Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 7
ki ji ta tashi ba tsufan da nayi kinga kaina babu furfura ko daya, ya cire hularshi yana nuna mun kan nashi nikam murmushi kawai nayi suka fita tare nacewa direba ina kwana da sauri cikin girmamawa ya amsa yana kokarin yi mun magana sai ga Yaya Ahmad ya shigo rungume da kaya bandir din shadda mai yadi goma goma masu asalin kyau kala uku da atamfofin mata kala shida da kudi naira dubu ashirin ya mikawa mai tasi yace gashi in ji Yayanmu yace ayi maka godiya bisa taimakon da kayi mana ko? Ya karba yana murna Yaya Bashir ya shigo ya mika mishi hannu suka Kara sallama zai fita Yaya Bashir yace rakashi mana Suhaila na bishi na yi mishi rakiya har wajen motarshi wai zai mun wani bayani na yi murmushi nace ka gaida matarka na gode na juya cikin gida, da yamma ran nan ni da Yaya Bashair da Hamamata da Yaya Ahmad muka fita a mota daya sayayya yaya Bashir ya yi mun har ban iya fadin irin kayayyakin da ya saya mun da muka gama da kasuwa sai yacewa Yaya Ahmad wanda shike tukin motar ya wuce damu wani asibitin ido nan ma idona aka duba aka bani magunguna akace sati guda zan dawo. Sati biyu Yaya Bashir ya diba yace su zan yi kafin inje Jos ganin Inna. Cikin sati biyun nan kuwa sai gani na mayar da wara-waran Inna a hannuna sun zauna cikin sati biyun nan ba karamin canzawa nayi ba, zan ma iya cewa na dawo kamar asalin yanda nake kafin rasuwar babana, ran nan kwalliyar da na yi zan iya cewa ban taba yin kyau haka ba wara warai da zobunan zinari, sun kama hannayena ga 'yan kunnc da sarka sun kama jikina sai walkiya nake yi atamfar Holland mai ruwan bounbita na faura takalmina da jaka tare da gyalenta irinsu daya gashi sai kamshi nake yi a ſalon kasa na samu Yaya Bashir a tsaye cikin shirin tafiya Ilamamata tana sanya mishi link din rigarshi yaya Ahmad kuwa tuni yana waje shi da dircban Yaya Bashir Hamamata tana magana cikin yanayin shagwaba tunda yayanki yace ba zai je dani ba Suhaila bari in aike ki wurin Inna na yi murmushi nace to Anti llama da sauri ta haura sama sai gata da leda a nade ta miko mun gashi kar ki bude abatashi a haka a kuma ce ina gaisheta Ilama kuwa ki gata mata uwargidancin dana bata fani kafin in gama 9 cin amarcina zan karbe tunda sau biyu ina aike mata bani dalafiya har yanzu bata zo ta dubani ba, na yi murmushi nace to sai mun dawo. A unguwarmu naga abin mamaki yanda unguwar ta canza a shekarun da na yi ban zo cikinta ko gidan da Yaya Ashiru ya dandasa ya isa abin kallo a kofar gidanmu dircban ya tsaya gidan yana nan kamar yadda na sanshi Yaya Ahmad ya nufi gidan Yaya Ashiru don ganin mutane a kofar gidan yasa suka ce yana ciki ni kuwa nabi bayan yaya Bashir zuwa cikin gidanmu Hamace a tsakar gdia ina jin Yaya Bashir yana ce mata yau dai Allah ya taimaki Alhaji Ali na kawo mishi amaryar da zata rinka zama mishi a gida ba kamar ke ba Hama kullum sai kin fito kin zo gidan nan in anyi magana kice 'yarki kika zo dubawa kafin ta mayar mishi da martini sai kawai ta gani wacece wannan kamar Suhaila nayi murmushi nace Suhailace Hama ni da Hama muka rungume juna Hama kam kuka take yi tana cewa Allah sarki Suhaila ashe da rabon zan Kara ganinki a rayuwata a dakin Inna kuwa na sameta zaune kan kujera suna gaisawa da Yaya Bashir yana gaya mata labarin zuwa na ina shiga na durkusa gaban Inna na kwanatr da kaina a cinyarta Inna ta dora hannu a jikina cikin farin ciki tsawon lokaci suna magana da Yaya Bashir yana yi mata bayanin komai da ya sani a kaina wanda da can bai gaya mata ba ya bata labarin rasuwar Malam Ahmad abinda ya yi matukar baiwa Inna tausayi har tazubar da hawaye suna hirarsu ni kama ina shakar kamshin Innata ina tunawa da al'amura iri-iri an dan jima kadan nace bari in je in ga Yaya Ashiru suka ce to. Ina shiga cikin falon gidan Yaya Ashiru da Yaya Ahmad suna tsayc cikin shirin fita Yaya Ashiru yana ganina ya bude baki cikin mamaki rungumeni ya yi cewa Alhamdulillahi yau ga Suhaila ta dawo gidansu kai Ahmad Yaya baka gaya mun tare kuka zo ba? Ina gaisawa da Yaya Ashiruu yana tambayata yaushe nazo ina gaya mishi ina bashi labarin yadda aka yi na dawo sai ga Sa'a tana shigowa rike da tire a bannunta alamar wani abut a shiryo musu tana ganina ta kwallara ihu tare da yin jifa da tiren dake hannunta, Suhaila da karfi ta sake kiran sunanan muka rungume juna cikin farin ciki, kama hannuna ta yi ta jani zuwa wurinta ta wuce falo muka shige can cikin dakinta muka fadi kan gadinta Suhaila ta sake fadi Allah sarki ai yau din nan zan vıwa Yaya Ibrahim waya in gaya mishi kin dawo ai bayan taliyarkı 10 kamar zai yi hauka, ta shiga bani labari iri-iri har labarin aurenta da Yaya Ashiru har tana mun albishir wai cikine da ita wata biyu, hira sosai muka tsunduma kafin waya ta katsemu yaya Ashiru ne ban san me yace mata ba na dai ji tana magana cikin hira da jan hankali tana cewa na sani Yaya ban mance ba sai dai ina yi laifi sai ayi hakuri don Suhaila ce ta sani ban san abinda yace mata na daiga ta yi murmushi ta ajiye wayar ta kama hannuna zo mu shiga kicin din sa'a ta hadu hakanan itama ta iya girki. Kamar in kwantanta girkin nata da na Hama sai kuma naga hakan ba zai yiwu ba don kuwa ita Hamamata girkin mijina kawai take yi sauran mutanen gidan mai girki ke yi musu, yayin da Sa'a take girkin mutane da yawa, na taimaki Sa'a ta kammala nau'o'in abincin da ta shirya inda ta yi abinci hark ala hudu dafa dukan shinkafa mai hade-haden kayaiyakin lambu, sai kuma potato cheese pie, wanda ta yi amfani da dankalin turawa butter, kwai sai fulawa 'yar kadan, datagama wannan sai ta hada 'curried rice, salad inda ta yi amfani da shinkafar kwali madaidaiciyar kaza, jajayen tumatur koren tattasai da jan tatasai albasa, kwai gishiri da curry dan kadan daga karshe sai ta shirya 'fish noodle dish' wanda ta yi da danyen kifi manyan kwanuka ta samu ta zuba abincin a ciki ta shiryasu kan firo tire yaya Ashiru ya turo aka diba daga gidan Inna har bayan La'asar ina wajen Sa'a muna ta hidimarmu Yaya Bashir ya aiko maza inzo mu tafi da gudu na shuri takalmana na koma wajen Inna na samu Hama tan ace mishi anya maigidan bazaka bar mana Suhaila, kwana biyu bay ace a'a zamu tafi ina so in gama mata shiryeshirye ta koma makaranta taci gaba da karatunta, sai ga Sa'a da lullubinta nace lah ban baki izni ba kika fito? Ta harareshi a kofar falon ta-tsuguna ta gayar da Inna ta gayar da Yaya Bashir cikin girmamawa sai tace Yaya da nace ko zaka yi hakuri ka bar mana Suhaila sati daya sai in rakota ta dawo, bai yi musu ba yace to Sa'a ta dan sunkuyar da kanta tace na gode ta tashi ta fita Hama tace uyu wannan da yake surukarka ce ai ka bar mata ita wajen biyar da rabi da shi da Yaya Ahmad suka tafi rannan a gidanmu na kwana a dakin mahaifiyata akan gadonta ina kwance a bayanta muna hira muna baiwa juna labarin al'amuran rayuwa iri-iri da muka gani washegari da safe nima na shiga gidan baban Sa'a na gaishesu na yi musu hira kamar yadda jiya suka zo mun da Azahar naje gidan Alhaji Ali sai dare yaya Ashiru ya zowa IHama 11 bira ya lasoni agaba muka dawo gdia tare rannan a gidanshi na kwana tare da Abba don shima biyoni ya yi wai zai kwana tare dani ziyara, sosai na yi tun daga 'yan uwa abokan arziki, kawaye har makarantarmu naje mafi yawancin malaman dana sani suna nan sunyi murna kwarai da ganina, ganin da na yi Sa'a da iyakacin gaskiyar ta take yi zata mikewa Ibrahim da labarin dawowana yasa na lalla6ata nace ke Sa'a kyale Ibrahim ya yi abinda ya kaishi kin dai san America ban an kusa bane bashi da amfani ki gaya mishi gani bayan yana can wata duniya kuma nib a aure zan yi yanzu ba, ina ganin ki bar shi kawai ai zai dawo ya sameni, tace to shikenan a hirarmu da Hama ne na ji labarin Hamamata cikine da ita har wajen wata biyu amma babu lamar hakan a tattare da ita na kara yarda da kyan halittar Hama na kuma yarda macece mai kamun kai da ņutsuwa sati daya na yi Yaya Ashiru da Sa'a suka maidani Abuja gidan Yaya Bashir shima Yaya Ashirs ba karamar sayayya yayi mun ba har da wayar GSM ya hada mun. Na dawo na samu Yaya Ahmad ya gama mun shirye-shirye shiga Edtra Moral Classes don in yin karatun shirin zana jarrabawar gama karatun sakandire wacce makrantarmu ta amince in je in zana a can, na fara zuwa babu dadewa Yaya Bashir ya yi mun kyautar ban mamaki. inda ya saya mun mota Honda Cibic sabuwa dal mai jan ruwa ya kuma umarci Yaya Ahmad da ya koya mun tuki, zamana gidan Yaya Bashir babu abinda zance mishi shi da matarshi sai shukura kullum a tayashi tattalina take macece da iya zama da mijinta tasan abinda zata yi ta kara karfin soyayyarta wurin mijinta tun zuwana gidan ban taba ganin wani abu da tayi wanda ya sosa mun rai ba, Yaya Bashir ba mutum bane, mai yawan dariya ba sai dai fara'a kawai amma in har Hamamata tana kusa dashi to zaka jishi yana yawan kyakyatar dariya ko me take gaya mishi oho? A wurin Yaya Ahmad ne kawai na ji labarin wai a farkon zuwania ba wani kirkine da ita ba ta fara fito da halaye iri-iri na rashin kirki sa'ar da muka yi kawai shi ne shi Yaya Bashir da wai ba wni sonta yake yi ba, itace ta yi ta zaman jiranshi wai har akwai wani lokaci da aka taba yin waya aka ce mata Inna bata da lafiya amma bata gaya mishi ba, har aka wuni aka kwana, sai da aka sake yi mishi waya yace ba a gaya mishi ba, day a kirata ya tambayeta sai tace mishi wai mancewa ta yi shine yace aka gaya miki uwata bata 12 da lafiya kika mance? To jeki gidanku Inna dawo zan zo, bai je ba har sati biyu suna ta aike da kyar Alhaji Ali yaje ya dawo da ita shine kika ga yanzu komai take yi lafiya, lafiya na yi dariya nace lalle baka gane tsakanin Yaya Bashir da matarshiba, daga yau kar ka sake tunanin ba wani sonta ke yi ba in ka lura da kyau duk lokacin da zai ambaci jiran da Hamamata tayi mishi yana matukar girmama lamarin banda wannan in har tana kusa dashi bai iya rufe bakinshi shi dai irin mutanen nan ne da bai yarda mace duk yanda suka kai da sonta ta wulakana mishi iyaye ko 'yar uwa matukar su din basu ne suka zubar da girmansu a wurinta ba, sannan a ganina Hamamata ko an aureta akan ba a sonta tana da halaye da dabi'u da zasu sa mijinta ya sota ko ba komai yanzun nan ka gama gaya mun tunda ta gane mijinta ba zai lamunci a raina iyayenshi ba tasa hannu biyu ta rungumesu ka gani ta nuna maka ita macece ta kwarai mai biyayya, uhun ke dai kina sonta kawai in ji Yaya Ahmad na yi dariya muka shiga wata hirar. Karatu sosai na shiga yi na addini dana bokon cikin watanni bakwai na zamana gidan Yaya Bashir na zama tamkar ba bakar fata bace ni saboda kyau ga ado da nake zubawa ga motocin da nake hawa bayan Honda cibic din day a saya mun wacce zamana take yi gaa daya motocin gidan babu wacce bana hawa inna yi ra'ayi abokin yaya kuwa tunda a lissafinshi ya gane wai n agama idda kusan kullum sai yazo gidanmu hira hidima kuwa da sayayya iri-iri, rannan ina shirya mishi abinci don ya shaidawa Yaya Bashir cewa daga office yake bai koma gida ba don haka yana bukatar abinci ina aikin ina jin yaya Bashir yana ce mishi gaskiya Engineer ba wai bana son baka Suhaila bane ai kai aminina ne na kuma sanka da kyau to amma abin shi ne tausayin Suhaila nake ji tafi kowa maraicin ubanmu auren nan da suka yi mata yawan rainc kawai ya fiddota a yanzu na fi son ta huta kafin ta sake wani auren na gama shirya abincin na kawo mishi Yaya Bashir ya tashi ya haura sama wurin matarshi wacce bamu dade da dawo daga asibiti ba saboda lalura irin ta maj tsohon ciki muna bira tare da Engineer Muhammad Yakub yana cin abincinshi yace ashe matar Ashiru ta haihu har annyi suna amma da zaki baki gaya mun ba, na yi murmushi nace gani nayi kamar harkar suna ta matane, ya harareni yace e da yake kina son yi mun wayo ba? To me muka samu? Nac sunan babanmu aka sanay mishi, yace a'a to ai sai musa rana ki rakan 13 in gano shi nace ni ko wane lokaci a shirye nake in ka shirya kawai kazo mu tafi yace to shakenan ran nan da asuba muka kai Anti Hama asibiti tana cikin dakin haihuwa ni da Yaya Bashir ne a waje ina kallon kaiwa da kawowar Yaya Bashir ina kallon yadda hankalinshin yake a tashe ya kasa zama sai kallon agogon hannunshi yake yi yana ganin lokaci na tausaya mishi na tuna rayuwar Sharif da matanshi mutumin da don ance mish matarshi ta kwana tana nakuda a daren jiya bai hanashi bin rakumanshi kiwo in ya tali kuwa ba zai juyo don yaga abinda baya ta haifar ba sai lokacin dawowarshi na kullum ya yi gab da za a yi salar walaha wajen karfe tara na safe aka shaida mana cewar Hamamata ta haifi diya mace ni da Yaya Bashir muka shiga Yaya Ahmad kuwa yana yin waya zuwa gida yana fadin haihuwar ban iya fadin kyan yarinyar nan da murna Yaya Bashir, muma dukanmu murna muke yi ban taba ganin yarinyar da nake so irinta ba, 'yan uwa suka yi ta zuwa taya mu murna Inna ma ta zo ganin yarinya rana suna Yaya Bashir ya rada mata suna Suhaila ni kam kidimewa na yi saboda urna na kara sonta bani da aiki in ina gida sai na tattalinta ita kam Hamamata tana wurin mijinta duk da yarta bata fi sati shida ba wurinshi take kwana na tuna Sharif da aurenshi wai in cikin mace yakai wata shida shi kenan bashi ba ita sia ta haihu ta yaye tukuna. • Na rubuta jarrabawata 'sai dai sakamakon bai yi kyau sošai ba credit uku na samu lissafi, physics da Islamic studies abinda na iya samu kenan sauran darussan kuwa duka D1 ne da P Yaya Bashir kam ya gamsu da abinda na samu a cewarshi wai ba karamin kokari na yi ba in aka yi la'akari da dadewar da na yi ban yi karatun ba, gashi kuma dama ba kammalawa na yiba don haka Remedial na Science na smau a jami'ar Abuja nan danan n agama shiri na tsunduma na fara karatu a jami'a. Rayuwata ta zamo wata sabuwa fil, samari ta ko ina bullowa suke yi sai dai ban basu hadin kai saboda kullum Yaya Bashir a cikin yi mun fada yake in har ya ga wani sabon saurayiu ya zo ba fa zan yi miki aure yanzu ba Suhaila bana son ganin mutune suna zuwa wurinki ko shima Engineer da kike gani yana zuwa dòn shi abokinane in yi murmushi in ce mishi to. Ran nan na dawo daga shan ice cream ni da Suhaila a cikin motata Honda cibic da fita kuwa ba karmain kwalliya na yi ban a kuma toshe idona da bakin madubi ina dosowa get din gidan mu na 14 hango Sharif da baba Ilamza suna farwa da maigadi ya barsu su shiga cikin gidan ya hanasu ina isowa maigadi ya bude mun get din nazo daidai wurinsu na zuge glass din motar na kalli Sharifnacc Mallam daga ina? Nan da nan ya zube a kasa yana cewa ranki ya dade taimakeni na biyo sawun matatane wacce ta gudo daga Bengazi na dai gane Sharif bai ganeni ba shima kenan mijina balle kuma baba Hamza dadi ya kamani na kalleshi nace kai kar ka kawo mana halinku na buzaye matarka kake neman anan gidan? Maigadi kira mun 'yan sanda su kamashi Sharif yana jin haka ya zube a kasa yana tuba wai inyi hakuri shi kuwa baba Hamza da bai riga ya karaso ba yana jin an ambaci sunan 'yan sanda ya karta da gudu, ganin zan yi dariya yasa naja motata na shie gida bayan na baiwa maigadi umarnin ya shigo dasu na dauki Suhaila na rungumeta a kirjina da sauri nah aura sama na leka dakin Anti Hama wacce ke fama da laulayin wani cikin na gayamata labarin zuwan su Sharif da abinda na yi musu tana dariya ta tashi ta fita na ske saukowa na smau mai aikin gidan ta kawo musu abinci suna ci na gaishesu na tashi na tafi, sai bayan dawowar Yaya Bashir ya aiko a kirani muu gaisa da su Baba Hamza nace to na sauko, na tarar Baba Hamza yana ce mishi ai tun zuwan mu Suhaila bata leko mu ba ina zama Yaya Bashir ya soma yi mun fada nace mishi ai nazo na gaishesu nice ma naje nacewa Anti Hama'sun zo Baba Hamza ya zuba mun ido ai kece Suhaila kece kika bani tsoro da 'yan sanda kika sani garin gudu har na buge gwiwa? Ya shiga nuna mun gwiwar yana kuka Yaya Bashir kuwa ya tunzura ya yi ta yi mun fada har ya koreni daga falon na yi tafiyata dama na fi son haka. Kwanansu bakwai a gidan kullum nayiwa Sharif hira in muna zaune babu abinda yake yi sai kallona wani lokaci kaga har kamar yawu yana zuba a bakinshi sai in ya daurc ya yi karfin hali sai yace yanzu shikenan ni dake Suhaila? In cc ai watarana zanzo Bengazi, Sharif ko don in ga 'ya'yanka sai kuwa ya yi murna, ya ji dadi, Baba Hamza ya gayawa Yaya Bashir rakuman Sharif da yaci sune suak fi damunshi, yaya Bashir ya biya alkairi Sharif kudin rakumanshi yace ya sayi wadansu, ya kuma yi musu mai yawa. aka nuna Yaya Ashiru da inna ma haka ita kam IHama kuka ta yi ta yi da mata Sharif akace shi ne mijina na da, shi kam Yaya Ahmad yana Kaduna wurin da yake aiki tunda ya zo ya gansu suka gaisa ya 15 tafi bai dawo ba, na samu kanımala karatuna na Remedial da gagarumar nasara na samu wucewa zuwa karatun digiri, inda zan karanta Pharmacy, Anti Hama ta sake haihuwa mun samu da namiji sannan Malam Ahmad ya ci nice kuwa na zabi sunan. Karatunmu na zangon farko ya zo karshe har ma mun fara jarrabawa na fito daga aji ran nan bayan na kammala paper ta cikin sauri na nufi inda na yi parking din motata tarc da tunanin wayar da Engincer Muhammad Yakub ya yi mun cewar a gidanmu zai ci abincin dare ina tunanin abincin da zan shirya mishi sai naji daga baya na an kwala mun kira, Suhaila Imam, na ja na tsaya a raina ina tambayar waye mai yi mun irin wannan kiran? Na juya na hangoshi yana zuwa wani doon mutum sosai yana da maidaicin jiki daya bashi damar zama ingarma fari ne sol gashi da kwarjini, tafiya yake cikin kasaita, bangane shi ba, Kasaitarshi kuma ta bani haushi na juya na ci gaba da tafiyata a zuciyata ina cewa kaji mu mutum don Allah ya tsayar dani kuma zai mun kasaita ko ina ruwana dashi oho. Na ji ya sake kirana Suhaila tsaya mana, nace ai sai ka yi naja tsaki daidai lokacin dana dora hannuna kan murfin motata zan bude in shiga sai kawai naji ya cire hannun nawa a jikin kofar ya mayar da ita ya rufe jarumtakarshi ta ban mamaki da haushi na dago kai cikin tsiwa muka haďa ido gabana ya fadi kwarjininshi ya dan firgitani sai dai ban bari ya gane ba, ban kuma fasa tsiwar da na yi nufin yi mishi ba, nace "Look who are you?" Ya yi wani lallausan murmushi yace "I am no body." Ya sake fadin Suhaila cikin wata irin murya data kadani, na yi karfin hali nacе ba fa sunana kenan ba kuma da ka bani wuri don kar mijina yaga shiru ya biyo bayana ya ganka ya dan motsa kafadarshi cikin gwanintar nuna ko in kula sai yace bana tsoron mijinki zan kuma ci gaba da tsareki anan matukar baki amsa kece Suhaila Imam ba kan iya kaiwa gobe da safe muna tsayc anan ba dai zai zo ya ganmu anan yace nayiwa matarshi fyade ba ko? Wane irin nacaccen mutum ne wannan? Na tambayi kaina a ina ya taba ganina, a ina ya sanni? Tambayoyin da suke zuwa mun zuciyata kenan, na sake dago ído da nufin in kara kallonshi ko zan yi sa'a in tuna inda muka taba gamuwa, idanuwanmu suka sake haduwa gabana ya sake faduwa, na ji ba zan iya ba, ba zan juri kallon da yake mun ba na mayar da bakin madubina dake rike a hannuna na toshe idona dashi don in rage karfin kallon nashi, ya yi 16 murmushi yace gara ki rufe idonki, Suhaila don ki jid adin bijirewa gaskiya, ban taba zaton zaki iya bijircwa sanina ba, ya soma magana cikin sanyin jiki da nadama na dauka saduwata dakc zata zamo abin farin ciki da tuna al'amura da yawa, nayi ta fata tare da addu'ar komai tsufa Allah ya bani ikon sake ganinki, jikina ya yi sanyi jin maganganunshi na rasa me zan yi? Na kasa fahimtar wannan mutum, Suhaila ya sake kiran sunan a hankali naga bani da bain yi illa in sauke jin wani abu in tambayeshi kawai ya tuna mun inda ya sanni, nace ban fa ganeka ba, yace ai ba zaki ganeni ba, saboda kin dade da mancewa dani, kin dade da maye gurbina a zuciyarki, kin dade da mancewa da cewar wata rana zamu sake saduwa, amma ni ban mance dake ba, ban daina fatan sake ganinki ba, ganin dana yi miki jiya shine ya dawo dani yau, ga zatona karshen bakin cikina ne ya zo, ban sani baa she wani sabon babin ne zan sake budewa cikin rawar murya nace wallahi ban ganeka ba, yace rantsuwar kice kawai zata sani in gaya miki ko ni waye? Ya kalleni yana murmushi yace na yi amaki kuma raina ya baасі da har kika iya mancewa da Teachern kin a primary four Hakeem Lamido, habawa tsugunawa na yi a kasa na 6oye fuskata cikin tafin hannuna cikin jin kunya mutumin da kullum nake fatan sake ganinshi in gaya mishi nima na yi maraici naji yanda yaji naga fiyc da abinda ya gani na rasa me zance mishi sai nayi karfin håli nace to ai kaine Teacħer ka canza da yawa, ya yi murmushi yace abin kunya dai kin yi shi ai canzawata bata kai taki ba, kefa tafiya nayi na barki ko kirgen dangi baki gama ba, na sake jin kunyar maganar teacher, tsawon minti biyu babu wanda yace wani abu, sai yace tashi mana Suhaila tashi kar ki yi dalilin da zan tabaki, inna zo dagaki tunda kince kina da aure ko? Nayi kokari na mike tsaye sai dai har lokacin bana iya hada ido dashi saboda jin kunyar tsiwar da na yi mishi, na dan kawar da fuskata nace ka yi hakuri teacher, yace haba Suhaila kar ki samu damuwa yanzu dai tunda magariba ta kusa maigida kuma yana jiranki sai kije gida kar inyi ta tsayar mishi dake ai gobe ma kuan da jarrabawa ko? Na yi hanzarin cewa e, yace to gobe zan dawo da wuri don mu dan gaisa ko? Nace to yaushe kike da paper na gaya mishi da rana, yace to inzo kafin ku fara ko sai bayan kun gama? Nace ka bari sai mun gama, to na gode, sai da safe nace nima na gode kayi hakuri na shiga mota na tafi na barshi anan yana tsayc ran nan gaba dayan daren kasa barci na yi 17 ga karatun jarrabawana na gobe ga tunanin teacher Hakeem a zuciyata canwarshi ta yi matukar ban mamaki komai nashi ya canza kwarmin idonshi ya ciko fatarshi ta zama fara sol maimakon wankan tarwada tsayinsi yayi matukar karuwagashi ya yikiba a haka na kwana gari ya waye, wajen karfe tara na safe na kammala shirina kwalliya sosai nayi ban san dalili ba ina son burge teacher wani yadi material mai ruwan malmo na saka dinki buba, riga da zani da dankwali ya zauna dab a jikina gashiu sai rawa yake yi, yana daukar ido na sanya takalmiuai tsinin diddige tare da jakarshi da gyale iri daya hadin daya dace da kayan 'yan kunne abin wuya wara warai da zobunan hannuna duka na zinarene na fito dakina ina rike da jakata tare da littattafaina a hannu Anti Hama ta fito daga dakinta zata shiga kicin ta kalleni tace kai Suhaila wannan kwalliyar duka ina zuwa? Na yi murmushi nace Anti kin manta ina da paper karfe goma, ta sake kallon tace kina nufin jarrabawa kika yiwa wannan

Chapter 2 of 7