Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 7
yanda muka yi zato matan babansu Sa'a dukkansu Hama da sauran matan Alhaji Ali, ita kanta Anti Hama iyaycnta sun zo ga kuma kawayenta data gayyata, gidansu Hakcem kuwa dama tun safe a cike akc nan da nan aka karôesu hannu bibiyu aka saukesu cikin karramawa ni kam can cikin dakin Inna na kule na kwanta ita cc kuwa ta sani n ayi hakan wai amarya bata bari a rinka ganin fuskarta, can Anti llama ta sameni dada mun duka ta yi a cinya tana cewa Allah sai na hadaki da Yayanki in ce mishi kai kana nan kana zullumin likita ya tafi da Suhaila ita kuwa tana can tana cin amarci har tana kiba, tana kara fari, na ce Anti don Allah kar ki mun sharmi 36 wanc kiba zan kara ni da kullum nake cıkın tunanın Yaya Bashir? Ta kyalkyale da dariya ta ce ai fa gashi nan na gani, ita ma Sa'a ta shigo itama tsiyar takc mun me kike ci haka kika canza a kwana bakwai? Na hararcta na ce to me zan ci kuwa wanda ya fi na gidanmu? 'Yan mintoci muna bira tana bani labarin yanda hankalin Yaya Bashir ya tashi da y aga har kwana uku ban dawo ba, na yi tsaki na ce sharrin teacher ne kawai na rantse miki, ta ce to ai ya yi kyau don naga kamar har an samu, na rike baki ina salati ita kuwa ta tashi zata fita tana cewa ke Sa'a ki fito mun bar mutane da aiki, Hama ta shigo suka gaisa da iyayen Hakcem ina can ciki na ji tana cewa ni ina amaryar ne? Suka ce mata ta shigo tana shigowa ta harareni, ho 'ya mai abin kunya, ashe dama shirywa kuka yi da mijinki, na soma yi mata rantse rantse, da dai ta ga da gaske na damu sai ta yi dariya ta ce ke ni fa mijinki ya burgeni ya taimaki kanshi kema ya taimakeki don da Allah kadai ya san lokacin da Bashir zai ce ya shirya, yanzu kuwa ai kin gani ya biyoku da kayanku, na ce yaya aka yi haka Hama? ta ce ato ya yi waya Alhaji yana mitar wai kwanaku hudu baku dawo ba, bayan ya cc biyu za ki yi kuma shi bai gaya mishi har dashi a tafiyar ba, sai daga baya ya ji labari shima ya taho, gida yanzu me ye abin yi? Shi ne Alhaji ya cemishi in dai gaskiya kake so to ka bisu da kayansu in kuwa ka fr so ya dawo maka da ita tayi renon ciki a gidanka shí kenan in ta haihu ka ga sai ka hada garar biyu data aure data haihuwa, na ce kai Hama to ni wai daga an yi aure sai a soma maganar haihuwa ne? Ta bude baki a'a to me ye albarkar auren? Ran nan tunda suka zo har cikin dare wai aikin jere suke yi ban dai sun me suke jerewa ba haka? Amma na ji kus kus wurin'yan uwan teacher suna cewa kai mutanen nan suna aiki a dakin Inna na kwana abina. Washegari wajen sha daya na safe su Hama suka ce su za su koma gida, Innar su Hakeem kuwa ta ce ai sam sai ka ce suna korarsu sai dai su bari sai gobe hakan kuwa aka yi Hakeem ya yi musu alheri mai yawa har da wasika ya bayar a kaiwa Yaya Bashir ban dai san abinda ya rubuta a ciki ba, kaya sosai Yaya Bashir ya yi mun har bai yiwuwa in tsaya kwatantawa bani ba hatta Hakeem da 'yan uwanshi sun yi farin cikin ganin irin gatan da ya yi mun zamanmu a Girc bayan tafiyar iyayena zamane na cin amarci da morewa juna ga tarairaya daga ko ina kowa ji dani da Suhaila yake yi. 37 Hakcem agidansu dan gata ne ga mahaifiyarshi da kakarshi wadanda baka raba bakinsu da ambaton Lamido gaba daya dangin ubanshi ji dashi suke yi, na tambayi Hakeerm menene ma'anar Lamido da yake amsawa bayan ni a sanina sunan babanshine ya yi dariya ya ce Suhaila Lamido sunan shugabancine ni sunan mahaifina Ahmad ni kuma tun ina yaro mutanen garinmu suke kirana Lamido don suna fatan in gaji mahaifina, na ce to kana sha'awar gadon nashi, Hakeem ya dan yi shiru jimawa kadan sai ya ce ba zai yiwu in ce ban son gadon mahaifina ba a ko me ye dana san yana yi amma na fi sha'awar in taimaki mutanen garina ta hanyar sana'ata kuma a yanzu ma babana ne yake sarautar tunda kanin mahaifina ne ai na kai ki kin gaisheshi kin ganshi ko? Na ce e, yayun Hakeem mata da kannenshi wadanda suke gidajen mazajensu kullum baka rabasu da gidan in dai har yana gari kowacce ta zo zaka ji tana cewa wurin Lamido ta zo, mutanen gari kuwa maza da mata kowa ji yake yi kamar ya yi ta ina aka saka dashi, a dan zaman da na yi dashi na fahimci babu abinda Hakeem yake so irin garinsu da mutanen garin bayan asibitin da ya gina wanda komai da ake yi a ckinshi kyauta ne shi mutumne wanda baya gajiya da hidimar jama'a komai dare in aka yi sallama fita yake yi ba tare da ya nuna bacin rai ko gajiya ba, bashi ke sarautar garin ba amma gidanshi ya fi na hakimin cika da jama'a mahaifiyarshi kuwa na lura shigen irin hikimar Hama ne da ita tasa hannu biyu ta rungumeni, ko 'yan uwanshi matane suka zo suka ce Inna mun zo bamu samu Lamido ba in ya zo ki ce mishi kaza da kaza sai ta ce a'a ku je ku samu matarshi ku bar mata wannan sallahun, Inna ai shirru ne sai ka ji ta ce sirrun Lamido kuwa ai na matarshi ne in dai kuna son gaskiya tunda ta zama taku zan iya cewa baiwar Allah nan ta fifitani akan 'ya'yanta yanda Hakeem yake shugaba akan komai haka nima ta shugabantar dani, nima na shiga taya Hakeem tattalin mahaifiyarshi don kuwa shi mai son uwane komai dare in ya dawo bai shiga wurinshi sai ya je jikin windonta ya ce mata Inna 'mi warti' tun ban san me haka yake nufi ba har na gane cewa yake 'Inna na dawo. In kuwa ya tabbatar ta yi barci kafin dawowarshi to baya shigowa gidan da mota don a sashinta yake parking din motocinshi, sai ya bar motar a waje ya taka ya shigo wai kar ya tasheta daga barcinta, tunda na zo gidan Ilakeem bai cin abincin kowa sai nawa, in 38 a kuwa zai yi baki masu aiki ko 'yan matan gidan yake sanyawa wai kar in wahala ni kuwa kullum zan yiwa Ilakcem girki na kan yi ne are da mahaifiyarshi. Suhaila kuwa ta zama 'yar gari ko maganar gida bata yi sai dai ka ji tana cewa 'yan matan gidan tunda dasu tafi har ka sunan babana na Abuja biyu yayan Suhaila da baba Bashir, babana na gidan nan ma sunanshi da yawa teacher, Lamido da kawu su yi ta dariya suna zolayarta tana musu surutu tunda maganane d aita, mun yi sati biyar ran nan a Gire cikin hutun Hakcem na watanni biyu hutun babban ma'aikaci na kwanaki arba'in ban da asabar da Lahadi na wayi gari ina hutun sallah a ranar tun safe ran Hakeem a бace yake wai ya ga ina al'ada menene haka Suhaila ni fa na dauka daga wancan al'adar da kika yi farkon zuwanmu shi kenan, sai kuma badi, na yi kamar ban ji shi ba, ya sake cewa Suhaila ni fa yara da yawa nake son ki haifar mun na ci gaba da abinda nake yi ban kulashi ba, ya biyoni har kicin kunun nono nake dama mishi, abinda ya ce mun sai sha kenan ni kuwa wurin mahaifiyarshi na koyi yanda ake damawa don ka'idane in dai Hakeem yana gida to kullum zai sha kunun nono, ya matso kusa dani., Suhaila ba ki ji ina magana bane, kika ki kulani? Ina gauraya kunun wanda na riga na zuba mishi nono, na ce in na ji ka me zan yi maka Lamido? A ganina duk abin baya hannuna in kuwa ina da wani laifi to gaya mun sai in yi maza in gyara, ya yi dariya ya ce laifinki ba kya tayani addu'a, Suhaila, kokarin da nake yi ina ganin da kina tayani addu'a da mun yi nasara na ce to shi kenan zan fara daga yau, ina kwance gadon Hakeem tausa yake mun har ina jin kamar barci zai daukeni gashi kuma na riga na galaßaita a hannunshi don kusan awa biyu da suka wuce shi ke sarrafani ta yadda ya ga dama cikin zolaya ya ce ni dai ina iyakacin kokarina Suhaila ke ce ina jin ba kya karba na rufe idanuwana da tafin hannuna cikin jin kunya na ce kai teacher ba ka jin kunyar irin wadannan maganganun ya jawoni jikinshi me yc abin kunya? Idan na fadi gaskiya bana kokarin ne? Na yi shiru me ye abin kunya, in na nuna ma matsu ina son ganin dan da zà ki haifar mun? Ina so ne in fara ganin tukwicin kai kawon da na yi ta yi dake a cikin zuciyata, na yi gwagwarmaya Suhaila kina makale a raina, duk inda nasa kafa kina tae dani, ke ce tunanina a duk lokacin al'amura suka mun sauki, duk wata mace da na gani in ba na surantata dake ba 39 bata burgeni balle bar ta bani sha'awa na yi mamakin yanda kika mance dani gaba daya kika kasa tuna komai nawa sai da tuna miki cewar ninc Hakeem Lamido na makale teacher na ce ban taba mancewa da kai ba tcacher kaine abin tunawa na a duk lokacin da wani alheri ya sameni, a ranar da muka ci gasar "MAN COMPETITION" n ayi sha'awar ganinka a wurin, na yi kewar rashinka a wurin liyafar da makaranta ta shirya mana, haka nan a Bengazi kaine ka zamo abin tunawata a duk lokacin da bakin ciki ya Rulleni in ji wani abu ya tokareni in rasa inda zan tsoma rayuwata in ji sanyi wani lokaci in ji kamar in yi ta shur-shure babu hali, babu wadanda zan yi wa wannan shagwabar ina tunaka teacher in yi sha'awar ganinka don in gaya maka maraici ya sameni ga halin dana tsinci kaina in tambaycka ko shi ne abinda ka yi ta kokarin kwatantamun na kasa ganewa, sai da abin ya sameni shiruteacher ya yi yana kallona cikin tausayawa, ya ce to ya ya aka yi kika kasa ganeni? na ce na yi karfin hali na cireka daga cikin zuciyata daga baya saboda nasihar da kakana ya yi ta mun cewar sanyawa zuciya burin abinda aka san samunshi zai yi wuya shi ke karawa dan adam wahalar rayuwa. Gaya mun zamanki a Bengazi Suhaila na kalleshi na yi murmushi na cerayuwa cè da ban son funawa da ita, teacher amma hakan ba zai hanani gaya maka ba tunda kana son ji na soma bashi labarin al'amuran da suka faru dani tun rabuwarmu dashi a wurin gasar cowbell yana kallona yana murmushi na gangaro har rasuwar mahaifina teacher ya tayani kukan da nake yi na gaya mishi yanda kakana MalamAhmad ya tafi dani Bengazi rayuwar dana tsinci kaina a ciki na wayi gari cikin wadanda ake yiwa dukan tsiya a kowane lokaci bayan ada ban taßa sanin yanda dukan yakc ba, zamana da Malam Ahmad yanda muka shaku da juna muka so juna labarin matan su Malam Ahmad, aurar da ni da Baba Hamza ya yi ga Sharif irin dauki ba dadin da aka yi dani kafin a kaina gidanshi artabun da muka rinka yi kafin wani abu ya hadamu yanda na samu ciki sau biyu kawai da mu'amalar mu irin wahalar danatsunduma a cikinta da irin mafarke-mafarken da na yi ta yi da Funke Farayc, haihuwar da na yi rayuwata da yarinyar bayan ita ke debe mun kewa, ta zo itama la rasu, zuwansu Yaya Bashir da mutuwar Malam 40 Ahmad, sakin da Sharifya yi mu da dalilin sakin yanda Baba Hamza ya karbi maganar mutuwar aurena, yanda na ke ta dajin nan ya iso tashar jirgi da namun dajin da na gamu dasu shigana hannun Hajiya 6oyon da ta yi mun bayyanar sirrinta na cewa itama muguwar ce shi ga hannun su Sharif da ta yi da yanda mutumin nan ya zo ba tarc da na sanshi ba ya kubutar dani ya kaini gidanshi ya nemar mun mota zuwa Sudan har kawo mai tasin da ya kawoni gidan Yaya Bashir da yanda muka yi dashi babu abinda ban gayawa teacher ba. Ajiyar zuciya mai karfi teacher ya yi ya cc hakika kin wahala Subaila, amma abin farin cikin shi ne wancan duk sun zama labari a yanzu kina hannun masoyanki ne Hakeem mijinki da Yaya Bashir, Suhaila ina sonki har ban san yanda zan yi in gaya miki ina sonki ba, na kara lankwashewa jikinshi n ace ko dogon tabon da ya ratsa bayana da kake yawan tambayata dalilinshi harna ce maka dashi aka haifeni na boye maka ne kawai sauran tabon dukan Sharif ne saboda gudunshi da nake yi ya zuga mun bulalar rakumanshi me ya sa su Yaya Bashir suka kyale Sharif din nan Suhaila da suka je Bengazi? Na yi murmushi na gaya mishi yanda Sharif da Yaya Ahmad suka kwashe, na ce su Yaya Bashir da Yaya Ashiru ne kawai suka lallaba suka ce a kyalesu kawai shi ya ci darajar auren da aka sagala a tsakaninimu Baba Hamza kuwa shi da zumuncin da ya tozarta na gaya mishi zuwan Baba Hamza da Sharif da yanda suka kasa ganeni har da tsiyar da na yi musu ya yi ta dariya, muni sati bakwai a Gire muka shiga shirye-shiryen komawa Abuja a wannan lokacin ni kaina na san na canza saboda yanda nake jin nauyin jikina, shiri sosai aka yi mana na tafiya, Abuja tamkar ba gida zamu ba, wani likeke rago Hakcem ya bayar ya cc a yiwa Yaya Bashir kilishi dashi mu kai mishi tsaraba mun isa Abuja ranar asabar da yamma washegari ranar Lahadi da sassaſe muka yi shirin cikin kwalliya sosai ni kaina kwalliyar da biyu na yi ta wai in samu in burge Yaya Bashir ya dai yarda da cewar mijin nawa ba karamin kulawa dani yake yi ba, n da Suhaila sai walkiya muke yi shima Пakeem ya yi ado cikin manyan kaya wanda ba kasafai yake sanyasu ba a cikin motar Hakcem Combatable muka isa gidan tun a kofar gida muka sha oyoyo wurin maigadi Anti Hama kuwa da ta gamu ihu ta yi tana cewa yayan Suhaila ga amarc sun dawo daga 'honcy moon' din da suka tafi ran nan ina zaune a gaban 41 Yaya Bashir kamar zai lasheni dadi ya kamashi ganin canjin dana samu lafiya dai ko Suhaila? Abinda yake tambayata kenan in ce mishi lafiya kalau, yaya ya ce to madallah shi da Hakeem I:uwa hira sosai suke yi suka ci abinci tare teacher ya tafi ya barni nan ma Yaya Bashir ya sake kirana kar fa ki boye min komai nine madadin mahaifi a wurinki in kina da matsala rinka gaya mun in mijinki ya yi miki ba daidai ba, ki zo ki gaya mun ina tace mishi to, sai dare Hakeem ya zo Suhaila tana ganinshi da gudu ta dauko mun jakata tana cewa Yıya Bashir baba mun tafi gidanmu, ya bita da kallo s,ai kuma ya juyo gareni ki bar yarinyar nan agida Suhaila kar ki tafi da ita. Kasa yi magana na yi na soma yi mishi kuka, teacher ya shigo yana rike da hannun Suhaila ya zauna gcfe daya cikin nuna alamar girmamawa Yaya Bashiryana mun fadan baya son rashin hankalin da nake so in yi, ina kuka n ace mishi Yaya ni in dai an bani itan yanda ka fada tunda aka haifcta to ka bar mun ita ta zauna inda nakc, kina so ki nuna mun ba ki yarda damaganar da na yi bane? Na ce a'a zan yi bayani teacher ya ce in shiga gida, na tashi na shiga dakin Anti Hama ina kwance a kan gadonta ina kuka tare da tunanin yanda zan ji idan Yaya Bashir ya hanani tafiya da Suhaila sai gata da gudunta Anti wai ki zo mu tafi in ji Kawu da sauri na taso na zo na yi mishi sallama muka tafi, a hanya Hakeem ya ke ban labarin wai da kyar ya bár Suhaila ta dawo saboda wai dawainiyar da ake yi dani din zai yi yawa mun koma hutun jami'a ina ci gaba da karatuna Suhaila ma na ci gaba da kaita makarantar da dama take zuwa kullum ni ke kaita da safe in je kuma in daukota teacher kuma ya daukar mata mai lura da ita agida saboda wani lokaci dukanmu bama nan. Zamanmu gwanin dadi ni da teacher shi mutum ne wanda kullum bai gajiya da hidimar matarshi matsalarmu guda daya ce a kowanc lokaci ya ga ina al'ada to shi kam a bacin rai yake na kasa ganc al'amarin ya ce mu je asibiti mun je an ce dukanmu lafiya an kara mana da wasu magunguna amma shiru in yana magana na kan yi kokarin kwantar mishi da hankali ta hanyar tuna mishí lamarin a hannun Allah yake shi ke bayar wa idan ya so yin haka din in kuwa bai bayar ba sai ayi hakuri daga baya sai na fahimci zargi ya shigo cikin maganar yana ganin kamar ni ke hana kaina daukar ciki don in samu in kammala karatuna kafin in soma haihuwa, tashin hankalin teacher in ina al'ada ya fara 42 ח a a Π さ damuna har na zama ina kokarin 6oyc al'adar tawa in samu in yi in gama bai gane ba don dai a zauna lafiya to ran nan ma ya gane saboda ya neme kasancewa tare dani da safe bani da yanda zan yi in bijire mishi haka kawai babu dalili don haka na gaya mishi gaskiya kawai bana sallah harya tashi ya fita sai kuma ya sake dawowa ba fa za ki ko ina ba yau na ce ai dama babu inda zani ina dai da lacca ne da karfe biyu da rabi, ya ce ba zaki ba, karo na farko dana ji ya ce ba zani daukar lacca ba sai na bukaci snain dalili ya ce haka kawa, na ce s'a to in haka kawai ne babu dalili zani ba zan fasa ba don kuwa ka aureni ne bisa sharadin zan ci gaba da karatun nan da nan ya tunzuro in na aureki bisa sharadin ci gaba da karatunki shi kenan sai ya zama hujjar hana 'ya'yana zuwa duniya? Kina nufin karatunki ya fi haihuwa muhimmanci a wurina? yanzu 'yar da matar Ahmad ta haifar mishi mai sunan Inna bata kai wata biyarba? amma ni-a gidana kullum ana cikin al'ada ko ina ganin kamar wata ya wuce sai kuma an san hikimar da aka yi aka yi jikina ya yi sanyi na ce haba Lamido kana nufin ina yin wani abu don haka kaina katseni ya yi in ba kya yi gaya mun problem din mu Suhaila gaya mun ki ce.ga abinda ya hanamu haihuwa zo ki gaya mun ya kamo hannuna ya samu wuri muka zauna ya shiga maganganu na ce amma ai anan gidan bani da wani sirri da zan rinka shan magungunan hana daukar ciki ba tare da ka gane ba tunda a daki daya muke, a'a kar ki nemi yi mun wayo ina binki ne? Na ce baka bina Hakeem ya ce bana binki za ki iya yin abinda kika ga dama ban sani ba, na ce to babu laifi na gode, na ja bakina na yi shiru, ya yi mita ya yi maganganu ya yi barazanar hana karatu, sai bayan na haihu, ina jinshi cikin zuciyata ina tunanin meye abin yi a gareni? Ina zuwa gaban Yaya Bashir da maganar zai ce abinda ya gudar mun kenan da saurin yin aure gashi tun ban rufa shekaru biyu a gidan mijin ba na soma samun matsala, in kuwa na je Jos ma duk dai ban Isira ba don sai ya ji ina zuane ina kallon teacher yana shirye-shiryen zuwa asibiti gun aikinshi nima ina tunanin abinda zan yi yana fita na dauki waya na bugawa wani ma'aikacin airport wanda teacher yake bulda dashi saboda zirga-zirga cikin sauri a jirgi na ce mishi akwai jirgiņe zuwa Yola ya ce e, karfe daya zai tashi na ce to ayi mun bukin ganin nan zuwa, ya cc to na tashi na shiga shiri na daidaici lokacin lashin Suhaila a makaranta na fita ba tarc da na dauki mota ba shata 43 na dauka na tasi na je na daukcta a makaranta daga can na wuce airport na samu jirgi zuwa Yola daga can na shige Gire ganina kawai kwatsam suka yi ta yi mun tambayoyi kan wai ko lafiya suka ganni haka ba tarc da mijina ba, na ce musu alyuka ne suka yi mishi yawa, na budc wurinmu muka yi zamanmu cikin kwanciyar hankali duk lokacin dateacher ya yi waya wai yana tambayata a ina nake? Kife wayar nakc yi in ki sauraronshi kwana na biyu a Gire ran nan da daddare sai ga tcacher, ban ma san ya iso ba sai da Inna ta aiko a kirani na shiga falonta na sameshi yana zaune cikin nutsuwa da alamar fada lake mishi na yi kamar ban ganshi ba na nemi wuri na tsuguna na cemata gani Inna ta ce mun zauna mana Suhaila ai ni kin burgeni wallahi Allah ya yi miki albarka ashe sabani kuka samu da Lamido kika zo kika zauna anan baki gaya mana komai ba? Ban ce komai ba gyara zama kawai n ayi ina sauraronta teacher ya gyara cikin ajiyar zuciya ya ce Inna ba fa wani abu mai girma bane ta dai ga damar zuwa nan din nene kawai ta ce kai Lamido ja bakinka ka yi mun shiru kai fa baka san tana nan ba ka zo ne kana gaya mun cewar ka nemeta a gidansu da kuma Jos bata nan kai kuma ka kasa gayawa 'yan uwanta cewar baka san inda take ba, shi yasa ka zo ka gaya mun in san yanda za a yi a nemeta, ko ba haka ka ce mun ba, ya sunkuyar da kai kasa ya ce haka ne Inna, ta ce to don kuma ka zo ka samu ta rufa maka asiri sai ka ce ta ga dama ne? In da abinda ta ga dama take yi ai da kararka ta kai gidansu me ke faruwa Suhaila gaya mun kawia kar ki boye mun komai, ni kin burgeni tunda kin nuna mun ke matar rufin asiri ce dama matar kirki a dakinta take yaji ba sai ta je tana tonawa mijinta asiri ba, a wurin 'yan uwanla tana zubar mishi da mutunci na dan yi shiru ta ce gaya mun Suhaila, na dan soma zan gaya mata abinda teacher ke mun duk lokacin da nake al'ada na ji ta soma salati tana tafa hannu na fasa kawai n ayi shiru duk da haka ba karamin fada ta yi mishi ba, sai da ya ji ta natsa sai ya ce to inna ai nima ta yi mun laifi saboda me da zata tafi da Suhaila ta barni ina nemanta ta kuma katse mata karatunta ai ni Yaya Bashir ya baiwa yarinyar tunda in banda na ce mishi ni zai baiwa rikonta ba Suhaila ba da ya karbeta Inna ta ce ke Suhaila daga yau wannan yarinyar ta Lamido ce kar ki sake kaita wani wuri bada izininshi ba, na cc to a dakinmu ran nan kudundune kaina na yi na ki sauraron teacher yana 44 fkarin cire rufata yana cewa haba Suhaila ba Inna ta sasantanmu ba, ce ai ban gaya mata rabin abinda kake mun ba, balle ka ce na gaya te duk laifinka ta ji ta ce in yi hakuri, to ai na gode miki Suhaila na ki yihakuri kin ji, ya sakejawoni jikinshi na sake dunkulewa, na a'a ni tunda in ba zan haihu ba bani da wani amfani a wurinka, sai aika yi ta gaya mun bakar magana to gara abari kawai, cikin sauri ya ce abar me Suhaila? Na ce a bar komai ma ai ba za a yi haka a ina lika ga ana zama haka? Ke dai yi hakuri 'yan matana kin ji? Ya shiga sumbatata. Tun daga nan na samu saukin al'amuran teacher sai dai kullum idonshi a kaina yake in lokacin al'adata ta yi muna nan ai da teacher kaina cikin zuciyata ina da damuwa ganin yadda shiru tun zuwana gidan Lamido ban taba tsallaken wat aba, mutumin da yake matukar son haihuwar kamar ya yi yaya? In tuna zuwana gidan Sharif cikin (saütsayi kawai sai gani da ciki shi kuwa Sharif da ace matarshi ta haihu gara mishi rakuminshi in gaji in ce to lamarin ba nawa bane na Allah ne tilas kuwa a bar mishi kayanshi, ana cikin haka sai gawani wata ya zo ina zuba ido in ga al'ada shiru wata ya zo ya wuce ban yi bø nan da nan kuma na shiga laulayi iri-iri sai đai đuka na yi kokarin shanyewa ban yarda teacher ya sani ba maganar al'ada ma da ya yi mun cewa na yi n ayi bayanan yana Leğos inda ya je ya yi sati guda na matsa mishi kwarai kan ni kam tunda ina cikin hutun zan tafi Gire in je wurinsu Inna da kyar ya hakura ya barni saboda ya ga raina ya 6aci da ya hanani tafiyar ban tafi da Suhaila ba don ya cc in bar mishi ita, a Gire na yi ta rashin lafiya iri iri Inna kam ta gane cikine dani ban kuma 6oye mata ba, bana son Lamido ya sani don ina tsoron kar a zo a nemi cikin a rasa

Chapter 5 of 7