Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 7
fasa kyautata musu ba don halinsu ba a' a sai don Allah sai don kuma kuna bauta kun san kuma duk abin da ku ka yi saboda Allah, to Allah shi zai saka maku. Ke kuwa Fiddausi ki godewa Allah ma yana hirar a gabanki, kin san abinda yake ciki, to in kina so ki daina damuwa da al'amarinsa, ki sa masa ido kada ki kula shi ko ma dai ai ya rabu da ita tunda saki uku ne tsakaninsu, me ruwanki da su, kafin ki shiga ita ta shiga. Ke dai kiyi abinda na fada miki, wato hakuri da sa ido, kiyi masa biyayya ki roki Allah mafita da na tsari daga sharrin duk wani sharri." Da naji Anti Nafisa tayi shiru, sai na saka masu baki na ce, "Kai Anti ni ina ga ma aurc ba zan yi shi ba, don babu abinda ke cikinsa sai cin amana. Wallahi a yanzu ba wanda nake ki nake jin takaici irin da namiji, bana da makiyi irinsa, su dukkansu mayaudara ne don halinsu daya..." "Ki ka ce ba za kiyi aurc ba?". "Ba zan yi ba Anti, na hakura da auren." "Wacce irin magana ki ke yi, ba ki son lada kenan ba ki son ki raya sunnar Manzon Allah (S.A.W) kenan?". "Eh! Gaskiya na fada Anti, ai an ce in ka zabawa kanka rashin aure sai kayi ibada, don haka ma ni ibada zan yi, in yi karatu duka boko da Islama, sannan in yi aikina in kuma karc mutuncin kaina." Page | 75 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] A daidai lokacin maigidan Anti Fiddausi ya ke kwada sallama. Tayi saurin mikewa. "Ba dai Mukhtar ba ne?". Anti Nafisa ta isa wajen kofa tana amsa sallam, ai kuwa shi na. "A'a, mutanen Kano ya hanya? iso mana." Ni kam bar masu gidan nayi don a gaskiya sun kara min ilimi a kan wanda na sani, tuni bakin cikin Sa'id ya dawo saboda a zuciyata na kuma Kara tsanar da namiji, dukkan su halinsu daya ba su da banibanci. Idar. sun aure ka in ban da su nemi su kashe ka ba su da buri a zuciyarsu, ga su sun iya hora mutum su kuma maida kai bayinsu. Allah Ya kiyaye, ni kam ai sai dai ayi ta yi, amma aure kam sai a Aljanna inshaa Allahu. Na isa gida na iske 'yan Allah sanya alheri suna zaune suna hira da Baba, na shigo na gaida su na wuce dakin Babah, nayi sallahr La'asar sannan na kwanta duk raina a bace yake. Daga can falo naji wata kawarta tana bata labarin wulakancin da mijin 'yarta yayi, wai da 'yar tata bata da lafiya. Da yake rashin lafiyar ya yi tsanani kuma mijin ba wani hali ne da shi ba. A gaskiya yayi nasa kokarin amma suma ba su huta ba, da su ake ta dawainiyar ciwon ya kai har Page | 76 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] mun ma cire rai, don ciwon har jinin jikinta yake tsotsewa. "Wallahi Mairo muna asibiti da yarinyar nan a lokacin, ma jini ake sa mata, ba ta ma san inda take ba, sai ga mijin ya shigo mana cike da rashin mutunci, ya mika wa kanwarta takarda tarc da katin יי daurin aurensa. "Kai Habiba, amma wannan mutumin da karfin hali yake, aurc ya yi?". "Hum! A lokacin bukatarsa aje a kwashe kayanta zai sa amaryarsa, sannan ya saki Binta saki har uku." "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! Kai maza na yin abinda suka ga dama a wannan lokacin, Allah ne kadai maganinsu. Allah Ya saka wa wannan yarinya. To ya yarinyar tayi?". "Ya zata yi Mairo? Dole ta rungumi kaddara, don baki dayanmu mun kasa sanar da ita abinda ake ciki, har sai da ita da kanta ta lura ba avi met zancen komawa gidan mijin ba, sannan ta zo ta same ni ta ce, "Mama yaushe zan koma gida, hala na fa warke." Na dube ta na ce, "Mijinki ya rabu da ke, duba wancan dakin da ke kulle kayanki ne a ciki. Ba kin san abin mamaki abun bai bata mamaki ba, cewa tayi, "Alhamdulillahi, ai dama ta gaji da zaman da suke yi." Ni kam kunnuwana na rufe da tafin hannuwana don kada in ji Karshen labarin, to me ke Page | 77 RMARUBUCIYA: Sameera Mustanh BAKI BIYU [1] shirin samuna ne? duk inda na zauna babu labarin da ake yi sai matsalar da namiji, shin duka maza sun zama shaidanu kenan? in ban da gasa mata babu abinda suke yi. Ni kam duk yadda za'ayi da ni ba zan yi aure ba, don halin maza sai su, gara in zauna haka ba sai nayi auren ba. Kiyayya sosai nasa tsakanina da da namiji, na tuna lokacin da zan gama 'yar dilana ta "kan da namiji (GP) na yayi kasa na fito da (Pass). Tabbas namiji da ne da yake yin abinda yaga dama a wannan zamanin, sai abinda yake so za ayi masa, sannan su kuma matan sun manta da Allah a cikin al'amuransu, don haka ni nayi alkawari da kaina. zan zama mace mai mutunci amma ba zan yi aure ba. Tare da Anti Fiddausi muka wuce Kaduna, ta ajiye ni sannan ta wucc. A lokacin Gwaggo ta shirya mana tafiya zuwa umara. Murna a guna ba a magana, sannan na kara sayan (JAMB) in rubuta saboda nasan zaman gida zan yi tun da (Poly) ba za su dauke ni ba sai nayi shckara biyu a gida saboda na fito da (Pass). Mun je kuwa mun yi aikin Umurah sosai muka yi addu'a ba na wasa ba, sosai nayi addu'a a kan Allah Ya kare ni daga sharrin da namiji. Allah kuma ya bani ikon kare kaina da mutuncina. Muna dawowa muka rubuta jarabawa. X Page | 78 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Cikin ikon Allah kuwa da ya fito na sami (Point) din da ake bukata, har (Point 210), na kuma saka (University) na Kaduna baki dyan (Choices) din cike da sa'a. A wannan lokacin na sami (Admission) suka bani (Economics). A saukake naje nayi (Registration) na fara zuwa Makarantar, abin mamaki sai muka hadu da Amina Aminu, sam ban san tayi (Appling) ba kuma (Caurse) din mu daya ba, sosai nayi farin ciki da hakan, ko ba komai mun saba tun can dama. A wannan lokacin ne Anti Badiyya ta haihu ta sami 'yarta sai dai ni ban sami zuwa suna ba, don muna karatu sosai itama Aisha cikinta har ya fito sosai, muna haduwa a Islamiyya. Muna zaune ni da Amina, a makaranta muna jiran (Lecturer) ya shigo aji, na lura kamar tana tare da damuwa. "Yar uwa me ke damunki ne? na lura yau You are not in the mood." "Uhm!." Ta fada tare da maida hankalinta guna ta ce, "Yau kam gaskiya ina cike da damuwa wallahi, kin san uwargidata mace mai dumbin hakuri, tana da imani daidai ita, don wani lokacin ma ganin nake yi ta fini. Matar nan 'yar aljanna ce, sai dai in ta canza daga baya da yake kin san dan Adam ajizi ne, wallahi kin san lokacin da nazo gidan nan a zatona Page | 79 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] zaman zamu yi har na soma yi mata ganin gari, sai daga baya na gano shirme nake yi. 1 1 Sosai muke zaman lafiya da ita, sai abinda ba a rasa ba, shima din sai dai ni in dauke shi da zafi amma ita kam tuni har ta manta ma mun yi, shi yasa in tana cikin matsala ji nake kamar ni ce a cikinta. Danmu, wato babban danta shi nc babba a gida, sunansa Abdulkadir, ba ya jin magana, shayc-shaye yake yi Dayyiba, amma cikin ikon Allah ba wanda ya fahimci hakan sai ni. Ina tunanin yadda zan fada mata, gashi duk gidan daga ita har Baban sun bala'in yarda dashi, sun sakar masa da yawa. A tunaninsu yana da hankali da natsuwa. Tabbas yana da natsuwa don ba ya da raini, ko ni Anti sama Anti kasa haka yake kirana, don in gaya miki ma ya girme ni da shckaru hudu. Ya ya zan yi in fadi wannan mummunar maganar ga mahaifiyarsa, sannan yana bin 'yan aikinmu da yakc muna da wata yare ce ita mai suna Monica, ita ke mana reno da 'yan gyare-gyarc. 'Yar aikita ce jiya da daddare na fito kenan na same su tare a nan dai kofar (Kitchen) dina ta baya yana (Kissing) dinta...na rasa matakin da zan dauka a kan wannan al'amari." Ajiyar zuciya nayi ina girgiza kaina don nayi (Shock) sosai da wannan labari, a kullum kam Page |80 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIT0 [1] Aruba sai ta yabi kishiyarta, ba ta taba fadan cbunta ba, dolc ne ta shiga damuwa tunda sun zama dava. ko ba komai kai ma kana da yaran, to dole ne ka shiga damuwa don kana tunanin abinda ya faru da dan wance kai ma fa ba wai kafi karfin hakan ya יי same ka ba ne, Allah Ya shirya mana amin. Shirun da tayi, nayi tunanin tana jiran shawara daga garé ni ne, sai na gyara muryata na cc, "Yar uwa kema ai mai imani ce, don haka dole ne ki san hanyar da za ki bi ki fadawa mahaifiyarsa abinda ake ciki, sai kuma ku tashi tsaye ku nema masa taimako kuma kuyi addu'ar Allah shi ne mai shiryarwa ku kai masa kukanku zuwa garc Shi. Amma kafin ki sanar da ita ina so kiyi hikima da dabara da Allah yayi maki ki zauna da shi, ki fara jawo shi a jiki. Na tabbata ba ya samun haka daga mahaifiyarsa, saboda shi dan fari ne kin san Bahaushen mutum da kawaici, duk yadda za ki yi ki jawo shi zuwa gare ki, ki maida shi tamkar abokin shawararki irin kin gane? Ki dai san yadda za ki yi ki hada wata alaka ta musamman tsakaninku. To ba mahaifiyarsa kadai ba, Allah ma yasan abinda ki ka yi, don idan yaron nan ya shiryu sanadinki to kin yi jihadi, kuma za ki daukaka a gun iyayensa. Ina so ki cire son kai a zuciyarki, kiyi saboda Allah ba wai don a biya ki a nan duniya ba, a'a shi Allah yasan sakamakon da ya dace da ke. Page | 81 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Kin san sau da yawa yanzu dan Adam yana abu ne don a rama masa abun da yayin, saboda son kai irin namu. Don haka nake ba wa dukkan mu mata mu shawara mu aikata alheri ba wai don mutum dan uwanmu ya maida mana ba, a'a sai don Allah Ya biya mu. Allah Ya shirye mu amin." Amina taji dadin shawarar da na bata. Ta се, "Dama kuwa wallahi haka nake tunani a zuciyata, duk da ban jawo shi a jiki ba, amma inshaa Allahu haka zan yi. Zan yi kokari in yi hakan, Allah Ya barmu tare Dayyiba, kin bani shawarar da ta dace dani, Allah Ya barmu tare amin. Bayan na koma gida ne, na iske Gwaggo cikin tashin hankali, na isa gunta da sauri tana zaunc ne a falo dirshan a kan kafet, idanunta jajir da alama kuka tayi. Na sassauta muryata na ce, "Gwaggo lafiya, me ya faru? Ba ki da lafiya ne?" Ajiyar zuciya tayi kafin tayi magana. Tayi magana a sanyaye ta ce, "Jikata ce ta rasu." Na zare ido na ce, "Kar dai Nana Asma'u?" "Ita kuwa." Ta amsa min. Tuni nima idona ya cika da kwalla ina fadin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raji'un!". Don yarinyar tana da shiga rai sosai, sau daya na taba ganinta, a take kuma naso ta don kwarjininta... Page | 82 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Gwaggo ta katse min tunanina. Ta ce min "Zan je Abuja yanzu nasa a yanka min (Ticket) zuwa Abuja, kafin su wuce Sokoto in yi musu gaisuwa." A raina na so zuwa amma ban san dalilin da yasa Gwaggo bata tsąra tafiyar dani ba, don haka dole na hakura na zauna. Da karfe hudu da rabi na rakata (Airport) suka wuce. Mutuwar yarinyar nan ya shige ni ba kadan ba, don ina bala'in son yarinyar. Sam bata biyo halin iyayenta ba, ita daban ce. Allah kadai yasan dalilin da ya dauke ta, gata ita kadai ce gun iyayenta, wai su Turawa! To ta Allah ba tasu ba, don gashi dai 'yar guda gudan ta tafi sai suyi saurin neman wata, babu wanda zai iya shiryawa kansa rayuwa sai Allah. A ranar sukuku na yini, don wallahi mutuwar yarinyar nan ya shige ni. Allah Ya jikan wadanda suka riga mu, mu kuma Allah Yasa mu cika da kyau da imani, amin suma amin. Wannan (Semester) ta dan yi dadi saboda ta zama kamar (Rivision) ce gare mu. Mun yi sati biyu da hutu Aisha ta haihu, ta haifi namiji. A ranar muka je mata barka, yaron sak Babansa. Ni dama ban damu da daukar jariri ba don ba sha'anin yaro nakc so ba, ko daukar ban iya ba. Sam babu ruwana da yaro. Page | 83 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Sau da yawa Baba nayi mın fadan hakan, ko 'ya'yan su Anti ba ruwana da su, kai ni fa duk abinda zai zama aiki gare ni bana so. Har da Gwaggo taje yiwa Aisha barka, a lokacin take cewa "Aisha anya kuna wa kawarku fada ta fidda miji tayi aure?." "Wallahi muna yi Gwaggo, cewa tayi ita ba za ta yi aure..." Da saurina na rufe mata bakin ta kasa ida maganarta, Amina ta caбe ta ce, "Da gaske ne Gwaggo haka ta ce." Ai sai nayi tsuru-tsuru ina rantse-rantse na rashin gaskiya, na ce "Kai don Allah, karya fa babu kyau. Ai Gwaggon kin san bana ce haka ba." "Humn! Lallai da gaske ne wannan al'amari, da Babanki ya fada min sam ban yarda ba. Menene dalilinki na fadar irin wannan maganar da babu ko dadin ji? To wallahi kiyi wa kanki fada, wannan ba rayuwa ba се. Tun a nan Gwaggo ke ta yi man fada, ni kuma na rasa dalilin fadan, don dai rayuwata ce bana son matsala. Da muka isa gida kuwa har daki ta same ni ta ce, "Shin maganar nan da gaske ne ko wasa? Ni fa ina so muyi magana 'yar kanwata." Na turo baki na ce, "Gwaggo don Allah ki taimaka min, so nake in gama karatuna kafin in yi auren. Page | 84 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha と BAKI BIYU [1] "Lallai kuwa yarinya da wasa ki ke, don yaron nan ya ki aurenki shi ne za ki ce ba za kiyi aure ba?". "Ba haka ba ne Gwaggo, wallahi ni gani nake ba zan iya rayuwar aure ba, shi ne kawai dalilina." "Za ki iya mana, me zai hana ki yin rayuwar aure ke kuwa? Lamarinki akwai ban mamaki, shekaranjiya Babanki ya bugo yake fada min abinda ya ji yayinki na fada, ashe da gaske ne? To da sake, dole ne ki fidda miji kiyi aurc. Ka ji min yarinya da shirme, in ba don aure ba za ki zo duniya ne? To ki kiyaye ni bari ganin ina ba ki goyon baya a al'amurranki, a gaskiya ba zan ba ki goyon baya a maganar kin aure ba, sai ki canza zanin dauri don wanda ki ka dauko bai dace da ke ba." Fuuu! Ta fita daga dakin rai a басе. Tunda nake a rayuwata da Gwaggo ban taba ganin bacin ranta ba sai yau. Nan da nan hankalina ya tashi, nabi bayanta muka isa falonta. Naje har gabanta ina kuka na ban tausayi. Na ce, "Gwaggo kiyi hakuri ba wai na ce ba zan yi auren ba ne, sai dai ina tsoron da namiji da cin amana ne, ni kuma a tunanina idan na zauna ba aure sai in ga kamar zan fi şamun kwanciyar hankali." "Wanne in kwanciyar hankali za ki samu a duniya? Dama mun zo ne don mu samu kwanciyar hankali? Duniya in ban da ibada me muka zo yi? So Page | 85 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] ki ke a nuna mu mutuncinmu ya zubc, iye? Tambayarki nake yi. To bari kiji in fada miki, duniya ba wurin zama ba ce, kin san yadda ki ke karatu don kiyi jarabawa ki ci to haka muke a duniya, sam bata da dadi sai wahala. Idan ki ka yi ibada Allah zai saka miki 'yar kanwata, ba ki burin ki samu gidan Aljanna ne abinda kowa ke burin samu?" Kuka nakce yi sosai saboda a gaskiya duk na manta da hakan. Tabbas duniya jarabawa cc, kowa abinda ya rubuta ita zai kwasa... Gwaggo ta tsinka min tunanina ta cc, "Kiyi tawali'u kiyi tawakkali ga Ubangiji Allah (S.W.A), ki bashi rayuwarki, ki bauta masa kamar kina ganinsa. Ki sani Allah yana biya wa bawansa bukatunsa na alheri na mutum ya naka ko na sharri, ki roki Allah bukatunki Shi zai biya miki bukatarki." Na sassauta kukana na ce, "Gwaggo kiyi hakuri, wallahi a da da gaske ne matakin da na dauka, amma yanzu na canza ra'ayina amma ina so ki taimaka min Gwaggo in dan yi nisa da karatuna, ki tuna abinda ya same ni a baya, ku dan bani lokaci in samu wanda nake so ba don halina ba Gwaggo saboda Allah nake rokonku Gwaggo." Page | 86 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Ajiyar zuciya tayi ta ce, "Babu komai, amma da sharadi idan har ki ka ki fitar da miji duk matakin da muka daukar miki za ki amincе." Shiru nayi na ce, "A'ah Gwaggo ni dai ku bani lokaci in samu wanda nake so don Allah.” Marairaicewa nayi sosai don Gwaggo ta tausaya min, kallona take yi sai ka ce yau ta fara ganina, amma ba ta ce min hanzil ba ta mike ta ce, "Allah Ya bada sa'a." Murna, nayi sosai sannan na wuce dakina ina tunanin ta inda zan fara, ko fuska bana bayarwa, sau da yawa an sha tare ni amma ko ci kanka bana ce maka, haka za kai ta zancenka ni dai nawa ido, kai ke kidinka kai ke rawarka, zagina ko su koma yi min habaici, ni dai nawa ido. Don na dauki maza dukkansu al'amarinsu daya ne, duk labarin da ma suke badawa daya ne. To don mene zan ansa su in batawa kaina lokaci in yi asarar yawuna. A da nayi wannan yanzu kam nima gwana ce gun iya takuna, in dai a harkar namiji ne. Haka dai iyayena suka hakura da maganar auren naci gaba da zuwa Makarantata, hankalina kwance zuciyata zaune. Haka kuma lokaci yake ta tafiya, gashi har na shiga (Two Hundred Level), kannena da suka yi aure abin kamar hadin baki tare suka haihu, kwana biyu ne tsakaninsu. Page | 87 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Ikon Allah sai kallo! Baki dayanmu muka hallara a Gusau, dukkanmu mun hadu. Na lura Baba da Babah ba karamin farin ciki suka yi ba, gashi iyayenmu sun yi iyakar kokarinsu nima a wannan lokacin na dan tabuka wani abun, na sai wa Babah turmin atamfa da turare shima Baba shadda ce na saya masa da turaren, sosai suka yi godiya, don gaskiya ban taba yin hakan ba, abinda ya kara sa na saki jikina sam ba ayi min zancen aure ba. Sun kauda kai, sai dai Anti Fiddausi da take cikin damuwa, don kishiyarta zata dawo gidan, hankalinta ya tashi sosai. Fada Babah take yi mata a kan kada tasa ma kanta damuwa, gata da juna biyu. A raina na ce, Su Anti kenan! ita ko dan (Planning) din nan da ma'aurata ke yi yanzu bata yi ba, ni kam ai yara biyu sun ishe ni zaman rayuwa ba don komai ba sai don bana son wahala. Ni ban ki ba ma idan nayi aure in shekara bakwai kafin in haihu ba... Baba ta katse min tunani da ta ce. "Ke Dayyiba dauki Ikram ki wanke mata kashi." Na bata fuska sosai na cc, "Kai Babah!". Nayi magana cike da kyama, na ce "Wallahi ni fa wankin kashin nan amai yake sa ni." Duk wanda ke cikin dakin dariya yayi, suna min tsiya. Ni dai a kan bakana nake, ba zan wanke kashinnan ba. Babah kam abin itama dariya ya bata. Page | 88 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha こ BAKI BIYU [1] Ta ce, "Yarinya za ki gane kema ai kina kan hanya.' Daga karshe dai ita ta tashi ta wanke wa takwararta kashin, sunansu dama daya amma ake kiran yarinyar Ikram. Da muka dawo (Second Semester) abun mamaki na dawo gida sai na iske Rahma, ba idona kadai na saki ba har da baki da hanci, ina kallonta. Abin mamaki ko digon bakin ciki ban ji a raina ba, sai ma naji dadin ganin nata, da alama ciki ne ma da ita. Ta rame sosai, gashi tayi duhu. Na karasa inda take na ce, "A'a su Rahma manya! Saukar yaushe?". Na zauna dab da ita, sai na hango kwanciyar kwalla a idaniyarta. Jikina yayi sanyi, nasan ba komai ya kawo ta ba illa ta bani hakurin abinda ya faru, tuni har ta fashe da kuka. Na dan kai hannuna a bayan da yake ta duka kan cinyarta ina lallashinta a hankali. Na ce, "Haba Rahma, nasan dalilin kukanki, kada ki damu dama haka nan Allah Ya shirya, kin san fa dukkan dan Adam tara yake bai taba cika na goma, don haka ki kwantar da hankalinki, ni ya riga da ya wuce a guna, don dama matar mutum kabarinsa." Ta dago idonta da yayi jajir ta ce, "Dayyiba ban isa in ce ki yafe min ba saboda ni nasan naci amana ce, don abinda nayi maki nasan ba za ki taba yafe..." Page | 89 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU (1] Nayi saurin katseta na ce, "Haba Rahma, na fa gaya miki ni ya wuce a guna, na kuma yadda da kaddara, inda Allah Ya yi ni matar Sa'id ce da komai rintsi duk wuya zan aure shi, to da yake ni ba matarsa ba ce ba zai taba faruwa ba." Ta sassauta kukanta ta ce, "Kin san Sa'id ya sake ni!" Gabana yayi bala'in bugawa, nan da nan idanuna suka yi ja na ce ina girgiza kaina. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raji'un! Me ya yi zafi haka 'yar uwa? Wallahi a raina nayi bakin cikin wannan lamari, sam bana son in ga ko in ji kalmar saki ga 'yan yara mata. Dududu auren yaushe aka yi shi, yafi wata goma kuwa? Na rasa dalilin da yasa yanzu saki ta zama abun wasa, a arewa ko menene dalili oho! Sai ga anyi aure har ma akwai 'yan wata biyu to Allah Ya shirye su ya ganar da su. Koda yake sau da yawa ba a nan take ba, irin yadda ka daukar wa kanka tun farkon haduwarku shi ne ke gabatar da irin rayuwar auren da zaku yi, tun faro sai ka ga namijin da na macen dama ba don Allah za suka auri juna ba. Ko shi ne ke son samun wani abu daga gun iyayenta ko kuma ita yarinyar dama tana sonsa ne don kudin da yake da shi. To dole ne a samu matsala tunda ba son juna suke yi ba saboda Allah sai don wani biyan bukatar mai shi...ta tsinka min tunanina da naji ta ce, "Dayyiba tun farko wallahi bani na kawo shawarar Page | 90 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU (1] auren ba, shi Sa'id din ne yazo ya same ni ya ce shi ya ji ya gani muyi aure, dama ai shi ba sonki yake yi ba, yana tare da ke ne kawai amma dama shi a matsayin abokiya ya ajiye ki, ba wadda zai aura ba, shi ne yake sona tun ranar da ya aza idonsa a kaina, na ce dashi to ya za mu yi da ke don ni na san ke kam sonsa ki ke yi. Ya nuna mini ai sam ba hakan ba ne, to a gaskiya tun ranar da ki ka kawo shi guna I have a sexual fantasy on him, ko in ce I had a crush on him shi yasa idona tuni ya rufe na amince da bukatarsa..." Nayi saurin katseta na ce, "Kadda fa ki damu ya riga ya wuce a guna, sai dai a tari gaba. Sannan Allah Ya ba mu wadanda za mu zauna da su." "Na gode da addu'arki 'yar uwa, bari in tashi in tafi dare ya soma yi." Na ce "Gaskiya kam, don har shida ta wuce, zan zo jibi inshaa Allahu." Nayi shiru ina tunani, muka soma tafiya har bakin (Gate) din gidanmu, sannan na dubeta na riko hannunta cike da fara'a na ce da ita. "A gaskiya Rahma kiyi hakuri, amma ba sai kin kara zuwa ba, don na riga nayi ma kaina wasu sharuda na musamman, don haka nake fatan alheri tsakaninmu, sannan tabbas wata rana ko ba jima ko ba dade zamu iya haduwa zan yi kokari mu gaisa, don Allah kiyi hakuri idan na bata maki..." Page | 91 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Ta rike ni gam ta ce, "Babu komai, na fahimce ki saboda hakan shi ne daidai da mai irin halina sosai na gano kuskurena, kuma naji dadin yadda ki ka yi min, don haka nake yi miki fatan alheri nima, sai mun hadu." Ta wuce nima na shigo cikin gida ina tunanin rashin imani irin na da namiji, shin wai me ke sa muke yin kuskure ne gun fidda gwani? A lokacin na kara bala'in tsanar da namiji a raina. Ni nasan mu ma muna da laifi sosai, to amma ai hankalin namiji da na mace ba a hada shi, me yasa namiji ke biye wa mace ne har a rika wulakanta su? Allah Ya ganar damu hanya madaidaiciya baki dayanmu, amin. Naje ina ba Gwaggo labari, ta ce ai da farko korarta naso in yi sai dai na kyaleta. "Bata fada miki dalilin sakinta da aka yi ba?". "Gwaggo ni na hana in ji, ni na gaji da jin matsalar da namiji. Saboda wallahi Gwaggo na tsani namiji saboda halinsu." "Kin ji ki fa! An fada miki duka aka taru aka zama daya? Ko mu mata haka ba shaidanu ba nc, ko ko shekaran jiya ba ki ji wadda ta kashe mijinta ba ne?". Na zare idona na ce, "Gwaggo mace ta kashe mijinta?". Nayi tambayar cike da mamaki. "Ki rika sauraren gari ya waye a Alheri Radiyo ko ki kalla a 4 Page | 92 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] D.I.T.V za ki sha kallon abubuwa iri-iri na tsoro da na ban mamaki, Allah ya tsare mu daga sharrin zuciyoyinmu amin. Abin ba wuya dama sai in ba ka shiga ba, gashi muna (Three Hundred Level). Na dawo daga Makaranta na shigo gidan duk na gaji, yunwa ma nake ji sai da na shiga daki nayi wankan nayi sallar La'asar, sannan na fito na wuce dakin Gwaggo don da na dawo ba mu hadu ba. Ina dosar dakinta da alama waya take yi, naji tana ta faman bada hakuri, sai na saurara in ji da wanda take yi, Babana ne. Naji kuma tana cewa, "Nima na bada hadin kan hakan." "Yayi daidai, Allah Yasa

Chapter 5 of 7