Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 7
ya ya dai Suhaila me ye ya faru na ga kamar kin yi kuka? Na soma gaya mishi wasu hawayen suna zuba, cito wayarshi ya yi ya danna lambobin Yaya Ashiru ya ya jikin Inna abinda ya fara tambaya kenan ya saurari bayanin da ake mishi na dan lokaci sai ya ce to amma ko za a kawota nan National Hospital mu gani in ya so in bamu gano ainihin damuwar ba, in za a tafi da itaň sai a fita ya sake sauraronshi sai n aji ya ce nan da awa daya dai za ku išo kenan? Tо sai kun zo, ya kalleni bari in taresu Suhaila sun kusa isowa, na ce to cikin sauri ya juya ya, ya tafi muna gida muna suararon isowar su shiru, tun tara ya kamata su iso har sha biyu babu su babu dalilinsu n ayi waya wajen sa'a ta ce mun tun asuba suka baro kuma itama ta 27 nemi Yaya Ashiru a waya ta ji layinshi a rufe nace wayyo Sa'a rmck faruwa ne, kowa ya rufc la yi? Muna gida hankalinmu a tashe wajea karfe biyar na yamma sai ga Yaya Ahmad ina ganinshi rungumeshi ina kuka tare da tambayar shi abinda ke faruwaya ce kwantar da hankalinki Suhaila tun taran safe muka iso National Hospital Dr Hakeem da wani likita jarfata sun yi wa Inna aiki kuma ALhamdulillahi ta farfado tana kuma cikin hankalinta yanzu k shirya kawai mu je ku ganta muka dauko kulolin da zuba abinci dauki Suhaila anti Hama ta bar Ahmad wurin mai aikinta muka nuj asibiti Yaya Bashir da Yaya Ashiru suna tsaye kan Inna yayin da teacher yake ta faman gwaje-gwajen Inna tana kwance idonta biy ina shiga Yaya Bashir ya ce mun kama bakinki ki yi shiru in kika yi muna kuka yanzu zansa a koma dake gida likita ya gama ya yi rubuce rubucenshi ya mayar da folder ya sagaleta ya cewa yaya Bashir zani gida yanzu zasu kawo magungunan da za a rinka bata mun gode Dr abinda Yaya Bashir ya ce mishi kenan, yaya Ashiru ya bishi don yi mishi rakiya, Anti Hama ta gaida Inna nima na matsa kusa da ita, ina mata sannu tare da zare ido wai in ga inda aka yankata lokacin aikin ban gani ba na tambayeta ina ak ayi aikin? Sai Yaya Ahmad ya cе mun an yi amfani da na'ura mai kwakwalwane Suhaila aka cire mata ciwon ba tare da an yanka jikinta ba ni kám duk bayanin da Yaya Ahmad ya yi mun ban fahimci komai ba, illa iyaka dai na gode Allah inna ta dawo cikin hayyacinta Yaya Ashiru ya dawo sai n aji wayar dake cikinjakata tana kara na fiddota a hankali na ce hello teacher Hakeem ya ce dadina dake ko kara baki daita wai ba zaki yi mun rakiya ba sai na roka a gaban su Yaya Bashir to ban tafi ba ina jiran ki kina fitowa ki yi kwana ta dama ina jiranki na ce, to a hankali na fito ina zuwa inda ya gaya mun na ganshi a tsaye kayan llikita ya kar6i teacher gashi komai ya saka sai ya kara mishi kwarjininshi wani office ya bude muka shiga girman office din da kyan tsarinshi ba kadan banc a nan ma ya rubuta kalmomin kamar haka, when clambing the lada of succèss behind to those you met on your wey up you may met tem again on your dawn' a kasa sai ya sanya sunanshi cikin bracket, Hakeem Lamido. Ma'ana duk lokacin da kake taka tsanin da ke kai ka sama ga cin nasara yi kokari ka aikata alheri ga mutanen da kake wuccwa a hanya ta yiwu ka sake gamuwa dasu 28 yayin saukowarka kasa, na zauna muna fuskantar juna tarc da tunanin hikima irin ta teacher a ko ina yake bai rabuwa da rubuta kalmomi na yiwa kai nasiha,ya hada hannayenshi wuri daya ya dogaresu kan tebur din dake gabanshi yana kallona cikin murmushi ya ce kiranki na yi ki yi mun rakiya zuwa gida, na zaro ido ina kallonshi na ce haba teacher me ye yasa kake mun irin wadannan maganganun ko kuwa kana nufin, ya yi maza ya katseni yi hakuri Suhaila bana nufin komai gani kawai na yi tunda zan je ne in dawo idan kin rakanin ba laifi bane, na ce to laifine ya ce na taba shi kenan ko? Na ce e, ya ce to dazu muna magana da Ahmad sai ya ce wai daurin aurenshi saura bai fi wata daya ba, na ce ko in turo iyayena ne Suhaila ko zai yarda a hada da namu? Na ce kar ka wahalar da su ga nisa Yaya Bashir ba zai yarda ba, ya ce ina mishi tsayuwar dare ban ni kawai in jarraba na ce kama dai bar wannan maganar sai inna ta samu sauki ya ce to. Kwana biyu kawai Inna ta yi a asibitin National Hospital cikin matsananciyar kula daga wurin likitoci da nurse din saboda ganin tsayuwar teacher akan ta ran da ta cika kwana biyun da yamma teacher ya ce a maida ita gida, shi zai rinka zuwa yana dubata dakin dake fakon kasa wanda dama Yaya Bashir ya shiryashi don saukarta in tażo nan aka sanyata. Kullum da safe teacher zai zo ya dubata inda sabbin magungunan da zata sha ya zo mata dasu in an yi sallar isha'i ma zai dawo ya dubata daga nan mu dan yi hira kafin ya tafi cikin kwanaki kadan shi dai Hama suka zama abokan juna kullum teacher cikin aike yake ina jin Yaya Bashir yana mita da Anti Hama ta gama mishi bayanin aiken teacher ya ce ni-fa hidimar Hakeem din nan ta isheni ga dawainiyarasibiti da magungunan Inna ya ki cewa komai na sa Ashiru ya kai mishi cek ya yi kememe ya ki karba gashi kuma agida ma bai huta ba Hama ta ce to ka taimaka ka bashi wacce yake hidima saboda ita mana kaga ai sai ya huta Yaya Bashir ya daure fuska ya ce a'a Hama ni ba zan yarda a tilasta ni auren Suhaila yanzu ba yarinyar ta riga ta wahala ba zan fauketa in baiwa wani ita yanzu ba, sai na tabbalar ta murmure sosaio ta maida kyan jikinta kamar da, Hama ta kyalkyale da dariya ta ce in dai ba jaririya kake so Suhaila ta zama ba ai iyakar kyan da zata yi kenan suna ta maganarsu ni kam ina kusa da Inna ina bata magani ba mu ce musu komai ba iyayen Hakeem maza da mata 29 sun zo duba Inna mahaiſiyarshi daga garinsu Gire an cc mun wai har da suka zo din, sai dai ni kam ban gansu ba, don ina da lacc a ranar da arzikin ya aiken teacher biyu wurin Yaya Bashir yana rokon daura mana aure a lokacin bakin Yaya Ahmad ga su Hama saſc a gida misalin suma sun matsawa Yaya Bashir ran nan ran wata Lahadi da Yaya karfe goma wasu tsofaffi su hudu ne suka yi sallama da Bashir dukansu babu wanda bai haura shekaru tamanin ba hannu biyu ya karbcsu ya sa aka yi ta shiga musu da nau'o'in abinci iri-iri suka gaisa ya fito ya basu wuri don su gama ya shigo dakinda Inna take ya zauna à kasa cikin sanyin jiki yana cewa Hama. Hama kin ga dattawan da Hakeem ya turo mun yau saboda da Allah Yaya zan yi dasu yanzu? Hama ta yi jugum tana tayashi jimami ya cc zan gaya musu kawai, ya turo ranar Juma'a a daura musu aure washegar asabar shi ne daurin auren Ahmad za a yi biki ayi komai amma tarewar Suhaila gidanshi sai na shirya tukuna kar kuma ya dameni, Hama ta ce e, to in ka yi hakan ai ka mutunta dattijan daya turo din ya tashi ya koma wurinsu Hama tana murna tana cewa ai gara da ya yi mishi haka din Inna kam murmushi kawai ta yi suka shiga lissafin kwana kin da suka saura. Hakeem ya turo jama'a don yuwa Yaya Bashir godiya nan da nan kuma ya shiga aiwater da shirye-shiryen aurenshi cikin sati guda sai gashi bayan gaisuwa, kayan na gani ina so kayansa lalle, kayan aure, duk sun kawo Hama ta ce ni in ce ko ba a gaya musu Suhaila ba budurwa bacc na yi dariya na ce to ai ko ke kin isa ki fallasani Ilama tunda kin gayawa tcacher na haihu an kuma biya Sharif rakuma ta cсе au hakanc amma duk da haka Hama bata ja bakinta ba sai da ta sake yiwa iyaycn Hakecm maganar wai Suhaila fa ba budurwa bacc suka ce e, sun sani amma su dansu saurayi ne don haka bikin saurayi da budurwa za su yi ranar Juma'a aka daura aurena da Hakeem Lamido washegari Yaya Bashir ya nufi Katsina karbar wa Yaya Ahmad nashi auren hidimar biki an sha ta babu abindą za a cc sai Allah ya bayar da zama lafiya, an yi biki an kammala ni kam ina žuane a gidanmu inna gamu da teacher a jami'a 'ya yi mun tayin zuwa gidanshi in ki office dinshi ma na daina zuwa tun daga ranar da ya ritsani a office din bayan ya kulle ya yi ta yamutsa ni sai da ya gaji ya budeni na fila ban sake yarda na shiga ba, shima bai cika zuwa gidanmu ba, mafi 30 yawanci ya kan zo ya gaida Yaya bashir nc idan har yana nan agari, ran nan mun samu hutun jami'a da kwana uku bayan mun kammala jarrabawa hutun kuwa mai tsawo ne don na karshen semester ne mun kammala karatun matakin farko wato 100 level, zamu shiga 200 ranar da safc Hakeem ya żo gidanmu wajen Yaya Bashir ya zo, ya zo ne peman arzikin wai in yiwa kakarshi sumaye da ta zo National Hospital aka duba lafiyarta rakiya zuwa gida Gire don shi ba zai samu tafiya lare da ita ba, Yaya Bashir bai yi musu ba don dama ya riga ya ga tsohuwar tunda har ya kawota wurina ta kwana sai ma yayi mun shirin tsaraba sosai, wai in kaiwa mahaifiyar Hakeem da 'yan uwanshi, ni da Suhaila ne zamu yi rakiyar tun darc muka kammala shirin kayanmu, itama sumayen ta zo gidanmu ranar anan zata kwana, ni da mutanen gidan muka yi ta ina muka saka da ita, Washegari wajen karfe tara direban Yaya Bashir ya kaimu airport muka hau jirgi zuwa Yola, tunkafin Azahar muka isa Gire, gidansu Hakecm Lamido gidansu Lamido wani irn makadeden gidane kana shiga cikinshi zaka gane gidan sarautane sassa-sassa ne gidan sashin mahaifiyarshi wacee suke kira inna Abu daban babbane kwarai ko da mijinta ya dade da rasuwa gidan a cike yake da jama'a yanayinta kawai in ka duba zaka gane 'yar gata ce ba kadan ba masu aikine kewaye da ita bata cas bata as duk gidan füllaci suke yi babba da yaro tun zuwanmu lasa aka bude kofar wata katanga dake rufe aka shiga ana ta gyara, ni kam ina kwance a dakinta tana ji dani kamar zata lasheni wajen biyar na yamma Sumaye ta leko, war Suhaila, na ji ta fadi na dago ido na kalleta ba tare da na san abinda ta fada ba, ta yi mun Hausar su ta fulani wai tsami tsami na biyota muka shiga wannan katangar tana mun bayanin ga sashin mijinki zo ki gani kafin ya iso, ban gane kafin ya ison ba, amma kyan wurin ya dauke hankalina fadin tsakar wurin ya yi kafa dari biyu har da hamsin, manyan gini ne guda biyu flat lat daya a bayan dayan sune kawai ata gaban suaran filin kuwa katange yake cikin waya an kana zuba su jimina, talo-talo agwagin ruwa farare sol sol, ana kiwonsu can tsakiyar wurin nasu an yi musu dan madaidaicin tafki da aka zuba kifayc a ciki ga dogayen bishiyoyi da kannan nasu mangoro, gwaiba da lemo ga koriyar ciyawa an daidaita tsayinta gwanin sha'awa can gefen flat din anan wata rumfacc cikinta an zuba kujerun roba, wurin ya ban sha'awa lat din farko shi ne na 31 Hakeem komai na cikin shir irin na gidanshi na Abuja ne daya lat din kuwa babu komai cikinshi in ji Sumayc shi ne nawa, na yaba kwarai cikin zuciyata da tsarin gidan Hakeem min dawo wurin mahaifiyarshi muna zaune har lokacin jama'a basu daina zuwa gaisheni ba, kowa dai ya zo ina kiyaye kalmomin farko da yake fadi cikin fullancinsu wai "Debbo Lamido Jokkike" sai in ji an ce e, sai kuma a zauna a gaisheni da wacce na iya 'yan mata biyune na fi lura da su a masu zirga-zirgar gidan Mariya da Sadiya kyawawa ne gasu da nutsuwa Şumaye ta kalleni, ta ce 'ya'yanki ne, babbar 'yar Hakeem ita ta haifi Mariya mai binta kuma ta haifi Sadiya amma dukansu anan gidan suka girma, misalin takwas na dare sai kawai na ji an ce wai Hakeem ya iso, abin ya bani mamaki na cewa zuciyata amma bai gaya mana zai zo ba. Dakin mahaifiyarshi ya fara shigowa suka gama maganganunsu cikin fullanci ban jin abinda suke fadi, ya kama hannun Suhaila ya fita da ita, wajen tara da rabi Sadiya ta shigo ta ce mun dada wai in ji kawu in zaku kwanta a kaiku can wurinshi, shi ya shiga gari, ban yi magana ba, Sumaye ta ce to ni kam cikin zuciyata na kasa fahimtar dama teacher ya san zai zo ko kuwa tafiyarshi ce ta sameshi babu shiri? Mahaifiyar Hakeem ce ta bani umarnin tafiya can wurin in kwanta, ra rasa yanda zan yi in yi musu da ita na ce zan jira Suhaila ta yi murmushi ta ce kar ki damu nan gidan yara ne in ma ta dawo bata yarda dasu ba zan sa a kawo miki ita, na ce to Mariya ta rakani zuwa wurin Hakeem na gama komai na shirin kwanciya na kwanta har n ayi barci sosai lokacin da hakeem ya dawo ya zo ya kwanta kusa dashi shima barcin ya shiga yi da asuba muka tashi muka yi sallah, teacher ya kalleni yana murmushi ni kuwa na sha mur sai nace ina Suhaila? ya ce na sayar da ita, na ce kana sayar da mutane ne? Ya ce ato shi ne na gani baki tambaycni komai ba sai inda na bar miki Suhaila, na ce to yi hakuri ya yi murmushi ya ce tana wurin Inna, don Allah Suhaila ki yi hakuri kin san an ce Allah daya gari ban ban mu a al'adarmu amarya idan ta kwana a gida tana yin abinci ta ciyar da mutanen gidan har da makwabta na sani ko baki yi ba, inna zata sa а yi amma zan fi farin ciki in ga an yi dake in san abincinki aka ciyar da mutane ba wasu ne suka yi ba, na ce to ai teacher ni bana zo zama banc na yiwo rakiyanc kuma gobe zan koma, ya ce e, na sani amma 32 dai taimakeni ki yi mun na cc to. Na shirya na fito na gayar da iyayen Hakcem na nuſi inda aka soma aikin na gane aikin gagarumi nc don ganin irin abubuwan dake zube shiga kicin din na yi na duba komai na karbi aikina na tsaya kan girkin don ganin komai ya yi kyau an fita kunyar mutane, ban da naman saniya, raguna har hudu Hakcem yasa aka yanka ga kaji, na sa aka gasa ragunan ba tarc da an yanyankasu ba, ta hanyar sagalcwa, ayi ta juyasu akan wuta a hankali a hankali, naman slaniya aka yi danbun nama, kajin aka soycsu, kayan ciki kuwa na juyeshi cikin miya, shinkafa aka yi ta dafata tukunya tukunya, sai wajen azahar muka kammala na je na gayawa Sumaye na gama ta yi ta sa mun albarka, dama abinda tcacher ya ce mun in yi kenan in na gama in gaya usu kawai su sun san yadda za su yi, na shiga wanka n ayi sallah na shafa mai na fito cikin kwalliya ta burgewa sai daukar ido nake yi, na yi nufin komawa sashin mahaifiyar teacher cikin wurin ya yi yawa, ba zan iya kutsawa wurinsu ba, na hakuri na dawo wurina na zauna, Hakeem ya shigo tare da wasu abokanshi su biyu ya sha kwalliyar manyan kaya farare sol, ya yi kyau ba kadan ba, sai fara'a yake yi ina ganinsu na jawo dan shaтa-sharan gyalena na rufe ido suka zauna suna dariya, a'a amaryar kunyarmu take ji? Dadi ya kama teacher ya ce ato gata nan sun dan yi fullancinsu wanda ban taba sanin teacher yana ji ba sai ko yau sai ya ce mun Suhaila wannan abokina ne Ibrahim tun munaa yara tarc muka taso tare kuma muka yi kakin yaya Bashir ma ya sanshi wannan kuma tare muka taho jiya abokina ne na wurin aiki Tijjani ban amsa ba, ina dai ganinshi ta cikin gyalena, da zasu tafi kudi masu yawa suka ajiye mun wai sun sayi bakin amarya, sai wajen magariba, ran nan na ga Suhaila hidimarta take yi gashi IHakeem ya maimaycta da kayan wasa kuma su Sadiya sai ji da ita suke yi wajen sha daya ran nan Hakeem ya shigo ya kammala sallolinshi da addu'o'inshi ya zo ya kwanta naga kwanciyar tashi ba irin ta jiya bace rikici ya tashia tsakanimu na ce gaskiya ni ba tarewa na yi ba rakiya na yi, Hakceem ya ce shi bai san tarewa ba, daurin aure ya sani, kuma an yi don haka shi dauko matarshi ya yi ba zan sake komawa gidan ba, sai dai in je gaishesu, na soma yi mishi kuka, dana ji ya ſadi haka ya ce kukanki ba zai hanani neman hakkina ba, don na saba ganinki kina yi sai kuma ya 33 shiga rarrashina haba Suhailata ke kin ga ya yi daidai a daura mun aure acc in jira wasu shekaru biyu nan gaba? Kafin a kawo mun ke? A farko na dauka za ki bani hadin kai in ya so idan Yaya Bashir ya ga za a haihu mishia gida ya tattara ki ya kawo mun ke to na ga alamar ke ma ba hadin kan zaki bayar ba, don haka na dauko matata in an kwana biyu sai in je in bashi hakuri shi kenan zance ya kare nana yafe kar a miki komai in shi ne shirin, ni zan yi ba shi kenan ba? Har cikin dare ina kuka da kyar teacher ya iya shawo kaina na yi shiru da asuba mun idar da sallah Hakeem ya fita gayar da iyayenshi na jira ya dawo nima in je in gaishesu yana shigowa sai kawai na ga ya shiga kulle kofa, ya shigo dakin yana tube kayan jikinshi a kidime na tambaycshi teacher me zaka yi? Ya kalleni kawai ya ce koma me zan yi in kika yi hakuri ai zaki gani, ya iso inda nake hannu biyu ya saka ya sureni zuwa wani daki da ban san da shi ba, ke matata ce Suhaila abinda ya fara gaya mun kenan, kafin in ce komai ya shiga sumbatata ya hanani sakat na kasa aiwatar da komai, Hakeem ya mallake komai nawa, kusan awa guda da wasu minto6i Hakeem ne kawai yanda ya ga dama haka yake sarrafani ni kam kasa hakuri na yi kuka nake mishi saboda ji nake tamkar yau ne zan fara Hakeem yana kwance a can gefe magana yake mun a hankali, Haba Suhaila menene na yin kuka haka? Iye yi hakuri don Allah zo kiji ya kara jawoni a jikinshi haba Suhaila ke ma kin san ina sonki bana daukoki don raina Yaya Bashir bane amma na gaji da jiranki Suhaila na gaji taimakeni don Allah ki bani hadin kan da nake bukata a wurinki tsawon lokaci yana rarrashina har barci ya daukeni ji na yi ana mun tausa a hankali a hankali shi ne abinda ya tasheni na bude ido na ga Hakeem tausa yake mun yana ganin na bude ido ya saki murmushi lokacin sallah ya yi Suhaila Azahar ta yi na dafe kirjina cikin kaduewa Azahar Hakeem, ban fa gaida su Inna ba, yau yanzu in na fita me zan ce musu? Ya ce haba Suhaila gidan mijinki ne fa, kowa ya san ke matata ce meye abin jin kunya, a ciki? Na ce ni kam ka mayar dani gida yau ne kuka yi da Yaya Bashir zan koma gashi har azahar ta yi babu alamar tafiya, to ki yi wanka ki yi sallah lokaci ya yi ya fita na idar da sallah kenan Mariya ta shigo Dada wai ki zo in ji Inna Abu na ce to na fito ina tunanin da wane ido zan kalli mutanen nan kila dukansu su ganc mun yi wani abu da teacher shi ne ya sanyani irin wannan dogon 34 barcin daurcwa na yi na shiga ſalon bayan ta amsa sallamar da na yi na shiga falon bayan ta amsa sallamar da na yi Suhaila kin tashi? Barcin gajiya ko? Na kalli tambayar tamkar da biyu na dai daure na dan yi murmushi, Lamido ya zo ya cc wai kuka kike yi kina so a kaiki gida shi ne na ce a kira mun ke mana in rokeki haba Suhaila nan ai gidan mijinki ne kin ga maganar tarewar nan ba fa dole bane a shari'a daurin aure shi ne muhimmi amma tunda kin ce cewa ya yi ki yiwa Inna rakiya na yarda kina da gaskiya ya maida ke ya tsaya kawai tunda an daura aure abashi matarshi amma ina so in rokeki kin ga tun zuwanki abokanshi da 'yan uwanshi suna ta zuwa ganinki to bari ya yi ko sati biyu a gida kin ga hutu ya dauko sai ku tafi ko? Nauyinta kawai na ji na ce to Suhaila na hango cikin motar yara tana tuka abinta na bita da kallo Inna ta ce ina Sadiya ku kawowa matar kawunku abinci ku hado mata da madara ta sake kallona tuntuni na so a tasheki ki ci wani abu kafin ki kwanta Lamido ya ce a barki barcin gajiya kike yi ina cikin cin salad mai wadataccen kwai 'cgg salad' Hakeem ya shigo ta hakurine Inna? Inna Abu ta ce a'a zan roketa ne ta ki amma ai ba ka kyauta ba ya ya zaka ce ta yiwa Inna rakiya sannan ta zo ka nemi hanata, komawa? Ta dai yi mishi fada ta ce to sati biyu ka mayar da ita gidansu, ya ce to Allah ya kaimu. Na dai shawa teacher mur na kwana biyu kafin daga baya nà hakura na watsar saboda ba zan iya ganinshi cikin 6acin rai ba, muka koma zamanmu na cin amarci ina dai tunanin in naje gida kome zan ce wa Yaya Bashir oho, kwanana hudu a Gire ran nan ina sallar La'asar teacher ya shigo ya ce idan na idar ina shirya in rakashi asibiti zaije duba marasa lafiya naidar na shirya na fito ba tare da na san a ina asibitin yake ba, hudu da rabi daidai muka isa asibitin wani makadeden asibiti ne a jikin Saint Pot dinshi an rubuta Lamido Memorial Hospital mun shiga ofice din Hakeem yana mun bayanin asibitin sai ga wani likita ya shigo da folders na marasa lafiyar da Dr. Ilakeem zai duba ya gaishemuya yi mishi bayani teacher ya ce a fara shigo da mutanen daya bayan daya suka yi ta shigowa yana dubasu wasu ya rubuta musu magani wasu yace su sameshi a garki rana kaza sai da ya gama ya kuma zaga dani naga wurin yana mun bayani ya gina asibitin ne don tunawa da babanshi komai da ake yiwa marasa lafiya kuwa kyauta ne in dai ba basu da maganin abin anan ba, sai su 35 H n C Π a S n g rubuta ajc a saya yana wannan aikin ne da ſatan Allah ya kaiwa babanshi ladan cikin Kabarinshi na kalleshi a hankali na cc amin, tcacher kwanan mu bakwai a Girc ran nan da yamma mun hadu a falon mahaifiyar tcacher muna zaunc hirarsu suke yi da fullanci Sumaye ta ce kai kuwa lamido matarka tana zaune sai ka rinka fullanci ba zaka yi Hausa don ta ji ba, ya kalleni da gefen ido ya ce in tana jin haushi sai ki ga ta koya nan da nan amma in ina yin Hausa tana jin dadi ai ba zata koya ba, kin san na san halinta ta yi dariya, ta ce zaka sani dai tukuna yashcnc aka yi auren naku da har ka wani san halinta? Cikin sauri ya ce lah Sumayc ai na dade da sanin Suhaila kin mance yarinyar da na rinka baki labarinta sanda nake koyarwa a Jos me cinyc mun gyada mai gishiri? Tana murmushi ta ce ban mance labarin ba, ya ce to ita ce wannan yana nunani da dan yatsa gaba daya suka yi dariya ni kam murmushi kawai na yi wayar Hakeem ta yi motsi kadan don "No care" ce bata kara sosai ya dauka ya kai kunnenshi kamar zai amsa wayar anan sai kuma muka ga ya yi maza ya tashi ya yi waje sai can an jima ya dawo yana murmushi ya се Inna Yayan Suhaila ya ce a gaisheku Inna ta rike baki ta ce muna amsawa ni 'yasu ya ganku shiru ko? Teacher ya sake wani murmushin ya cc ya ce ne a gaya muku gobe in Allah ya kaimu iyayen Suhaila za su zo ta ce kai madallah nan da nanta shiga àike gidan yayun Hakeem mata da kannc wadanda suke gidan miji a gaya musu gobe iyaycna za su zo makwabta da abokan arziki duk aka bisu teacher ma ya shiga kaiwa da kawowa ni kam bar na yi barci ban san shigowarshi ba. Washegari tun kafin azahar sai ga su Anti hama sun zo da yawa fiyc da

Chapter 4 of 7