ya gani ya sa yaron ya miƙe a zabure yana ihu ya shige ɗakin mahaifiyarta.
Tun da Mai gari ya fisgi hijabin Inna, ba shi ya tsaya a ko ina ba sai a uwar ɗakin Salame a can ƙarƙashim gadon ƙarfenta. Ya shiga sauke numfashi da ƙyar yana muzurai, hannunsa ya kai wurin wandonsa ya ji ya yi sharkaf. Jiki yana karkarwa ya zura kansa cikin hijabin Inna ya ce.
"Salame ina jin fa gudawa na yi, wallahi har yanzu ji nake abu yana tsiyaya a jikina kamar an kunna fanfo."
Inna da kunya, haushi da baƙincikin Mai gari suka cika ta murya a dakushe ta ce.
"Ai kana da hannu ko?Sai ka yi ƙoƙari ka kashe fanfon."
A razane Mai gari ya ɗago, sai a lokacin idanunsa suka sauka a kan fuskar sirikarsa. Ya fito daga ƙarƙashin gadon a guje, yana zuro kai ya ga Laraba ta ƙwalla wata irin ƙara ta yanke jiki ta faɗi. Daga Mai gari har ragowar mutanen garin da suke leƙowa tsaye suka yi suna kallonta, aka rasa wanda zai tunkare ta ballantana ya yi yunƙurin tashinta. Laraba ta ɗan jima a haka sai kuma ta fara buɗe idonta a hankali tana salati, tashi ta yi zaune tana kalle-kalle kamar mai neman wani abu ta ce, "Kai, waye ya kawo ni nan?"
Shiru gabaɗaya suka yi mata, ta tunkari wurin mai gari a ɗan razane ta ce.
"Mai gari me nake yi a nan?"
Baki yana rawa Mai gari ya ce, "Ni ma tambayar da nake son yi miki kenan, amma yanzu ki fara zuwa gida tukunna."
Laraba ta saki murmushi a fakaici ganin yadda duk ya birkice, sannan ta fito ta nufi hanyar gida. Kamar sun ga sabuwar hallita haka mutane suka dinga bin Laraba da kallo, ita kuwa ta maze tana tafe tana hura hanci tana buɗa kafaɗa har ta je gida.
Baba Inu yana shiga gida kai tsaye ɓangarensa ya nufa, tun daga bakin ƙofa ya tsaya ya yi gyaran murya yana haɗe fuska, lokaci ɗaya yaran suka fara shiga taitayinsu. Iyayensu kuma suka shiga tsawatarwa 'yan ƙananun da ba su yi wayo ba.
Larai ce da girki ranar, a tsakiyar gida ta ajiye tukunyar abincin rana sai ƙanana da manyan kwanuka birjik a gabanta. Waɗansu ƙananan yara ne kusan su huɗu waɗanda ba su wuce shekara ɗaya zuwa da rabi ba, biyunsu riƙe suke da kwanuka suna kukan yunwa suna kama zanin Larai.
"Gaskiya Indo ba kwa kyauta mini, da wanne zan ji? Da aikin abinci ko da waɗannan yaran. Ke Kulu zo ki janye mini su don ubanki!" Ta ƙarasa maganar a fusace ta fisge kwanukan hannun yaran.
Baba Inu ne ya ƙarewa tukunyar kallo, ya matsa gabanta a kausashe ya ce.
"Ke Larai satar mini abinci kika yi? Kika ƙara a kan wanda na ɗebar muku, da na ga kin rafka wannan rafkekiyar tukunyar?"
Jiki yana rawa Larai ta buɗe tukunyar ta ce.
"Mai gida tukunyar girkin ce ta ɓule shi ya sa na ɗora wannan." Leƙa tukunyar ya yi ya hango abinci a can ƙasan tukunyar sannan ya sauke ajiyar zuciya ya wuce ɗakinsa.
Mukulli ya saka ya buɗe, ya ɗauko wata 'yar madaidaiciyar tukunya ya miƙa mata yana daga tsaye ya ce.
"Maza ɗumama mini miyar nan." Da sauri Larai ta karɓa ta ɗora a kan murhun, Baba Inu ya koma kan benci ya kasa ya tsare yana ganin yadda take rabon abinci. Kowanne kwano idan ta ɗauko bai fi ta yafita ludayi ɗaya da rabi ba, saboda idan da sabo sun saba a kullum abincin ba isarsu yake yi ba.
"Mai gida a zuba maka kana marmarinsa?"
Larai ta tambaya tana gyara goyon Fure da ke bayanta.
"A'a ku ci kawai!"
Baba Inu ya furta a daƙile. Larai ta ɗebi ragowar wanda ta rage masa cikin murna ta shiga ƙara wa kwanonta.
"Ke Larai wallahi son zuciyarki yawa gare shi, ba za ta saɓu ba wallahi sai kin ƙara wa kowa." Hansatu ta yi caraf ta yi maganar ganin abin da Larai take yi. Babu yadda ta iya ganin Baba Inu yana wurin ya sa ta shiga ƙarawa kowanne kwano bai fi cokali ɗaiɗai ba. Bayan ta gama ta ce kowa ya ɗauka, a guje yara da 'yan matasan cikinsu suka ɗauka da sauri, wasu tun a tsaye suka fara zuba loma duk da abincin yana ƙona su.
Ƙamshin ɗumamen miyar ne ya fara dukan hancinsu, Larai ta sauke har za ta kai masa ɗaki Baba Inu ya ce ta kawo gaban bencinsa ta ajiye. Abu da ke da tsohon ciki wani irin ƙwaɗayi ya taso mata. Kwanon abincinta ta ɗauka ya ƙarasa wurinsa cikin marairaicewa ta ce.
"Don Allah mai gida ko man miyar ne, ka taimaka ka yafa mini na ci ko na samu sauƙin abin da nake ji. Wallahi ƙwaɗayi ne ya addabe ni."
Wani banzan kallo Baba Inu ya yi mata ya ce. "Cewa aka yi idan ba ci ba za ki mutu?"
Abu ta yi saurin girgiza masa kai, Baba Inu ya sake haɗe fuska ya ce.
"To yanzu baƙincikin wanda zan ci kike yi? Idan kuma ba na cin mai maiƙon, ta ya ya zan iya samun ƙwarin jikin nemo muku abincin da kuke ci." Abu ta haɗiyi yawu tana kallon farantin da Baba Inu ya zuba miyar da ƙirjin kaza, sai da ya rufe tukunyar ya miƙa wa Larai ta mayar masa ɗaki sannan ya ce, "Wallahi ba don cikin jikinki ba, da idan ba ki matsa daga kaina ba sai na sheme ki. Dubi yadda kike ɗebo mini fuska kamar an matse lemon tsami."
Abu babu yadda ta iya, haka ta ja jiki a sanyaye ta koma ƙofar ɗakinta ta zauna.
Ƙaton biredi ya ɗauko ya gutsira sannan ya mayar ya saka kwaɗo ya rufe ɗakin nasa. Kan bencin ya koma ya fara yagar biredin yana dangwalar miyar da ita, daga yaran da suke wurin har iyayensu ban da haɗiyar yawu babu abin da suke yi. Wani ɗan ƙaramin kwanon sha ya buɗe kusan cike yake da nono, ya zura hannu a aljihu ya zaro wani ƙullin maganin ƙarin kuzari da ya saya a daren ranar. Ragowar ƙullin ya kunce ya zuba ya jujjuya ya ajiye shi a gefe, ya ci gaba da yagar kazar yana dangwalar biredi da miya.
Baba Saleh sai da ya gama loda duka magungunansa a cikin mota sannan ya koma gida, domin ya yi wa Ɗan Bishir sallamar tafiya yawon tallar magani.
Yana shiga sashensa, ya samu ɗan bishir yana tsanyara ihu kamar wanda ake ƙwaƙwalewa idanu. Wani irin bugu ƙirjinsa ya yi, kamar wanda ya yi tozali da gawar mahaifiyarsa. A hargitse ya janyo Ɗan Bishir ya rungume yana jin zuciyarsa tana zafi ya ce.
"Ɗan bishiririna, waye ya taɓa ka? Me aka yi maka?"
Ɗan Bishir ya sake narkewa yana wani tale baki irin na shagwaɓaɓɓun yaran da aka sangarta ya ce.
"Innaaaaaa! Inna ce ta dungure mini kai. Wayyo Allah kaina."
Jikin Baba Saleh har karkarwa yake, saboda a duk duniya idan da abin da yake ɗaga masa hankali ganin kukan Ɗan Bishir. Ya nuna Uwale idanu cike da masifa ya ce.
"Sau nawa zan ce ki daina zalintar yaron nan Uwale? Ke wacce irin uwa ce kamar ba ke kika haife shi ba tsabar rashin imani, wallahi ba don kin ci darajar ke kika haife shi ba yau sai ranki ya yi mummunan ɓaci."
Ran Uwale ya gama ɓaci ta nuna masa randar ruwan da suke sha ta ce.
"Wallahi Mai gida wannan abin da kake yi ba soyayya ba ce, ɓata tarbiyyarsa kake yi. Dubi fa randar ruwan shan mu ya ɗauki omo da mai ya zuba mini, don na dungure masa kai kake yi mini wannan tijarar? To wallahi na gaji, na gaji da wannan abin da kake yi mini. Kai kuma don ubanka ko yau ka sake yi mini irin wannan ɓarnar sai na dungure ka." Uwale ta ƙarasa maganar tana sakarwa Ɗan Bishir ƙozo a ka. Wata irin gantsarewa ya yi yana canyara ihu tamkar wanda aka caka wa wuƙa, a fusace Baba Saleh ya kai wa randar duka ta bada tus! Ruwanta ya mamale a tsakar ɗakin, cikin ƙaraji ya ce.
"Ba dai a kan randa za ki illata mini Ɗan Bishir ba? To wallahi idan ba ki da gaske ba, yadda na ragargaje randar nan kema sai na ragargaza ki."
Baba Saleh ya yi furcin yana sunkutar Ɗan Bishir da zai yi shekara shida a tsaye, ya ɗauke shi yana shafa bayansa zuwa kansa yana lailaya shi kamar zai mayar da shi ciki. Ya rungume shi a ƙirji cike da so, ya waiga yana wurga wa Uwale mugun kallo. Har lokacin Ɗan Bishiri bai daina tale baki yana kuka a shagwaɓe ba, Baba Saleh ya kalle shi har lokacin zuciyarsa zafi take ya ce.
"Me kake so ka ci Ɗan Bishirina."
Ɗan Bishir ya wale baki yana duban mahaifiyarsa tana mata harara sannan ya ce.
"Namaaaa!"
Baba Saleh ya sauke shi ya ce, "Don nama banza Ɗan Bishir, bari na je na yanko maka na zabi ko kaji."
"Na zabiiiiiiiiii."
Ɗan Bishir ya faɗa a sangarce.
Harara ya wurga wa Uwale sannan ya fice daga sashensu, yana zuwa ƙofar gida ya yi turus ganin abokinsa Sani yana ba wa yaro sakon a kira shi.
"Ga ni na zo a daidai ya aka yi?"
Sani ya ƙare masa kallo tun daga sama har ƙasa, sannan ya sauke idonsa a kan jakar wanzaman da ke rataye a kafaɗar Baba Saleh.
"Karenka ya kai tsaiko ko Sale? Wai har ni za a kira na cire beli na yi wa jaririya aski, amma sai na ji labarin ka yi mini shigar ɓurtu alhalin ka sani ni ɗan gado ne a harkar wanzanci ba ɗan ka-ta-haye kamar kai ba?"
Baba Sale ya saki tsaki cikin halin ko-in-kula ya ce.
"To mene ne marabar dambe da faɗa? Don kana ɗan gado ka koya mini harkar wanzanci, na zo ni kuma Allah Ya saka mini nasibi duka costomers ɗinka sun dawo wurina wani avu ne? Wai ma da kake wannan abin, kai da kake jin ka ɗan gado da ni ta-ka-haye ba duka wanzamai za a ce mana ba? Kai matsa ka ba ni wuri Ɗan Bishiri ya aike ni, don aikensa ya fi mini wannan sokiburutsun banzan da kake yi mini."
Baba Sale ya gegara ya wuce shi, ya nufi wurin Sadau mai nama.
Bayan fitar Baba Saleh cikin takaici Uwale ta ɗauko zani ta shiga tsane ruwan tana matsewa. Mugun kallon da take jifan Ɗan Bishir da shi ya sa ya yi saurin ficewa daga ɗakin. Kai tsaye sashen Baba Inu ya nufa don tun da ya ji shiru ya san abinci suke ci. Ɗan Bishir irin kwaɗayayyun yaran nan ne da duk abin da suka ga ni, za su ce suna ci koda a hannun babba ne. Sangartar da Baba Sale ya yi masa ce ta sa ya koyi wannan mummunar ɗabi'ar. A lokacin da ya shiga sashen Baba Inu da bencinsa ya fara cin karo, ya hangi Baba Inu a can ƙofar ɗakinsa yana rabawa yaransa waɗansu ƙananun alewa.
ragowar naman kazar da ya gani ya saka hannu ya ɗauka, ya kai ba ki ya fara zuge tsokarta yana lumshe ido. Sai da ya gama cinyewa tas, sannan ya ɗauki kindirmon nonon da Baba Inu ya zuba magani ya ɗaga kansa ya ɗaɗɗaka, a shagwaɓe ya wurgar da kwanon ƙasa bayan ya shanye ya ɗauki ƙashin kazar ya fara tauna.
Ƙarar jefar da kwanon ce ta ja hankalin Baba Inu, da yara da suke gabansa. Ganin abin da Ɗan Bishir ya yi ya sa Baba Sale ya ƙarasa wurinsa rai a ɓace ya kai masa duka a baya.
Ɗan Bishir ya tale baki a shagwaɓe ya saka kuka yana yi wa Baba Inu daƙuwa haɗe da faɗin.
"Uwakaaaa!"
Zuciyar Baba Inu ce ta fara tafasa, ya saka hannu zai dake shi da sauri Ɗan Bishir ya fita da gudu yana faɗin.
"Allah Ya isa."
Zucya tana tafasa Baba Inu ya rufa masa baya, suna zuwa mararrabar hanyar da take haɗa kowa da ke cikin gidan ya samu nasarar cafko shi, bai yi wata-wata ba ya tsinke shi da mari. A daidai lokacin Baba Sale ya ƙarasa wurin, ganin abin da aka yi wa Ɗan bishir ya sa shi wata irin zabura a haukace ya yi kukan kura ya tunkari wurin da suke tsaye.
Share pls
07062062624
Ummou Aslam Bint Adam🌚
[02/02, 15:02] Ameerah Adam🌚: *GIDAN LIKITOCI*
©®AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITERS ASSO...*
Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye.
*MARUBUCIYAR:*
MARWAN
JARIRI
ASEELA
BAƘAR DAULA
AN YA BAIWA CE?
ƊAN BA ƘARA...
SHU'UMAR MASARAUTA
DUBU JIKAR MAI CARBI
UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA
YAWON SALLAR HAJIYA IYA
ZAUJATU JINNUL-ASHIQ
SANADIN RAGON LAYYA
SHAFI NA UKU
Jikin Baba Sale har karkarwa yake yi, ya ƙarasa wurinsu ya suri Ɗan Bishir da ya gantsare yana wani irin ihu da kuka, rungume shi ya yi tsam a ƙirjinsa ya shiga lailaya masa baya yana sasshafa shi. Lamo Ɗan Bishir ya yi yana sauke ajiyar zuciya don dukan da Baba Inu ya yi masa ba ƙaramin shigarsa ya yi ba, Baba Inu ya dube su rai a ɓace ya ce.
"Idan ubanka bai koya maka tarbiyya ba, ni idan ka shigo gonata ladaftar da kai zan yi. Shashashan banza da wuri, yaro ya duk ya bi ya sangarce kamar tasowar gidan gwauro."
Ran Baba Sale ne ya sake ɓaci, saboda dama ba ya ƙyale shi ba ne. Yana jiran ya gama lallashin Ɗan Bishir ne kafin ya dawo kansa. A hankali ya dire Ɗan Bishir, ya sunkiya ya yi masa raɗa a kunne.
"Tsaya a nan zan rama maka ka ji Ɗan Bishiririna!"
Ɗan Bishir ya kwaɓe baki a shagwaɓe ya ce.
"Da ƙarfi za ka rama mini."
Baba Sale ya gyaɗa masa kai, sannan ya tunkari Baba Inu da ya juya baya yana shirin shiga sashensa. Wani irin kukan kura ya yi haɗe da sufa sai ya yi tsalle ya ɗafe masa wuya, maƙure shi ya yi sosai ya shiga kai masa duka yana harbo shi da ƙafarsa. Jin irin shaƙar da Baba Sale ya yi masa ya sa Baba Inu ya zuciya ya wulwulo shi ya damfara shi da ƙasa, a galabaice Baba Sale ya yarfe hannu yana dafe ƙugu ya ce, "Wayyo Allah Uwale ki zo ya karya ni."
Ihun da Baba Sale ya saki ne ya janyo hankulan mutanen gidan, ba a ɗauki lokaci ba mutane suka cika wurin kowa ya yi carko-carko.
"Subhanallah me yake faruwa Sale?"
Baba Ibrahim ya tambaya a razane, don irin ihun da Baba Sale ya yi za ka ɗauka farke masa ciki ake yi.
Yana daga kwance ya ɗaga hannu yana fitar da numfashi da ƙyar ya ce, "Yaya Inu ne yake ƙoƙarin datse rayuwata da ta Ɗan Bishir, don Allah ku nesanta mu da shi kada ya hallaka mu." Ajiyar zuciya Baba Ibrahim ya sauke, Baba Inu ya yi kicin-kicin ya haɗe rai yana hura hancin yin galaba a kan Baba Sale.
"Don Allah Yaya me kuke yi haka kamar ƙananan yara? Kai ne babba fa, ko me Sale ya yi maka ba sai ka rabu da shi ba ko ka yi masa faɗa. Amma yanzu ina daɗi a ce yara suna ganin irin wannan abin da kuke yi? Ta ina yara za su haɗa kansu?"
Baba Ibrahim ya rufe su da faɗa, saboda lamarin gidan nasu a kullum ƙara taɓarɓarewa yake yi. Baba Inu ya dube shi a sheƙe ya ce, "Kai Iro, dube ni da kyau ka kalli ƙwayar idona."
Baba Inu ya yi maganar yana ware dara-daran idanunsa da girma ya sa suka fara shigewa, sannan ya ɗora da cewa.
"Wane ne wannan?"
Ya tambayi Baba Ibrahim yana nuna Ɗan Bishir.
"Ɗan Bishir ne!"
Baba Ibrahim ya ba shi amsa.
"Yanzu Iro ko Sale ya isa ya zage ni ballanta wannan yaron mai zubin buhun bagco!"
Duka mutanen wurin suka girgiza kai cike da son ƙara ingiza Baba Inusa, saboda kowa ya san rashin kunyar Ɗan Bishir don haka yake da baƙin jini a wurinsu.
Nan take Baba Inu ya ba su labarin abin da ya faru, da abin da Baba Sale ya yi masa. A razane Baba Sale ya miƙe jiki yana karkarwa, ya nufi hanyar sashensa da gudu ganin Ɗan Bishir ya yi hanyar, ya rarumo shi ya riƙo shi sai kawai ya ɓarke da kuka. Kallonsa suka tsaya yi suna mamakin kukan da yake yi, ya tako wurinsu a guje yana saɓule burmemiyar doguwar rigar Ɗan Bishir ya ce.
"Jama'a ku taimaka mini Ɗan Bishir ya sha maganin ƙarin kuzari, wayyo Allah yaya don Allah ka kawo mini ɗauki." Ya ƙarasa maganar yana miƙa wa Baba Ibrahim shi sannan ya ɗora da cewa.
"Don Allah ka yi masa wani abu yaya kai ne likita, Allah Ya sa ba ajali ne yake kiransa ba ban da haka ina Ɗan Bishiri ina shan maganin kuzari?"
Yana gama maganar ya sake ɓarkewa da kuka.
"Ka ga Sale kada ka ɓata wa kanka lokaci, idan har kana son rayuwarsa ka ba ni wani abin ni kuma zan ba ka lambar mai maganin sai ka nemi makarin maganin a wurinsa. Bokan turai ta ina ya san abin da aka haɗa?"
Baba Inu ya yi maganar yana sakin murmushin ƙeta.
Baba Sale ya yi zaman 'yan bori a wurin ya ce, "A kan Ɗan Bishir zan iya sadaukar da komai da na mallaka, Yaya nawa zan ba ka don Allah ka ba ni lambarsa."
Baba Inu ya ɗauke kai gefe cikin basarwa ya ce.
"Dubu ashirin!"
A firgice Baba Sale ya ce, "Ashirin fa Yaya?"
Baba Inu ya yi gaba abinsa cikin halin ko-in-kula ya ce. "Kada ka biya matsalarka ce, ni ko yanzu na mutu akwai masu yi mini addu'a da yawa."
Jin haka ya sake ɗaga hankalin Baba Sale, ya janyo ƙafarsa yana ba shi haƙuri, babu yadda ya iya haka ya shiga cikin gida ya ɗauko dubu ashirin ya damƙa masa. Sannan Baba Inu ya karanto masa lambar mai maganin, jikin Baba Sale har rawa yake ya yi masa bayanin abin da ya faru. Mai maganin ya tabbatar masa da babu abin da zai faru da shi, sai dai ya ja hankalinsu a kan su dinga lura sosai saboda kar gaba a samu matsala.
Ɗaya bayan ɗaya suka fara watsewa, Baba Inu ya koma sashensa zuciyarsa fes don shi wannan abin da ya faru ya zame masa alkairi.
Yana nan zaune ya ji sallamar Malam Jibrin, jin haka ya sa ya dubi su Abu a kausashe ya ce.
"Ke Abu da fatan kun haɗa wa yaran nan kayansu ko? Ga sallamar Malam Jibrin can na ji, bari na je mu gaisa."
Tun da Baba Inu ya fara magana ta haɗe fuska, saboda Allah Ya sani ba za ta iya bayar da yaranta a kai su makarantar allo ba.
Yana zuwa ƙofar gida ya samu Malam Jibrin, daga gefe wata ƙatuwar motar Bus ya gani kusan rabin motar cike take da yara waɗanda za a kai makaratar allo. Bayan sun gaisa Malam Jibrin ya ce. "Malam Inu ina fatan an gama kintsa yaran? Saboda direban motar sauri yake akwai sauƙon da ake jira zai bayar a hanya." Yaya Inu ya faɗaɗa fara'arsa yana jin kamar za a sauke masa wani gingimemen nauyi daga kansa ya ce.
Malam Jibrin ba ka da matsala yanzu za su fito, amma fa an samu ƙarin yara uku." Shiru Malam Jibrin ya yi ya ce, "Yaran kuwa ba su yi yawa Malam Inu? A baya fa yara shida ka ce za a tafi da su. Idan mun yi gaba akwai 'ya'yan Malam Sallau guda biyu da za mu ɗauka."
Duk da yana jin zafin fitar kuɗin amma sanin sauƙi zai ƙara samu ya sa ya zaro dubu uku ya miƙa wa Malam Jibrin ya ce, "A ƙara da wannan Malam Jibrin, ka sha ruwa a hanya, ka san yaran ne duk kansu ɗaya. Da su Barau masu shekara huɗu zuwa biyar ne zan bari amma su ma ai sun tasa, Allah na tuba abu da girman ɗan mutum babu wuya."
Malam Jibrin ya kalmashe dubu ukun saka a aljihu yana murmushi ya ce, "Yo shekara huɗu mene ne ba za su iya yi wa kansu ba? Ai duka sun tasa, kuma Allah ai shi yake raya bawa ba mutum ba."
A daidai wannan lokacin Malam Isiya ya ƙarasa da ɗansa Musbahu mai kimanin shekara goma sha biyu, hannunsa riƙe da ƙaton buhu wanda ya haɗa masa ƙanzo, garin kwaki, sabulu da omon wanki. Bayan sun gaisa da Malam Isiya, ya kawo 'yan kuɗi ya ba shi. Malam Jibrin ya ce, "Malam Isiya ya na ganka da ƙaton buhu bayan jakar hannunsa, akwai yaran da za mu ƙara a motar fa."
Malam Isiya ya yi murmushi ya ce, "Kayan abincinsa ne a ciki, ai ba ka da damuwa Malam Jibrin zan biya kuɗin kujera biyu, don tare za mu tafi. Saboda na je na ga mkarantar da za a kai Musbahu, mu gaisa da malamin kafin daga baya lokaci zuwa lokaci na dinga zuwa ina gano shi ina kai masa kayan abinci."
Malam Jibrin ya kalli Musbahu ya ce, "Lallai Musbahu kai ɗan gata ne, abin da iyaye da dama ba sa yi kenan! Kai ma Malam Isiya Allah Ya sa da gaske kake."
Malam Isiya ya ce, "Me ka ɗauke ni Malam Jibrin? Ai yayansa Ɗahiru da ke garin Kaduna yana karatu, duk bayan wata biyar nake zuwa wurinsa, domin na ga halin da yake ciki kuma na kai masa kayan abinci da 'yan kuɗaɗen sayen abin buƙata. Kawai kuma saboda ka kai yaro makarantar allo sai ka manta da shafinsa? Yara fa amana ce da Ubangiji Ya damƙa mana kuma ranar Lahira sai ya tambaye mu a kan kiwon da ya ba mu."
Malam Jibrin ya jinjina kai, Yaya Inu yana jin haka ya zame ya shige gida yana faɗin zai haɗo kan yaran su tafi. Saboda sho ko ɓarin gyaɗa babu wanda zai ba wa a cikinsu, abin da yake ciyar da su ma Allah amfana.
Yana shiga tsakar gida ya ci karo da su Basiru kowanne ɗauke da ƙaton buhu a kansa, iyayensu ne suka ɗauko ƙanzo da garin kwakin da suka tanadar musu.
"Ku yi sauri ku shirya su Barau, Idi da Iro ƙarami, su ma da su za a tafi."
Sororo suka yi jiki a sanyaye Larai ta ce, "Don Allah malama..."
"Wallahi sai an tafi da su, tun da na rantse babu kaffara. Idan sun zauna yaran uwar me za su yi musu? Kun fi son yara su zauna babu ilimi mutanen gari su dinga zagina."
Sanin halinsa na kafiya ya su Larai suka shiga shirya ƙananan yaran kowacce tana share hawaye, ban da Abu da ta ja ta tsaya ta ki motsawa.
"Ke ba ki ji abin da na faɗa ba ne?"
Yaya Inu ya faɗa
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 24