Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 7
ya ce ni ce na zubar mishi, haba Suhaila ai ba zai yi haka ba ai gara a gaya mishi don ya san abinda kike ciki na soma yi mata kuka ta shiga rarrashina to yi hakuri Suhaila shi kenan a barshi kawai ai shima da laiſinshi na yi zamana anan inna kuwa ta shiga hidimata tana ina taka saka dani komai yi mun take yi ina jin inda da hali ma da ta karbeni numfashin da nake yi, Hakcem yana Abuja sai dai waya yake yiwowa yana tambayar yaushe zan dawo, ina ce mishi kwanan nan ina lura mishi da asibitine ina tayasu aikin jama'a ya bani Suhaila mu yi magana ta gaya mun yau baba teacher ko baba Lamido ya kaita wuri kaza da kaza ya saya mata kaza da 45 Ashiru ta Kara haihuwa Lamido da kanshi ya kaini sunan muka yi da an na ga na ai la kwana daya muka wuce Abuja muna dawowa na fara zuwa asibitin Garki awon ciki shi kanshi likitan mata na asibitin da ya ganni da ciki Karamin murna yayi ba don kuwa dama kusan kullum sai mun zo gabanshi ni da teacher kan matsalar rashin ciki kulawa ta musamman samu a asibitin, kan harkar karatun kuwa na ci gaba da zuwa jami'a karbar lacca, teacher kam hankalinshi da matsuwarshi suna kan cikin danake dashi shima Yaya Bashir kusan hakane kowane lokaci ai turo Anti Hama wai ta zo ta dubani, itama Hama zirga-zirga ya semeta ta kai ta kawo, gashi dama teacher ya ki yarda da yawan ufiyc-taliya ko Jos zashi zuwa duba lafiyar Inna kamar yanda yake yi aduk karshen wata tun daga lokacin da ya yi mata aiki baya yarda ya je dani wai shi jami'ar da nake zuwa ma a dolene, kuma wai da yake ya san yana da kyau in dan rinka motsa jiki amma ba mai tsanani ba, tun cikin yana da wata shida Hakeem ya gama shirye-shiryenshi na haihuwa a Gire da Abuja ya kammala shirya dakin jaririn kullum yana baiwa Suhbaila labarin nan bada dadewa ba zata samu dan uwa ita kuwa ta yi ta tambaya ta Antina zaki kawo mana sabon baby nc? In ce in sha Allahu Suhaila, ko ciwon kaina ce ina yi zai kaim asibiti cikina ya kai wata bakwai, ya yi girma sosai tamkar ba cikin kuruciya ba, sati biyu na kara kan wàta bakwai din hakeem ya yi tafiya zuwa Legos kwana uku kawai zai yi tafiyarshi dakwana daya na wayi gari ina matukar jin nauyin jikina, fuskata, idanuwana da kafafuwana gaba daya suka tattashi ban dai damu dahakan sosai ba saboda na saba ganin mata masu ciki da makamancin wannan kumburin a ranar da Hakcem zai dawo ne na wayi gari ina fan ganin alamar jiri-jiri waya na yi Garki na shaidawa likitan da nake gani Dr Tijjani na gaya mishi abinda yake faruwa cewa ya yi in zauna cikin shiri yanzu zai turo a daukeni muna gama magana dashi na bugawa Anti Hama cikin sauri ta iso, tarc muka tafi asibitin Dr Tijjani ya gama gwajin da zai yi ya labbatar mana da ccwar dan dake ciki yana gicciyene bayan haka kuma yana cikin matsala Yaya Bashir ya iso don jin abinda ake ciki likita ya yi mishi bayani ina ganin yana da kyau a sanar da Hakeem ko da dai yau zai dawo ina cikin fama da wahalar kokarin da ake yi na gyara kwanciyar yaro sai kuma na samu da ciwon nakuda, haka e r a aka hakura aka zubawa sarautar Allah ido Hakeem ya iso asibitin 47 kusan sallar Azahar ne hankalinshi ya yi matukar tasbi ga balin da nake cikı ga zullumin dan da za a haifar mishi wajen hudu da rabi na yamma Hakeem yana cikin likitocin dake tsaye & kaina na haifi sambalelen yaro namiji wanda girmanshi ya kai masu wata tara gashi jazur sambalele gwanin sha'awa sai dai numfashi ya gagara babu juyin da ba ayi da yaron ba ya yi kuka abin bai yiwu ba cikin banzari Dr Tijjani ya fita dda yaron zuwa wani daki wai za su sanya mishi abin taimakon numfashi Hakeem yana tsaye jikin gadon da nake kwance yana rike da hannuna cikin wani irin yanayin da ba zan iya bayyanawa ba ta ko ina gumi sai keto mishi yake yi har aka fito dani daga dakin haihuwa aka kawoni inda zan kwanta, in huta Dr Tijjani ba su fito daga dakin da suka shiga da yaron ba Yaya Bashir ma yana wurinsu ni kaina a kidime nake ina son sanin halin da ake ciki na kalli Hakeem a hankali na ce Lamido duba mana su mana ya yi murmushin karfin hali ya ce babu amfanin zuwana Suhaila bar ni in zauna kusa dake ganinki yana sanyaya min zuciya bana zaton yaron zai rayu sai dai Alhamdulillahi tunda kina da lafiya, hawaye suka gangaro mun a ido yayi maza ya sharesu ki yi hakuri Suhaila kar ki yi kuka zaki sani cikin matsananciyar damuwa yaya Bashir ne ya fara shigowa Dr Tijjani yana biye dashi ya iso inda muke a hankali ya cc Hakeem sai mu yi hakuri Allah ya sa yaron ba wanda za a ci amfaninshi anan bane sai mun je can tukuna sun yi iya kokarinsu har ya dan fara numfashi yayi kamar sau biyar sai kuma ya tsaya, ka sani kokari kawai ake yi amma rayuwa ta Allah ce, Hakeem ya ce haka ne, ni kam kasa hakuri n ayi kuka sosai nake yi Dr. Tijjani ya kama hannun teacher suka fita, Yaya Bashir ya matse kus adani yana mun nasiha, har dai na hakura na yi shiru, an sallamomu mun dawo gida, jama'a suka yi ta zuwa gaishemu ni kam kunci ya dameni cikin raina tausayin wahalar tcacher na yi ta yi da irin yanda ya matsu ya samu da gashi an samu namijin da yake nema, gashi bai rayu ba na tuna haihuwar da na yi a gidan Shariftunda na yi cikin har na haihu Sharif bai taba bata lokacinshi wajen sanin abinda cikin ke ciki ba, amma na haifar mishi 'yar shi a raye, satina biyu dahaihuwa na nemi teacher ya kaini wurin mahaifiyata bai yi musu ba, ina shiga falon Inna kwanciya na yi a jikinta kukan da kullum nake daurewa bana yi agaban teacher don ganin da nake yi tamkar ya fini dmauwa kar in 48 mishi da yawan kuka ran nan kasa daurowa na yinaco wayyo Inna ni karn ya ya zan yi? Duk wani abinda nako so mutuwa yake yi nabarina, na shiga kuka sosai, yi bakuri Suhaila, hakuri ake yi, huwar da ya mutu akwai ciwo to amma kuma akwai sakamako i yawa ga iyaye masu hakuri da tawakkali, tsawon lokaci tana wazikafin su teacher da yaya Ashiru suka shigo tare don dama danya fara shiga, bayan tafiyar Yaya Ashiru Inna ta sake yi mana asiha ni da teacher kan mu mayar da dukkan al'amuranmu ga Allah, arokeshi alheri mu yarda kuma da duk abinda ya yi mana koda Lbanin abinda muka sone shi ne mafi alherin a garemu, kwana dayan muka yi a wurin Inna mn samu cikakkiyar nutsuwa da kwanciyar ankali da karfin jiki muka dawo Abuja ni kam na koma zuwa jami'a sukar karatuna teacher kuwa ya ci gaba da ayyukanshi shi dama ba azauni bane, yawan aikine dashi ga duba marasa lafiya, masu ciwon uciya a Garki gashi yana daukar dalibai masu karatun likita a jami'a asibitinshi na Gire wanda duk karshen wata sai ya je ya duba arasa lafiya da ciwonsu ya yi tsanani ga tafiye-tafiyenshi kan kinshi ran nan teacher ya dawo daga London sati uku ya yi a can, na kwance kan doguwar kujera wai barci yake so ya dan yi anan ma ba mai yawa ba don yana son zuwa duba wani mara lafiya da ke shirye-shiryen yi mishi tiyata a wannan satin. Ina zaune ta wurin kafafunshi ina matsa mishi su kafin barcin ya ukeshi sai na ce mishi ni kuwa teacher ina damuwa fa ban dai gaya aka bane amma kuma abin yana kara damuna ya bude ido yana llona tare da tambayar me ya faru? Na ce to ni tunda na haihu ban al'ada ba balle in sa ran sake samun wani cikin amma kuma tun ekaranjiyar can sai in ajin kamar wani abu yana mun motsi a ciki kara zuba mun ido ya ce musu ne dake Suhaila tun kwanaki nake miki ina ganin kamar kina da ciki kika ki yarda wai ke baki ma yi ada ba tunda kika haihu sai ki shirya mu je Tijjani ya dubaki in na ma da wannan mutumin sai in zo in sameki in ji abinda kuka yi, n to ina kwance kan gadon fikita Dr Tijjani yana tsayc a kaina van ya gama gwaje-gwaje da aune-aunenshi Yaya aka yi haka ciki girma a jikinki amma baki sani ba? Na ce to ni bana jin komai a kawai nake yi amma bani da wata lalura, ya ce to kiki wata hudu ma 'ya'ya biyune na rike baki cikin mamaki n ace don Allah Tijjani 49 kar ka gayawa llakeem a barshikawaı ya san ina da ciki bana son ya sake kwallafa ranshiakan cikin da yawa Dr Tijjani ya yi murmushi ba tare da ya ce mun komai ba, Hakeem ya gama zaga marasa lafiyar da yake dubawa a asibitin ya dawo ya sameni yaya dai Tijjani? Abinda ya fara fadi kenan yana kallona yana 'yar fara'a Tijjani ya tayashi murmushi ya ce to ai kaima dama ka san dashi Dr. Hakeem ya cc a'a to ai ni an yi mun musu, Tijjani ya ce to akwai har ma ya yi kwari don wajen wata hudu ne har da kwanaki, muna dawowa a hanya tcacher yana zolayata har yau din nan fa ba ki cika wata shida da wancan haihuwar ba, wannan karon dai ina jin gami da kasawa kawai aka yi na ki kulashi, to ga Mr Biggs a gabanmu zaki shiga ko kuwa mu wuce? Na ce a shiga zan shi shawarma, ya ce uhum ai kuwa in banda nima da tun lokacin da na ga an tsananta mun aiken shawarma har in na mance ayi mun fushi sai na sake fita na kawo da tunlokacin kawai na soma lissafi, wannan cikin ya bambanta kwarai da wancan gashi dai an gaya mun 'ya'yan biyune a cikin nawa amma kuma garau nake ji na bana jin wani kasala ko tashin zuciya kuma a yanzu ne na yarda da zancen teacher cewar mace mai ciki kafin ya girma sosai tana da yawan bukata, kullum cikin tsala kwalliya nake don in kara jan hankalinshi gareni, kowane lokaci cikin soyayyarmu muke sai ko yawan barci mai dadi yawancin aikace-aikacen da da nakc yi a yanzu Hakeem ya karbeni su Suhaila dai mai renonta ke kulawa da komai nata, ni kuwa ran da na samu dama in yi mana girki ni da mijina in ban samu ba in yi kwanciyata in ya dawo y ayi mana in kuwa naga zai yi magana in langwabe in ce mishi ga wani abinda na ji bai mun ba a jikina sai kuma ya shiga tambayar ko ya akaini asibiti in ce a'a zan ma ji sauki nan da an jima, cikina yanagirma a hankali a hankali, yana tafiya tare da watanninshi saßanin wancan da ya yi girma na farat daya ya bayyana kowa ya ganshi cikin kankanin lokaci wannan bin jikina ya yi sai dai ni da nake dauke dashi nina san nauyinshi a wannan lokacin na shiga zana jarrabawata ta karshe ta kammmala karatuna na digirin farko kan ilimin harhada magunguna wato Pharmacy teacher ya yi iyakar yin shi wajen ganin ya taimaka muna gidane ko a makaranta, kulawar da teacher ya nuna kan jarrabawata mai yawa ce dake mun komai yayi ko wani dan aiki ya zo ya samu in ayi karbewa yake yi ya ce je ki ki zauna Suhaila ko ki 50 C E Eha ka ha tar ka da kol mu shi hat ek kav mo na ma an un kwanta ki huta an jima zan tasheki ki yikaratu ko kin manta gobe ko jıbi za ki zana paper kaza da kaza, in ce to Hakeem ai wannan din ne ya ce kawo kawo ki gani nima na iya zan yi miki ya karba yayi in kuwa karatu nake yi to komai darc ba zai kwanta ba sai in nace mishi na gaji zan kwanta in na bukaci wani bayani kan karatuna daga wurinshi ya rinka yi kenan da baki da biro har sai na ce mishi na gane, ya ce mun to fadi abinda kika ganen in ji, in gaya mishi уa сe с, to na yarda kin gane saboda haka jarrabawa mai dadı na yi nayishi na gama cikin kwanciyar hankali ba tarc dana gamu da wata matsala data tayar mun da hankali ba, muna kammala jarrabawa teacher ya shirya mun liyafa kasaitacciya don tayani murnar kammala karatuna, 'yan uwan, abokan arziki har daga Gire mutane sun zo da yawa, cikina ya shiga wata shida da sati biyu ina kwance kan gadona shan iska nake yi na bude windon nan dakin gaba daya iska sai kadawa take yi, Hakeem ya fito daga toilet din dake cikin dakin nawa wanka ya yi ya zo ya tsaya a kaina, Suhaila bude mun cikin nan in gani na harareshi na ce tafdijan haka kawai kuma sai in bude maka ciki a waje kayi ta Kallonshi shi ba kyau ba ba komai ba, ya ce bude mun kawai kece baya miki kyau akwai abinda nake so in gani, na ce menene ya ce to bude mun mana ni fa ban yarda da awon da ake miki ba a ganina yara biyu ne a cikin amma kallum kika dawo na tambayeki sai kice wai basu ce miki komai ba mu gani zan dubaki da kaina na ce a'a teacher abinda na saba jin kana yi shi ne duba zuciya da abubuwan da suka shafcta, amma ba da a ciki ba barni kawai in na koma asibiti zan gayawa Tijjani ka ce baka gamsu da awon da ake yi mun ba sai ya dubamaka ni ko ba haka ba? Na gama abinda zan yi na shigo wajen tsuntsayen Hakeem ina watsa musu abinci sna ci wasu har sauka a jikina suke yi don mun riga mun saba da juna, teacher ya leko zo ki rakani nan Suhaila na ce to na yi maza na fito,jallabiya cc kawai a jikinshi sai silifas din wanka na biyoshi na ga ya shiga motarshi Honda 98 model, nima na shiga na zauna ina tambayarshi ina zamu, bai cc komai ba, ya fara tuki sai gamu a gidan Tijjani matarshi bata nan don haka a falonshi muka zauna, lafiya na ganka yanzu? Hakeem ya ce lafiya Garki na yi nufin zuwa in sameka sai na tuna kana gida so nake yi abinda ke tafiya game da cikin Suhaila, Tljjani wake lura da awon nata ne ni fa ban gane ba, Tijjani ya сc 51 kamar ya ya Hakeem ya yi mishi bayani Tijjani ya dan yi murmushi sai ya ce ita ta hanani gaya maka biyune, Hakecm ya kalleni ranshi a bace sai Tijjani ya ce amma fa ta yi haka ne don a baka mamaki kuma wai ta rage maka yawan zumudin abin ina ganin taimakonka ai ta yi ko kuwa? Ya ce to ni ba a burgeni ba, kuma har dakai dukanku masu laifine, ya ce to na ari bakinta na nemar mana gafara ya ce to an gafarta muku. Duk da sanin da Hakcemya yi 'yan biyune a cikina komai a cikin nutsuwarshi yake yi sabanin wancan karon da komai yake yin shi cikin zumudi a yanzu ya fi maida hankalinshi wajen yin addu'o'i rokon Allah ya in haihu lafiya yaran ma lafiya a wannan karon Hakcem bai taba ambata abinda ya fi so ba ko ni ce na zolaycshı na ce ace dai in haifi 'yan mata biyu masu kama daya da sai in yi ta yi musu kwalliya iri daya su yi gwanin sha'awa, dariya yake yi ya cc duk abinda Allah ya bamu muna so Suhaila, Allah dai ya bamu masu albarka, in ce mishi amin, wannan lokacin Hakeem ya samu shiga cikin kungiyar lafiya ta duniya "WHO" wato "WORLD HEALTH ORGANIZATION" har ma sun nadashi wakilinsu mai kula da jihohin arewa masu gabas guda shida Baushi, Borno, Yobe, Adamawa, Taraba da Jigawa a wannan lokacin ayyuka sun iwa Hakeen yawa ga tafiyc-tafiyc inna ta aiko mishi cewar ya malar dani Gire in haihu a can kusa da ita ya ce a bata hakuri ta barni in haihu a Abuja a babban asibiti inda zan samu cikakkiyar kulawa dani da yaran duka don haka sai ta turo Sumaye wai ta zo ta tayani zaman gidan, Sumaye jarumar tsohuwace wacce ko kadan baya son ganin kazanta ksua da ita don haka na ji dadin zama da ita ba kadan ba, cikina ya shiga wata na tara lokacin da takardun tafiya hidimar kasata suka fito zan kuma yi ne anan Abuja dama abinda teacher ya nema kenan, tare da teacher muka je hedkwatar 'yan bautawa kasar na yi komai da zan yi a matsayina na sabuwar zuwa da muka gama sai kuma muka mika takarda mai d'auke da sa hannun likita na umarnin in huta a gado wato bed rest har sai na haihu suka amince. Hakeem yana wurin taron kungiyar lafiya ta duniya wanda a wannan lokacin ake yi a babban birnin kasar [Holland, taken laron a wannan lokacin kuwa shi ne "Illar kanjamau ga tattalin arzikin duniya.' Na wayi gari da safe ranar litinin ina ciwon mara da baya ni 52 kam na san nakuda tunda ba baihuwar farko zan yi ba ta uku ce don baka kai tsayc na shaidawa Sumaye cewar nakuda nake yi Sumaye ta so wai in daurc in haihu a gida amma ban yarda ba bawai don ba zan iya dauriyar bane, a'a sai don sanin da nayi cewar matukar na zauna na haihu a gida to ko jariran da zan haifarwa Lamido sune za su fi kowadannen jarirai lafiya sai ya nuna mun bacin ranshi don kuwa kullum a cikin gargadi yake ko juyi kika yi irin wanda baki saba dashi ba ki yi waya a zo a duba ki ran nan wai ni zan zolayeshi na ce haba Hakcem a gidan Sharif fa ni kadai na haihu a dakina kawai na ga fuskarshi ta canza ranshi ya baci ya zuba mun ido kamar zai yi mun magana ya kuma fasa ya juya zai tafi da sauri na bishi durkusawa na yi na kama kafarshi taba nakc Lamido Allah ya huci zuciyarka ban taba zaton ambaton sunan mutumin nan a kusa da kai zai iya bata mka rai ba gani nake kasan komai ka san yanda aka yi na shiga hannunshi kasan zaman da na yi a gidanshi ka san shi ne mutum na karshe da zan zabarwa kaina to meye abin jin zafinshi? Hannu biyu ya saka ya kama kafadura ya dagoni na tsaya ya ce duk dahaka wani lokaci ya kan mintsini zuciyata Suhaila yawan sonki kan tilasta mun kishin mutumin duk da na san bai taba samun matsuguni a zuciyarki ba, duk da haka gani nake tamkar ya zalunceni tunda ya karbe mun budurcinki wanda ya kamata ace nawa ne na yi narai-narai da idanu tamkar hawayc zasu zubo na ce amma ba haka muka yi da kai ba Lamido na yi maka korafi tun farko cewar kana bukatar budurcina ne wanda babu ya tafi ka ce mun ba budurcina ne muhimmin abinda kakc son mallaka a jikina ba zuciyata kake son mallaka muhimmin al'amari a wurinka shi ne kana sona ka kuma sameni don haka ba zaka waiwaya baya ka kalli komai ba don ba zai yiwu ka tuhumi kaddara dalilin da ya sa ta yi aikinta ba amma kuma a yau kana gaya mun wai kana jin za fin budurcina da ka rasa alhalin ni na sani budurcina a haka kawai ya tafi don shima bai mori komai akai illa wahala da matsananciyar azaba, yi hakuri Suhaila na tuba Suhaila ba zan sakc miki maganar komai na baya ba, Suhaila gaba kawai zan rinka kallo in har zan yi waiwayc tunda an ce shi ne adon tafiya to zan waiwayoki ne a aji in tuna shiriritarki ke dasu Eze in tunaki lokacin da kullum sai na kawo mun sunanki cikin masu surutu, murmushi na yi na kwanta a kirjin tcacher shi kuwa ya sa hannu biyu 53 ya kankamenıi, don haka na baiwa Sumaye hakuri na ce mu je asibiti kawai awa uku bayan isarmu asibiti ina kwancene tare da jariraina guda biyu na ce da namiji macen kamarta daya da Lamido ya dauko tamkar kakinshi ta yi Anti Hama ta tasasu agaba sai kallonsu take yi, Sumayc kuwa sai tasbihi takc yiwa Ubangiji tana cewa godiya ta tabbata gareka ya Allah da ka azurta zuciyarmu da wadannan lafiyayyun yara, a ranar kawai aka sallamoni muka dawo gida yaya Ashiru da matarshi Sa'a har da yaran su gaba daya suka iso gidana ganin yara muka sha hira sai yamma ya tafi gidan Yaya Bashir ya bar Sa'a da yara muka kwana sai washegari ya zo ya daukesu akan sai kuma suna shima Yaya Ahmad tare matarshi da 'yarsu Aisha suka zo suka wuni suka tafi, Haka bata zo ba saboda mijinta bashi dalafiya, Yaya Bashir kuwa da matarshi babu abinda zance musu sai dai Allah ya saka da alheri hakika Yaya Bashir wa ne na kwarai dake rikidewar ya zamewa kannenshi Uba tsayayyc mai tsarewa 'ya'ya dukkán hakkuwansu, in kaga yanda 'yan uwan Lamido da iyayenshi kai in ce ma danginshi gaba daya da mutanen garinsu ke ta zarya tsakanin Gire da Abuja kai kace tafiya ce da fa bata fi 'yan kilomita kadan ba sai in an ce maka nisan wurin ya kusa kilomita dubu ka rike baki don mamaki abokan Hakcem suma ba a barsu a baya ba, sun nuna halarci yara sna da kwana uku a duniya Yaya Bashir ya zo ya sameni kan maganar yiwa yara huduba na gaya mishi bayanin da mahaifiyar Lamido ta yi ya yi murmushi ya ce anya ayi haka Suhaila wannan ai shi ne wani da tusa wani da karbe riga, na yi murmushi kawai ban ce mishi komai ba, komai na shirye-shiryen suna ya kammala tamkar Hakeem yana gida aka yi haihuwar gashi Yaya Bashir ya ki yarda a aike mishi da labarin haihuwar wai abarshi kawai in ya dawo ya gansu, su Tijjani tare da su Yaya Bashir suka isa Gire gidan kanin mahaifin Hakeem sunayen da Yaya Bashir ya yi musu huduba dasu su din aka sanya musu wato Ahmad mahaifin Hakeem da kuma Zainabu Abu mahaifiyarshi, sa6anin yadda da Innarshi ta yi kara ta се asa sunan Yaya Bashir dana Innārmu hidimar suna kam babu abinda zan ce sai Alhamdulillahi, satinmu biyu innarmu tare da Hama suka zo dubani zuwan Inna na farko dakina tunda nake aure na yi ta ina naka saka dasu sumam suka yi ta yi da 'ya'yana har na rokesu sun yarda za su kwana a wurina kawai misalin karfe takwas na dare sai ga 54 mota daga gidan Yaya Bashir an dawo mun da Suhaila da taje wuni gidan kuma wai a tali mishi dasu Inna haka dole na hakura sai dai kam gaskiya na zobara baki na yi ta korafi kan Yaya Bashir baya so ya ji wani ya kwana a gidana, satinmu biyu da kwana uku Dr. Hakeem Lamido ya dawo gida da asuba misalin karfe hudu da kwata sun yi isowar darene, oyoyon da na yi mishi ya yi matukar girgizashi daga baya kuma ya bashi sha'awa ya faranta mishi rai bai lura dani sosai ba don aki sanya fitila mai haske sai da ya rungumeni a jikinshi ya ji fayau nan da nan ya bar rungumar ya kai hannunshi cikin ya shafa, Suhaila ina cikinmu? Na yi murmushi na ce ciki ya fiddo yaran dake cikinshi tcacher mai jegoce nan a tsaye a gabnka ya sureni da gudu ya nufi dakin da dama ya shirya don yaran "Alhamdulillahillazi lamyahid ya lam ya lad wa alm ya kun lahu kufuwan ahad" Ma'ana godiya ta tabbata ga sarkin da bai haihu ba ba a haifeshi ba, kuma agareshi kadai ne bashi da abokin tarayya, irin godiyar data fito daga bakin Hakeem kenan sanda ya ga 'ya'yanshi ya fara daukar macen ya sumbaceta ya yi mata addu'a, ya tofa mata ko ina har a gabanta ya tubeta gaba daya ya kare mata kallo yana fara'a tare da murmushi ya ce wannan dai ni ne Suhaila bari kuma in ga malamin shima ya yi mishi yadda ya yiwa 'yar uwarshi ya tubeshi yana kallonshi dariya ta subuce mishi saboda ya kasa daurewwa ya ce Suhaila wannan ai Inna ce ya ya aka yi haka? Ya juyo yana kallona ya sake cewa "Hamdan kasiran daiyiban mubakarakan fihi" Sannan ya mayar dashi ya kwantar ya zuba musu ido yana kallonsu ya ce to gaya mun sunayen da kika zabar musu da dalilin da ya sa kika yi hakan na ce wannan dai Hakeem ne wannan macen kuwa Suhaila ya-kyalkyale da dariya ya ce ban yarda ba ai sai ace mun yi rashin kunya za mu yi Hakeem da Suhaila amma sai a can gaba ba yanzu da sauri haka ba na ce to kai ka cika ya ce uhh ina jin dai wannan babana ne Ahmad mace kuwa sunnan Innar Jos Aisha in dai da nine na zabi sunayen abidna Inna zan sanya musu kenan na yi murmushi na gaya mishi sunayen da sanya ta Ahmad ce asa da yanda nima na baiwa Yaya Bashair shawarar ya sunan iyayenka da Aisha shi kuma ya ki yarda ya ce a sanya maka murmushin jin dadin duka, ya cc wato Zainab cc anan a kwance na yi ce to ALlah ya yi musu karin farin cikin dana gani a fuskar teacher ya albarka Suhaila n ace amin, muna barin wurin 55 ga 'ya'yanshi da a yanzu haka su biyar ne banda Suhaila don baya ma sata a lissafin

Chapter 6 of 7