Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 7
tura (Text) shi ma shiru. Ina tare da Anti Badiyya ina fada mata halin da nake ciki. "Anti ya zan yi? Ni gaskiya Sa'id nake so, ya zan yi tunda muka yi waya kwana bakwai da suka wuce a kan ya turo in ya shirya saboda iyaycna sun fara min zancen aure, wallahi Anti har gaya min yayi shima dama iyayensa suna so yayi auren, don haka ba matsala ba ce zai yi kokari ya turo, to tun lokacin bana samun wayarsa. Wayyo Allahna Anti, ya ya zan yi?". Ta dafa min kafaduna ta ce, "Anya Dayyiba Sa'id zai aure ki kuwa?". Da sauri na dube ta na ce, "Don me ki ka ce haka Anti?" Ta ce, "Saboda a gaskiya yadda ki ka bani labarin halin da ku ke ciki, to Allah kadai Ya sani, amma da alama akwai yaudara a al'amarinsa." Tunda Anti ta soma magana gabana ya soma faduwa, don ni ban taba kawo tunanin yaudara tsakanina da Sa'id ba. Anti ta katse min tunanina. Тa сe, "Ya kamata ki kwantar da hankalinki gu daya, kiyi tunani a kan Sa'id, saboda a gaskiya ni dai Page | 56 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1} kin san ban taba ganinsa ba, sai dai yadda ki ke bani labarinsa ina zarginsa." "A'a Anti, Sa'id ba zai yi min haka ba, kin san yadda yake kuwa? Yana da alkawari, ko abu yayi min alkawari sau da yawa ina mantawa, sai dai in ga ya kawo min shi..." "To ai sai kiyi, ni dai shawara ce na baki kiyi kuma tunani a kai." Ta mike tana dauke da tsohon cikinta, na kuwa tsurawa cikin ido don na lura tunda cikin ya samu, Anti Badiyya ta koma mai fada, don haka na tashi na dauki 'yar jakata na bar mata gidanta. Gidan su Aisha na wuce na iske ta ita ma laulayi ya sa ta gaba, sai amai take yi. Na tsuguna gefenta ina yi mata sannu. Ta rike kan famfon da ke gabanta tana wanke bakinta, na taimaka mata muka shiga cikin falonta, na zo da niyyar muyi magana amma dole na kyale ta saboda bata da lafiya, ni nayi mata abinci kafin in koma gida. A falo na sami Gwaggo Hauwa zaune tana duba wata (News Paper), na karasa kusa da ita na zauna tare da gaida ta. Ta amsa cike da fara'a. "Yar kanwata kin dawo?". "Eh, na dawo Gwaggo. Ya gida?". "Lafiya kalau. Yau fa Babanki ya kira batun turo wanda ya ce kiyi sati biyun da ya diba maki ya cika, wai me ke faruwa ne?". Page | 57 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU (1) Na tsuke bakina cike da shagwaba, na ce, "Gwaggo kin san fa yadda aikin 'yan Banki yake, sai ana ta kokarin son ya zo sai dai aiki ne yayi masa yawa... Gwaggo ta amshe maganar. "Shi ya fada maki aiki ne ya hana shi zuwa?". Na dan yi shiru da kamar in yi karya, sai kuma na kasa na ce, "A'a." "To kin yi min shiru, ba ki san da yaron nan bai da niyyar turowa, ba ki san dama ina hake da shi ba. Tun yaushe ku ke tare da shi, ya taba shigowa ya gaida ni? Sai dai mu gaisa idan na hadu da shi waje. Don haka na san akwai matsala. Yau shekararku nawa tarc? Kusan uku har da rabi amma bai taba shigowa cikin gidannan ba, kema ba ki taba tunanin ce masa ya shigo ciki mu gaisa ba, da yake ba ki da hankali." Sai a lokacin na soma tunani kala-kala. Anya ni wace irin sakarai ce da nayi sakaci haka? To amma ai ni ban yi tsammanin wani abu ba ne don bai shiga gida an gaisa da shi ba, a tunanina gaisawar da suke yi a waje ma ya wadatar. To me yasa kowa yake masa shaidar mayaudari? Ni kuwa sai naga ma wani sonsa ya karu a zuciyata, saboda a ganina dabara ce ya yi wa 'yan uwana na rashin bayyanar da halinsa, saboda ni nasan Sa'id Page | 58 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] mutum ne adali, yana da natsuwa ga hankali da sanin ya kamata..." Gwaggo ta tsinka min tunanina da naji ta ce, "Тo Mal. Sabi'u dai ya bani sako in ba ki, ya ce ya kara miki sati biyu, idan yaronnan ya ki fitowa to zai yi miki miji, nima hakan yayi min sai ki shirya. Nayi murmushi na gamsuwa da tunanina, na zan basu mamaki inshaa Allahu Sa'id ne mijina. Ikon Allah! har na kara kwana hudu tun lokacin da muka yi magana da Gwaggo, amma ban samu Sa'id a waya ba, abun ya fara bani tsoro a dan wannan lokacin kuwa har na fada. Washegari muna Makaranta tare da Rahma take ce min, an saka mata rana nan da wata daya. Abin ya bani mamaki, sai dai ban nuna ba. Ban yi tsammanin Rahma ta tashi aure ba, don ko zancen bata yi. Sosai na nuna mata farin cikina, ni kuma na kwashe duk yadda ake ciki da Sa'id na fada mata. Ta tabe baki ta ce, "Allah Yasa ba yaudararki yake yi ba, nima dai tun bana yadda da hakan har na soma yarda. Wayata ta ke (Ringing) na dauka ba tare da sanin mai lambar ba, na kara a kunne na ce; "Hello!" Sai naji muryar Sa'id. Tuni na mike har jakata ta fadi, ban damu ba sai na soma yi masa surutu. Page | 59 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] "Haba Sa'id, lafiya kwana biyu ina ta nemanka amma shiru, me ke faruwa ne? wai ka san halin da ka jefa ni saboda rashin magana da kai na kusan sati uku? Haba Sa'id!". Daga can yake cewa, "To ki bari in yi magana mana, ko gaisawa ba ki bari muyi ba. Ya ki ke? Ya makaranta?". Ban amsa ba, don tuni raina ya soma baci. Naci gaba da magana. "Sa'id so ka ke yi ka yaudare ni kamar yadda mutane ke fadi?". Yadda naji yayi shiru nasan tambayata tazo masa a ba zata, sai da ya dau lokaci sannan ya ce min. "Kiyi hakuri Dayyiba, ba ni da niyyar hakan, amma... "Bangane ba ka da niyyar menene ba? Haba Sa'id!, ka bani mamaki. Kai ka sani ba wanda nake so nake kuma bukata a wannan lokacin sai kai, don me sai da abu ya kawo karshe ka ke son gasa min gyada a hannu? Tun ina kawaici bana son in yi magana har ka kai ni bango? Yanzu dai ina son jin magana ta karshe, yaushe za ka turo saboda gida fa suna son ganin magabatanka." Bai jira wani abu ba ya ce, "Ranar sati suna nan zuwa." Yana fadin haka duk wani bakin cikina ya washe, nan da nan na sauke wata ajiyar zuciya. Na Page | 60 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] tabbata shima ya ji sannan kuma a take hankalina ya dawo jikina... "Kina ji na Dayyia? Ranar sat..." Wayar ta tsinke, sam ban damu da katsewar wayar ba. Da murnata na isa gun (waggo na rungume ta ina dariya. Ta ce, "Ni sakanni don Allah kada ki kada ni, ke har yanzu da.. hankalin nan da 'yanmata ke yi ba ki yi ba, a kullum rawar kanki karuwa yake." Na ce, "Kai Gwaggo, in ban yi maki ba wa zan yi wa? Na zo maki da albishir ne sai ku shirya ranar Asabar magabatan Sa'id suna nan zuwa. Gwaggo ta washe baki, farin ciki ne ya shige ta. Та сe, "Тo Allah Ya kai mu, har naji dadi wallahi ba ki ga yadda na damu ba." "Kai Gwaggo, duk damuwarki har kin kai ni?". "To uwar marasa kunya, za ki fara?". Na rufe fuskata ina dariya. Tun sadda muka yi magana da Sa'id, har gashi yau Monday (Litinin) bai zo ba, bai kira ba, sannan babu magabatansa, wayarsa ma bata shiga kwatakwata. Tun ranar Lahadi dariya a fuskata ta kau, a lokaci daya kuma na rame sai ka ce wadda aka tsotse. Gwaggo kam don takaici magana ma ta kasa yi min; gashi tana tausaya min, ita ba komai ya kona mata rai ba sai irin shirin abinci da kuma gayyato Page | 61 MARUBUCIYA: Sameera Mustaphs BAKI BIYU [1] Kawunnaina da tayi musamman suka zo daga Gusau, haka suka koma babu karfin gwiwa. Ni kam na rasa abinda ke min dadi, a ranar ma Rahma tazo gidan ta ce muje kasuwa mu fidda ankonta. Dolena naje ba don ina so ba. Ita ta lura da yanayina, har muka yi maganar. Sam hankalina ba ya tare dani, ba komai nake tunani ba sai irin yadda nasa son Sa'id a raina da har bangane mayaudari ba ne. Tun daga lokacin ko abincin kwarai bana iya ci, gashi Rahma taki kyale ni ta ce, ni ce babbar Kawarta. Don haka dole nake biye mata ya zan yi. Ni ba abinda ya fi tayar min da hankali irin yadda naji Baba yayi shiru bai ce komai ba, shi kenan nasan auren dole za ayi min. Tun ina jiran wayar Sa'id har na saduda na hakura, nemansa ma da nake yi dole na bari. Cikin sati daya tal na zabge na rame sosai kai ka ce mai maleriya da yaci ya cinye. Abincin gabaki daya ya zama madaci a bakina, sai dai in sha abu mai ruwa-ruwa, gaba ki daya na lalace. Tun Gwaggo na kauda ido dole ta dawo tana lallashina, ba abinda nake ciki sai zurfin tunani, gashi har saura kwana biyar a fara bikin Rahma, na shirya kayana zan je gidan Gwaggo ta ce, a'a sai dai in rika zuwa ina dawowa. Na dai roke ta na nuna Page | 62 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU (1] mata ni ce mai gabatar da yawancin abubuwan bukata. An daura aurc ranar Juma'a, da daddare za a yi (Dinner). Ikon Allah! kayan da zan saka ranar suna gun dinki ba a gama ba, ga shi ban sami dama naje karbowa ba sai bayan Magariba. Na isa gurin mai dinki shi kuma ya kai min wai gida da yaga ban je karba ba, don haka sai na kama hanyar gida. Kawai nayi niyar shiryawa a gida tunda lokaci ya riga yayi, koda na isa ma tuni an cika. A (High Table) idona ya ganc min abinda bangane ba, Sa'id ne zaune a gefen Rahma a daidai lokacin kuma naji ana jawabin cewa ango da amarya su taso yanka (Cake). Abin mamaki, Sa'id ne da Rahma suka mike suka isa gun (Cake) din, matar da take jawabi ita tayi (Cake) din, don haka ita take ba da umarnin yadda yankan zai kasance, matar ta ce in tayi (Spelling) din (Love) sai su yanka. Tabbas abinda matar ta tsara abin sha'awa ne ga Jama'a, amma ni haka na rika tafiya a hankali idona da bakina, kunnena har da hancina duk a bude suke. Wallahi ban san lokacin da na isa gabansu ba, ina kallon ikon Allah. Jikina kuwa rawa yake yi, take kuma idona ya cika da kwalla, fuskata tuni ta lalace da hawaye, sai Page | 63 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] ajiyar zuciya nake ina bala'in tausayawa kaina, zuciyata kuwa kamar zata fita saboda yadda take bugawa, yawun bakina ya bushe. Sam ban ji abinda mai jawabin ke magana a kai ba. "Don Allah 'yammata kije ki samu wuri ki zauna, Ango da Amarya kuma su koma wurin zamansu. Ban iya matsawa daga inda nake ba, ina nan dai tsayc a inda nake, jikina sai rawa yake yi, suma kansu sun kasa tafiya sun yi tsaye suna kallona. Can dai ban san abin da ya canza min shawara ba, na juya na bar wurin da saurin gaske. Da na karasa waje kuwa da gudu na karasa tsakiya wurin na rika wani irin kuka mai sauti. Ni dai ban san yadda aka yi ba, fitilar mota na gani a gabana mai tsananin hasken gaske, ji kawai nayi an buge ni gabb! Ka ke ji, daga nan ai ban kara sanin inda nake bа. Ina bude ido, abin mamaki a dakina na ganni. Da sauri na duba jikina, ba ciwon komai a tare da ni, sai na zauna a bakin gado da na fara tunanin ko mafarki nake yi? har na soma kyakyatar dariya ina yi wa Allah godiya. Tuni zuciyata ta nemi daukewa da naga kayan da na saka ranar dinar Rahma, na mike na nufi inda Page | 64 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] kayan suke sai naji an taba kofar dakina, Gwaggo се rike da kayan abinci. "Alhamdulillahi, kin tashi?" Ta fada cike da sakin fuska. Ta ajiye abincin ta riko hannuna muka zauna bakin gado. Ta dube ni cike da kulawa. "Ya jiki? Ba inda ke miki ciwo ko?" Na saki idona ina kallonta. Na ce. "Gwaggo me ya same ni hala?" Ajiyar zuciya tayi. Nan da nan kuma idonta ya sauya zuwa bacin rai. Ta dai daure ta ce da ni. "Ci abincin tukunna sai in fada miki..." Na katseta, "Gwaggo kar dai da gaske ne Rahma ta aure min miji...?" Kuka ya subuce min. Ta се, "Haba dai! Yaushe ya zama mijinki?". "Dama ba mafarki ba ne?" Na fadi hakan ina kuka mai sauti. "Haba 'yar kanwata, hakuri za kiyi kin san fa shi mutum ba ya auren wanda ba nashi ba, Allah bai kaddara Sa'id mijinki ba ne, shi yasa ya sauya al'amarin." "Amma Gwaggo sun ci amanata su dukkan su, koda wasa ba su taba nuna min akwai wata alaka tsakaninsu ba, daga ita har Sa'id Allah Ya isa ban yafe ba." "Haba Dayyiba, ba ki san haka shi yafi zama alheri ba? Duk abinda ki ka ga ya sami dan Adam, to jarabawa ce a gare shi, kuma a karshe ya zama alheri. Don haka ina so ki kaiwa Allah (S.W.T) Page | 65 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] kukanki, Allah Shi zai biya miki bukatarki, kin ji 'yar kanwata! Kiyi hakuri tabbas ba mafarki ki ke yi ba haka dinne, Rahma ta auri Sa'id, sai dai ina so ki daurc ki kuma cije ki sa Allah gaba... Na katse ta, "Allah sai Ya saka min tsakanina da su, Gwaggo sun ci amanata. Ya zan yi da zuciyata da take tashen son Sa'id? Shi nake so Gwaggo, don me zai yi min haka? Don me ya 6oye min halinsa? Na shiga uku Gwaggo ya ya zan yi da son Sa'id? Gwaggo a ruhina fa yake. Kaicona Gwaggo, dama wannan abu ba gaskiya ba ne, dama mafarkin ne dai Gwaggo...?" Gwaggo a katse ni da fadin. "Wai Dayyiba ba ki ji abinda na fada miki ba? ba ki san a rayuwarka baki daya Allah Ya shirya maka ita ba? Ki dauka wannan abu kaddara ce." Ta tallabo fuskata ta ci gaba da cewa. "Karamin misali ma kaina shi ne, Allah Ya shirya min rashin haihuwa na kuma hakura, ba wai don bana so ba a'a, sai don na riga na yadda kuma na amince haka Allah ya shirya min rayuwata." Da sauri na rungume Gwaggo don kam haka maganar take. Tun ranar gini tun ran zane, Allah Shi ke shiryawa kowa rayuwarsa. Ji nayi nawa ma ba komai ba ne, na Gwaggo shi ne babban abin dubawa. A wannan dare da kyar na iya bacci, tare muka kwana da Gwaggo a ranar. Washegari idona Page | 66 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU (1] kamar za su fadi don sun kumbura sosai, ina daki ba inda najc, ko nan da kofar daki ban leka ba. Tunda nayi sallah na koma kan gadona na kwanta naci gaba da kokc-kokena, gani nake kamar ba zan iya hakura da Sa'id ba, zuciyata shawara take bani a kan in san yadda zan yi in auri Sa'id, ko don in rama wulakancin da Rahma tayi min. Da wannan tunanin bacci ya dauke ni. Da na bude idona Aisha da Amina na gani a gabana, ban san lokacin da na farke da kuka mai ban tausayi ba. Tuni suma suka taya ni da kwalla. Na dauki lokaci mai tsawo ina kuka kafin na sassauta. Suna ta lallashina tare da fada min maganganu na kwantar da hankali, Amina ta debo abinci ta bani, ko kamshin abincin bana so, ai sai na fara yunkurin amai. Sai da nayi aman kumallo saboda babu komai a cikina. Haba, nan-da-nan zazzabi ya shige ni. Na koma na kwanta, ga wani irin ciwon kai na damuna, a raina cewa nake yi dama in mutu da in yi rai, zuciyata suya take yi kamar an diba ruwan wuta an saka min. Kai Allah Ya raba ka da (So) kalmar ita kanta abin tsoro ce a gare ni, tabbas na yadda so na kisa. Daga jiya zuwa yau son Sa'id karuwa kawai yake yi a raina, ni nasan halina ban iya son abu ba..." Page 67 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Gwaggo ta tsinka min tunani da ta aza hannunta akan goshina. "A'a jikin da zafi sosai. Amina taya ni rike ta muje asibiti, da mota ku ke ko?". "Eh, muje Gwaggo mu kai ta". Dolc aka kwantar da ni saboda da aka duba ni an gano ma har da (Thypoid) dina ya tashi, ai tuni aka sa min ruwa, ban san lokacin da su Aisha suka tafi ba, don an yi min allurai gashi dama baccin baya isata. Gwaggo ce a gefena ta cc, "Sannu 'yar kanwata, Allah Ya baki lafiya. Za ki ci abinci?" Na girgiza kaina, ma'ana a'a. Ta ce, "To ga (Juice) ki sha." "Dayyiba ki ci wani abu kada ki ba kanki wahala." A lokacin Alh. Shehu ya shigo ya zauna yana yi min sannu, sai can cikin dare sannan ya wuce gida tare da Gwaggo muka kwana. Kwana biyu nayi ina fama da kaina har da allurar jijiya ake min, a kalla sai da na samu kwana bakwai a asibiti, a kullum kuwa sai Anty Badiya ta zo ta kawo min abinci da kayan marmari. Sai da suka tabbatar da na samu lafiya sannan aka sallame ni na koma gida. Kallo daya za ka yi min ka ji na baka tausayi, kamannina baki daya ya canza, duk haskena ya Page | 68 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha 2 BAKI BIYU [1] dishe, idona kuwa sun koma kamar tsokar nama don tsananin kukan da suka sha. Na kara kwana hudu Gwaggo ta shirya mana tafiya zuwa Gusau, hakan yayi min dadi, ko ba komai ina son in san matsayina gun Babana, ina son in san hukuncin da ya yanke min. Da yake mun tashi da wuri, karfe goma da rao: muna tare da su Baba Mairo. Na gani a cikin kwayar idona ta tausaya min da sam bata nuna min wani abu ba, Baba ma da ya shigo sai da ya ji tsoro. Ya kura min ido ya ce, "Dayyiba ki kwantar da hankalinki, Allah ne bai kaddara shi mijinki ba ne, kin san fa ita matar mutum kabarinsa." Tuni nakc kuka na kara tausayawa kaina. Ban yi zaton Baba zai sauko ba, amma abin mamaki sai cewa ya yi zai kyale ni ayi auren su Zaliha tukuna, in yaso daga baya sai a san abin yi. Gwaggo ta ce, "Haka shi ne daidai Malam Sabi'u, Allah Ya ji da mu alheri." Gwaggo ta wuce ta bar ni nan Gusau, yadda iyayena ke yin nan-nan da ni shi yasa na dan sakí jikina har nake cin abinci, sosai Baba ke kula dani, komai za ka ji ta ce a kai min in ci. Sai dai fa daga (Smiley) na koma (Bonny), don yawan dariyata na daina, shisshigina da rawar kai ma na daina, sai kaje Page | 69 AMARUBUCIYA: Sameera Musta BAKI BIYU [1] gidanmu ka wuni baka sani a ido ba, in har baka leka dakina ba, sosai na canza na zama shiru-shiru. A kowace safiya zan tashi in shiga dakin Baba da Babah in gyara masu, to in na gama na shiga daki kuwa ba ka sake ganina ko a tsakar gida sai ko ma washegari sai kuma in ya zama dolen dolc. Babah kuwa sam bata matsa min, a kullum dai zata dan leko ta ce, "Kin ko ci abinci? Kin ci wancan kin ci wannan?". Irc-iren haka dai, duk wata kula na musamman na same shi a gun iyaycna, sai hamdala. Duk wani shirye-shirye na auren su Maimuna tare muke yi da Babah, tare muke zuwa kasuwa mu sayi kaya, nasan Babah tana yi min haka ne don in saki jikina, ni kuma na rika yin kokarin danne damuwata. Ana saura kwana biyar a fara biki, gidanmu ya soma cika da mutane. Su Anti Fiddausi da Badiyya ba karamin kokari suka yi ba, don kayan kicin suka yi masu, babu abinda ba su saya ba sai abinda ba a rasa ba. Ita kuwa Anti Nafisa (Electronics) ta saya ita ta saya musu ma firij (Medium size), abin sai wanda ya gani, 'ya'ya kam sun yi albarka, Allah Ya ba su masu yi musu suma. Ba su tsaya a nan ba, duk kusan abincin da za a ci a bikin su suka tanadar dashi, mijin Fiddausi kuwa Page | 70 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] har da gudunmuwa ya aiko wa Baba na dubu dari uku. A gaskiya Allah Ya rufa mana asiri, shi yasa komai ya zo mana da sauki. Ni kam na sha kuka ni kadai a bayi, don a ganina nima ya kamata in zama daya daga cikin ma su yin wannan hidimar, sai dai ni ban sani ba ko ni zakka zan zama a cikinsu, sai da nayi mai isa ta sannan na fito muka zauna baki dayanmu muna hira. Faisal dan Anti Fidduasi ya yi wayo, 'ya'yan Anti Nafiša su biyu nc, naga kuma ciki ne a gabanta. Ita kuwa da Anti Badiyya sai faman jan ciki take yi, cikin ya girma da yawa. Naji ta ce ma sun shirya ba zata koma ba sai bayan arba'in. Haka biki ya soma gwanin sha'awa. Ranar sati aka daura auren su Zalihat da Nura, sai Maimuna da Nasiru, a ranar aka yi walima da yamma. Amaren sun yi kyau sosai, da daddare aka kai su gidajen mazansu, su duka a nan Gusau suka tare. Bayan biki da kwana biyu an watse ni da su Anti muka je gidan Anti Nafisa, kafin mu isa tasa an shirya mana abinci da ya ke itama a gaskiya mijinta yana da abin hannu, yanzu haka a Abuja yake, amma Karkashin (Nepa) dai ya ke, sai dai girman da aka kara mashi. Ina daga kwance naji Anti Badiyya ta cc, "Anti Nafisa ni kuwa ina son muyi wata magana, Allah Yasa za ki iya taimaka min. a Page | 71 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Anti Nafisa ta ce, "Amin 'yar uwata. Mece cс matsalar?" "Anti, Sahabi (mijinta) shi ne, wallahi na soma gajiya da halinsa." "Wanne irin hali?" Anti Nafisa ta tambaya cike da kulawa da maida hankalinta sosai ga Badiyya. Nima bude kunnuwa nayi ina saurare, sai dai nayi kamar T.V nakc kallo. Ta ce, "Anti, Sahabi in ban da harkar 'yanmata babu abinda yasa a gaba, babu abinda yafi damuna irin idan ya fita tun safe ba ya dawowa sai karfe shidda na yamma. Wallahi yana idar da sallar Magriba kamar ina korarsa, za ki ga ya ci gayu daga gani ka san inda za shi, duk da ban shaida ba, amma irin (Text) din da nake gani a cikin wayarsa su suka fi tayar min da hankali, gani bana iya gani in kyale dole ne in ya shiga wanka sai na dauki wayarsa na duba..." Ko kafin ta gama idonta ya ciko da kwalla. Sai da tayi ajiyar zuciya sannan ta ci gaba da cewa, "Anti na gaji da halin nan nasa, na gaji ya ya zan yi?". Riko hannuwanta Anti Nafisa tayi ta ce, "Tabbas a wannan lokacin mu mata muna fuskantar wannan matsalar, to amma bari in fada maki kalma daya da nasan ta ishe ki tunani, sannan ita ce kadai abun da zan iya fada miki, kuma inshaa Allahu ita kadai ce Page | 72 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] hanya in dai kin kula, kuma ki ka yi amfani da ita. ita ce hakuri..." Anti Fiddausi ta katseta, ta ce "Anti nima fa matsalar da ke damuna kenan, duk da shi Mukhtar ba ya fitar dare, don shi yana son yin bacci da wuri, yana yin sallar Isha'i zai je ya kwanta, amma nima ina cin karo da irc-iren (Text) a wayarsa. Sau da yawa kuma suna kiransa ni nake amsawa, idan na tambaye shi sai ya ce me yasa ban tambaye su ba? wannan maganar ko kalma ba karamin bata min rai yake yi ba, sannan kun san ya taba aure suka rabu da matar, to wannan matar na gaji da abinda take yi min, kun san tun safe zata yo masa (Text) wai tana yi masa barka da asuba, sannan kuma ta kira shi su sha hirarsu. Abin takaici wata rana ma (Speaker) yake budewa ina jin duk irin hirar da suke yi. "To ai ke gara ke Badiyya tunda ba ya hira da su a gabanki, me yafi takaici irin a rika hira gabanka?". Ajiyar zuciya Anti Nafisa tayi, ta ce, "A gaskiya a wannan zamanin mata da maza baki daya muna fuskantar matsalolin aure, saboda rashin bin matakai da addinin Musulunci ya tanadar, babbar matsalar kuma ita ce, miji bai san hakkin matarsa a kansa ba, itama matar ba ta san hakkin mijinta a kanta ba, saboda wani lokaci mu mata muna da girman kan daukar laifinmu, idan mijinki ya fada maki laifinki Page | 73 ENMARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] sai ki dauki zafi, saboda ke kina ganin laifinsa yafi naki shi yasa ba za ki saukar da kanki kasa ba ki nemi gafararsa kamar yadda Allah ya ce mu yi. Ina so ku gane cewa, aurc ba abin wasa ba ne, ku dauka cewa ibada ku ke yi duk da soyayya na zuwa a cikin sharudan aure, to amma a wani sashc na zuciyarku ya kamata ku rika daidaita al'amuranku ga zan yi wannan abu saboda Allah kawai, za ki fada a zuciyarki kamar ke Badiya nasan idan kin sauko da kanki ki ka bishi a yadda yake ki bashi hakkinsa wurin kwanciya ko ya musguna maki, sannan ki ka lura da cinsa da hansa, ki ka share shi, ina nufin ki ka fita hanyar wayarsa, nasan akwai wahala amma ina so ku daurc ku kauda idanunku a al'amarin wayoyin mazajenku. Ku rika tashi da daddare kuna kai kukanku ga Mahaliccinku, ba wai a darc daya matsalar zata wuce, ba a'a wai a dare daya matsalar zata wuce ba, a'a wani ma har ya mutu yana rokon Rabbi bukata, sai dai abun baya kasancewa har sai a lahira, sai yaga sakamakon abinsa a can, wani kuwa tun a duniya zai gani, wani kuwa yana roko Allah (S.W.A) zai ba shi saboda Allah shi ya fi sanin abinda ya fi dacewa da bawansa, kunga ina son ku kwantar da hankulanku, ku natsu wallahi idan ku ka kwatanta abinda na fada muku inshaa Allahu za ku ga sakamako, kada ku taba jan su da fada, ku sa Page | 74 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] musu ido kawai, kada ku

Chapter 4 of 7