yana haɗe rai.
"A gaskiya Malam ba zan iya bayar da Bukar da malami a tafi da su ba, dududu shekarar Bukar nawa? Ko biyar da rabi bai rufa ba. Shi kuma malami shekara huɗu, idan sun je wa zai kula da su ya ba su abinci?"
Abu ta faɗa tana ƙanƙame Malami. Ran Yaya Inu ne ya ɓaci, suka shiga ja'inja yana jan Malami tana ja, daga ƙarshe ya ɗauke fuskarta da mari sannan ya fisgi hannunsu suna ihu da kuka Abu tana yi ya nufi hanyar fita. Da gudu Abu ta bi shi duk da tsohon cikin jikinta, ya waigo a fusace ya ce.
"Wallahi Abu idan har kika tako zuwa soron gidan nan a bakin aurenki tun da ba ki da hankali."
Abu ta yi turus, tana jin wani irin ɗaci a ranta.
"Iyataaaa!"
Malami ya faɗa cikin kururuwa, da gudu Abu ta rufa masa baya har ƙofar gida yana zuwa ya damƙawa Malam Jibrin su, ya fisge su kamar kaji ya watsa a cikin mota.
A zafafa Yaya Inu ya koma cikin gidan Abu ta bi shi tana kuka, ya waigo a zafafe ya ce.
"Daga nan ki wuce gidan ubanki, na warware ragowar igiyar kanki."
Daga haka ya shige cikin gida. Ɗaya bayan ɗaya 'yan masu wayon suka fara fita cike da ɗoki, musamman da suka leƙa suka hango motar da take jiransu a ƙofar gida. Su Barau da yake ƙanana ne suka dinga kuka suna tirjewa iyayensu ma suna kuka. Jin kuka da ihu tare da hargagin Yaya Inu ya sa rogawar mutanen gidan suka fito suka yi carko-carko, Inno ce ta tambayi abin da ya faru a nan Yaya Inu ya sanar da su. Takaici ne ya kama Baba Ibrahim rai a ɓace ya ce.
"Yaya wai saboda Allah wacce irin rayuwa kake yi haka? Yanzu don Allah kamar su Barau za ka kai birni makarantar allo? An ya kana tunanin goben yaran nan?"
Yaya Inu yaji kamar Baba Ibrahim ya zuba masa ruwan zafi, rai a ɓace ya mayar masa da martani.
"Kai Iro kada ka faɗa mini maganar banza da wofi, ba ɗazu ka gama faɗa mini magana a kan rashin iliminsu ba. Kai za ka faɗa mini na hango gobensu, akwai shege ɗaya a cikin gidan nan da yake ciyar mini da su? Tun da ni na samu kaina a gobena ai shi kenan! Daga yau ma kada wani ƙaton banza ya sake shiga hurumin iyalina." Yaya Inu ya ƙarasa maganar yana fisgar Idi da ko wando babu a jikinsa ya yi waje da shi. Su Larai suka durƙushe a wurin suna sakin kuka.
Suna nan tsaye suka ji tashin motar, hakan ya sake ɗaga hankalansu, a daidai lokacin Yaya Inu ya dawo yana muzurai yana harare-harare.
Bayan Sallar Isha'i
Zaune yake a matsakaicin ɗakin da aka ware masa, daga gabansa wani ƙaton fulas ne cike da farfesun kaji.
Sai da ya zuge tsokar cinyar kazar hannunsa, sannan ya ɗaga ƙaramar wayarsa ya danna wata lamba. Bugu ɗaya ta yi ya ji an ɗauka, ya yi ƙasa da murya ya ce.
"Barka da hutawa 'Yar gwal!"
Malam mai Yasin ya furta yana kurɓar romon naman, amsa masa ta yi sannan ta ce.
"Ni fa na gaji wallahi..."
Da sauri ya katse ta.
"Haba 'Yar gwal, na faɗa miki kwantan ɓauna na yi wa mutanen gidan nan, har na samu na aure tsohuwar nan. Ni na san Inno ba za ta ba ni matsala ba sai dai 'ya'yanta, amma ina aure ta magana ta ƙare. Tatsarta zan ta yi har na tara mana kuɗin da za mu hole, kada ki ji muryata ƙasa-ƙasa har yanzu nuna musu nake ba ni da lafiya."
Daga can ɓangaren 'Yar gwal ta saki dariya ta ce. "Shege Malam Gambo wallahi ko shaiɗan bai kai ka shaiɗanci ba."
Malam mai Yasin ya saki dariyar shakiyanci, suka cigaba da hira sannan suka yi sallama.
Ya kai kusan awa guda a zaune a bakin gadon yana yi mata firfita, saboda ko kaɗan ba ya son abin da zai dagula lissafinta. A hankali Rahina ta buɗe idanunta ta sauke su a kan mai gidanta Labaran, murmushi ya sakar mata ganin za ta tashi ya sa ya ɗago ta zaune sannan ya rungume ta sakar mata kiss a goshi.
"Barka da tashi masoyiya!"
Labaran ya furta cike da so yana jin kamar zai lashe Rahina. Fari ta yi masa da ido ta ce, "Wai tun da na kwanta kana zaune masoyi?"
"Ina zan matsa daga wurinki ƙaunata. Yanzu dai bari na sirka miki ruwa ki yi wanka. Ya ƙarasa maganar ya fita daga ɗakin."
Rahina ta bi bayansa da kallon soyayya tana jin tamkar ita kaɗai ta yi dacen miji a duniya. Tana nan zaune ya dawo ya riƙo ta, ganin za ta tuɓe kaya ya saka hannu ya fara rage mata.
Rahina ta ɗaura zani ta yafa ɗan kwali a kanta, Labaran ya riƙe mata hannu ɗayan hannun nasa yana riƙe da kwandon wanka suka nufi hanyar banɗaki. Sai da ya ga ta shiga banɗakin, sannan ya koma domin ya zuba mata abincin da za ta ci idan ta fito. Rahina irin matannan ne masu tsayi da ƙiba, shi kuma Labaran ɗan tsamurmuri ne ko tsayin kirki ba shi da shi. Yadda yake son Rahina da kishinta ji yake zai iya aikata komai a kanta.
Malam mai Yasin yana daga zaune a ɗakinsa ta labule ya hango wucewar Rahina, ya jima ransa yana biyawa da ita don haka bayan tafiyar Labaran ya yi zaraf, bayan ya ji ta fara sheƙa ruwa ya nufi banɗakin cikin sanɗa. A hankali ya tura ƙofar banɗakin, da yake dare ne sai Rahina ta yi tsammanin ko Labaran ne ya shiga domin ya tayata wankan. Malam mai Yasin yana shiga da sauri ya wara hannuwansa ya dadumo ta, cike da so da ƙauna Rahina ta ce.
"Wallahi ba don kada na saka son zuciya ba, da sai na ce duk duniya babu matar da ta kai ni sa'ar miji masoyi."
Malam mai Yasin don kar ya yi magana ta ji muryarsa sai kawai ya ce, "Ummmmm!" Ya cigaba daduma hannunsa a jikinsa. Rahina tana shafo fuskarsa ta ji gemunsa da gashin bakinsa sun yi mata ƙababa, a razane ta ja da baya da ta ce. "Wayyooo Allah! Masoyi ka zo kwarto a banɗakin nan."
Da gudu Malam mai Yasin ya fice daga banɗakin ya faɗa ɗakinsa, Labaran da ke ɗaki jin ihun Rahina ya sa ya zaro wani kafcecen almakashi irin na aikin gona ya tafi da shi.
Yana zuwa banɗakin ya shiga jera mata tambayoyi, ba ta tanka masa ba sai ji ya yi ta fashe da kuka. Ganin ba shi da wata mafitar ya sa shi ma ya rushe da kuka har da majina, sai da ta yi mai isarta sannan ta ce.
"Kwarto ne ya shigo mini banɗaki, kuma tas ya gama lalube ni."
Wani abu ne ya soki ƙirjin Labaran tsananin soyayya da kishinta ya rufe shi.
"Sai da na laluba gemu da gashin bakinsa, na gane ba kai ba ne tun ba ka da shi." Rahina na ƙara faɗin haka ta sakin kuka. Jikin Labaran ne ya shiga karkarwa zuciyarsa tana zafi, cikin huci ya ce.
"Na tabbata Ado ne! A cikin gidan nan shi ne tuzuru sako zaninki ki tafi ɗaki, wallahi yau sai na guntule shi da almashin hannun nan nawa. Nan gaba sai na ga da me zai nemi yin kwartoncin."
Labaran yana gama magana ya fita a guje yana wani irin ihu kamar wanda zai tunkari maƙiya a filin yaƙi.
07062062624
Ummou Aslam Bint Adam🌚
[02/02, 15:02] Ameerah Adam🌚: *GIDAN LIKITOCI*
©®AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITERS ASSO...*
Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye.
*MARUBUCIYAR:*
MARWAN
JARIRI
ASEELA
BAƘAR DAULA
AN YA BAIWA CE?
ƊAN BA ƘARA...
SHU'UMAR MASARAUTA
DUBU JIKAR MAI CARBI
UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA
YAWON SALLAR HAJIYA IYA
ZAUJATU JINNUL-ASHIQ
SANADIN RAGON LAYYA
SHAFI NA HUƊU
Kasancewar yaya Ado dawowarsa daga wurin aiki kenan, ya sa ya shiga rage kayan jikinsa domin ya watsa ruwa ya gabatar da sallar Isha'i. Yana daga cikin ɗakinsa ya fara jiyo ihun Labaran, ya girgiza kansa cike da takaici, yana jin haushin yadda gidansu ya zama tamkar gidan haya saboda yadda zuciyar kowa take a kusa. Ihun da Labaran yake kurmawa ne ya janyo hankulan mutane wasu suka fito, wasu kuma suka tsaya suna leƙensa daga window. Yayin da wasu kuma suka rifa masa baya, domin su ga irin wainar da zai toya. Sashen Yaya Ado ya shiga, ya tsaya daga bakin ƙofa yana sauke numfashi cike da zafin rai. Yaya Ado ne ya leƙo da kansa daga shi zai gajeren wando, ya haɗe fuska ganin Yaya Ado da ragowar mutanen gidan a sashen ba tare da sun nemi izininsa ba. Saboda yaya Ado mutum ne mai tsattsauran ra'ayi, kuma yana da ƙa'idoji don haka suke cewa karatun boko ya mayar da shi mai aƙidar yahudawa.
"Me ya sa ka shigo mini ba tare da izinina ba?"
Yaya Ado ya tambaya fuska a haɗe, Labaran ya ji kamar ya watsa masa ruwan zafi mai haɗe da attaruhi, saboda ganinsa da ya yi da gajeren wando kaɗai ya sake harzuƙa shi, musamman da ya tuna Rahina ta ce kwarton yana ta shafe ta a banɗaki. A hankali Labaran ya fara takawa jikinsa har karkarwa yake, hannunsa riƙe da ƙaton almashi. Ganin haka ya sake ɓata ran Yaya Ado, saboda a duniya ya tsani wani ya raɓo ɗakinsa saboda muhimman takardunsa da ba ya son wani ya taɓa masa. A harzuƙe ya tunkari Labaran ya ce.
"Kai Labaran ba magana nake yi maka ba?"
Mutanen wurin carko-carko suka yi cikin mamaki suna kallon Labaran, cikin shammata Labaran ya yi kukan kura ya yi kan yaya Ado yana ɗaga almashin sama, kamar yadda sojoji suke yi a filim yaƙi ya ce.
"Zuwa na yi na halaka ƙasurgumin fasiƙi da wannan almakashin." Yana gama magana ya kai hannu yana ƙoƙarin fisgar gajeren wandon Yaya Ado.
Nan take suka shiga kiciniya, Yaya Ado yana ƙoƙarin kare kansa shi kuma Labaran ƙarfi da yaji yake ihu da kururuwar sai ya guntule shi. Ganin haka ya ɓata ran yaya Ado, ya fusata ya ɗaga Labaran ya damfara shi da ƙasa. Labaran bai daddara ba ya sake miƙewa duk da ya ji zafin buguwar ya ce.
"Wallahi yau ko kashe ni za ka yi sai dai mu kashe juna, ko banza na san zan mutu a fagen shahadar kare mutumcin matata."
Yana rufe baki sai kawai ya saka hannu ya zugo gajeren wandon ƙasa. Matan da suke wurin suka saki ihu suna fita waje a guje, yayin da Baba Ibrahim da Baba Sale suka yi kansu Labaran da gudu ganin da gaske yana shirin aikata abin da yake faɗa.
Fitar Hansatu ya yi daidai da parking ɗin motar Fadil, da gudu da ƙarasa wurinsa cikin kururuwa ta ce.
"Likita don Allah ku taimako wallahi kisa za a yi, Ado ne da Labaran." Cikin izza ya sauke baƙin gilashin idonsa, ya zuge gilas ɗin motar cikin golden voice ɗinsa ya ce.
"Lafiya?"
Ya tambaya saboda bai ji abin da ta faɗa ba, sakamakon gilashin motar da ke rufe.
"Ado da Labaran ne za su kashe kansu har da makami, don Allah ku zo ku kawo ɗauki."
Hansatu ta sake maimaitawa a hargitse, ganin yanayin da take ciki na firgici ya sake tabbatar masa da abin da take faɗ. Ya saka hannu ya dafe goshinsa cikin takaici, saboda a kullum danasanin sakancewar zamansa a wannan gidan gandun yake yi. Bai tanka mata ba, ya ajiye lapcoat ɗinsa ya buɗe murfin motar ya fito. Ƙamshin turarensa ya bugi hancin Hansatu, ita dai haka kawai rayuwar Fadil take birge ta don haka ma ta ci alwashin aura masa Badariyya, idan ta ƙara zama budurwa tun da dama namiji ai mijin mace huɗu ne. Kuma matar Fadil ko kaɗan ba za ta nuna wa Badariyya komai ba, sai kyau da iyayin da take taƙama da ita likita ce.
"Suna ina?"
Fadil ya katse mata tunanin da take yi.
Da hannu ta nuna masa mangaren Yaya Ado. Da sauri Fadil ya shiga, a daidai lokacin Malam mai Yasin da Inno su ma suka ƙarasa. A lokacin yaya Ado ya samu nasarar ƙara ɗaga Labaran ya buga da ƙasa, hakan ne ya sake ɗaga hankalin Inno sai ta fashe da kuka, da ƙyar aka samu aka riƙe Labaran, shi ma yaya Ado aka riƙe shi kowannensu sai sauke ajiyar zuciya yake yi. Malam ya kwantar da murya kamar bai san abin da ya faru ba, ya shiga tambayarsu abin da ya haɗa su.
Rai a ɓace yaya Ado ya ce.
"Kun san dai a cikin gidan nan ba sabgar kowa nake shiga ba, saboda ba na ɗaukar raini ba zan ɗauki cin zarafi ba. Yanzu saboda Allah shekara nawa na ba wa Labara? ko Sale da yake bi na, ya isa ya zo ya yi mini iskancin daLaraban ya yi mini ballanta shi ƙanina na biyu? Wallahi ko da wasa ka sake kwatanta mini abin da ka yi sai na ba ka mamaki sakarai bawan mace." Daga haka yaya Ado ya fisge hannunsa ya shige ɗakinsa.
Tun ba su ji ta bakin Labaran ba suka fara ba shi laifi a zuciyarsu, saboda kowa ya san yaya Ado shi kaɗai yake gudanar da rayuwarsa bai cika shiga shirgin kowa ba bayan gaisuwa. Don haka ma ake zargi da raɗe-raɗin ko aljana ce ta aure shi, tun da ga ƙannensa nan har biyu sun daɗe da aure amma shi shiru.
"Kafin ku ji abin da ya faru don Allah zan tambaye ka Likita!"
Labaran ya yi maganar yana kallon Fadil. Gyaɗa masa kai ya yi alamar yana sauraronsa Labaran ya ce.
"Idan yanzu na saka almashin nan na guntule yaya Ado, akai wani dashe da za a yi masa a likitance?"
Takaici da kunya suka hana Fadil yin magana, kamar dai ba zai magana ba sai kuma daƙile ya ce.
"A'a"
Labaran ya haɗiyi yawu mai ɗaci yana jin kishin Rahina yana nukurkusarsa ya ce, "Yaya Ado ne ya shiga banɗaki ya lalube mini masoyiya tana wanka, saboda ya ga dare ya yi kuma wallahi idan duk garin nan gatansa ne sai na gama da shafinsa." Labaran yana gama faɗar haka ya shamace su ya fisge ya faɗa ɗakin Yaya Ado cikin ƙaraji yana faɗin.
"Gafara ga maza nan bisa kanka."
Ganin haka ya sa su ma ragowar mazan da ke tsaye suka rufe masa gaya. Da ƙyar suka samu suka sake yage Labaran, sai da aka kai ruwa rana sannan aka ba wa Labaran haƙuri ya haƙura. Dalilin da ya sa Labaran ya haƙura, saboda Baba Inu da Baba Ibrahim sun tabbatar da yaya Ado a kan idonsu ya shiga sashensa, kuma suna tsaye Labaran ya zo yana cewa an shiga banɗakin da Rahina take wanka.
"To kuwa idan haka ne akwai kwarto a cikin gidan nan, kuma ni da ma daga cikin ilimin da Allah Ya ba ni akwai na gane kwartaye. Kuma ni dama tuna zuwa ban yarda Ado zai aikata hakan ba. Za mu zuba aiki cikin ɗan ilimin da Allah Ya ba mu, Allah Ya sa mu dace."
Malama mai Yasin ya yi maganar da wata irin murya, kamar irin waliyan bayin Allahn nan. Gabaɗaya suka amsa masa sannan kowa ya watse.
Washegari
Tun da asuba bayan da Inno ta tashi Laraba yin Sallar Asuba, ta tabbatar mata da ba za ta je makaranta ba, saboda irin cin zarafin da Mai gari ya yi mata a gaban mutane da yaran gari. Don haka har kimanin ƙarfe tara na safe tana kwace a kan gado tana bacci, daga ita sai rigar atamfa da ɗan kanfai a jikinta. Zanin ya zame ya faɗi gefen gado, yayin da ɗankwalinta ya faɗo ƙasa.
Sallama ɗauke a bakinsa ya shiga ɗakin Inno, Inno tana ganinsa ta haɗe rai fara mita sama-sama.
"Haka kawai a dinga tayar mini da zaune tsaye, ina dalili a ce duk bayan kwana uku sai an auna jinin mutum. Ni dai tun farko Burema ya cuce ni da ya sayo abin nan ya ce ka dinga auna jinina."
Fadil ya zaune a gefenta bayan ya gaishe ta ya ce.
"Ba ni hannunki!"
Inno ta watsa masa harara ta ce, "Kai Boka ni fa na gaji da wannan ɗaurin hannun. Kaf zuri'armu babu mai ciwon hawan jini, sai da ubanka ya ƙaƙaba mini."
Fadil ya sake haɗe fuska ya ce. "Inno sauri nake fa." Ya ƙarasa maganar yana riƙo hanunta, Inno ba don ta so ba Fadil ya gama gwada mata hannu. Kasancewar ta taɓa fama da ciwon hawan jini, yana shirin fita ya hango Laraba a kan gado tana sharar bacci.
"Yarinyar can me ya hana ta zuwa makaranta?"
Inno ta ɓata fuska don ta san yanzu sai ya tilasta mata zuwa.
"Tun asuba ta ce mini jikinta yana ciwo ba za ta je ba, ka san jiya zanen zabuwa Mai gari ya yi mata. Ni ma kuma da ma ko ba ta faɗa ba, ba zan bari ta je makaranta da ɗanyan jiki ba."
Fadila bai tankawa Inno ba ya ƙarasa ya buɗe firjinta, ya ɗauko ruwa mai sanyi ya ƙarasa ya kwara a kan Labara. A hargitse ta tashi cikin masifa ta ce.
"Uban waye ya zuba mini..."
Maganarta ce ta maƙale ganin Fadila tsaye a kanta, ya naɗe hannuwa a ƙirji fuska babu walwala. Ta shiga murtsuka fuska tana kawar da kanta fege.
"Tashi ki yi shirin makaranta.
Labara ta tura baki ta ce.
"Ni ba za ni makaranta yara su raina ni ba!"
"Idan na sake magana wallahi sai na karya ki biyu!"
Fadil ya faɗa a tsawace.
Jiki yana rawa Laraba ta tashi ya janyo kayanta a cikin drower, waɗanda suka cukukuɗe kamar an ƙwato daga bakin kura. Uwar ɗaki ta shiga ta sako kayanta duk sun yi ɗauɗa, wandonta kuwa saboda rashin guga duk ya tattare ta baya da kaɗan ya fi gwiwarta.
"Ni fa yunwa nake ji!"
Laraba ta faɗa cikin ƙunƙuni.
"Ba dole mutum ya ji yunwa ba ƙarfe tara na safe, a gaskiya Boka kada ka tura Laraba makatanta ba ta ci abinci ba..."
"Wuce mu je!"
Fadil ya katse Inno.
Labara har da hawayenta ta ɗauko jakarta wacce ta kasance ta ɗinki buhu ta rataya. A tsammaninta ita kaɗai za ta tafi, sai ta ga Fadil ya bi ta tana gaba yana biye da ita a baya. Laraba tana zuwa ƙofar ajinsu ta ja ta tsaya ganin Fadil ba shi da niyyar tafiya. Ɗagowa ta yi za ta yi magana, kallon da ya wurga mata ya sa ta shige cikin ajin jiki a sanyaye.
"Ke daga ina kike?"
Malam Sule ya wurga mata tambaya. Laraba tana shirin yin magana Fadila ya yi sallama a ƙofar ajinsu. Malam Sule ya ƙarasa ya miƙa masa hannu suka gaisa.
"Ga yarinyar nan na kawo, don Allah malam a saka ido a kanta ba ta son zuwa makaranta. Kuma duk ranar da ta makara ko ba ta zo ba, matuƙar babbu wani ƙwaƙƙwaran dalili a hukuntata."
Fadil ya faɗa. Malam Sule ya washe baki ya ce.
"In Shaa Allahu Alhaji za a yi yadda kace."
Fadil ya yi masa godiya, sannan ya shiga ofishin Headmaster ya sake jaddada masa maganar da suka yi da Malam Sule, Headmaster ya ji daɗi sosai domin yana son ya ga iyayen da suka tsaya a kan kula da shige da ficen yaransu. Daga ƙarshe Fadil ya yi masa godiya, sannan ya wuce gida a gurguje saboda ya kusa makara.
Malam sule dama abin nema ne ya samu, saboda yana daga cikin malaman da suke hora ɗalibai. Yana shiga ya dubi Laraba ya ce ta je gaban allo ta tsaya, sannan ya ce mata idan ya gama biya musu darasi sai ta karanta masa abin da ya rubuta.
Laraba ta wurga masa harara a fakaice, ta koma ta tsaya ta haɗa rai domin ko kaɗan ba ta san raini. Tana daga tsaye wasu daga cikin 'yan ajin suka dinga yi mata gwalo, wasu kuma suna tsokanar dukan da aka yi mata. Malam Sule subject ɗin English language yake ɗaukarsu. Kuma a ranar Comprehension ya yi musu, sai ya rubuta musu short story mai taken 'Tortise and the goat' kasancewar duk cikin ajin babu mai textbook. Sai da ya karanta da turanci sannan ya fassara musu da hausa, ya dubi Laraba da tun da aka fara karatun hankalinta yana kan ƙofa, tana kallon dukan makarar da ake yi wa sauran ɗalibai. Don ko bayanin da ya yi da hausa ba ta gama saurare. Malam Sule ya haɗe rai ya ce.
"Maza biya mana, ki fara yi da turanci sai ki fassara."
Shiru laraba ta yi tana bin allon da kallon, don ta tabbata da allon yana magana ƙila zai iya baya mata kansa saɓanin ita da babu abin da ta gane sai baƙaƙen a b c d, su ma idan da za a saka mata wuƙa a wuya ko guda goma ba za ta iya karantawa ba.
Laraba ba ta yi tsammani ba ta ji ya zuba mata bulala a baya, don haka ta taƙarƙare ta fara yi masa wani irin yare wanda ita kansa ba ta san me yake nufi ba. Duk yadda Malam sule ya kai ga mazewa sai da ya kawar da kai ya saki murmushi, sannan ya ce ta fassara da hausa. A nan ma Laraba babu tsiyar da ta tsinana, sai sokiburutsu da ta dinga yi masa. 'Yan ajinsu kuwa suka shiga ƙyaƙyata dariya suna yi mata ihu, Laraba ta ƙulu sosai don haka ta yi kukan kura ta faɗa kan Suwaiba ta rufe ta da duka, don ta fi jin haushinta dama saboda har gwalo take mata tana raɗawa na kusa da ita abin da za su faɗa. Da sauri Malam Sule ya fisgo Laraba saboda ya yi mata maganar duniya ta ƙi ji, ya shiga dukanta da zafafe. Zuciya ta kuma ciwo Laraba ta sake cukumo Suwaiba, tana kai mata naushi a baki har sai da ya fashe. Malam Sule mari ya zabga kata, sai a lokacin Laraba ta ja da baya ta dube shi a haukace cikin ɓacin rai ta ce.
"Kai malam kada ka sake dukana, wai ba kai ne ɗan gidan Bala mai satar agwagwa ba ko an faɗa maka ba mu sani ba." Wani abu ne ya caki zuciyar Malam Sule, saboda bai taɓa tunanin za ta yi masa wannan bankaɗar ba. Cikin borin kunya ya rufe ta da duka, sai da ya zane Laraba sannan ya riƙe hannunta ya dinga bin ajujuwa da ita, yana saka kowanne prefect ya yi mata bulala biyar kuma 'yan aji su yi mata ihu. Ranar zuciyar Laraba ta gama dagulewa, don haka ta ci alwashin ko sama da ƙasa ce zaata haɗe ba za ta ƙara zuwa makarantar ba. Kuma sai ta hukunta iyaye da 'ya'yan da suka ci zarafin, shi kuma Malam Sule ta ci alwashin sai ya yabawa aya zaƙinta a wurinta.
Duk irin zaman doya da manjar da suke yi tsakanin matan Yaya Inu, sai da suka ji jikinsu ya
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 3 Chapter of 24