ba shi!" Uwani ta furta cikin rashin damuwa.
"Rance fa? Ta ya ya zama rance bayan a kan idona kika ba shi?"
"Allah Inna kada ki damu zai dawo miki da kuɗinki har ma ya ƙara miki wasu." Jin sokiburutsun Uwani ya sa Maryama ba ta sake bi ta kanta ba saboda takaici.
"Maryama yaya aka yi kika bari har ya ga lokacin da aka ba ki kuɗin nan? Kin fa san halin mutumin nan sarai, ba shi da tausayi ko kaɗan." Indo kishiyar Maryama ta furta ƙasa-ƙasa.
"Ai kin san tun da ya gan su ya san za su ba ni wani abu, kuma ragowar ma ba ni na ba shi ba yarinyar nan ce ta ba shi." Maryama ta furta. Suka gama jajantawa juna, don zaman da suke yi sam babu kishi a ciki saboda dukkansu ba wani daɗin zama da shi suke ji ba.
Wuni ɗaya da Uwani ta yi a gidan ta fahimci irin zaman ƙuncin da mahaifiyarta da kishiyarta suke yi a cikin gidan, a kan idonta ta ga Aramma ya yo cefane har da nama ya ce a yi masa jar miya da shi. A yadda ta lura hatta abinci ma daban ake yi masa, su kuma duk kwamacalar da ya ga dama sai su dafa. Don abincin dare sai da ƙyar Uwani ta iya cin miyar kukar da aka kaɗa, saboda haka ta ci alwashin gyara masa zama kafin ta bar gidan.
Tun da doshin magriba Uwani ta hangi wani ludayin silba a kwandon wanke-wanken mahaifiyarta, a fakaice ta ɗauke shi ta ɓoye sai da dare ya tsala kowa ya yi bacci sannan ta saci jiki a hankali. Har za ta fita ta hangi wani zumbulelen farin hijabin Inna Suwaiba, wani tunani ne ya faɗo mata da sauri ta saki murmushi. Ta figi hijabin a hankali ɗayan hannunta ɗauke da ludayin sulba, can hanyar soro ta nufa da yake a baki-bakin ƙofa turakar Aramma take, daga ɗakinsa kuma sai ɗakin da suke ajiye kayan abinci. Toka ta ɗiba ta bursune fuskarta da ita sannan ta saka zumbulelen farin hijabin, ta leƙa ɗakin ta hango Aramma a kwance ya sharɓe sai sakin munshari yake yi daga shi sai gajeren wando. Da yake irin mutanen nan gajeru masu ƙiba ga uban tumbi. Tana shiga ɗakin ta tsaya a kansa, sai da ta gimtse dariyarta sannan ta daidaici gefen goshinsa ta ba shi raaaal da ludayin hannunta. A firgice Aramma ya miƙe yana dafe da goshi, "Wane ɗan iskan ne a tsohon daren."
"Tawagar fatalwar 'yan iskan lahira ne!" Uwani ta faɗa da wata irin murya, ta sa hannu ta cikin hijabin ta buɗa shi, sai ta ƙara faɗi ta cikinsa. A razane Aramma ya ja da baya ganin hallitar da ke tunkaro shi.
"Mu sababbin ƙawayen 'yarka da ta baƙunci lahira ne. A cikin fatale ma mu tawagar shaiɗanu ne domin fatattaka ɗan adam muke yi da kulkin lahira. Ita da bakinta ta gaya mana irin zalincin da kake yi wa iyalinka, don haka muka zo domin mu tsintsinka hanjin cikinka, ko kuma mu gayyato 'yan uwanmu mu yi daga-daga da kai." Uwani ta yi magana tana wani miƙa wuya gaba.
Jin kalaman Uwani ya sa Aramma ya fashe da wani irin kuka mai cin zuciya, cikin tashin hankali ya ce.
"Ku dubi Allah ku yi haƙuri wallahi zan daina duk abin da nake yi..." Da sauri Uwani ta katse shi.
"Zo nan maza-maza, matso nan."
"Don Allah ku yi mini rai." Aramma ya faɗa fuska haɗe da hawaye da majina.
"Za fa ka taka ɗan tsiti a bayanka, wallahi tawagarsa ta fi ta mu bala'i ka matso na ce maka." Da sauri Aramma ya matsa tiɓi-tiɓi sai haɗa gumi yake. Yana zuwa ya tsugunna a ƙasa, hannun Uwani mai ɗauke da ludayin da ke cikin hijabi ta ɗaga da sauri ta sake ba shi raaal a ƙeyarsa. A zabure Aramma ya miƙe sai da ya yi tsalle uku ya faɗi a can gefe cikin azaba.
"Fatalwar 'yarka ta gaya mana duk abin da matanka suke samu karɓe musu kake yi, a jiya ma ka karɓe wa uwar marigayya kuɗaɗenta to ko ka mayar mata da abin ta ko kuma mu mayar da kai kuɗi. Domin muna cikin irin fatalwar da ke yi wa 'yan ƙungiyar asiri aiki, za ka zama kuɗi wayyo kuɗi, kuɗi masu daɗi." Uwani ta yi maganar tana wani tsalle tana ɗaga hannu ta cikin hijabi kamar mai shirin tashi sama.
"Na rantse da Allah ko wasu aka ce na ƙara mata yanzu zan ƙara mata su." Uwani ba ta bi ta kansa ba ta ce.
"Da ma ga hantarka da zuciyarka nan muna gani manya ne, ko su kaɗai muka tsaface za ta kawo mana miliyoyi." Da sauri Aramma ya dafe cikinsa da hannuwansa biyu, ya sake ɓarkewa da kuka.
"Idan ka sake ka tona mana asiri wallahi a yanzu za mu hallaka ka." Jin haka ya sa Aramma ya haɗiye kukansa, ya sa hannu biyu ya toshe bakinsa. Uwani ta sake jingina da bango ta furta. "Ganin yadda muka ga ka yi nadama za mu ɗaga maka ƙafa na kwana biyu mu ga idan za ka sauya halinka, kuma ka gaggauta mayarwa da mahaifiyar 'yar uwarmu kuɗinta. Sannan ita da kishiyarta dole ne ka ƙara musu dubu hamsin-hamsin. Kuma ya zama wajibi duk sati ka dinga ba su dubu uku-uku na kashewa."
"Duka na ji kuma na yi alƙawari zan yi yadda kuka ce, na gode muku Allah Ya biya ku." Aramma ya yi maganar yana rissinawa.
"Ba ma buƙatar godiya, yanzu dai za mu tafi da kai ka je ka ga makwancin 'yarka, sai mu baro ka a can bayan sadakar uku sai mu dawo..."
Tun Uwani ba ta gama magana ba ya katse ta cikin kuka.
"Wallahi na haƙura da ganin ta, Allah ba sai na ga halin da take ciki ba. Na san mai sunan Iya tana da halin na gari."
"To kuwa ya zama wajibi ka zaɓi ɗaya, ko mu ɗauke ka ta ƙarfin tsiya mu tafi da kai. Ko kuma ka zo ka ku yi sallama da shugabar tawagar 'yan iskan fatale." Jin haka ya sa jiki na rawa ya matsa gaban Uwani ya ce.
"Zan gaisa da ita..." Maganar bakinsa ta katse sakamakon jin saukar ludayin da ya yi a gaban kansa. Wannan karon kasa motsi ya yi ganin haka ya sa Uwani ta sake sauke masa na biyu aka sannan ta ɗora da cewa.
"Yanzu haka za mu fita mu ba ka wuri, sauran tawagarmu na tsakar gidan nan. Kuma duk abin da ka ji ko kuma duk hukuncin da ka ji muna aikatawa matuƙar ka leƙo to zai dawo kanka. Sannan saura idan gari ya waye ka ce ga abin da ya faru da kai." Daga haka Uwani ta fice tana wani shagiɗewa gefe tana tura wuya gaba.
Kusan duk abin da ya faru tsakanin Uwani da Aramma, Yaya ƙarama da su Rahane 'yan uwan Aramma sun ji, sakamakon ɗakin da suke kwance a jikin na Aramma yake. Da yake dama idan wani abin taro ya kama a gidan to duka danginsa a wannan ɗakin suke sauka. Kowannensu na daga kwance cikinsa ya ɗuri ruwa ko motsin kirki babu mai yi, babban abin da ya ɗaga hankalinsu yadda suka dinga jiyo kukan Aramma ƙasa-ƙasa, da ita kanta saƙon fatalwar da take faɗa. Suna nan kwance suka ji motsin Uwani a ƙofar ɗakinsu tana ɗan wani gurnani, take fitsari ya jiƙe zanin Yaya ƙarama. Uwani na ɗaga labulen ɗakin ta hango yadda aka jere yara a ƙasa, ɗaya bayan ɗaya haka ta dinga jidar yaran tana kai wa tsakar gida. Yaya ƙarama na daga kwance ta ji Uwani ta dafa ƙafarta, jiki na rawa ta ce.
"La'ilaha'illahu Muhammadur Rasulillah."
"Ba za ki mutu yanzu ba sai mu fafe ƙwayar idonki." Uwani ta faɗa da wata irin murya, har ta juya za ta fita ta ce. "Su kuma waɗancan yaran zan ba wa ƙananan fatalenmu umarni su gama da su." Uwani na ƙarasa magana ta wuce wurin yaran da ke kwance a tsakar gida, idan ta ɗauko yaro ɗaya sai ta gasa masa mintsini ta tura shi cikin ɗaki. Ganin yadda yaran ke shigowa a firgice cikin kuka ga magagin bacci ga kuma zafin mintsini, ya sa su Yaya ƙarama suka banka uwar ɗaki a guje. Uwani ta yi wata irin sufa ta rufa musu baya tana faɗin. "Ya Ahalul fataleeee ku zo ga nama mun samu."
07062062624
#Ummou Aslam Bint Adam🌚
[13/06/2024, 13:37] Ameera Adam: *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA*
©AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye.
SHAFI NA TARA
Sai a lokacin Uwani ta fahimci ashe ba iya su Yaya Ƙarama ce kaɗai idonsu biyu ba, hatta mutanen da ke cikin uwar ɗakin lakur suka yi sai da suka ji Uwani ta yi sufa za ta faɗo uwar ɗakin suka fara ihun neman ceton rai. A daidai bakin ƙofar uwar ɗakin Uwani ta tsaya sai ta hango wata wuƙa a gefen randa, ta janyo ta ta fara wasawa. Naziru ɗan wurin Sa'a da a lokacin ya wartsake ya kafe Uwani da kallo, ganin haka ya sa Uwani ta kalle shi tana zare ido ta ce.
"Ga wani ɗan ƙwage da shi za mu fara." Uwani ta ƙarasa maganar tana fusgar hannun Naziru da bai wuce shekara huɗu ba.
"Wayyo Iyata! Wayyo Iyata." Ya fara ihu hankali a tashe don ƙiri-ƙiri ya ga wuƙar hannun Uwani. Sa'a na ganin haka ta fara jan hannun Naziru Uwani na jan ɗaya, Sa'a ta waiga wurin su Yaya ƙarama ta ce. "Ƙarama don Allah ku kawo mini ɗauki Naziri zai tafi."
Yaya ƙarama da ke ƙuryar uwar ɗaki ta ce. "Sa'a ki haƙura da Naziru tun da ba wuce haihuwa kika yi ba, wallahi a yanzu ko Habibu (Shi kaɗai ne ɗanta) suka ja sai dai na bi shi da addu'a." Sa'a na shirin magana Uwani ranƙwala mata ludayi a ka, a guje ta saki hannun Naziru cikin kuka ta faɗa uwar ɗakin tana faɗin.
"Wayyo Naziru."
Shi ma Naziru sai tirjewa yake yana faɗin. "Iyata wayyo Iyata." Yaya ƙarama ce ta yi sauri ta banka ƙofar ɗakin ta danna sakata tana sauke ajiyar zuciya.
"Idan kun rufe ƙofa za mu ɓullo ta ƙarƙashin ƙasa, mu dama ai daga kabari muke. A wannan lokacin babu buƙatar mu yi muku bayanin mu su waye, domin hukunta ku muka zo yi ɗaya bayan ɗaya, a kan cin zarafin da kuke yi wa mahaifiyar 'yar uwarmu da kishiyarta. Mu tawagar fatale sai mun saɓule fatar jikinku sannan mu tsotse romo da ɓargon jikinku. Amma za mu ɗaga muku ƙafa zuwa nan da ɗan wani lokaci, don mun lura kun fara nadama. Sai dai muna mai tabbatar muku babu wanda zai tafi gidansa sai an yi sadakar uku, idan kuma mutum ya yi kuskuren tafiya gida gobe, to a daren ranar sai dai ya kwana a ƙiyama."
Uwani ta furta a lokacin da ta fita da Naziru tsakar gida da ke ƙwala ihu. A yadda ta lura kusan ilahirin mutanen gidan duka sun tashi, wata dabara ce ta faɗo mata don haka ta buga tsalle a tsakar gidan ta ce.
"Waɗanda kuke leƙenmu muna gano ku, ke wato har da ke ko. Wallahi ɗaya bayan ɗaya za mu bi ku mu ƙwaƙwale idanunku idan ba ku koma kun kwanta ba." Ta saki hannun Naziru ai kuwa da gudu ya faɗa ɗaki yana ihu, sai ta tafi da gudu ta nufi ɗakin mahaifiyarta, a guje ta ji mutanen ɗakin suna shigewa uwar ɗaki wasu na hantsilawa. Nan ma ta nufi ɗakin kishiyar mahaifiyarta ta razana su, sai da ta tabbatar da sun gama tsorata kowa ya shige uwar ɗaki sannan ta lallaɓa ta isa banɗaki ta wanke fuskarta. Ta duƙunƙune hijabin Inna Suwaiba ta soke a hammata, sai da ta shirya sosai sannan ta nufi ɗakin mahaifiyarta da gudu tana faɗin. "Wayyo Allah! Ku taimaka mini za su ƙara janye ni." Tana shiga ɗakin ta tarar falon mahaifiyarta babu kowa an banke uwar ɗaki sai ƙananan yara da ke kuka suna buga ƙofa, saboda kada a gano Uwani ita ma ta fara bubbuga ƙofar tana ihu. Da ta lura ba za su buɗe mata ba sai ta janyo ƙofar falo ta datse.
Har aka yi assalatu babu wanda ya yunƙurin fitowa daga ɗakin, duk da duka baƙin gidan a zuciyarsu kowa ya ayyana gari na wayewa tafiya zai yi. Amma da sun tuna kashedin da aka yi musu a kan kada wanda ya bar gidan har sai an yi sadakar uku sai jikin kowannensu ya yi sanyi. Sai da gari ya yi tangararan sannan Indo ta yi ƙarfin halin buɗe ƙofa, kamar sababin munafukai haka mutane suka dinga leƙowa ɗaya bayan ɗaya suna fitowa suna yin alwala suna sallah. Duk wannan abin da ya faru bayan da gari ya waye babu mutum ɗaya da ya jajantawa kowa, domin kowa a tsorace yake. Su Uwani suna zaune sai ga Aramma ya shiga ɗakin kansa ya yi waɗansu ƙulalai sun fi biyar, daidai tsakiyar hancinsa har wani ja ya yi yana maiƙo. Da mamaki suka bi shi da kallo, Aramma ya zauna daɓar jikinsa zafi zau da zazzabi. Gaishe shi mutanen ɗakin suka yi, suna son jin abin da ya faru da shi suna tsoro. Hannu ya sa a aljihu ya zaro kuɗin ya ce. "Ungo wannan Maryama, kuɗinki na jiya ne. Wannan kuma kyautar dubu hamsin ce na ba ki ita ma Indo zan miƙa mata nata." Baki sake Maryama ta bi shi da kallo, ta ce.
"Malam dubu hamsin fa? An ya ba mantawa ka yi ba?" Aramma ya dube ta a fusace da ya tuna gargaɗin fatalwa sai ya wayance ya sassauta murya ya furta. "Maryama shaidar da za ki yi wa mijinki kenan? Kyautatawa ce kawai ta sa na ba ku." Maryama hannu na rawa ta sa ta karɓa tana zuba masa godiya, Aramma har ya miƙe zai fita Inna Suwaiba ta ce. "Aramma ungo shafa-shafa sai ka shafa a malolon nan na ka, Allah dai ya sawaƙe sanyi haka yake lokaci ɗaya ka ga wuri ya luluye. Ko kuma bige wa ka yi ne da dare?" Aramma da ba ya son a ja doguwar magana ya karɓa ya yi gaba ba tare da ya amsa mata ba, ɗakin Indo ya faɗa ita ma ya sallame ta ya koma ɗakinsa don ilahirin jikinsa ciwo yake masa. Aramma na shiga ɗaki sai ga Indo jiki na rawa ta shiga wurin Maryama suka fara tattaunawa cikin mamaki, ba su ƙara nutsa wa a tekun mamaki ba sai da suka ji Aramma ya ce a yi shinkafa da miyar dage-dage da rana. Wannan sabon sauyi da suka samu daga wurin Aramma ba ƙaramin daɗi ya yi musu.
A na gobe Uwani za ta koma gida wurin ƙarfe goma sha biyu na dare ana zaune ana ɗan hira, ta hangi Aramma ya suri buta ya yi banɗaki. Sai da ta tabbatar da hankulan mutane ba ya kanta ta saci jiki ta nufi banɗaki, da yake banɗakin ya yi nesa da ɗakuna don haka ta laɓe a can kusurwar bango ta fara magana.
"Baba ga tawagar 'ya'yanka sun dawo. Kada ka tsorata mune dai fatalen nan." Aramma da ke tsugunne a kan masai sai abin ya yi masa a daidai, saboda wata sabuwar gudawa ce ta tsarge shi. Gumi ya fara tsattsafo masa ya ce. "To 'ya'yana don Allah kada ku taɓa lafiyata, wallahi har yanzu ban warke ba."
"Ba za mu sake cutar da kai ba, domin ƙawarmu wato matacciyar 'yarka ta ce ta ga irin kyautatawar da kake yi wa iyayenta da 'yan uwanta. Ki yi masa magana ya ji sabuwar muryarki ta cikin jinsin fatalwa." Uwani ta yi maganar tana wani fuffuka, sannan ta maƙale murya ta furta.
"Baba ni zan tafi da kai na fi so na dinga ganinka." Tamkar an buɗe fanfo haka cikin Aramma ya birge, ya ci gaba da sakin gudawa babu ƙaƙƙautawa. Cikin tashin hankali ya ce. "Na yafe don Allah ki je ki ɗauki mahaifiyarki."
"Shi kenan Baba zan dai dinga kawo muku ziyara a ɓoye duk dare ina ganin rayuwar da kuke yi, idan na ga saɓanin abin da ka fara yi wallahi cikin tumbinka zan shiga, na kannaɗe hanjinka ita kuma kodarka na fansarwa shugaba." Uwani ta furta tana gimtse dariyarta.
"Wallahi komai zan ci gaba da yi idan na saɓa ki mini duk abin da za ki yi mini."
"Mu zamu tafi Baba sai mun sake zagayowa." Uwani na gama faɗar haka ta fara wata fuffuka tana gurnani sannan ta saɗaɗa ta bar wurin. Saboda yadda Aramma ya razana bayan da ya gama uzurinsa a duƙe ya dinga tafiya, saboda yadda ya ji ƙafafuwansa sun yi sanyi har sun gagara ɗaukar nauyin gangar jikinsa.
Ranar da aka yi sadakar uku dai tun da safe wasu daga cikin 'yan gaisuwa suka fara watsewa, domin dama wasu tamkar a kan ƙaya suke. Ita ma Uwani sai da aka yi sallar la'asar sannan Aramma ya zo ya sanar da Maryama an zo ɗaukan Uwani, ta so Uwani ta ƙara kwanaki amma babu yadda ta iya haka ta danne. Wasu daga cikin 'yan uwan mahaifiyarta sai tsokanarta suke suna amarya sai sun zo biki. Kafin Uwani ta fita sai da Maryama ta sata a gaba ta yi mata nasiha sosai.
Fakare Uwani ta yi tana sauraronta kamar nasihar na shigarta, sai gyaɗai kai take tana amsawa. Sai da ta gama sauraron mahaifiyarsa sannan ta ce. "Ni kam Inna don Allah zan faɗa miki wata magana amma don Allah kada ki faɗa wa kowa." Take gaban Maryama ya faɗi amma sai ta basar ta ce. "Ina jin ki babu wanda zai ji Uwanina." Duk abin da ya faru tun daga farko har ƙarshe ta sanar da ita tana dariya, ita kanta Maryama dariya take sheƙawa sanna ta riƙe baki ta furta. "Allah Ya shirye ki Uwani ni dai wallahi ban san halin wa kika ɗauka ba, mahaifinki dai har ya fi ni sauƙin kai. Allah Ya shirya ki ko ba komai kin samar mana 'yanci." Suna cikin haka suka ji ƙarar horn da sauri Uwani ta sungumi jakar kayanta, ta ɗauko hijabinta ta saka. Sai da ta yi wa mutanen gidan sallama da Aramma sannan ta ƙarasa bakin motar cikin murna, don tun daga nesa ta hango motar baba Mamman. Don haka da saurinta ta buɗe motar tana faɗin.
"Daddy wallahi na yi kewar Dada, ƙila ma ita tana can ko a jikin..." Kalamanta suka maƙale a maƙoshi sakamakon ido biyu da suka yi da Jafar. Wata uwar harara ya banka mata, ta yamutsa fuska tana ƙare masa kallo ta ce.
"To kai kuma ina motarka ka ɗauko ta Daddy?" Jafar bai tanka mata ba ya fisgi motar da gudun gaske har sai da wasu yara suka matsa a guje.
Suna cikin tafiya babu wanda ya tanka wa wani sai Uwani ta fashe da dariya har da ƙyaƙyatawa, a fusace Jafar ya waigo ya zuba mata manyan idonsa. Sai kuwa Uwani ta sake kwashewa da dariya, gangara motar ya yi ya faka ya ɗauke kai gefe a daƙile ya ce. "Fice mini daga mota."
Uwani ta gimtse dariyarta sannan ta ce. "Kamar ya na sauka ai ba motarka ba ce."
"Uban me kike wa dariya?"
Uwani ta yi murmushi ta ce, "Wallahi dariya ka ba ni, ni dai ba baƙuwa ba ce a wurinka atoh. Kuma dai komai na ka Dada ta ba ni labari tun kana jariri har fa tunbiɗin da ka dinga yi kana yaro. Sai kuma na ga ka fafaki mota kana yin wani irin tuƙin 'yan Kaduna-Zaria, to wai ni birgar me za ka yi mini?" Jafar ya haɗiyi wani yawu mai ɗaci haɗe da fusgar da iska mai zafi, jin irin maganganun da Uwani ta faɗa masa. Yana shirin yin magana Uwani ta sake sakin wata dariyar tana faɗin.
"Kasan Allah yadda ka iya fafakar motar nan da Inuwan Toyota zai ganka tsaf zai ɗauke ka kwandasta, saboda wataran idan ya gaji ya ba ka ɗani..."
"Fice mini a mota." Ya furta mata cikin tsawa.
"Wallahi ba zan fita ba ai motar Daddy ce, malam kada ka yi mini gori ni nan gaba ma jirgin sama zan tuƙa." Kalamanta na ƙarshe suka kusa ba shi dariya. 'Yarinyar da cikakkun sentence na hausa ma ba ta iya haɗawa ba ita ce za ta tuƙa jirgin sama.' Ya raya a ransa. Ganin za ta ɓata masa lokaci ya sa ya fisgi motar ya ci gaba da sharara gudu, har suka ƙarasa gida wani bai sake kula kowa ba.
Tun Jafar bai gama faka motar ba Uwani ta suri jakar kayanta ta ɓalle murfin motar ta fice a guje ko rufe motar ba ta tsaya yi ba, tun daga soro ta fara ƙwalla wa Dada kira tana washe baki. Mami da ta rako aminiyarta Hajiya Falmata ganin Uwani ya sake tado mata da wani malolon baƙin ciki.
"Ƙwata wannan abar ce fa aka aura wa Jafar, imagine a ce wannan ce sirikata." Hajiya Falmata ta ƙare wa Uwani kallo sannan ta saki wani malalacin murmushi ta furta.
"Haba ƙawata wai da wannan 'yar abar ce ke barazana da aurenki? Tun da ƙuruciya ba ki yi yaji ba sai yanzu? Babu inda za ki, matuƙar kin bi duk tattaunawar da muka yi wallahi na faɗa miki da ƙafarta za ta kori kanta babu boka babu malam." Sai a lokacin Mami ta ƙara jin ƙwarin gwiwa, Hajiya Falmata ta ci gaba da biya mata miyagun shawarwari sannan suka yi sallama.
Da murna Dada ta tarbi Uwani don ita kanta ba ƙaramin kewarta ta yi ba, dalilin da ya sa tun safe ta sa baba Mamman ya ɗauko ta. Shi kuma ya ce a bari zuwa bayan azahar sai Jafar ya ɗauko ta. Kuma ya yi haka ne domin so yake kafin lokacin tariyarsu su ƙara samun fahimtar juna.
Sai da aka yi sallar Margriba kamar yadda Baba Yunusa ya ce za a zauna ya tara 'yan uwansa, Dada, na Madina, Uwani, Jafar da kuma Mami. Sai da ya buɗe taron da addu'a bayan kowa ga gama sannan ya fara magana.
"Alhamdu Lillah! Na san wasu daga cikinku sun san dalilin wannan zaman yayin da wasu kuma ba su sani ba. Maƙasudin zamanmu a kan kai Jafar da kuma ke Uwani ne." Jafar ya sunkuyar da kai ƙasa rai a bace. Tsabar takaici ya sa Mami yin ƙwafa a fili, Dada ta dube ta haɗe da taɓe fuska ta ce.
"Aure dai Allah Ya haɗa duk mai hassada sai rabo ya kashe shi, yara su haihu kuma a mayar da sunansa." Mami ta shiga aika wa Dada harara a fakaice.
"Jafar a yanzu wani nauyi ya hau kanka domin aure ba wasa ba ne, ka riƙe yarinyar mutane amana don a yanzu da kake gani komai nata ya dawo ƙarƙashin ikonka. Ke kuma Uwani wannan da kike gani aljannarki na ƙarƙashin ƙafarsa, ki bi mijinki sau da ƙafa yi na yi bari na bari. Duk abin da kika san zai faranta ran mijinki shi za ki yi, abin da ba ya so sai ki haƙura da shi don zaman aure ɗan haƙuri ne." Sai da Baba Yunusa ya numfasa sannan ya ci gaba.
"Mun tattauna ni da 'yan uwana a kan za ku tare tare da Mahaifinku tun da an riga an ɗaura aure babu fa'idar a ce za a zauna har sai nan da wata biyu idan auren su Shukra ya zo. A don haka idan Allah Ya kai mu ranar Laraba mai zuwa ne mahaifinku Mamman ya ce za a ƙarasa gyara komai da saka komai na gidan, tun da
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 21 Chapter of 24