Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 7
ke ce silar rigimar ban sani ba?" Ya nufo ni gadan-gadan zai duke ni, ai ban san lokacin da nayi tsalle na je gun Gwaggo ba, ina kuka ina ba da hakuri itama Gwaggo hakurin take badawa. Та сс, "Нaba Malam Sabi'u! abinda ya riga ya wuce, kayi hakuri." Ta rike ni ta ce, "Ke me ya hada ki da rigimar?" Ai kuwa ina kuka ina fadi masu abinda Ya Amir yayi min, nan fa jikinsu yayi sanyi. Gwaggo Hauwa ta gyara zamanta ta ce, "Wannan abu bai yi kyau ba, amma ai komai ya wuce. Tunda Allah Ya raba, yanzu haka da nake fada maku Alhaji ya saki Hajiya Basira saki daya, dama saura biyu tsakaninsu. Kowa ido ya zaro, nan Babah ta ce mu tashi muyi cikin gida. Suka ci gaba da hirar. Ni kam dadi naji a raina, ko ba komai an nuna wa Mama matsayinta, tunda ga lokacin nasan lallai yarinta ciwo ne, dama haka Haj. Basira take, wallahi na tsane ta fiye da yadda mutum kc zato. Ji nayi har da duka 'ya'yanta halinsu daya, dama a da nake cewa Ya Amir mutumin kirki nc, ashe shima shaidani ne. A lokacin Gwaggo Hauwa ta nemi alfarmar Baba ya bata ni in zauna gunta, tunda dama ai yanzu saura shekara biyu in gama Makaranta. Page | 38 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Ba yadda Baba zai yi, ya ee "A'a, saboda ko ba komai Gwaggo Hauwa tana da mutunci, duk da dai ransa bai so hakan ba saboda yana da son yara, gashi dama sai da ya wahala har ma ya cire rai kafin ya same mu, shi yasa bai iya musa wa Gwaggo Hauwa ba, yasan irin yadda zata ji har ya ce a'ah. Don haka ne ya ce, "Ai babu damuwa, dama gashi Makarantar tana kusa da ku, sai dai kuma kin zabi raguwa da dai Maimuna ce da take son aiki." "A'a, ni ina sonta a haka, kasan tun can dama da Dayyiba muke shiri, kasan tunda Tahir yayi aure shi kenan gidan yayi min girma, ba kowa a tare dani, dama dalilin zuwana kenan na iske wannan Kurar." Haka kuwa aka yi, kayana tsaf! na kwashe ban manta da ko kyalle ba, murna a guna tamkar za a sa ni Aljanna, don dama ina ta addu'ar hakan ta faru. Ranar Litinin tunda safe muka wuce Kaduna. Na sami yadda nake so don bana aikin komai, hatta kwai ban iya soyawa ba, don bana ma gwadawa. Masu aikin gidan har takaicina suke ji, don komai bana tashi in yi sai dai in kira ayi min, dan zaman da nayi ma sai da Gwaggo ta sallami 'yan aiki biyu. Gwaggo Hauwa tana da son yara, don haka ne dole ma ka shagwabe idan kana gunta. Ba aikin da nake yi a gidan, hatta (Under wears) in na ga dama, jika su nake yi kamar dai yadda na saba yi a gida. Page | 39 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Uwale ita ce matar da ke kula da dakina, ita ke wanke su. Da yake tana da hakuro sosai, sam bata damuwa da iskancina, hatta abinci sai an bini daki an kai min, don haka ne na murje sai ka ce irin 'ya'yan sarauta, 'ya'yan sarautar ma na fada a gani. Navi kvau sosai, har ma da muka koma Makaranta sai abokaina su rika tambayar man da nake shafawa, ni kuwa tunda na koma Kaduna Gwaggo la saya min (Oil of Olay) ina shafawa, a gaskiya man ya karbe ni sosai. A wannan (Term) din nc su Anti Badiyya da Fiddausi suka zo min, murna a guna kamar zan yi hauka. Ni dai nasan na zama 'yargata ta ko'ina, cike da murna da jin dadi muka shiga aji biyar, wannan shekarar ma haka nayi ta cike da nasara. Kowa a lokacin samari suka rika kunno kai suna sona, sai dai ni bana kula su, don ma ni haushi sukc bani sai in ta ganin kamar duk halinsu daya da Amir. A kullum ina bakin cikin abinda ya faru tsakanina da Amir, shi yasa sam bana yadda in tsaya da kowa. Ba wai bana son yi ba ne, a'a! ni fa bana son namiji wawa, bana son ire-iren maza masu sanyi, ina nufin irin wadannan masu saukin, ko shiga ba su iya ba. Nafi son namiji gaye, gayen ma mai sakin hannu, irin wadanda suka san (WhatApps), ai kun dai gane abin da nake nufi. Sannan bana son kananan mutane Page | 40 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1) duk da ni karamar yarinya ce dududu ban wuce shekaru goma sha shidda a lokacin ba, amma nafi son maza da suka fi karfina. Ni ba wai abun hannun mutum ke burge ni ba, a'a ni dai ina son in ga namiji mai kudi kuma yana more abinsa. Yana shiga irin na 'yan gayu masu ji da kansu, sannan suna da aji. Sam ban son (Gentleman), nafi son darjeje in na fadi hakan a raina na kan yi murmushi saboda ni kadai nasan abinda nake nufi. Ni nasan na taso ina da bala'in rawar kai, ga surutu, ga son abokai. A tunanina a set dinmu bakı daya ba wanda ban sani ba, don saboda tsabagen surutu, sai dai bana da fada amma akwai taurin kai zan iya zama da mutum ko kai wane iri ne saboda ni bana da wai sai na zabi aboki, a'a kowa ma abokina nc. Shi yasa a Makarantar ake kirana (Smilcy) a kullum ina cikin dariya da sakin fuska, kamar Kwai ko (Laughing gas), saboda haka ne ma sunana ya bace a ke kirana (Dayi Smiley). Da muka shiga (SS.III) a lokacin kam na batse, don ni a ka ba wa (Social Prefect) saboda iya yi na, dama tun can ina cikin iya rawa ba (Night) din da za ayi ba a sani ba, saboda irin rawar kaina. Makarantarmu tana daya daga cikin Makarantun da ake ji da su a Arewa na Gwamnati, ba ita kadai ba ce amma kun san kowa nashi ya sani. n 1 Page | 41 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Tunda na koma gun Gwaggo Hauwa, wata irin wayewa da kaifin ilimi ya shige ni. Ni kaina ina mamakin hakan. Koda yake dama in dai kana zaunc a Kaduna dole ne ka samu kanka haka, har dai in kana tare da masu halin, sannan in kana tare da masu wayewar. Lokacin da muka kai (Third term), da yake muna shirye-shiryen rubuta jarabawar gama Makaranta ne, a ka ba mu hutun sati biyu, in mun koma Makaranta ba zamu dawo ba sai mun gama rubuta jarrabawar baki daya. Muna isa gida Direba ya ajiye ni, sai na lura da baki a gidan, don (Jeep) ce kirar (Land Rover 2010 Spootware)din (Parkc). Na san motocin Gwaggo Hauwa daga (KIA) sai (HONDA) Judgement Day. wadda mijinta ke hawa, sai kuma (Honda Jeep) itama (2010). Koda yake dama na saba ganin baki irin wannan ba tun yau ba. Da na shiga gidan, na iske wata mata a falo tana da kiba, wai! Kibar da ta baci ba tana da haske sannan hasken nata na hutu ne saboda kayan da ma ke jikinta abun kallo ne. Tayi shiga ne na alfarma, gata ta iya shigar. Tayi min kyau sosai, don ta iya (Dressing), kayan da ta saka (Ash) ne da baki (Material) ne me bala'in kyau. Page | 42 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU (1) Daga gani matar manya ce. sai dai bata da sakin fuska don tunda na shigo muka hada ido da ita. Kallo daya tayi min ta ci gaba da abin da take yi. Waya ce a hannunta tana latsawa. Sai da na kai kusan tsakiyar falon sai na dan risina na cc, "Ina wuni?" Ba tare da ta kalli inda nakc ba ta amsa, yadda ka san dole ce ma amsa gaisuwar. "Lafiya." Ta fada tare da kara wayar a kunnenta. ta fara magana. Ni dai ina jinjinawa wannan bakuwa tamu don ina ga 'yar gidan sarauta ce, na kusa da Kofar falon Gwaggo naga wata yarinya mai kyau ta fito, anyi mata kwalliya sosai. Ina ganinta nasan bata wuce diyar bakuwar nan. don itama an shirya ta sosai. Na kai hannuna na shati gashin kanta na ce, "Yar baby ya dai? Me sunanki?" Take ta saki fuskarta da murmushi ta ce, "Asma'u, amma Nana ake kirana." "Nana How old are you.?" Tayi fari da ido ta ce, "Am five years old." "Da kyau!" Na fada ina kara son yarinyar a raina saboda wayonta. Na karasa cikin falon nayi saurin isa gun Gwaggo na rungumeta na ce "Kai Gwaggo yau ko tarbana an ki saboda an sami wasu 'ya'yan ko?" Та сс, "Кai 'yar kanwata ba haka ba nc, ai jikata ce ba ki waye su ba ne?" Na zare ido na ce, "Kaddai yarinyar W Idris ce?" Wane Idris kuma? 'yar Tahir dai." Page | 43 MARUBUCIYA: Sameera Mustaphа BAKI BIYU [1) "An yi haka Gwaggo, ashe wannan matarsa ce a falo." "Ita ce, ke da ashe ba ki santa." "Ni kam ban san ta ba sai a hoto shima din lokacin tana Amarya, sannan duk zuwan da suke yi ina Makaranta, hala wani zuwan suka yi da Dayyiba?" Kwata-kwata zuwansu na biyu kenan, tunda Tahir yayi aurc, shi kadai yake zuwa ya yi kwana daya ya wuce bayan kowane wata biyu. Kai amma shi kuwa wane irin namiji ne da ba zai iya tursasa matarsa tayi zumunci ba? Gwaggo ta saki fuska ta cc, "Ni kuwa ba ki san wani abu ba 'yar kanwata, duk a cikin 'ya'yan da na rika babu wanda yafi kyautata min irin Tahir, haihuwarsa ne kawai ban yi ba, amma ni kam nasan dana ne, don yana da mutunci, ga shi yana da kula. Ke a rayuwarsa baki daya babu abinda yake yi bai fada min ba, dole sai da amincewata sannan zai aikata wannan abun. Da ne gun liaj. Basira, amma rayuwarsa baki daya a gidannan yake, shi yasa take adawa da ni sai dai ni bata ishe ni kallo ba, babu yadda ba tayi ta raba mu ba amma Allah ya kare ni daga sharrinta mai dunbin yawa. In fadi miki abinda ba ki sani ba, wannan matar tasa Suwaiba ba karamin rigima aka yi ba kafin ya Page | 44 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] yada ya aureta, sai da na nuna fushina sosai sannan ya amincc. A lokacin babu cin mutuncin da Basira bata yi min ba a kan auren, hár cewa tayi na wanke na bashi yasha ba ya ganin kowa da gashi sai ni, ni kuwa wallahi ban ga dalilin da zai sa in yi wa dan mutane asiri ba, don dai ko ba komai na rike yara sama da goma sha biyar, Allah kuma ya bani abin da zan taimaka musu da shi, suma kuwa suna nasu Kokarin..." "Ai Gwaggo ba sai kin fada ba, wallahi kowa ya shaida hakan. Allah nc zai biya ki." Nayi saurin katse ta ne saboda na lura ranta yana baci, idonta take ya sauya kala, har da kamar kwalla za su fito daga idon nata. "Kai mata irin Haj. Basira Allah ne kadai zai iyaа da ita, amma shaidan ce. Allah Ya shirycta in mai shiryuwa cс." "Amin." Gwaggo Hauwa ta katse ni, ta ce "Duk da ban taba haihuwa ba, wallahi ina da kwanciyar hankali tunda Allah Ya hore min baiwa ta zama da 'ya'yan mutane. Ina alfahari da hakan ko 'ya'yan sun butulce ballantana' ma Alhamdulillahi baki dayansu na aurar da su..." Na sake katse ta. "Gwaggo ke uwa ce da ba ki haifan ba ma nayi miki alkawari Giwaggo inshaa Allahu zan yi miki Page | 45 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] biyayya tamkar mahaifana a kaina, ina so in zama 'ya a garc ki, kuma inshaa Allahu za ki zama mai alfafahari da ni. Fara'a ta saki sosai da har hakoranta suka bayyana, sannan na lura a cikin kwayar idonta akwai wani nishadi na daban da ya shige ta. Tasa hannu ta rungume ni tare da shafa min gashin kaina, tana sa min albarka tarna kuma hamdala ga Allah, ni kuwa a raina kara daukar wa kaina alkawari nakc yi, zan zama mai cikakken biyayya gare ta. Muna cikin haka sai muka jiyo sallama daga bakin kofar falon, Gwaggo Hauwa naji ta ce, "A a! Tahir har ka dawo?". Murmushi ya saki wanda bai kai ciki ba, ya Karaso yana cewa, "Gwaggo na dawo an wuni lafiya?". "Lafiya kalau." Har sai da ya zauna sannan ya ce, "Gwaggo madarata nake bukata." "Ai ko na manta da shi a can (Gardiner), bari in kira Babale ya dauko maka." Sai a lokacin na gaida shi, ya amsa ba tarc da ya dubi inda nakc ba. "Umm!" na fada tare da mikewa tsaye. A raina kuwa ina tunanin hali na masu wulakancin nan daga shi har matarsa ai halinsu daya, sam basa da bambanci, saboda dai dukkansu Allah Yayi masu girman kai, duk da rawar kaina Page | 46 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] sam ban nemi in shige masu ba, don na yi wa kaina alkawarin ni da 'ya'yan Hajiya Basira sai dai ido, don dukkan su halinsu daya ba su da bambanci da uwarsu... Gwaggo ce naji tana cewa, "Anya Tahir ka san 'yar uwarka Dayyiba?" A daidai lokacin kuwa muka vi ido hudu da shi. Sai da gabana ya fadi, saboda idanunsa suna da wani irin abu da ban san ko menene ba. Da sauri nasa idona kasa, naji ya ce, "Ok, ita cc Kanwar taki da ki ke bani labari?" "Haba dai Tahir, ka ce ba ka san 'yar Malam Sabi'u ba ce? Uwa ce fa gare ka." "Haba dai Gwaggo, ta ya za ayi ta zama uwata, sai dai in a Hausance ko?" "A'a wallahi ana iya kiranta uwa a gare ka, saboda kanwa ce a gare ni da kuma Baban falo, ko ka manta mahaifiyarta Gwaggonmu ce, tunda Kanwar su Babanmu ce." Ya ce, "Ikon Allah! ashe haka dinne dai uwa ce a gare ni: Ni dai ina jin su amma na riga na karasa daki, nan kuma ya canza hirar zuwa ga ta (Business). Can naji Gwaggo na cewa. "Wai Tahir na ba ka shawarar ka kwantar da hankalinka, ka ki ko? Dubi yadda ka fada sai ka ce ba kai ba, shin zaman duniyar nan nawa take da zakа Page | 47 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] sa wa kanka tunani kana ba wa kanka wahala, ka duba ka gani babu abinda ka rasa, Allah Ya hore maka a duniya shekaran jiya nan Babanka ke bani labarin ka sami kwangilar da ka ke nema ta harkar mai, to menene naka wai iya ka ci ka kwantar da hankalinka kaji dadin dukiyar da Allah Ya baka." Shiru yayi yana saurarenta, Gwaggo duk yanayin zamana da Suwaiba kin sani to ni wallahi na gaji da matsalarsu daga ita har Mama, wai cewa tayi in rinka tafiya da ita gun aiki duk garin da za ni sai naje da ita, shin Gwaggo domin za a takura ni a kan abinda ban yi niyya ba, ni shi kenan bana da ikon sa doka a gida sai Mama ta shirya min yadda zan yi?". "Hakuri za ka yi, yarona dan albarka. Wata rana sai labari zai wuce..." a daidai lokacin Suwaiban ta shigo, sai naji Gwaggo tayi shiru. Can kuma naji ta ce, "Ashe ba barci kike yi ba, dama kina falon kenan? sam ban ji amsar da ta ba wa Gwaggo ba, duk da kasa kunnenta da nayi. Hum! Lallai matar nan tana da jin kai, ko magana wato dole ce ta zama mata, kai mulki dadi, Allah ba mu wanda zai amfanc mu amin. Haka na gaji idan ina son jin gulma sai dai bukata bata biya ba, don falon suka bari daga nan na shige bandaki don in yi wanka in yi sallah. Ban Kara yadda na hadu da ko dayansu ba, saboda na lura mulkin nasu sai su, ban ma fi kwana Page | 48 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] biyu ba na wuce Sokoto, don dama na kan je lokacin hutu amma ba kowanc ba. Kwanana tara na koma gida Kaduna, a can Gwaggo ke bani labarin ai da kyau Suwaiba tayi kwana hudu, sai da suka yi rigima da Tahir, karshenta ma sai ita cc ta wuce ta bar shi a nan. Ni dai bai ko taba bani tausayi ba saboda ai hali shi yake ja wa mutum, halinsu ne. Don haka sun dace da junansu. Kwana biyu na kara na koma Makaranta, muka hade da Aisha takc bani labarin an sa mata rana. Muna gama (Graduation) da wata biyu za ta yi aure. Nayi mata murna kwarai, don dai tayi sa'a ta auri wanda take so, ba tun yanzu suke tare ba, tun muna aji biyu yake sonta har gashi Allah Ya nuna mana mun gama. A gaskiya duk da rashin biye wa abokai Aisha daban ce, saboda muna shiri sosai da ita, tun haduwarmu muke tare gashi mun gama fara jarabawa. Cikin wata biyu kuma muka gama har da Neco, muna gamawa a ranar muka wuce Kaduna. Tunda na koma gida ba inda nake zuwa a koda yaushe ina gida tare da Gwaggo, a lokacin wata shakuwa ta musamman ta karu tsakanina da Gwaggo, in ban da shagwaba da iya yi ba abinda nake yi, sam bana shiga (Kitchen) balle in koyi girki, hatta taliyar (Idomie) zan ci to dafa min za ayi. Page | 49 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Ana saura kwana shidda za'a fara biki, Aisha ta hada ni da babban abokin mijinta. Abin mamaki sai naga kamarmu daya da shi. Ita kanta Aisha abin da ya bata mamaki da sauran wadanda muke tare da su, sunansa Sa'id. A gaskiya tun bai furta yana sona ba naji a raina ya yi min, don yadda nake son suffar da namiji haka yake. Yana da tsawo, ga shi ya iya shiga, shigar Kananan kaya yake yi, sannan ga shi da sakin hannu saboda shi ya dauki nayin (Dinner) din su Aisha ma. A gaskiya ya kashe ni da birgewa, don duk wani mafarki a kan da namiji da nake burin samu yana da shi. Motar da yake shiga ma abar kallo ce. (Ford) ce kuma (Jecep) mai fadin gaske, in ka shigeta sai ka се kana cikin Jirgi. Da bai furta yana sona ba da ban san yadda zan yi da rayuwata ba, sau da yawa in na tuna irin halina na kan dantanshi da 'yar karya, saboda irin rayuwar da na daukar wa kaina abun mamaki Aisha tana hakurin zama da ni, donni komai nawa nafi son hadadde. A kullum idan ina bata labarin irin rayuwar da na zaba wa kaina ta kan cc min in dai bi a hankali don duk mai irin halina a karshe burinsa baya dacewa da shi, sau da yawa irin rayuwar da ka ke so ita ce bakа samu gara dai kai ta addu'a, ai maganar da nake yi Page | 50 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] ina yiwa kaina baki ne don in sami hakan а rayuwata. Ni nasan ba karamin kyau nayi a wannan auren na Aisha ba, don a gaskiya Gwaggo bata wasa wurin sai min kaya da kayan kwalliya, shi yasa sam Sa'id ya ki yadda in yi nisa da shi, in dai taro ya hada mu da shi mu kan samu kamar kusan awa muna hira, sai dai duk da haka bana gajiyawa da ganinsa. Gidan Aisha a Malali G.R.A yake, muna kusa da su, don mu muna Unguwar Rimi ne a Inuwa Wada, shi yasa na ce da ita sai ta gaji da ganina. Mun bala'in sabawa da Sa'id, a cikin raina kam ban san dalili ba, ina sha'awar ganin sa ko don yana kawo min kayan dadi ne oho, amma ba wai nasa harkarsa ne a gabana ba, saboda ina tsoron in so shi yayi min irin na Amir, sai dai ni na sani tuni na kamu da sonsa. Mun sami kamar wata goma a gida kafin (Admission) ya fito, ikon Allah ni ban sami (Admission) ba shi ne fa mijin Gwaggo Alh. Shehu Magaji ya bada shawarar a nema mini (Polytechnic Kaduna), sam ban ki ba saboda zaman gidan ya ishe ni, gashi Baba ya soma maganar aure, Gwaggo ta nuna masa ai aurc za'ayi shi sai da wanda nake so ne bai fito ba amma in sha Allahu za a zauna da shi ayi magana. Cikin ikon Allah kuwa na sami (Period) a nan (Poly Cabs) na sami (Business Admin). Page | 51 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Soyayyarmu da Sa'id kuwa a kullum karuwa take yi, ni dai ban taba yi masa maganar aurc ba, sai dai shi a kodayaushc bai da magana sai na in ya aure ni zami yi kaza zamu yi wancan, to shi ne dalilin da yasa na saki jiki da shi sosai, kuma na kara sa wa raina shi ne dai zabina. A nan Makaranta (Poly) a gaskiya duk da rawar kaina ina kokarin kama kaina, don wata rayuwa ce ta daban, na samu kawa Rahinatu, ita 'yar Lagos ce a nan ta sami Makaranta sanadin Kawunta, don haka ma a gidansa take zaune. Itama kyakkyawa cc, fara ce sosai tana da kyau. Kawancenmu ya yi karfi saboda kusan halinmu daya, sai dai ita tafi ni iya yi, har a raina na kan yi mamakin ashe akwai wadda tafi ni rawar kai. Ga ta da shisshigi, komai kuma aка сe a kan wani abu ta ce miki ta fiki saninsa. To haka dai muke zaune da ita, da yake ni kuma halina ne duk yadda halin mutum yake ina iya zama da shi ba tare da na matsa wa kaina ba. Haka mukai ta zuwa Makaranta har muka gama (First Semester), Allah Ya taimake ni bana da (Spil over), Rahma ce ma take da guda uku. Ni na san haka na iya faruwa, don Rahma in ban da karya ba abinda ta sa a gaba, ga son hira da maza kala-kala, in yau ka ga wannan to gobe wani za ka gani, ba abinda yafi bani haushi da ita irin shisshiginta, ta fiye shisshigi. Page | 52 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] Sau da yawa wani abun in tayi ni nake jin kunya, gata dai Allah ya bata duk wani abu da cikakkiyar 'ya mace take son samu, ita tana da shi. Koda yake dama an ce mutum bai taba cika goma ba, a taba halittar mutum cikakke. A wannan hutun ne suka hadu da Sa'id har gidansu muka je nayi (Introducing) din Sa'id ga Rahma, a matsayin wanda zan aura. Sosai ta jinjina min na samun gwarzo irin Sa'id, itama sai da ta gaya min irin kamar da muke yi da shi. Ban sami zuwa Gusau ba wannan hutun, ban kuma damu in je ba saboda na lura Baba ya soma matsa min da zancen aure, ni kuwa ina son samu ne so nake ko 'yar (Diploma) in samu, sai dai naje gun Anti Fiddausi da ta haihu ta samu Faisal, nayi kwana hudu na dawo. Mun koma makaranta, Rahma dai tana nan da halin nan nata sai dai ma abinda ya karu, haka kuma nake tare da ita, to ya zan yi tunda haka nima na zabawa kaina, sai ka ce dole. A wannan (Semester) din karatu yayi mana yawa, don ta shiga (N.D.I) ce don haka dole ne ma na fidda komai a gabana, karatu nake yi sosai. Sa'id kuwa kusan sau biyar yana shiga Makarantar in ya shigo gari ya ke ina (School) sai kawai ya wuce can. Mun gama wannan (Semester) sai hutu, Gwaggo ta ce min inshiga makarantar Islama, a take Page | 53 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] na amince na shiga (AL-AMANAR ARABIC SCHOOL), na kuma yi sa a (Pre Basic) suka bani, duk da ina da izifi talatin suka ce ai makarantar ta arabic ce, don haka dole in soma daga farko. Shi yasa na rage fita sosai don na maida hankali sosai. Ina zuwa Islamiyya, ga shi ina jin dadin karatun sosai, a nan kuma na hadu da Aminatu Amin, ita kuma 'yar asalin Kano ce, ita kusan halinta daya da Aisha, shi yasa na nace zan haďu da su. To da na ba Aisha ma labarin Makarantar sai ta ce zata shiga itama da yake nima na matan aure na shiga. Cikin sauki kuwa itama ta shiga muka hadu mu uku, ita Aminatu tana da kishiya tare ma suke zuwa. Sai dai tana gaba da ita, ga shi tayi dacen kishiya sam ba sa da matsala zaman aminci da yadda suke yi, don a kullum tare suke zuwa kuma tare suke tafiya, duk da kowace na da motarta, amma ba za ka taba fadan wacece ta wancan ba, kowace shiga suke yi har na maigidan nasu. Mun koma makaranta, Alhamdulillahi nayi (Passing) ina da (Lower Credit) a (GP) dina, don haka muka ci gaba da karatu, ita kuwa Rahma ta sami matsala, amma tana da (Pass), don haka dai muna tare. A wannan lokacin ne ganin Sa'id ya soma yi min wuya saboda (Transfer) din da ya samu zuwa Lagos. Sai muyi sati uku har wata ma ba muga juna ba, Page | 54 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] waya ma mun rage sai ya ce aiki ne ya yi masa yawa. Na yadda don karin girma ya samu, don haka dole ne yanayi ya canza. Ya ce min in ya fita tun safe ba ya samun kansa har sai karfe tara na dare, don haka ne muka koma yin wayar dare shima din bai wuce na minti sha biyar zai ce don Allah in yi hakuri yayi bacci ya gaji da yawa. Ina tausaya masa sosai, don dai mutum ya kasance yana aiki tun safe har dare, gashi sonsa yayi ambaliya a raina, ina bala'in sonsa. Su Aisha har cewa suke yi da alama ni na fi son sa a kan yadda yake sona, ni dai ban yarda ba, gani nake yi shi din ne yafi sona ni tausayinsa ne kawai yayi min yawa. Haka rayuwa ta rika wucewa har gashi muna (Final Year) dinmu na (Diploma), har ma mun yi nisa don mun kai kusan wata biyu da rabi da karatu a (Final Year) din. A wannan lokacin nc Baba ya matsa sai dai in fito da miji in yi aure, saboda su Maimuna da Zalihat sun fitar da wanda suke so, suna gama Makaranta za suyi aure ba za su fi wata biyu da gamawa ba, don haka in fitar da wanda nake so don a hada ayi biki gaba daya. Hankalina ya tashi sosai, don kwata-kwata yanzu sai muyi kusan sati ma ba muyi magana da Sa'id ba, Page | 55 MARUBUCIYA: Sameera Mustapha BAKI BIYU [1] tun abun bai damuna har na fara damuwa, gashi Gwaggo ma ta bi bayan Baba, ta ce in yi wa Sa'id magana ya fito. Na rasa inda zan sa kaina. Tun da satin nan ya kama nake ta faman neman Sa'id a waya bana samu, sannan na

Chapter 3 of 7