Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 7
a dace." Tana aje wayar na kwada sallama na shiga dakin, ina yi mata sannu da gida ta amsa ni cike da fara'a, ban tambayc ta hakurin da take ba wa Baba ba, itama bata yi min zancen ba, don haka sai naji hankalina ya kwanta don na lura ba zancena suke yi ba. Bayan kwana biyu da faruwar hakan, dan Gwaggo yazo gidan naji kuma sai rigima ake yi a falon, ashe Tahir ne da iyalinsa ake shari'a, Gwaggo ce Alkali, daga karshe dai naji an banko kofar, matarsa ce ta fito cike da fushi ga masifa fal a fuskarta. Page | 93 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1) Ni dai ina zaune ina son sanin (Current) din abunda ke faruwa, amma babu hali dole na hakura na shige dakina. Da daddare muna cin abinci da Gwaggo, Tahir ya shigo fuskar nan tasa kamar cabo don babu annuri a cikinta. Ya sami wuri ya zauna, ni kam banza nayi dashi don bai ishe ni kallo ba dama. An kawo masa abinci amma ko kallon abincin bai yi ba. Ya dora kafarsa kan dayar yana girgizata. Ina kallonsa ta gefen idona, can kuma ya dauki (Remote) din (TV) yana latse-latsensa. Sai da Gwaggo ta gama cin abinci sannan ta ce masa. "Dana ya ya dai ba za ka ci abincin ba ka shigo ko sallama babu? Ka dauki komai da sauki mana." "Gwaggo na riga da na yanke shawarar aure zan kara." Ta ce, "Aure Tahir?" Ya ce, "Eh Gwaggo, lokaci yayi da zan sami farin ciki a rayuwata. Haba Gwaggo, ki duba ki ga aurena ya shekara kusan tara amma in ban da tashin hankali babu abinda nake ciki, a gaskiya Gwaggo aure nake so kuma ke za ki zaba min mata." Gwaggo tayi murmushi mai cike da nishadi. Na lura abin yayi mata dadi, tunda naji ya soma surutunsa sam ban yarda da maganar bai da kwanciyar hankali ba, bayan duk halinsu daya, shima namiji ne gashi da kudi, don haka ban ga Page | 94 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] laifin Suwaiba da take gasa shi ba, kila ma sharri yake mata. Sai sun tashi son kara aure sai su fara fito da rashin kirkin matarsu, sai ka ce su basa yi, in auren ma yake son ya yi me yasa ba zai fada (Straight to the point) ba, sai ya fadi aibun matar? Ina tunani na bar wurin don wani irin haushi ya bani, na isa dakina na kwanta, dama ni bana wuce karfe tara nayi barci. Bayan kwana bakwai da yin wannan abu, Gwaggo ke tambayata randa zamu rubuta jarabawa na wannan (Semester) din, na ce da ita nan da sati uku. Naga ta saki fara'a sosai ta ce, ya yi kyau, Allah ya nuna mana Ya kuma bada sa'a nayi wake. Na ce amin. Sai dai ina ji a jikina kamar da wani abu da ake shirya min da ban san da shi ba. Ikon Allah! ji nake yi kamar ban da lafiya, tun lokacin da Gwaggo tayi min tambayar hutunmu abinci ma ya soma fita raina, gani nake yi auren dole za'ayi min, don a koda yaushe za ka ji Gwaggo da Baba suna waya, sannan Gwaggo taje Gusau har sau biyu na rasa ta inda zan fara tambayarta dalilin zuwanta, amma saboda ina tsoron abinda zan ji shi ne nake da kewa naki tambayarta. Itama bata ma kula ina cikin damuwa ba, a kullum tana cikin nishadi. Rannan ina zaune a falo sai wayar Gwaggo ta fara ringing, da sauri na dauka. Babu suna lamba ce, Page |95 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1) na kara a kunnena na ce, "Hello!" sai naji anyi shiru, na kara maimaitawa. Can naji an ce, "Ke!" sai da gabana ya fadi don ba karamin tsoro naji ba, sai ka ce ina ganin mai maganar. Ban san lokacin da Gwaggo ta iso guna ta amshi wayar ba. Ji nayi tasa hannu ta karba ta ce "Hello!" wuri na samu na zauna ina sauraren abinda Gwaggo ke fadi, sai da tayi shiru na kusan minti uku sannan naji ta ce, "Hajiya Basira bana da abinda zan ce da ke sai. Allah Ya shirye ki ya ganar da ke, in ke mai ganewa cc." Tana gama fadar haka ta ajiye wayar. Na lura ranta a bace yake, na tashi na matsa kusa da ita na ce, "Gwaggo me ke faruwa ne?" Na marairaice fuskata kamar zan yi kuka sam bana son in ga Gwaggo cikin damuwa, wallahi ina bala'in tausaya mata shi yasa a kullum nake kara yiwa kaina alkawarin ba zan taba saba mata ba, zan yi mata biyayya a kan ko menene. Ta dube ni ta sassauta muryarta ta ce, "Yar kanwata, ina so ki bani hankalinki baki daya, ki fahimci abinda zan gaya miki, ba wai nayi hakan da wani manufa ba, sai don in aikata alheri, 'yar kanwata nayi miki miji." Baki nayi saurin budewa ina kallonta, sannan a lokacin naji cikina yayi wani irin kuka tare da murdawa, kulululu! Ka ke ji, idona kuma kan ka ce wani abu hawaye zuba suke yi, wato a cikin zuciyata Page | 96 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1) kuwa wani irin zafi nake ji wanda ba na iya misaltawa. Ta ci gaba da cewa, "Yar kanwata ba zan yi abin da zai cuta maki ba, ni na sani inshaa Allahu za iyi dace da shi, yana da kirki ga hakuri yana da fahimta tiye da yadda ki ke zato, don Allah kiyi hakuri nasan na takura miki, amma insha Allahu alheri ne a gare ki da mu baki daya. Duk da tashin hanalin da ke tare da ni ban nuna mata ba, sai dai kwallar da ta gani a fuskata. Na soma magana a hankali. "Gwaggo ba komai na fahimce ki, zan yi biyayya gare ki in yi duk abinda ki ke so." Na mikc a sanyayc zan wucc, ta rikc hannuna na juyo a hankali na dube ta. Ta saki fuska ta ce, "Yar kanwata ba ki tambaye ni mijin ba." Na kauda fuskata don wani daci da ya taso min a baki da kyar na ce, ai ba sai na san shi ba Gwaggo, duk abinda ki kayi yayi daidai, ta ce ko nakasasshe nc? na dubeta da sauri naga tana dariya. Ban iya cewa komai ba sai murmushin karfin hali da nayi mata. na ce, "Eh Gwaggo, ba komai zan aure shi." Ta jawo ni na zauna dab da ita ta ce"Dana ne Tahir." Ai ban san lokacin da na kwanta a jikinta ba ina rusa kuka, gaba ki daya na saki ukan sai ka ce irin 'yan yaran nan 'yan shekara uku, ina fadin "Gwaggo na shiga uku! Haba Gwaggo! Ki rasa duk Page | 97 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] namijin da za ki hada dani sai wadannan mutanen mara mutunci? Gwaggo na yadda ki hada ni da kowane irin mutum amma ban da shi, ni ba zan iya ba, ba zan iya zama da shi ba Gwaggo na tsani duk wanda yake da alaka da Haj. Basira, wallahi 'ya'yanta ba su da bambanci da ita, dukkansu halinsu daya, ni ba zan iya ba." Gwaggo lallashina take yi tana bani magana, amma ni fur naki, kuka nake yi kmar zan cire kayan cikina. Tun tana lallashina har ta ture ni ta mike ta soma fada. A kalla ta sami kusan awa biyu tana bani hakuri, amma ko saurarenta naki, shi ne fa ta ture ni ta mikc tana cewa, ke yarinyar nan ba ke jin lallashi, to in ba ki sani ba komai an gama don har rana an saka nan da wata daya in Allah ya kai..." Ai ban bari ta gama ba nayi cikin dakina da gudu ina ihu, tsayawa tayi tana kallon ikon Allah, daga karshe dai ta ce Allah shirye ki Dayyiba, dama ita ai kullumk kalamanta kenan in kayi mata abinda ba daidai ba. Tun daga ranar na daina zuwa gun Gwaggo, ko gaisuwa da nake zuwa musamman in yi mata na daina, itama tayi kunnen uwar shegu dani ta share ni, abinda yafi daga min hankali kenan, shi kenan Gwaggo tafi ta ba tuna kenan, na shiga uku ai kan ka ce wanina fita hayyacina, watan ni ba ma auren ne yake tayar min da hankali ba, a'a share ni da Page | 98 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU (1) Gwaggo tayi har na tsawon kwana biyu, ai ba zan iya kara kwana ba ban je na neme ta gafara ba. Da yamma likis na dawo daga makaranta, na shiga falon na iske ta zaune tana kallo, na karasa gun ta in yi mata sannu da gida, abin mamakii cike da fara'a ta amsa min. "Ya makaranta ya jarabawa?". Na dan sassauta murya na ce, "Ai ba mu fara ba." Ta ce, "To Allah ya ba da sa'a." da sauri na ce "Ammin." Na zauna sukuku kamr wadda aka fashewa rubabben kwai a ciki, na ce "Gwaggo." Cikc da shagwaba nake magana. "Don Allah kiyi hakuri da abinda nayi miki, ni dai ban yi tsamamanin haka ba shi yasa." Ta rungume ni ta ce, "Yar kanwata ba komai, ni na san za ki yi dace da miji irin dana, don ni nasan abuna na." Na bata fuska sosai na ce, "Gwaggo na lura kin fi sonsa da ni." Ta kyalkyale da dariya ta ce, "Kai wa ya fada miki, ai ke na fara sani kafin shi." Na turo baki na ce, "Gwaggo ni fa bana son shi, wallahi bana Kaunar in hada wata alaka tsakanina da wadannan mutanen saboda halinsu." "Ka ji ki fa! Shi Tahir din an gaya miki halinsu daya ne, shi fa daban yake da sauran yaranta,. Na ce, "Ni dai Gwaggo ki canza min wani, wallahi bana iya hakurin zama da irin wadannan mutanen.. Page | 99 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] "Ke wai wace irin yarinya ce da ba ki jin abın da nake fada miki? To ai sai kiyı, miji ne an ba ki shi da yake namiji ma bai damu ba sai ke?" kuka na rika yi mata na kwanta a kan cinyarta ina kukan shagwaba. Tunda wannan magana ta fito sai naji ni tamkar lokacin da Sa'id ya ci amanata, ba abinda ke min dadi sai dai ikon Allah ban yi ramar da nayi a wancan lokacin ba, amma nasa wa kaina tunani sosai, babu abinda ya fi tada min da hankali irin idan na tuna da matarsa da mahaifiyarsa, gashi mun fara rubuta jarabawa, kuma auren sun saka shi kamar bayan mun gama jarabawa da kwana hudu, kwanakin kuwa sai gudu suke yi. ASALIN WAYE TAHIR SHINKAFI Tahir Moh'd Shinkafi tun yana dan yaye Нај. Hauwa ta dauke shi daga wurin mahaifiyarsá. Ba komai yasa mahaifiyarsa ta amince ba sai don wani irin rashin lafiya da yayi lokacin yana dan shckara daya da wata daya, to sai ya ki shan nono ya yayc kanshi. Ba ya cin abinci duk ya lalace gashi a lokacin Haj. Basira tana zuwa makaranta, ita mahaifiyar tasa a ranta ba ta zaton zai rayu, don yadda ya zama an je asibiti anyi-anyi amma abin ya faskara. Rannan da yamma Haj. Basira bata gida, Haj. liauwa tajc gidan ta iske yaron yana ta kuka, mai 4 Page | 100 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] aiki itama ta gaji da rainon ko in ce lallashı, sai ta ajiye shi a falo taje tana wani abun a daidai kuma lokacin shima Alh. Muhammad Shinkafi ya shigo gidan, shima kuka ya ishe shi, sai ya shiga sashen Haj. Basira ya iske Yayarsa Haj. Hauwa tana fada, shima ransa ya 6aci sosai. Ta dube shi ta ce, "Muhammadu ina so ka ban: damar daukar yaron nan, yana bukatar uwa, don Allah ka bani shi don darajar Annabi (S.A.W)." "Haba Yaya, har sai kin roka, ai abinda na haifa kina da iko da shi, don haka na ba ki shi dama ai danki ne." Bata jira komai ba ta shiga dakin da kayansa suke ta kwashi kayansa, zata fice kenan sai ga Haj. Basira. Tana ganin Haj. Hauwa sai ta bata fuskarta, tabi bayanta da yake Haj. Hauwa bata ma jira yi mata bayani ba, "Ke ar..." bata karasa ba Alh. Muhammad ya tsaida ita da hannunsa, ta hanyar wani irin bacin rai a cikin idonsa, duk wulakancinta in ta lura da yanayinsa sai tayi sanyi Duk da mutane na cewa ta gama dashi, amma shima wani halinsa ba ya gushewa don ba karamin kyalle ba ne idan tsiyarsa ta motsa, don haka ne dole ta tsaya tana kallon ikon Allah. Haj. Hauwa ta raini Tahir tamkar ita ta haife shi. don komawa da yayi gunta cikin wata hudu ba za ka ganc shi ba. Cikin ikon Allah da yake shi magani dace ne, ta shiga kasuwa gun 'yan maganin Page | 101 MARUBUCIYA: Sameera Museyhа BAKI BIYU (1) gargajiya, a nan tayi dace da magani takc ba Tahir sai da ya kai shckaru uku sannan ta daina yi masa wanka da ruwan dauri. Jc ka ga yadda yaron ya zama, ya yi bul-bul, ga rashin ji, yana da kuzari sosai sai ka ce ba shi ba, yayi kyau sosai. Sam ba ta kai shi gun uwarsa saboda wata kalma guda daya da Hajiya Basira ta fada mata, ta ce in ita mayya ce to sai ta cinye shi danye ba sai ta dafa ba. Lokacin da ya kai shekara biyu tashin hankali aka yi da ita, wai don rashin mutunci da cin fuska irin na Haj. Basira ga rashin kunya, sai da taga yaro ya warke yana ta hidima shi ne taje ta ce a bata danta. Shi yasa ita kuma Haj. Hauwa ta nuna mata matsayinta, ta kore ta daga gidanta ta ce kuma Tahir da ita sai ido. Tahir ya girma cikin kulawa ta musamman da tarbiya tagari, dama ita akwai (Displine), cikin ikon Allah da ya girma sai Allah yasa masa son Haj. Hauwa a ransa, duk da yasan mahaifansa. Duk shige-da-ficen da Haj. Basira tayi a kan Tahir ya dawo gunta, abun ya faskara. Dama ita Haj. Hauwa yadda take nema wa kanta tsari to haka ma take yiwa Tahir, a kan dole Hаj. Basira ta kawo na Mujiya (idanu) tasa masu. Duk da akwai lokacin da yaso ya koma gunta, shi da kansa Page | 102 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha 2 BAKI BIYU [1] ya koma gun Haj. Hauwa sam ba ya son halin mahaifiyarsa, inda ana canza uwa da ya canzata. Da ya gama Makaranta (Secondary) cike da sauki ya sami gurbin karatu a Jami'ar Danfodiyo, wato (Usman Danfodiyo University, Sokoto), da yake yana da ilimi (Sociology) ya karanta, ilimi a kan rayuwar dan Adam. Sau da yawa za ka yi mamaki idan Tahir ya fada maka ra'ayin ka a kan rayuwarka. Kallon ka kawai zai yi ya fahimci irin abinda ka ke tunani, Allah ya kara masa wannan baiwar saboda dama shi đan baiwa ne, saboda yana da natsuwa da hankali. Ba ya da hayaniya, ba ya da surutu, gashi santalelen yaro mai jini a jiki, shi irin samarin nan ne da suka sa abinda ya dame su a gaba, bai da son shiga mutane shi yasa ake kiran sa da (Gentleman). Sam ba ya ra'ayin shashanci irin shaye-shaye da neman mata, a kodayaushe yana gida abokinsa daya ne Sahabi mijin Badiyya, dama sanadin sa ya ganta har suka yi aure. A kasar (London) ya yi (Masters) dinsa, yana dawowa Alh. Muh'd ya samar masa aiki a (NNPC), cikin ikon Allah ya buda masa fiye da yadda ake zato, shi da kansa ya yi tunanin barin aiki don Allah Ya ba shi sa'a, yana da (Connection) sosai. Lagos ya koma yana shigo da (Crude oil), wani lokacin kuma ya shigo da (Petrol) ko kalanzir daga kasashePage | 103 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Kasashe, idan Allah Ya tashi baka ba ya kallon ko kai waye yana baka abinda yaga dama. Tahir dan shekaru talatin da biyu, gashi (Young) amma akwai kudi. Shi yasa Haj. Basira ta haukace a lokacin sai dai ya auri 'yar 'yar uwarta, a lokacin ko maganar aure ba ya yi, don a ganinsa bai da lokacin wannan. Tahir yana bukatar mace amma yana Kokarin kame kansa, duk da kun san matashi, ba wai bai taba harka da mace ba ne a'ah, kun san idan matashi yana da abin hannu to in dai ba Allah Ya kare shi ba komai kamun kansa sai ya fada tarkon wata. A can (London) yake da wata 'yar Baturiya da ta amsa sunanta, Christiana sunanta, a makaranta suka hadu. Tahir yana da ka'idojinsa da ya tanadar wa kansa, yana da (Displine) sosai ma'aikatansa ma sun sani, sam ba ya wasa da aikinsa, gashi dama yana da ilimi gun fahimtar dan Adam. Sau da yawa ma'aikatansa na mamakin hali irin nasa, yana da kauda ido a al'amuran ka amma duk randa abin ya taso masa ya fara zayyana maka irin rayuwarka to abun sai kayi mamaki. Tunda mahaifiyarsa ta matsa masa a kan auren Suwaiba ya daina zuwa gunta baki daya. Ya dauke kafarsa daga gidan, dama can ba zuwa yake yi ba don sam ba ya ra'ayin irin halin mahaifiyarsa, amma ya zai yi tunda haka Allah Ya shirya masa, shi dai 3 Page | 104 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha A BAKI BIYU [1) yana yin abinda ya dace. Yana kyautata mata amma kullum bata gani tana hangen na Gwaggo. Tabbas mijin Gwaggo yana da hali kuma yana yiwa Gwaggo abinda bata bukata ba ma, yadda amaryarsa ke jin dadi haka itama. Sau da yawa 'ya'yan suna zuwa mijinta ma suna zuwa mata hutu. Mijin ya so kwarai ya bata daya daga cikin 'ya'yan amma taki, ba don komai ba sai don irin wulakancin da tasha a kan Tahir, shi yasa take taka tsantsan da irin zaman su da kishiyarta, dama tunda suka hadu da Haj. Basira suka zama abokan juna, shi yasa bata karba ba, sannan dama Hausawa sun ce abokin 6arawo бarawo ne. Tahir yaso kwarai ya ki amincewa auren Suwaiba, sai dai kuma bai sami goyon bayan Gwaggon tasa ba, dole ne yasa ya aure ta a cewarsa bai ra'ayin irin Suwaiba, don yasan bata da kamun kai, ita kuwa Suwaibar a (America) suka hadu, abin ikon Allah ne, ya dan zauna da ita a can ba wai zaman batanci ba a'a ita ce ta makale masa, sonsa take yi sosai tun ba ya biye mata har ya fara saurarenta, da ya dawo gida don dama kwas yaje lokacin yana aiki da (NNPC) a nan Lagos sai itama ta biyo shi. Abin mamaki ashe 'yar uwarsa ce, don 'yar kanwar Haj. Basira ce, tana Lagos ne da zama, da yake ita kadai ce 'yarta ta mace duk 'ya'yanta maza Page | 105 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha SAKI BIYU [1] ne shi yasa ta shagwabata, komai tayi daidai ne sam ba a kwaba mata Babanta ma haka yake bala'in sonta ba ya son yaga digon hawayenta, duk da ba ita ce 'yar auta ba ita ce ta biyar a gun iyayenta da yake su bakwai ne, amma ko autan baya yin abinda take yi. A (American) tayi karatunta na (Secondary), har Jami'a, yadda taso Tahir ya kwana da ita ya ki, shi fa ba sai an fada masa ba iliminsa kenan, duk irin kwadayin da ta nuna masa ya ki amincewa. Ya dai bar ta a matsay in abokiyarsa. To shi ne fa tana dawowa tayi musu maganar Tahir, tayi mamaki kwarai da gaske, ashe da gaske ne da ake cewa jini daya duk inda yake aka hadu sai ya nuna. Suna jin ta haukace a kan Tahir suka nemi mahaifiyarsa, cike da murna ta amince, dama hakan ya yi mata daidai. Ta shirya tafiya ta musamman don suyi shirin da kyau, ita kanta ta san halin Suwaiba, bata da tarbiya lo amma hakan yafi mata dama tana neman yadda za ayi danta ya dawo gunta, asirin duniyar nan tayi amma abun ya faskara. Ta rasa ita Haj. Hauwa wane irin asirin take yi da yafi karfinta, in da bukatarta zata biya da tuni ma ta nakasa Haj. Hauwan, amma ta Allah ba tata ba, dole ta fita hanyarta, to yanzu ta sami hanya me sauki da ta amu damar kwato shi daga gare ta. Page | 106 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU (1] Ya kai sati hudu da liaj. Basira ke nacin taga Tahir, amma ya ki zuwa, sai da tayi masa ziyarar ba zata a Lagos. Sai ganinta kawai yayi. Bai yi mamaki ba, don ya lura wata bukata ce ta ke nema a gunsa, ta nuna bacin ranta sosai, shi dai hakuri yake bata suka zauna don suyi maganar. Tana fada mishi tayi masa mata, tun kafin ya san Suwaiba ce hankalinsa ya tashi, don dai shi bai shirya wa aure ba, ta kunduma mai zagi ta ce don kaza-kaza ka inda Haj. Hauwa mayya ce ta fada maka kayi aure za ka ki ne? Ni na rasa maita irin na wannan mata, ta riga da ta lashe ka tas ba ka jin maganata sai nata, to ko ka ki ko kaso ni dai ce uwarka, sai dai ka kashe ni ka huta, tun ma ba ka ji yarinyar da na samo maka ba, haka za ka je ka kwaso wadda bata da usuli ba 'yar mutanen manya ba, irin yarannan na kananan mutane wadanda ba su san su ci arziki ba..." "Mama kiyi hakuri, ni ban ma nemi matar ba, ban tashi aure ba." "Iye! Sai yaushe zaka yi auren? Haka marikiyarka ta shirya maka? Don na lura sai abinda ta shirya maka ka ke yi, duk ransa ya 6aci shi baya son yadda Mama ke zagin Gwaggo, itama tana so ya yi auren shi ne dai bai shirya ba. A karshe dai ta fashe masa da kuka tana magiyar ya taimaka mata yayi wannan aure don a rayuwarsa Page | 107 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU 1] bai taba yi mata alfarma ba, ita yanzu alfarmar da take bukata yayi mata kenan. "To shi kenan Mama, ki daina kuka zan duba in gani. "Au! Abinda za ka ce kenan, duk wannan hawayen da na zudda ya zama na banza kenan?" Ta Kara rushewa da kuka ta ce, "Oh ni Basiratu na shiga uku! Matar nan ta gama da Tahir, ai kuwa zata ga sakamako, don karfin hali kai da haihuwa wata da kwatar maka da, ba ka da iko da dan nan sai..." Ya katse ta, "Haba Mama, don Allah ki bari shi kenan naji zan zo muyi magana a ina yarinyar take ne?" Nan da nan ta kare kukan da ta kwakulo take yi, ta washe bakinta a nan garin take itama 'yar Antinka се Haj. Basira, ai ka santa sai dai ba ka da zumunci. Tahir yau shckararka nawa ba ka je gidan ba, ai ta fada min zuwanka biyu na karshen ma sako da na baka kai baka ma shiga ba maigadi ka ba ka tafi, dama tana da 'ya mace ne? ch mana, tana da ita ita kadai ce kwal mace a gun iyayenta, tasa hannu a jakarta ta zaro hoto. "Ga hoton ta nan." Ta mika masa, ya karba ya duba. Suwaiba ce da ya sani a (America), hankalinsa ya tashi amma sai yayi ta maza ya cc, a'ah Mama a ina take hala don ko zuwan da nayi gidan bamu hadu da ita ba? uhum ai tana Makaranta ne a (Boarding). A ina? Ta dan yi shiru tana tunanin abinda zata ce Page | 108 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] masa, shi kuwa ya kura mata ido. Mits! Tayi tsaki ni dai kaman a nan Lagos tayi karatunta, ya riga yasan mahaifiyarsa da karya, ta saba yi masa, ta san shi yana (Against) kai 'ya mace kasar waje karatu don duk karatun da ka ke so mutum yayi ana yi nan Nigeria. Shi dai sam ba ya shalawar hakan don ko a Nigeria ya aka kare ballantana a tura ta waje karatu, har gara namiji duk abinda yayi ado ne a gare shi a kan mace. Saboda lokacin Amina itama taso taje, tare ma ne da Suwaiba. Tahir ne ya hana, don mahaifinsa ma suna dasawa. Shi dai ya kyale ta ne don babu yadda za ayi ya ce karya take yi, kuma zancen ya ishe shi haka sai ya ce, kawai da ita yaushe za ki koma Sokoto? Tayi murmushi, ai akwai jirgin karfe shida na yamma, shi zan bi. To shi kenan zan je in ganta, rungumarsa ne kadai bata yi ba don dadi, ta rika cewa Allah yayi maka albarka Tahir, na gode da ba ka watsa min kasa a ido ba, Allah Ya yi maka albarka, shi dai so yake su rabu lafiya, shi yasa ya ce mata hakan. A ransa kuwa in ban da tir da yake yi da wannan aure, ita dai Mama tana yin abu ne (With Interest) shi yasa bukatarta kullum a baya yake. Lokacin da Gwaggo ta koma Kaduna abin ba karamin dadi yayi masa ba, don in ya shigo kai tsaye gidan yake zuwa yayi kwana biyu ya koma. Page | 109 MARUBUCIYA: Sameera Misapha BAKI BIYU [1] Bayan yaje gun Gwaggo da wannan labari, ta ce Allah kara tun yaushe na ce kayi aure ka ki? To ai kuwa dole ne kayi don dama ni ban ga amfanin zamanka a hakan ba, gashi kuma na gida don haka nima na bada goyon baya don ban ga-abinda ka ke jira ba. Gwaggo a dan bani lokaci, in samu ko kuma ke ki samo min hankalina zai fi kwanciya, kai dai dama haka ka ke duk aka yi ma zancen aure sai ka ki, ni dai kaje ka aure ta don nima ina son in ga jikokina. Murmushin takaici yayi ya rasa yadda aka yi, Gwaggo taki ta fahimce shi koda yake ya karanceta, so take yi yayi abinda mahaifiyarsa ke son don kadda wata masifa ta taso sarai ya san halin Gwaggo. Bai samu goyon bayan Gwaggo ba dole ya koma Lagos da sanyin gwiwa. Bai yiwa mahaifinsa maganar ba, don ya san shima ba zai goya masa baya ba, sai abokinsa ya samu Sahabi suke shawarar inda za'a bullowa al'amarin, Sahabi duk shashancinsa ya kan daina idan Tahir na tare da shi, don yasan ba zai lamunta ba, in dai yana Kaduna to yana gidan Sahabi. Badiyya tana jin dadin zuwansa don a wannan satin mijinta yana gida gashi da sakin hannu ga tsaraba haihuwar da tayi ma bata iya sanin ainihin alherin da ta samu ba, don har kullum in zai zo sai Page | 110 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] ya kawo tsaraba. Mamana ya ke kiranta tunda ya san matsayinta a gare shi. An sami kusan wata uku Mama na son jin abinda yake ciki amma ya ki, ko Gusau ya ki lekawa don bai son maganar a kullum ta bugo 'masa waya ba ya kin dauka sai dai ya ce mata ya

Chapter 6 of 7