji a gabana, nan take sai jikina ya kama rawa, saboda sai naji kamaı kukan damisa naji, tafiya sosai a bayana, amma in na waiga bana ganin komai, Babu zancen tsayawa shawara, sai kawai na auna da gudu, sai naji an biyoni, me zanji? wani abu ya gifta ta saman kaina, innalilıahi, kuwa a bakina tafi dubu, har ya zamanto na koma salati tafiya kiyama. Mai zanji a bayana a lokacin da kafata ta kara tsayin zirin gudun da take, sunana naji ana kira ana cewa kada ki karasa, "Hamida kada ki karasa kofar nan, dawo baya, dawo baya, na tsaya cak, amma na kasa waigawa, tsoro ma yasa na zame na zauna jiran koma meye ya zo ya karasani in huta. Ji nayi an tsugna kusa dani, "Hamida," na dago da sauri zansa ihu, sai naga Mustapha tsugune, ban san lakacin da na chukumeshi ba, ina kiran ka fitar dani, so kake ka kashe ni dama nasan kai dan mafiyane. Yasa hannu ya rufe bakina, "ke ke, ba komai, kasan da kika lafi ya janyo haka, masu gadin wajan ne, ba,a tafiya kasa a wanan wajan sai in tare da ni kike, sunyi zatan wani abu kika yi a ciki, 35 shine kikagudo," ya dago fiskata, kallarsu suna kallanki," na waiga sai naga Aku da wani tsuntsu katu gaske, sai wani kata kare sai wani zazzalo halshe yake, idanunshi kuwa kamar kwallan dan kadanya saboda ja da ginna. Baku bata hakuriba,' sai naji akun yana cewa, sorry, sorrу, mama," shi kuwa dayan tsuntsun sai naga ya kawnta yana wani kuka, kare kuwa ya daga hannayenshi sama yana zazzlo harshe," to ku tafi ta hakura kada ku karayi mata haka, ku kalleta sosai. Sai naga ko wannanasu ya kuro mani ido, to ku tafi ya isa haka nan, a kara bata hakuri suka kara yin irin na dazu su dukkansu, tukuna suka juya, suka tafi,"ya tun tsire da dariya ya lakaci hancina, "sarkin tsoro,yayanki ne fa, da kin kuskura kin kai kofar fita harbeki za'ayi da kofar ta bude" Na mike tsaye, ina mayar da numfashi sama sama, "alkawali ko Hamida?" na harareshi, na juya zan tali, "na gaya maki ba'a tafiya a kasa, sai in na bayar da izinin haka, na tsaya zo mu bau na rikeki har mu kai," "ni ba zan hau ba, sai dai ka fada cewa a kafa zan tafi." "Naji zanyi maki duk abinda kika ce in yi maki am na nima ina: on in kin koma gida kiyi shawara da zuciyar ki, da at niniyarki ki janye maganarta" "ba zai taba yiyyuba,""to shikenan naji zanyi shawara nima, ina bukatar nambar wayar ki." Na bude jaka na dauko katin gidan mu na bashi, shima ya mik mani nashi, "Complimentary card" talfon din hannu na ga ya dauko daga aljihunsa, ina jinshi yana jaddadawa yaransa cewa gamunan fitowa amma a kafa, ya kashi ya mayar aljihu. Muna tafe, amma wai ni Mustapha zai jawa aji, sai wata irin tafiya yake a hankali, ni kuwa bukata ta in fita in bar mashi gidanshi, saboda hankalina ya tashi, akan gidan Har zan fita, ya dan waigo ya kalleni, kisa takalmanki mana," a lokacin nema na tuna ashe fa bani da takalmi a Kafata, na kalleshi, wai tunanin ko zanga yayi yar dariya, anıma sai nagama kallonshi ba a gareni yake ba, gefe daya kawai yake kallo, wani haushi ya kamani, na sunkuya na saka takalmana, na mike kawai da sunan in tafi "Kamata yayi ace kin fita cikin natsuwa, saboda kare ginnan ki a idon yarana, baki sani ba ko wata rana kece uwar dakinsu, in 36 kuwa bake bace, nasan zumunci zai hadamu tunda mun riga mun hadu yanzu, kinga in kin zo nan gaba, zai kasance sun girnamaki, kinga har abada raini ba zai shiga tsakaninku ba. Amma fa ba dole, shawara ce na baki?" ya daga riga yasa hannunshi a aljihu, ya tsaya daga gefe, tare da yi mani kallan da na lassara kallan jan aji, watau kallan kasan gira, mai kama da za'a lumshe ido Muje mana kayi tsaye," "kin gama kintsawa?" nace masa "I,' hakan da na fada yasa nayi gaba, yayi saurin janyoni," jirawa zamuyi, ya kuma zamu kin saki fisakarki, alamar kina cikin farin ciki, "na lizge hannuna, tare da sakar masa hararar wulakanci, Yayi munnushi, "ba mamaki tunda yanzu kujera milki da takama tana hannunki, in ma kina so, na hada maki da takobin yakin zinari, sai muga wanda zai yaki wani tsakanina da ke," sai ya cigaba da tafiva, dole tasa na bishi da sauri na jera da shi ina yaken baki. Kofa na budewa, gaba dayan kartin nan majiya karti, ga bakaken kayan rashin mutunci sun saka a jikinsu, sai suka mike tsaye da saurinsu, suka taho garemu, a cikin layi, wai gaisuwa suke kawo mani, Wani mugun haushi ya kamani, katin in isa ga motata kuwa har an bude Kofofin gabanta, da yaken fara'ata na amsa masu gaisuwa yan kudin da ke jakata, dubu uku ne na bude na mikawa daya daga cikinsu, har da wata kankan bar basu hakuri wai ban fito da kudi da yawa ba, sai kace su ke gareni, Na fahimei wani daya daga cikinsu da gani shine dan gaban goshin sa, ina kuma kyauta ta zatan shine shugabansu, saboda ganin sun jero tare da Mustapha bayan na danyi gaba kadan, ganin har murmushi yake, yasa nasan shine dan gaban goshin Mustapha. Ni kuwa har na shiga mota na zauna, gudun kada in tayar in tafi, su gane cewa bamu shiryaba da ogansu, yasa nayi sakato ina jiran isowarshi, Tare suka iso da wannan Katon, saboda ba zan kırashi yaro ba, ina ji suka bude but din motata, suna yan surutaı, sannan suka mayar suka rufe ya zagaya ya shiga gaban motata shima, katon ya mayar da Kofa ya rufe ya zagayo ga tawa Kofar ya rufe (madam to 37 miji ki dinga surutu, har ya kai ga jin haushinki, Hamida jan aji abune mai fadi da girma, in dan nace zan fassara maki shi sai mu kwana a zaune, ban gama ba. A dunkule dai su wadannan abubuwan da kika lissala mani, shine nuna wa koma waye ke fa macece ba halittarku daya dashi, ragowar Hamida sai mun samu natsatan lokaci zan warware maki su daya bayan daya." "momi in na je na gwada in yayi inzo in gaya maki," ta tuntsure da dariya, "to shi kenan jeki ki gwada mu gani lamida. Dama ai irin wadannan abubuwan, inu iyaye mata mu ya kamata mu dinga koyawa 'yayanmu mata, saboda su tsira da mutuncin su, amma yin shiru garemu, yana haifar da babbar illa, tunda ita yarinya bata san yarda zata yi ba in ta hadu da saurayi da ya fita wayau. Wai mu kunya, kunya ta wuce ki saki yarki ta lal un kamin kiyi mata aure, ai wannan shine babban abin kunya Allan ya kiyaye amin. Allah ya baki sa'a ki sauke nauyi akawali da kika dauka, karin baya nı kuwa, sai kin kusan aure." "kai momi ni fa ba aure zanyi ba." "Dafaki zmuyi a tukunya mu cinye, in ba aure zakiyi ba, kin san dai ba zai yiyyu ba mu dinga kallanki kina sintiri a cikin gida, gamu ga ki, "kai Momi wallahi ni ban san aure," sai me kike SO.... ?" "sallamar da Halimatu tayi ita ta katse maganar Momi, muna shiga daki Halimatu ta cukumeni, "yaya lamida an dace?" nayi dariya an dai kusa," "yanzu ba zance maki komai ba sai gobe ki sameni gida tunda ba lacture sosai, sai mu hakura da zuwa makaranta, tunda kinga yanzu nayi yamma." "Ni dai lamida gobe tayi mani nisa, in zo yau da dare inji bayanin mana," "to shikenan ina jiranki, ni zan koma gida, hudu ta wuce yanzu Daddy ya dawo," ta rakoni har motata, bayan nayi wa momı sallama. karfe takwas na dare Halimatu ta iso gidan mu, bayan ta gaisa da Mamana, ne muka wuce (dakina, in da nayi dubarar kunna, abun daukar maganar wani a rediyo ta. wanda dama tuni nayi mata, saiti da sabon kaset. 42 Muka zauna, har da dukan cinyata da dan zagin nan na kawayc yan makaranta, wai in fara bata labari. "sai kin bani goron albishir tukuna zan gaya maki," "me kike so, Hamida gaya mani wallahi ko meye zan baki in dai har ina dashi," nayi dariya, "to tsaya in fara, kema dariya kike bani, lallai Hamida har yanzu da sauranki." "Naga Mustapha, munyi magana da shi, amma da farko yace mani shi ba yanzu zaiyi aurc ba", "ni ko nan da shekara nawa ne zan jirashi, in dai har ya amince," nayi tsoki," "banza mai zubar mana da mutunci, Allah yau ba karamin haushi kika bani ba, kin sani ina ta bin namiji, kamar wani mijina, shi kuma sai wani kankanba yake yi mani. Na danyi shiru, wai shi dan ance ana sonshi, dan girman Allah Halimatu ki hakura da wannan mutumin ki samu wani ki aura, sai ma yaga ko dan yana da kudi, ko dan yanda ruwan indiya, shi yasa muka ce muna sonshi," in "Hamida, yace baya sona ne?"tafada asan yaye a'a cewa yayi bashi lokaci yayi shawara," "Alhamdulillahi, nayi zatan cewa yayi baya sona da sai ince mki ajalina ne ya matso," "kinji,ki kan namiji zaki ce zaki mutu," "! Iamida ina tsoron ranar da zaki fada tarkon so, so bala'l ne kinji," sai kuka, Hamida gani kike wasa nike ko? Hamida kina ganin Mustapha zai aureni," "in nace maki e nayi maki karya Halimatu, haka in nace a'a, sai dai mu dage da addu'a kawai, ni wallahi Halimatu bacin kin kafe, da kin hakura da Mustapha, saboda sai in ga ko ya aureki, anan gaba zai iya wulakantaki, tunda ke kika fara cewa kina sonshi. Karki damu da soyayyar da kike yi mashi ki dogarashi da Allah, Allah sai ya misaya maki wani, ni bazan so inga ana wulakanta ki ba, zuciyata ba zata so ba," "Hamida ki yi hakuri ba shawararki naki bi ba, na gode da shawarar da kike bani, ba yau ba kawai, harda ta baya, amma ina son ki sani, ni Halimatu tsakani da Allah nike son Mustapha, ba don kudi ba, ko wani yanayin fatar jikinshi ba. A'a, domin raya sunar Manzo (SAW) ko da Mustapha ya aureni ya wulakantani, dai dai da shine, tunda shi miji nane, in har da cin zali tsakanina da shi, sai in danganashi ga Allah ya saka 43 mani in munje gobe kiyama, ni dai ai buri na ya cika tunda na auri wanda nike so, zuciyata ma naso Komai zaiyi mani, tunda ina sonshi, ba zanga laifinsa ba, in dai har kinyi niyyar taimaka mani, ki taimaka mani sai Allah ya hiyaki kema, in kuwa kina ganin ba zaki iya ba, ki hadani da shi ki bamnu, ni na janyo hankalinshi har ya soni." "Halimatu tunda nayi maki alkawalin, kinsan ba abinda zai hana in cika shi, wai dama shawarace, insha Allahu zanyi iya hakin kokarina, amma duk da haka, ki cigaba da addu'a Allah ya tabbatar da wanda yafi alheri a gareki ya cire maki son shi a zuciyarki." "Amin Hamida, ni dai duk da haka na danka maki amanar komai a hannunki," "ba komai in sha Allahu zaki sameni mai rike maki amanarki, "a haka mukayi sallama na rakata, In dawo wa daki na kashe rediyo na tariyo kaset din baya na karajin hirar da mukayi da Halimatu, nan take na dauko jakata, na dauko katin Mustapha na dadda mashi waya nambar sallularsa. Nayi murmushi jin ya kama sunan a waya, hakan bai bani mamaki ba nasan a jikin salular sa ya ga sunana "barka da dare yallabai." Kamar 'a zai amsa ba, cen kuma sai naji yace "ina mika gaisuwata, ya mutanan gida, nace masa "lafiya kalau, amma hasu gaisheka, tunda basu san zanyi wayar ba, "zasu sani ne kinsan komai yana da lokaci." "Haka ne, dan Allah yallabai ina son yaro daya gobe, wajan karfe goma na safe, zan ba shi sako ya kawo maka, amma makaranta zai sameni, "to ranki ya dade, amma "why not" in zo da kaina in karba." "Ka rufa mani asiri, yarinya karama kamata, in ce ka zo kasan abinda ba zai taba yiyuwa ba kenan," yayi ımurmushi da ya dan daga sautin da har naji a waya, "Ilamida ke nan, sai anjima, "ya kife kan waya. Lallai yau ni Hamida naga tasku, wai ni namiji ke jawa aji, yana neman wulakantani, kan wata, kai alkawalin nan da wahala yake, na ajiye kan waya nima na shige bandaki abina domin watsawa jikina ruwa inji sanyi a zuciyata, Me zai neme takura mani zuciya? Wai da na kwanta barci, sai na samu kaina da tunani abubuwan da suka faru yau tsanina da 44 Mustapha, wai sai na samu kaina da jin da din tunanin da nike, kamar dai yarda budurwa ke tunanin saurayin da take matukar Kauna. Me nike nufi ni lamida? Ina son Mustapha ko yaya kenan?, nayi tsoki na juya na cigaba da addu'a ta ta kwanciya barci, amma abin ikon Allah, sai kuma naji zuciyata ta karra kamo mani tashar tunanin Mustapha. Na tashi zaune tare da kara rungume filon hannuna, na tallbe kumatuna da shi, a take kuma na lumshe idona hade da murmushi na da na tuno ni a kwance jikin Mustapha, dazu, gaskiya ni dama zuciyata tafi son irin su Mustapha, yana mutukar birgeni, saboda irin yaukinshi da yatsina kamar angon sarki. Ga jan aji na karshe, gashi duk maganar da za kayi bata girgizashi, ko kuwa dan yana cikin gajiyar kudi?, nayi tsoki, bude idona, sam bana son Mustapha, Mustapha sai Halimatu,"a fada a fili, da naji tunanin zaiyi mani yawa a zuciyata. ASP S Na koma da baya na kwanta, tare da sa dariya, ba wani abı ya sakani dariya ba, illa tunoni da nayi dazu a gidan Mustapha d na zama bakauyiya, na tuna irin tallan kasan idon da yake yi mani k na girgiza kai, Halimatu zata shı miskilanci wai, ace mutu baya kallan dan 'uwansa da ido, sai dai kasan ido. Nayi tsoki kuma, "kai ban son Mustapha, na juya na kwan sosai a take anan nayi tunanin cire Mustapha daga zuciyata kada tabka abiu kunya kan son zuciya, atake anan na tuno maganganu da mominsu Halimatu tayi mani nan take na kudıri niyvar sai rama jan ajin da Mustapha keyi mani, ni har kuka masai na sal shi. Tare da nuna masa nima fa na iya, gannin yarda zuciyata ke ta yi mani sake-sake, yasa na yanke shawarar yin sallah Nafil in dogara komai ga Allah, haka akayi kuwa ban tashi daga k sallayata ba, sai karfe uku na dare, ina kwanciya kuwa sai barci. Karfe goma na safe ne aka kirani a dakin daukar karatu, w inje nayi bako, da jin haka nasan dan aiken Mustapha ne, na fita samu wannan. wanda naga a yaran Mustapha, kamar shine d gaban goshinsa, wanda naji ya cewa Abdul Rashid har kasa ya tsuguna ya gaisheni, ni kuwa na amsa tare da masa, daga yau kada ya kara yi mani haka bana so, nan na dau 45 S 1 takardar sakon da zai kaiwa yallaba dinsa ya karba, na kara da cе masa, in yaje yace ya bashi amsa ya kawo mani yanzu, yace to, na bude jakata na dauko bandir din dubu biyu na mika mashi, sai yaki karba sai da nace masa in yaje yace ni na bashi Kaset din hirar da mukayi da Halimatu ne na aika mashi, domin samun wata hanyar shawo kanshi, da ya guntauwar takarda kamar haka. Assalamu alaikum. Ina fatan ka tashi lafiya, dama na rubuta maka wannan takardane, domin ka kara sanin da gaske muke fa, ga kaset nan kaji dan Allah, Sai anjima daga Kanwarka Hamida Haruna masari. Awa daya tsakani, aka kara aikowa kirana, na bi malamin a baya har zuwa wani ofishin malamai, yana zaune nayi sallama na shiga, amma ko dago kanshi bai yi ba, balle in samu sannu da shigowata, Mustapha Najib Bauchi kenan. Na shiga na zaura kujerar nesa dashi, nima na dan dauke kaina, sannan nace, "sa ınu ko," yayi shiru kamar bai jini ba, nima sai na share na janyo wani littafi dake gefena a kan wani tebir, na bude na kama karatu. Ba tare da na daga kaina daga karatun da nike ba, nace "ina kwana? na sauri da Allah, saboda ina cikin lecture na fito, in kuwa ba wata matsala ce ta kawo ka ba, zan iya ce maka, kayi hakuri da Allah sai wani lokacin ka iya tambaya izini sai ka zo, Yayi murmushi da fitar sautinshi kawai naji, ya dura wani abu akan tebir,ban kalleshi ba, balle in san me ya (fura, "lafiyata kalau ni, ga kaset dinku nan naji komai amma da wuya abinda naji yasa ni in fasa abinda ke zuciyata, ya mike tsaye, daga yau ni dan Allah bana son ki kara fadar sunan wannan yarinyar a gabana, balle ta kaiki ga yi mani hirarta. Na rufe littalin hannuna na ajiyc, nima na mike tsaye "ina son nima daga yau kada in kara jin sunana a bakinka, balle kayi tunanin kana sona, ni Hamida Haruna masari, nace bana sonka, bana kaunarka, balle wauta ta kaini ga auranka, saboda na lura, 46 koma wautar ta kaini na aurcka, ba zaman lafiya zamuyi ba, tunda tun a yanzu ka nuna baka son abinda nake so, Na danyi shiru tare da taku uku, kaga kuwa hakan ya nuna mani cewa kai namiji ne wanda sai abinda yasa kanshi zaiyi, ban isa ka tausayawa rayuwata ba, kaso abinda nike so, a matsayina na mace, kuma matarkа. Saboda haka, daga yau ni Hamida na barka har abada, tunda kafi son in shiga kamun Allah fiye da kai danuwana mutum ka taimaka mani, ni Hamida nace ko zan mutu, Halimatu ta mutu, ba zan kara ko kiran sunanka ba. Kada kuma in kara jin ko miryarka, ta ambaci sunana na juya zan tafi, yayi saurin taryar gabana, yasa hanuwa a aljihu, ya dago ido sosai ya kalleni, kallan da zai iya sa budurwa ta kamu da son saurayi a take, na kawar da kai na gefe. "Meye na taryar gabana? Kasan dai da ganina ni yar gidan mutunci ce, saboda haka, ba namijin da ya isa ya ce zai wulakantani, ko da kaga muna neman alafrma a wajenka, kada kayi tunanin kudi, ko kyau ko wani milki ya kawomu, sam, Allah ne ya jarrabemu da son hada zuriya dı kai ta sunnan aure. Bai wai ta shashanci ba, sanna in sanar da kai wani sabon abu, Halimatu ma da kaji tace tana sonka ni nasan sharin shedanne kawai, amma Halimatu na da samari na gaske, wadanda ma suka fika komai. Sannan ni nan da kake gani, na isa in sa Halimatu kuma na isa in hanata, saboda haka, ka sani daga yau Halimatu bata sonka, dama girmamawa da nike maka, ita tasa na 6oye maka duk wata halaiyata kunya tasani nasunkuyar da kaina dama ga maganar tawa a hankali nike yinta yarda zata shiga ko ina na dakinshi. Ni nan da kake gani maza 'yan uwanka ma shakkun yi mani magana suke, balle su iya budar baki suce suna sona. "Hamida duk maganr bata kai ta zafi haka ba, tunda nace ki bani lokaci inyi shawara, ki bani mana, ni yawan zancen ne bana so, kona mani zuciya yake yi. Ni kuwa tawa zuciyar ta buga kenan tunda ni kiri kiri ka nuna baka kaunata kwata-kwata "Hamida yaushe na fada? "karya nayi maka?" tun da ka nuna baka son abinda nike so, ka kuwa nuna mani kiyayya a fili." 47 "Ya isa, na, ki banı lokact zanyi shawara, in na gama shawarata, zan aiko maki da ko mai, shi kenan ko, an hucc?, na Kara daure fiska, tareda harareshi, ya dan kauce kadan, "Allah huce zuciyar gimbiya, har yanzu dama kujerar milki na hannunkı. navi gaba ban tsava bashi amsa ba, shi kuwa ina jinshi yana kırana amma ban ko juya ba. *** *** Tun shirun da Mustapha yayi, bata damu na, gashi yanzu har ta kai ni ga zama na musamman domin in tunaninshi, hakan ta farune sakamakon, daukewar kafa ko wani,aike ko wata waya a tsanina da msutapha, yau gashi har tsayin sati biyu dai dai. Wannan shirun da Mustapha yayi mani yasa zuciyata ta fara raunana tana son ta kamu da kaunar shi, gani nima wai jan aji da vake yi mani shi nike son in dinga ramawa, anya kuwa zuciyata bata karanto mani karya, ko ban tamabayi kowa ba, nasan zugani zuciyata keyi in so Mustapha ko dan ta raba zumuncin da ke tsakanina da Halimatu. Na samu na mike bna haye gado na domin in ga ko zan iya komawa barci bayan sallat asuba da mukeyi gidan mu, ranakun asabar da lahadi, maimakon in komawa, sai na samu zuciyata da karanto mani, abinda nasan ba zai ma taba yiyyuwaba a kaina, sai dai ko a kan Halimatu, shine ai yano na auri Mustapha. Na kwanta har da Kokarin rintsi idanuwana, wai ni a dole bari nike son yi, amma abin mamaki, sai ma na samu idanuwa na, da Kinyin bukatar da na nufesu da yi mani. Nayi tsoki na mike zaune, tare. da kallon, agogon dake ajiye gefen gadona, karfe shidda da minti uku, nayi imanin sai takwas na safe ake fita falo gaba dayan gidanmu, ko ince motsi ma ba zaka samu ba, sai karfe takwas na safe. Hakan yasa na janyo littafin 'RISALA na bude na soa karantawa, amma sai na samu zuciyata da aiyano mani, ta wacсе hanya zanbi in ga Mustapha, donin Karasa zancen Halimatu,ko zuciyata ta daina yaudara ta. Gaskiya nasan ba zan iya bin Mustapha har gidansa ba, saboda ina ganin zubarwa kaina da mutunci ne, na dinga tuno, maganganun da mukayi da momi su halima, kenan momi tana 48 nufin in ja Mustapha a jikina ya sone, so na gaskiva a cikin son da vake yi mani sai in cusa son Halimatu a zucivarshi. Na tashi kawai na shige bandakı navi wankana, na fito

Chapter 4 of 7