Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 7
na hakura da shiga cikin gidan." "Habawa Mairo, tun ba yau ba nace ki daina shiga kin ki, to ga irinta nan. Duk kokarin da kike yi na ķauda kai a al'amarinta, duk ta rage ba ko don darajar Alhaji ma ai ya kamata ta rika..." "Ni kuwa a ganina don ma ina 'yar uwar Alhajin ne yasa take yi min haka." Ta katse Gwaggo, "Kin san abinda ya hada mu ta fada miki?" "A'a ba ta fada ba, ni dai Alhajin ne ya ce in zo in ba ki hakuri kafin ya shigo gari." "Daga fa na dauki naman kajin da na soya na ba Nafisa, da yake tare muka yi aikin, wallahi ni ko bakina ban sa naman nan ba, ina mika mata tana shigowa, shi ne da sauri ta fizge naman ta maida tukunya, ta kuma ture ni yadda ki ka san 'yarta. Ta rika nuna ni da dan yatsanta har dungure ni take yi Page | 19 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1) tana ci min mutunci a kan fiffiken kaza da na ba Nafisa, ai ban san sadda hawayc ya zo min ba, itama Nafisan sai ta fashe da kuka. Mun yi kusan minti ashirin Basira na cı min mutunci kafin ta bar ni ta fita daga kicin din tare da ja min kunne a kan in kiyaycta, dama mun riga da mun asirance Alhaji, ita kuwa an yi kadan ayı da ita. Ban taba maida mata martani ba, duk irin abinda tavi min ni nasan akwai ranar da zan rama. "Ai gara da ki ka kyaleta, kin maida ta mahaukaciya. Ni da son samu ne ma Alhaji ya samo muku haya tunda ya ki gina gidan da ya yi alkawari tun ba yau ba. "Ai tuntuni yaso yin haka Hauwa, Baban Nafisa ne ya ki. Kin san halinshi ba sai na ba ki labari ba." "Haka ne. Ba komai, Allah Yaga zuciyarki Mairo, Allah Shi zai saka miki." In ji Hauwa. "Haka nc Hauwa, babu komai." "Kin san tunda Alhaji ya jawo Sabi'u a jiki nasan sai an yi haka, tunda yanzu duk vawancin tafiya in zai yi tare suke zuwa." "Nima nayi tunanin haka Hajiya Hauwa, ban dai furta ba ne, don bana son tashin hankali." A ranar nayi bakin ciki da wannan labari da naji, don sai naji duk na tsani Haj. Basira. Ban taba tunanin haka takc ba, ban taba tunanin tana da : Page | 20 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] makamancin hali irin haka ba, don ban taba jin Babah ta fada ba, ashe Babah hakuri take yi da ita. To ya aka yi ban taba sanin halin da ake ciki ba? koda yake gaskiya kwata-kwata bana shiga cikin gidan, tunda na so shiga Babah ta dake ni, dama ni ina da gudun zuciya, saboda bana son abin da ya taba ni, don haka duk abinda ne an za a taba jikina to zan nisanci wannan abu. Duk wata daraja da nake gani na Haj. Basira ya fice min, don a gaskiya nasan wannan abu da tayi wa Babah ba yanzu ta soma ba, dama tun can tana yi. Sannan tun da aka yi a kan kaza da ba wani abu ba, to nasan anyi mata ma a kan komai... Ji nayi Gwaggo Hauwa ta shafa min gashin kaina ta ce, Dayyiba ni zan wuce fa! Don Allah ki rika cin abinci kin ji ko?" Na ce, "To Gwaggo zan ci." Sannan suka yi sallama ta wuce, har waje gun motarta nayi mata rakiya, ta zaro Naira dubu ta miko min. "Ungo ki sai abin dadi kici, kiyi hakuri ban sai miki komai ba." Na karba ina godiya sannan ta wuce. Da zan shiga gida naga Ya Amir, ya fito da motarsa yana taje kansa. Sosai na tsaya ina kallonsa, da yake ban da nisa dashi. Sai a ranar na lura sosai da bakin bakinsa. Ya kara min kyau a ido, ban ankara ba muka hada ido yayi saurin sakin Page | 21MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] murmushi tarc da miko min hannunsa da ya dunkulc, na isa gun ina kallon hannun nasa. Tafin hannunsa baki ne shima. Ya ce, "Kin san rannan ba ki karbi ashirin dinki ba." Ya fadi haka tare da bude hannunsa. Ashirin biyu na gani, ya mika min na dan juya na duba haguna da dama sannan na kalle shi na girgiza kaina ina nufin a'ah. Sakin fuskarsa ya karu, ya ce "Me yasa?" Na cc, "Haka kawai bana so." Ya ce, "Amma ban taba ba ki kudi ki ka ki amsa ba,." "Haka ne. Kayi hakuri, amma ba zan kara karba ba." Cikin rashin damuwa ya daga kafadunsa ya се, "Ok, ba damuwa tunda haka ki ka cc." Ya ja motarsa ya wuce. Ya kara burge ni saboda da wani ne nasan sai ya ji haushina. Na shiga gida ina tunanin abinda naji a kan mahaifiyarsa, "To Allah kadai Yasan wanda ya biyo a kirki." Na fadi hakan a zuciyata. A haka muka cinye hutunmu har jarabawarmu ta fito, na samu (admission) a (Boarding school) har guda uku (F.G.G.C Zaria), Gusau da kuma (F.G.C Sokoto). Baba da kansa ya zabar min Zaria don haka can zan tafi a take a ka soma shirye-shirye a gidanmu ba wacce taje (Boarding) amma ni Baba ya ce ko don saboda son jikina dole ne ma ya kai ni Page | 22 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] (Boarding). A lokacin kuma Alh. Muh'd Sani ya ware mana motar da mahaifina zai rika yin nashi hidimar da yake ya ce ya daina yin Direba a gidan, vana zuwa daya daga cikin gonakinsa yana aiki ana biyansa albashi. Carina II aka ba wa Baba a ranar kamar ya zuba ruwa a kasa yasha, mu ma mun yi murna sosai. Lokacin da za'a kai ni Makaranta ma da ita muka tafi. Cikin sauki aka gama min komai na makaranta. Da su Baba za su tafi nayi kuka kamar raina zai fita, sai dai daga baya dole na hakura. Cikin sati na dan saba har na samu kawa sunanta Aisha Mansur, dakinmu daya da ita, ita ce a saman gadon da nake. Nan da nan muka shaku saboda tana da hakuri. Abin ya bani mamaki. Tabbas bana son aiki amma sai naga na fara kula da kayana na makaranta, sannan ina wanki sai dai basa fita. Sau da yawa sai Aisha ta karba ta sake wankewa, da yake tana da kirki. Daga baya ma hada wankin muke yi muyi tare, ni in yi sabin farko ita kuma sai tayi na biyun muyi shanya tare. Nayi dacen abokiya, don cikin Karamin lokaci muka shaku sosai. Baba kuwa da yake ni kadai ce 'yar (Boarding). sai ya zama kuma kayan abinci wato (Provisions) yana min shi sosai, musamman kuma Gwaggo Hauwa ke zuwa min (Visiting) da (Provisions) Page | 23 MARUBUCIYA: Sameera Mustaphr BAKI BIYU [1] itama. Sai a lokacin na san lallai Gwaggo ba karamin sona take yi ba. Rannan muna hutu har na koma gida na iske ana shirye-shiryen auren Anti Nafisa, ta sami miji a nan Gusau, yana aiki a Nepa na nan Gusau. Mun sami sati biyu aka soma biki, ranar Juma'a aka daura auren, ranar kuma aka kaita. Sai a lokacin na kara yarda da irin bala'in Hаj. Basira, sam ta hana ayi taro a gidan, dole aka je gidan Gwaggo Hauwa aka yi walima, daga can ma aka kai Amarya. Sosai na kara tsanar Hajiya Basira, saboda a gaskiya bata da mutunci. Ina mamakin duk kwarjini da rashin saukin da nake zaton Alh. Muh'd Sani Shinkafi yake da shi amma ya kasa tankwasa matarsa, to Allah ya sauwake. Gidan Anti Nafisa yayi kyau sosai, don ba abinda ba a sa mata ba, daidai gwargwado gashi dama family din Baba da yayinta sun taimaka don haka tubarkallah kawai zan ce. An gama biki da kwana uku muka koma makaranta, sai dai kam nayi kuka sosai har Baba na sa kwalla. Haka dai rayuwa ta ci gaba da tafiya har gashi muna rubuta jarrabawar kare aji daya ta (Secondary). A wannan hutun ma dan Baban falo na biyu yayi aure, ya auri wata diyar 'yar uwar Hajiya Page | 24 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Basira, auren gida yayi. Biki aka yi sosai saboda a gaskiya yafi wansa wadata, don shi a (N.N.P.C Kaduna) yake aiki, shi yasa duk a cikin 'ya'yanta tafi ji da shi, da da kanwarsa aka so a hada ama sai aka fasa don saurayinta bai shirya ba, naji kuma ana cewa Haj. Basira ce ta ki saboda yaron bai da kudi dan Makaranta ne. Da muka koma ne muka shiga (J.S.2), ni nasan ba wai ina da kokari na azo a gani ba, amma sai Aisha tayi ta cewa wai ina da kokari, a gida ma ba a cika matsa min ba kamar yadda ake wa Nafi'u, don haka zan iya cewa ni (coverage) cc, a ganina shakuwa ta musamman ta shiga tsakanina da Aisha, ko ina muna tare da yake ajinmu ma daya. Hatta (Visiting) aka zo are muke a dalilin haka muka hada iyayenmu, sai dai su Aisha a Kaduna suke, amma su asalin 'yan Maiduguri ne. Kwanci-tashi gashi har muna (J.S.3), abun ba wuya. Da muka zana jarabawar, Gwaggo Hauwa ta roki Baba a kan zata zo ta dauke ni in yi hutu wajenta Kaduna. Baba bai musa ba, don haka ma hutar da ita muka yi na bi Aisha. A gaskiya naji dadin hutun, saboda yadda nake zato na iske, ni dai bana aikin komai sai dai ayi min. Ina ma a ce gun Gwaggo nake, nayi kyau sosai fatata kuwa har da sulbi take yi, sai da hutunmu ya kai Karshe sannan muka je Gusau ni da Gwaggo, Page | 25 MARUBUCIYA: Sameera M BAKI BIYU [1] (Provision) sosai tayi min a wannan zuwa ne want abun al'ajabi ya faru. Ni na sani cewa na soma zama cikakkiyar budurwa, saboda kirjina duk ya ciko, sannan kyau ya soma bayyana sai dai ban da kibar dai. Ina zaune tsakar gida kamar yadda na saba ina hutawa, kamar an tsungule ni na mike na nufi lambun gidan da yake a kusa da sashenmu yake, na sami wuri na zauna ina sauraron kukan Tsuntsaye daga cikin lambun. Ji nayi an yi min darr a bayana, wtaon an sa hannu a kasan hammatata. Da sauri na dago kaina na dubi mai yi min wannan abu, Ya Amir ne, duk da nayi bakin cikin abin da yayi ban nuna masa a fuskata ba, na dai dan bata fuskata cike da tsarguwa. Na cc, "Kai Ya Amir, har ka bani tsoro. Da sauri ya nemi wuri kusa dani sosai ya zauna. Sam bai ji dadin hakan ba, saboda kamar zamu shafi junanmu. Ya dubc ni kuma kaina a kasa ya ce. "Mamana ya ki kc ne?" Na kara sunkuyar da kaina kasa ina murmushi na cc, "Yau kuma na zama Mamanka?" Ya cc, "Ai dama ke uwata ce tunda dai ke kanwar Alhajin falo cc." Na сс, "Haka ne, to amma ai ni na dauke ka wa." Ya cc, "Da ki ka dauke ni wa ni kuma na dauke ki mata. Page | 26 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU (1] (rabana ya fadi ras! bai sau uku. Sai naji kamar har da jikina rawa yake yi, na kasa kallonsa. Cikin raina kuwa farin ciki ne sosai ya kama ni, ni a guna wannan abun al'ajabi ne, don ban taba tunanin haka zai faru ba. Ni nasan abu ne mai wuya hakan ta faru, to amma gashi abunda nake buri ya faru cikin sauki, ashe ba ni kadai na kamu ba..." Ya tsinka min tunanin da nake yi, ko ke ba ki sona a matsayin mijinki? Nan ma shiru nayi. Dayyiba tun ba yau ba, tun kina 'ykar Karamarki nake sonki, don Allah ina rokonki da ki amince ki karbi soyayyata. Naji abun ne kamar a mafarki, na rasa inda zan sa kaina don dadi, don Allah kada ki cc a'a my love. ni na sani ba tun yau ba ke matata ce. Ya kara dubana. Ni dai har lokacin kaina a kasa yake, kunyarsa ce ta kama ni. Sai na sake kama jikina. "Kin amince min 1Dayyiba? Ina so in ji amsarki." Ji navi ina ce masa "Eh, na amince." Ina kallonsa ta gefen idona naga ya daga hannuwansa baki daya yana fadin. "Alhamdulillah! Nayi wa Allah godiya." Sannan. ya kara dubana ya ce, "Ina son mu yi soyayyarmu a boye saboda 'yan sa ido, gashi kin ga ba ki gama Makaranta ba, ko da za mu yi hira sai mu rinka Page | 27 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] haduwa nan." Nayi saurin amincewa da abinda ya fada min, saboda ni ma ba zan so a sani ba yanzu saboda da sauran lokaci. Muna nan zaune a wurin muna hira har aka kira sallar Magriba, sannan muka rabu. A ranar ruwa ne kadai ban zuba a Rasa na sha ba, saboda farin cikin da nake ciki, a wannan daren har sar da nayi nafila saboda murna, na roki Allah yasa hakan yafi zama alheri a gare ni. Mun shiga aji hudu cike da nasara, ranar visiting Baba ke fada min an sanya ranar daurin auren Anti Fiddausi da Anti Badiya, da yake ita Anti bata fitar da miji da wuri ba, shi ne har Badiya ta gama a ka hada bikin nasu. Dadina daya da sai mun samu hutu za ayi bikin. Soyayya tsakanina da Ya Amir kuwa mun shaku sosai, sonsa kullum karuwa yake yi a cikin zuciyata. Ranar da muka fara rubuta jarabawa ne Mallam Tanimu Kaita, mutumin da naki jinin ganinsa, ba tun yau ya furta yana sona ba amma saboda tsana da nake yi masa duk yadda zan kwace wa ganinsa to zan yi shi, don haushinsa da nake ji. Da yamma lis muna komawa (Hostel) da yake Masallacinmu da dan tazara muna tare da Aisha da wasu 'yan dakinmu da muka fito Masallaci tare, Salima take bamu labarin kanwarta da ta karyc a hutun da muka dawo. Page | 28 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Daga bayanmu muka ji ana fadin, "Don Allah ku tsaya an aiko mu gun ku." Mu duka muka tsaya kuma muka kalli mai maganar, na kula idonta a kaina ya tsaya. Ta ce, Dayyiba Sabi'u, Malam Tanimu na kiranki, wai ki same shi a (Staff Room)." A take nayi tsaki tare da wani irin bakin ciki. Suwaiba Alhassan ta ce, "Kc kuwa wallahi wannan mutumin na sonki, ki duba ki ga rannan da muka yi lattin zuwa (Assembly) da ya lura kina tare da mu sai ya ce mu wuce, da ba don ke ba da mun ci duka wallahi." Na kara jan tsaki "Mitss!" Aisha ta ce, "Hakuri za ki yi kije ko don ku rabu lafiya." Salima ta dube ni ta ce, "In kin san yadda 'yammatan Makarantar nan ke sonsa, wallahi kin yi sa'a." Saboda takaici ban iya cewa komai ba. Na kalli Aisha na ce, "Don Allah zo ki raka ni." Mun isa bakin kofar sai kuma muka tsaya daga wajc. Ya ce "Ku shigo mana." Aisha ta fara shiga sannan ni, yana zaune yana rubutu. Malam Tanimu shi ne (Displine Master) a Makarantar, yana da cin zalin yara, abinda yasa nake hakuri da irin damun da yake min kenan, sannan irin mazajen nan ne masu nacin tsiya... Ya katse min tunani da ya ce, "Yammata kuna lafiya?' Aisha ce tayi saurin amsawa. Ya ci gaba "Ku zauna mana." Ba musu muka zauna. Ya dubi Page | 29 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Aisha, "Ke Aisha ke ce 'yar rakiya? Kina sa min baki a kan Kawar taki kuwa? Ko wasikar da na ba ki ki bata ba ki bata ba?" "Na bata Mallam." Ajiyar zuciya yayi. "Haba Dayyiba, nayi iyakacin kokarina a kan neman soyayyarki, ya ki ke so in yi da kaina?" a A zuciyata ni ban da tafasa da zuciyar take yi babu abinda take kulawa, tsanarsa ce ke kara yawa tare da ni, ko kallonsa bana yi, idona a kasa yake ina wasa da 'yan yatsuna. "Dayyiba!" 2 Ya kira sunana tare da kai hannunsa kan tebur din da ke gabansa, ya tsura min ido na kusan sakwan uku. Ajiyar zuciya ya kara yi kamar mai tunani. Ni dai ban kalle shi ba ina nan a yadda nake. Can muka ji ana buga kararrawa ta lokacin cin abinci. Zumbur! Na mike na ce, "Malam za mu je cin abinci." "Ashe dama yunwa ki ke ji ki ka kasa cewa komai?". Ni kam tuni na kama hanyar fita. A hanya Aisha ke ta tsokanata, nayi mata dundun wasa. Haka dai nayi iya gwargwado don 6oye kaina daga Mal. Tanimu, tun daga wannan term ya kare. Mun koma gida da kwana shidda aka fara bikin su Anti. Mijin Anti Badiyya yana zama ne a Kaduna, don haka can za a kaita ita kuma Anti Fiddausi Kano, Page | 30 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] biki yayı armashi sosai. Dukkan su rana daya aka wuce da su. An shirya mota dai-dai zuwa gidajensu, a wannan bikin naga naci gun Ya Amir, a cewarsa ana iya ayi masa snatching idan bai yi hankali ba, da kyar muka rabu don tsabar son da muke wa junanmu. Ni motar Kano na bi don akwai wadanda za su wuce Kaduna tare damu. Anti Fiddausi an sha kuka. ni kam dariya nake tayi mata, ban san mijinta na da kudi ba, kai kowa ma yayi mamakin irin gidan da ya shirya musu. Gidan flat ne amma na gani na fada, itama cewa tayi bata san yana da kudi ba, don bai taba nuna mata ba. Ta samu gurin zama kam, Allah Ya ba su zaman hakuri kawai za a ce. Kwana daya muka yi muka wuce Kaduna, itama gidan Anti Badiyya ba laifi, don dai kawai gidan ba nasa ba ne amma shi ma gidan ya hadu duk da su gidan sama ne suna kuma flour na uku a gidan. Ita kam ba mu kwanan mata ba a gidan Gwaggo Hauwa muka yada zango. An gama biki da sati biyu muka koma Makaranta, duk da ban je Gusau ba a nan Kaduna Gwaggo tayi min komai na siyayya. Tun daga wannan lokacin na gano na cika budurwa sosai, don kirjina ya cika gashi na daurawa Page | 31 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] kaina wata akida na rashin rayuwa da kowane da namiji in ba Ya Amir ba. Kowa kuma ya shaide ni da kunya sosai, ba wai don ina saka hijab ba ne a'a, sai dai a koda yaushe za ka ga na yafe jikina da gyale (Pashmina), in kuwa kayan Makaranta na saka to zan tabbatar na sauko da shi ya rufe min kirjina, don a yadda na lura kamar nafi duk kawayena cikar kirjin. Hatta gun wanka ban taba yarda a ga tsiraicina saboda nauyin da nake ji shi yasa ma bana wanka sai na davo daga class irin da rana din nan. Tun ana tsokanata da akidar har aka sa min ido. A wannan hutun na second term dinmu a Gusau nayi shi, sai dai ba ma tare da Ya Amir, saboda a lokacin suka je Ummara da shi da mahaifiyarsa, duk da irin hali irin na Maman su Ya Amir bai hana ni son dan nata ba, so da ban taba yi wa wani da namiji shi ba. Sai dai Allah bai hada mu ba, wannan zuwan har muka koma school ba su dawo ba. A haka na koma Makaranta cike da damuwar rashin ganin Ya Amir a Makaranta kuwa karatu muke yi sosai don muna third term ne. Cikin wata uku muka rubuta jarabawarmu, mun koma gida da sati daya kuma kura ta tashi gida. Dalili kuwa shi ne, ranar Talata naje gidan kawata Page | 32 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] da yake makotanmu ne, sunanta Amina. Yawanci dama tare muke idan na dawo hutu. Na dawo na shiga gida sai kawai na wuce kai tsaye gidan kiwo, dama a cikin gidan akwai lambu gidan kiwon kuwa yana daga bayan lambun daga can na shiga lambun nayi zaune ina shakatawa cike da nishadi. Ji nayi an kai hannu kan kafaduna, cike da tsoro na mike tsaye gabana kuma yana faduwa kamar zai fita. Raina a bace na dubi dan rainin wayon da yayi min haka. Ya Amir ne saboda 6acin ran abinda yayi min yasa nayi tsaki, na kuma banka masa harara, sai dai ban ce komai ba na tsare girar sama da ta kasa. Sam fuskata babu annuri, takaicinsa da naji a wannan lokacin ba kadan ba ne. A rayuwata ban taba tunani ko shafa namiji yayi min ba saboda irin cin amana irin wadda nasan wasu mazan suke yi. Tun ba yau ba nasha jin labarin irin mazan da ke cewa su in dai ana soyayya ba a taba juna, to ba so a tsakani. Ni kuwa na dauki alwashin da namiji ko shafata ya yi to na tabbata bai da bambanci da irin mazan da nake zargi... Ina cikin tunanin Ya Amir ya tsinka min tunanin nawa, inda ya kara riko hannuna. Wallahi ban san lokacin da na ware hannu na kai masa wani irin Page | 33 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] wawan mari ba, tas! Ka ke ji. Na kuma nuna shi da dan yatsa na ce da shi. "Ashe kai ma dan iska ne kamar sauran mazan da nake zargi masu irin wannan halayen? To bari ka ji, tabbas naso ka amma a yau wallahi na tsane ka! na tsane ka!! kuma bari in fada maka between me and vou is over... Na juya zan wuce, dama tsaye ya yi galala kamar dan shckara biyun da ya yi kashi a wando, rike da kuncinsa ya cc, "Ke kin san abinda ki ka yi kuwa? Marina fa ki ka yi? an gaya miki ke kin kai irin matan da za su mare ni in kyale su?" Ina jin ya fadi haka na ruga a gujc, ya biyo ni da gudun tsiya, saura kadan ya kama ni. Allah Ya bani iko na shige gidanmu. Ai kuwa har cikin gidan ya shiga. Muka iske Babah na zaunc a tsakar gida, naje bayanta ina ihu. Da sauri ta mike tana fadin "Lafiya? Lafiya Amir?" Bai tsaya saurarenta ba ya kai hannu zai kamo ni sai ta rike hannunsa. "Haba Amir! An cc fa ko mutuwa na kunyar idon mahaifi..." Rai bace ya nuna ta da yatsa cike da fushi yana cewa, "Ke ba ruwanki, ki fita hanyata mara mutunci." A daidai lokacin Baba ya shigo gidan, ya shiga tsakaninsu da Babah ya ce, "Haba Amir, me ya yi zafi haka?" Page | 34 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1) Hannu ya daga wa Baba ya cc, "Kai! kaima munafuki ba ruwanka..." Tas! Tas!! Tas!!! Ka ke ji, Baba ne ya mare shi. Ai kuwa nan shima ya daga hannu zai rama sai Sahabi maigadi ya rike hannunsa ya fitar da shi waje, sai zage-zage yake yi, har da gori. Wai dama Baba ya mallake Baban falo shi yasa ya samu gindin zama, sannan dama shi bai ga laifin Mama da take wulakanta wadannan kaskantattun mutanen ba. A waje yake ta fadin wadannan maganganun da ba dadi, ya zage su Baba tas!. Ni kam kuka na dinga vi ba sassauci, don ni na jawo akc zagin su Baba haka. Ban taba tsammanin Ya Amir haka yake ba, dama ashe dukkan su haka suke ba su da mutunci? Lallai Baban falo yana da aiki gabansa. A ce duk cikin 'ya'yansa ba mai halin kwarai? Dama duk abinda aka ce suna yi saboda ba su taba yi ba ne a gaban idona ba, ashe dukkansu nc haka? kai Allah ya waddaran naka ya lalace.. A cikin tunanin naji muryar Mama tana zagezage, ita ce har tsakar gidanmu tana ta faman fadar ashar, har da cewa tayi, yau shi ne zai zama rana ta Karshe da zata sakc zama da mu, ta shiga fitar mana da kaya tana football da su. Daga Babah har Baba ba wanda ya ce da ita ci kanki, suna zaune cikin daki Baba suna sauraren irin Page | 35 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] cin mutuncin da Mama ke yi masu, ai tuni naji duk na tsani kaina, don dai saboda ni ake al'amari. Da gaske ne fa gida ba lafiya, yanzu haka ga ni tarc da Malam Sabi'u yana so ya bar gidan." Tayi shiru tana sauraren abinda yake fada. Sai kuma ta amsa da "To." Tana kuma mikawa Baba wayar. "Ungo Alhaji na son magana da kai." Sai da Baba yayi ajiyar zuciya sannan ya amsa. Bai dai ce komai ba, bayan sallama da ya yi. Sun sami kamar minti ashirin yana sauraren abinda Alhaji ke fada masa, sannan ya amsa da "To ba komai, Allah Ya saka da alheri." Ya mika wa Gwaggo suka yi magana kadan sannan suka yi sallama. Ta dubi Baba ta cc, "To ka ji yadda aka yi Mujc gidan da ya fada maka ku zauna can." "A'a Hajiya Hauwa, ni da kin bar wanhan maganar. Ni wallahi na hakura da wannan zanman, Katsina zan wuce." A take Gwaggo Hauwa ta żaro ido ta ce, "A'ah ba za ayi haka ba, ya ka cc da Alhaji ka amince da zuwa gidan da ya ba ka halak-malak? Baban Dayyiba hakuri za ka yi, ni nasan kun yi hakuri kowa ma ya sani, sai da aski yazo gaban goshi sannan zaka yi fushi? Haba dai wannan gida ma dama sunanka aka gina shi don Allah, don darajar Annabi (S.A.W) kayi hakuri muje gidan, wa ke maida hannun kyauta baya? Sai shaidan. Haba Baban Dayyiba!." Page | 36 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha 3 BAKI BIYU [1] Wata ajiyar zuciya Baba yayi, ita kuma Gwaggo sai hakuri take faman ba Baba. A kan dole Baba ya hakura muka wuce sabon gidanmu. Na juya nayi wa gidanmu kallon karshe, a raina nayi alkawarin ban sake shiga gidannan. Baki dayanmu mun yi mamakin sabon gidanmu, flat ne ya sha fenti, gashi ya tsaru sosai. Sashe uku ne duk da dayan ba girma ne da shi ba, shi ne sashen maza sai na Baba daga wajc, na Baba kuwa shi ne daga ciki, sashen Baba katon falo ne hade da dakinsa, sai aka shirya dakin baki daga gefe. Ba abin da ba a saka ba, maganar tsaruwa ma bata taso ba, duk wani bakin ciki ya gushe, dadi sosai muka ji. Gwaggo ta zaga damu ko'ina gefen Baba kuwa bedroom uku ne kowane da bandaki a ciki, sai katon falo da kicin. Abin dai sai wanda ya gani, ba abin da ba a saka ba hatta (Kitchen) an saka su (Freezer, freign, Gas cooker da blander), komai an yi shi cikin tsari. Sai da muka natsu muna zaune baki dayanmu a falo sannan ne Gwaggo ke tambayar abinda ya haddasa rigimar, Babah ce ta nuna ni da dan yatsa ta ce, "Kin ganta nan ita ce mafari, ina zaune tsakar gida ta shigo gidan a guje tana ihu. Page | 37 MARUBUCIYA: Sameera Musiapia BAKI BIYU [1] Baba ya mike a fusace ya сс, "Ja'irar yarinya, dama

Chapter 2 of 7