Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 7
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels MATTO DUNITA2Hoj. Halsat C. Sodangi (Mrs Abdullahi Dabai) WAYYO DUNIYA 2 Na HAJIYA HAFSAT C. SODANGI GODIYA Har kullum godiyata ga Allah takc daya bani lafiya da basira na rubuta wannan littafi, tsira da aminci su tabbata ga shugaban manzanni Annabin Rahama SAW TUKWICI Wannan littafin tukwici ne ga masu karanta littattafai da masu zuwa don mu gaisa, nag ode Allah ya bar zumunci, amin.. SADAUKARWА Ga 'yan uwan masu zumunci da hakuri da junansu Allah ya kara dankon zumunci da hakuri baki daya, amin. Nuni hankalin mutanen dake cikin jirgin ya dawo kan Sharif T wanda yake gab da yin kisan kai tarragon da suke ciki ya cika makil da jama'a wani gabjejen katonc yake kokarin banbare hannun Sharif daga wuyan matar nan yana yin nasarar hakan kuwa ta zube a kasa sharaf alamar ya jikkata, shima Sharif din haki yake yi yana numfarfashi na rantse in baki nuna mun inda matat take ba yanzun nan zan karasa ki abinda yake fadi kenan cikin karfın hali da jarumtaka don shima a gajiye yake. Ana cikin hakan ne na ji an bude larragon da nake ciki ta baya na ji an kamo kafafuwana ana jana cikina ya sake bada wani sauyin na kulululu saboda tsoro yana fincikoni daga cikin buhunnan nan ya kama hannuna biyoni kawai abin da ya ce dani kenan ban yi mishi musu ba, ya rinka ketawa da gudu dani da cikin dajin dake bayan tashar jirgin nan kusan minti goma sha biyar muna gudu bamu tsaya ba gab naked a sarewa in fadi kasa saboda gajiya, ban sani ba ko ya gane hakan ne sai na ji y ace ki kara hakuri ki kara dauriya wancan kauyen da kika fara hangowa nake so in kaiki in suka kamamu bamu riga min kai ba to kashinmu ya zai bushe wani sabon karfin ya sake zuwa mun gudu sosai muka yi har muka iso kauyen nan bamu tsaya ba kai tsaye ya shiga dani wani dan gida dake zagaye da kara da su aka yiwa gidan Katanga a jikin katangar kuma bishiyoyin zogala ne gidan a share yak etas rabon da in ga tsabta irin wannan har na manta ga wani shimfideden dutse mai fadi can nesa an yi rumfa a inda yake da alama hutawa suke yi a wurin muna shiga na ji ya soma kwala kira ina Ramatu take? Daga cikin dakinta na ji t ace gani yau lafiya malam ya dawo gida yanzu? Y ace to ki fito mana kya zauna a daki kina tambaya? Ta fito tana gyara daurin zani sannu da zuwa malam tana ganina ta saki murmushi bakuwa muka yin e y acc e, kawo mata ruwa ta shat a je ta dibo min ruwa a randarta mai sanyi ta kasa ta kawo mun ta nemi wuri ta zauna tana sauraron bayanin da mijinta ke mata, ya soma yi mata bayani tun daga lokacin da naje wurinsu neman jirgi mai tafiya sadan, wandani in banda na ji yace sun a tambaya ban san na taba ganinshi ba, da ganina da ya yi lokacin da Hajiya takc sawa ana sanyani cikin tarragon kaya da hirar Sharif da baba Hamza da yaji inda baba Hamza yake cewa ko shakka babu in har suka ganni to suna komawa gida shi zai karya mun kafa daya don kuwa na wahalar dasu, Sharif ya ce a'a dai yi mun 1 dukan tsiya amma kar a karyani shi za a bari da daiwaniya baba Hamza yace sam duka wane iri ne ba a yi mun ba tunda bai san a daina kokarin komawa gida ba to yanzu karyawanc ya kamace don haka day a ga irin kamun kazar kukun da Sharif ya yiwa Hajiya ya kuma tabbatar ko bata kaunar uwarta dolene ta nuna musu inda nake shi yasa taga bai kamata ya bari in sake shiga hannunsu ba don haka in gaya mishi gaskiya meke tsakanina dasu? Na yi mishi bayanin komai tun rasuwar mahaifina zuwana Bengazi da yanda Baba Hamza ya aurar dani ga Sharif mutuwar Malam Ahmad da yanda Sharif ya dauko takardar sakin aurena ya bani babu abinda ban gaya mishi ban a kuma nuna mishi takardar sakin da Sharif ya bani ya karba ya gani ya bani na mayar cikin bujen siket dina. Ramatu ta tashi ta kawo mun kunun tsamiya na karba na kwankwada ya mike tsaye bari in koma Ramatu kar su gane bana wurin su yi zaton ko ni na tafi da ita da ikon Allahzan samar miki mota mai tafıya Sudan yau komai dare dare in Allah ya yarda za ki koma cikin 'yan uwanki nace nag ode Allah ya saka da alheri yace ba komai yarinya ai da na kowa ne ya fita ya barni da matarshi wacce take ji dani ta tausaya mun kwarai nan da nan ta juye mun ruwan zafi naje na yi wanka naji dadin jikina ta turara mana gurasa muka ci muka sha ruwa bayan sallar La'asar sai ga maigidan ya dawo da saurinshi ina yarinyar nan? Ramatu tace gata nan yace to maza fito zo mu tafi ga motar katako na saman miki sai ki shiga ki tafi, nace to muka yi sallama da Ramatu har tana kwalla muka kamo hanya ni da mutumin nan yana gaya mun wai komawarshi ya tarar an sauke duk wani kaya dake cikin jirgin nan wai ana nemana saboda Hajiya tace a cikin buhuna tasa aka 6oycni da basu ganni ba kuma suka ce sam basu yarda ba suka tasata a gaba wai zasu kaita gaban hukuma tashar mota mutumin nan ya wuce dani daidai an gama lodin motar da yake shirin sanyani a ciki ya kira direban wanda yarone matashi yace mishi ga yarinyar nan dana gaya maka don Allah in kunje Sudan ka sanya mu ita a mota mai tafiya Nigeria. Direba yace to ai babu damuwa ya taimakeni nah au gaban motar na zauna muka yi sallama da mutumin nan dircba ya hau mota ya tayar zamu fara tafiya na ciro kullin kudina na kasar Libiya duka na mika mishi ya yi ta murna yana sanya mun albarka mun iso Sudan kusan asuba tashar da nuka tsaya mahadacc 2 sosai ta garuruwan Alirka, muna shiga muka ji &na ccwa in amai tafiya Kano Nigeria, direban motar dana zo wanda ya dan fita zageye ya dawo yana rike da lcda baka da kaza gasasshiya a ciki mai dumi ya miko min yana tambayata karamar mota zaki shiga ko babba? Nace ko wace aka samu. Yace to in kina da isasshen kudin mota zo muje ki shiga wancan Karamar tafiyar zata fi miki dadi, nace mishi to yazo ya sanyani cikin Peugcout station wagen na zauna a ciki bayan na biya kudin motar na kalli direban mai dimbin kirki nayi mishi godiya aka samu ciko muka kamo hanya, gamu nan gamu nan har muka iso Tashar Kuka a Kano anan cikin tashar na dauki shatar tasi, nace mishi Abuja ya gaya mun abinda zan biya ban nemi ragi ba nace muje tare da mika mishi katin yaya Bashir ya kalleni ya kara kallona yace to kudi na fa ko sai munje can maigidan zai biyani nace c, yace to shiga Asokoro ai ba karamin wuri bane ko baki da ko kwabo zan kaiki don nasan ba zamu ace an rasa kudin da za a bani ba muka fara tafiya direban mai dan Karen surutu sabanin wanda ya kawoni Sudan wanda shi aikinshi kawai ya sanya a gaba, wannan son hira ne dashi sai lambayoyi yake yi mun ya yi aka yi kika samu wannan katin? Nayi shiru, waye kika sani a gidan Engineer Bashir Imam? Na sake yin shiru ko kuwa babankine yake aikin gadi a gidanshi? Nace e, ya gyada kai yace na yi muku murna don yazo Nigeria a sa'a tunda har ya samu aiki a wannan unguwar, ya shiga bani labarin Asokoro da irin mutanen dake zaune a cikinta. Ni kam shiru na yi ba uh babu uh uh, amma bai hanashi yin magana ba cikin zuciyata nikam tunani nake yin a kubuta kenan daga hannun baba Hamza da Sharif nan da dan lokaci kankani zan sake saduwa da mahaifiyata da 'yan uwana da abokaina da Adah na saba dasu, na matsu kwarai in sake ganin Innata bayan rabuwarmu ta kusan shekaru uku da rabi bamu sa juna a ido ba to amma na sani gidan yaya Bashir ya kamata in sauka a yanzu shine madadin babanmu shi ya kamata in fara zuwa wurinshi shi ya kamata ya riga kowa sanin Allah ya kubutar dani daga wahalar da ya sameni cikinta shi ya kamata in dankawa takarda sakin aurena da Sharif. Mun iso Asokoro bari in rinka bin gidajen a hankali ina kallon lambar dake rubuce a jkin katangar ba zance ki tayani dubawa ba tunda ke kam nasan baki san komai ba ko yaya kika ce 'yanmata, wannan duka bayanin direban tasin da nake cikine bance mishi komai 3 ba muna cikin haka muka iso jikin wata Katuwar Katanga mai farin fenti bisanta ya kai kafa goma sha uku can saman kuwa an zagayeshi da sikiriti waya tsawonta a mike zata kai kafa dari biyu daga inda muke bana iya hangen cikin gidan ya miko mun katin dana bashi ba tare da ya juyo ya kalleni ba dubi lambobin dake jikin katin nan irin na jikin katangar nan ne, ina ganin naci kudina na kawoki gidan da kike nema sai ki fita ki kwankwasa kofar get din kinsan dai ba zaki turani in kwankwasa get din gidan nan ba don ban iya tsokalar sama da tsinke ban a tsaya na kalli get din gidan cikin zuciyata nace anya nan ne gdian Yaya Bashir din kuwa? Ko kuwa an yi bata kaine aka baiwa gidaje biyu lamba guda daya? Surutun mai tasi ya kutsc mun tunani ya sani fita babu shiri na doshi katangar gidan inda naga get na dan kwankwasa babu bata lokaci naga anzo an bude kofar maigadine wani matashi majiyin karfi yana kallona sama da kasa na yi karfin hali na tambayeshi gidan Engineer Bashir Imam nake nema ya sake yi min wani kallon a lalace kafin yace nan ne lafiya? Wa kike nema? Na hadiye yawun bakina kafin nace mishi matar gidan nake son gani, ya sake kallona bana zaton zata ganki yanzu in dai ba itace tace miki yau kizo ba don jiya ta dawo daga Canada ita da mijinta tun safe kuma bata ga kowa ba, nace gaya mata bakuwace daga Bengazi ya juya ya shiga gidan yana fadin zan dai jene kawai don naji ance maigidan yana zuwa Bengazi amma ku sadakar yalla ai kun riga kunci ganye kuma hikimomine daku iri-iri na rokon jama'a, daga bayana kuma direban tasi ne yake kwala mun kina kina fa 6ata mun lokaci in sun salami baban naki ne ki tambayesu in sun san inda ya koma sai kizo in kaiki ina cikin sauraron maganar mai tasi na hangeta tana tahowa a bayan mai gadin doguwar mace sanbaleliya wankar tarwada mai asalin kyau kana ganinta zaka san lalle Yaya Bashir ya iya zaben mace mai kyau tana isowa ta kalleni sama da kasa tun kafin ince mata komai sai naji tace anya ba Suhaila bace a tsaye a gabana nace nice rike baki tayi cikin mamaki kafin tace komai sai muka hango Yaya Ahmad ya bullo ia daya kusurwar gidan da karfi ta kirashi Ahmad ga Suhaila da gudu ya taho yana isowa ya sureni ya sabani a kafada ya juya da gudu ya nufi cikin gdian Suhaila oyoyo Suhailar inna oyoyo Suhailar Yaya Bashir oyoyo abinda yake ta fadi kenan tamkar wani dan yaro bai ajiyeni a ko'ina ba sai da ya wuce dani ya kaini falon saman gidan 4 tukuna ya ajiyc Suhaila ya sake fadi daidai ya zauna a kasa a gabana, Hamamata ta hauro tana dariya hala baka san ta gaji da gudun mota ba kake wani gudun da ita? Suhaila ta ambaci sunana cikin fara'a walwala da farin ciki lalle yau zan karbi goron albishir wurin yayanki don ni na fara ganan mishi ke nayi murmushi ta sake cewa kai kinsha hanya barka da dawowa gida na dai san kin dawo kenan, nace bakunta ta na zo, tayi dariya tace ina ai yayanki yayi alkawarin koda Sharif kika zo kasar nan ba zaki sake komawa ba nayi murmushi kawai ta juya cikin sauri ta ſita shikam Yaya Ahmad kallona kawai yake yi mutumin da yake na kara figewa a dalilin wahalar dana gamu da ita da kuma faduwar gaba da nasha Hamamata ta dawo dauke da katon faranti cikc da kayan ciye-ciye, iri-iri ta ajiye Ahmad hala baka san Suhaila tana jin yunwa ba, dan bata wuri ta ci abinci mana nace zamu ci tare fara'ar Hamamata da yanda farat daya ta nuna mun kauna tamkar ta dade da sanina nace wai ni yaya aka yi kika ganeni daga ganina? Tayi dariya tace lalle baki san yadda kike ba wurin yayanki ko ina a gidan nan kina nan a samane ko a kasa, ko bayanki can kika duba kece a wurin na juya na kalli inda take muna mun din hotona ne ni kadai ina tsaye, na tuna lokacín dana dauki hoton a wurin liyafar da Ibrahim ya shirya mun ne. Mai gadin gidan ne yake ta sallama yaya Ahmad ya leka falon kasa daga benen Yaya dai Malam iro? Ya tambayeshi bana jin abinda yake fadi sai Yaya Ahmad kaga rashin kara ko? Mun shigo mun bar mai taso din da ya kawo Suhaila a waje ka shigo dashi falon kasa yaci abinci. Yaya Ahmad ya dawo yana yiwa Hamamata magana nikam ina ta cin abubuwan data tara mun wadanda don dadinsu nake jin tamkar bazan taba koshi dasu ba. Yaya Ahmad ya sauka kasa wurin mai tasi Hamamata ta kama hannuna tace zo mujc ki shiga daki, dakin dala kaini ya tsaru muka shiga ciki tace ina ganin wannan ne ya kamata ya zama dakinki, ta wuce ta zuba mun ruwan wanka tare da turaren wanka cikin ruwan daga nan inda nake nikam kamshin nake ta ji ta ſito zata fita tace mun shiga kiyi wankan nace to ina shiga bandakin na ganni cikin mudubiu na matsa kusa dashi ina kara kallon fuskata wacce ta yamutse tamkar ta tsohuwa saboda wahalar duniya na tambayi kaina ko yaushe rabona da kallon mudubi oho? Na kalli tsunmokaran dake jikina na ciro kullun zinarina da kudina da wara5 waran Innata da takardar sakin aurena na hadasu wuri daya kayan ma na saka su wuri daya, na shiga cikin ruwan nan na kwanta tun kain in cuda jikina datti ya mamaye saman ruwan don an zute maganin fidda datti a ciki na fito na zubar da wannan na sake zuba wani ruwan nayi wanka na sake na kara har said a naji fatata tana santsi tukunna nan take najini sakayau don rabon da in yi wanka irin wannan har na manta ita fito na daura tawul din dake ajiye a toilet din na shigo dakin tuni har Hamamata ta ajiye mun dogayen riguna cikin ledojinsu alamar ba a taba sakawa ba har kala shida ga underwears a zube na tsaya gaban mudubi da kyar na iya taje gashina saboda shi kanshi ya manta rabon da yaji kum ya tabashi na zauna nayi shafa na gyara jikina sai kamshi nake yin a zabi wata doguwar riga mai ruwan madara tasha adon duwatsu a gabanta na rufe kaina da gyalenta nzyi matukar yin kyau har na tuna da rayuwata a da kafin in rasa babana, Ha mamata ta sake shigowa rike da kofin madara ta miko mun tana murmushi ai mantawa nayi da na daukeki a hoto yayanki ya ganki kafin kiyi waka nayi murmushi nace yaya Bashir ai ya ganni agidan Sharif kin kuwa san Karewa kenan. Ta zauna ina shan madara muna kara gaisawa ni kuwa bini-bini sai sunsuna jikina nake yi saboda kamshin dake fita daga gareshi ice Suhaila nace kara jaddadawa zuciyata don kar layi tantamar haka din babu ni babu Sharif abinda nake ta gayawa kaina kenan, Baba Hamza kuwa ba zan taba gayawa kowa abubuwan da yayi mun ba yayiwa kanshi da zumunci da ya tozarta, a kofar dakina naji muryar Yaya Ahmad Suhaila ba zaki fito bane ku, dan yi kira da wannan mutumin da ya kawoki? Nace kai rabu dashi na riga na gaji da hirar tashi ba a sallameshi bane? Yaya Almad yace a'a ai gara su gaisa da Yaya Bashir tukuna kafin ya tafi na dai bashi kudin da yace kun yi tsada sai nayi mishi layin ko zai jira maigidan ya dawo su gaisa tukuna? Yace to ni ka ina idar da sallar isha'l na dare makadeden gadon nan na kwanta Ilamamata tana zaune a gefe wai muna hira ai ban san lokacin da barci ya daukeni ba mafarki irin wanda rinkayi ran nan suna da yawa har ban iya bada labarin guda daya kwakkwara, Na farka cikin dare na jini daban gabana ya fadi ina ganin ko dai a cikin barci nake mafarki sai dana tuna ai na dawo gida na shafa filona na jike da yawun barci rabon da a yi barci mai dadin wannan har na manta na kalli agogon dake sagale 6 1 a dakin karfe hudune na dare na daure na tashi na yi alwala nayi sallah raka'a biyu na yiwa Ubangiji godiya da ya dawo dani cikin dangina lafiya. Said a na idar da sallar asuba na sake hawa gadona zan kara danashi sai ga Yaya Bashir shi da Hamamata dukansu sanye da kayan barci sun shigo Hamamata sai lankwasa take mishi tamkar ta marce ina wurin shima hankalinshi yana gareta, na tabbatar sudin suna matukar sonjunansu yana fara'a tare da murmushi na dawo cikin dare Suhaila Hama take ce mun kin dawo gida kuma ita ta riga kowa ganinki hakane? Na yi murmushi nace hakane yaya. Tayi mishi wani irin farin da tasa kunya ta kamani tare da cewa ato ai na gaya maka ta fita, sai gata da kofin madara mai dumi ta miko mun na karba ina sha muna gaisawa da Yaya Bashir yana tambayata yanda aka yi na dawo gida, na bashi labari na ciro takardar sakin auren Sharif na mika mishi na mika mishi zinarina da kudin dana iso dasu na kuma bashi labarin rasuwar Malam Ahmad kusan awa biyu ni da Yaya Bashir ne kawai a dakin muna hira yana tambayata abubuwa ina gaya mishi na dai yi kokari na 6oye mugun halin Baba Hamza don kar in kara bata shi a wurinshi ya bani labarin an yi auren Yaya Ashhiru da Sa'adatu na rike baki cikin mamaki nace yaya aka yi? Yace to babansu Sa'a ne kin sani mutumin nan babu abinda zamu ce mishi ya rike amanar dake tsakaninshi da baba kusan ma dai ince miki shine mutumin da bai juyawa gidanmu baya ba, na dawo kasar nan na samu Inna da Ahmad cikin matsanancin hali Inna da Hama sun zama yau fari gobe tsumma, na dai dawone ma na samu Inna cikin matsanancin rashin lafiya ga Ahmad shi ne ya zama jagora a gida da kasuwa kuma ga karatunshi, sai babansu Sa'a shi ne mai tallafawa zuwana ne al'amuaa suka soma tafiya itama Inna ta dan ji dadi al'amura suka soma gyaruwa sai kuma da aka ganni Suhaila wai lokacin ne tsofaffin abokai suka rinka zuwa dubata to tun zuwana babansu Sa'a ya tuntubeni kan aurenta, naga ba zan iya ba, ba don komai ba sai don zaman jiran da Hama tayi-tayi a kaina wanda ina sane da irin kuncin data shiga a kaina, ana ganin taki sauraron masu zuwa nemanta tana jiran wanda baya nan na kuma taба yin waya da Ashiru muka yiwa juna ta'aziya bayan na samu labarin baba ya rasu da yanda na ji labarin al'amura sai Ashiru yace mun yana da kyau cikinmu wani ya auri Sa'a tunda an yi nufin hadaki da Ibrahim gashi hakan bai yiwu ba don mu kara karfafa zumuncin mu nace mishi 7 e, to sai dai ko shi don nikau ina da Hama, to dawowar Ashiru da na yi mishi tuni kan hakan sai ya yiwa Alhaji Ali magana yaje ya tuntubi babansu Sa'a babu wani bata lokaci aka sanya biki an yi namu babu dadewa suma aka yi nasu nace to Allah ya sanya alheri nima na yi murna da Yaya Ashiru ya auri Sa'a to yanzu yaushe zan je gida kenan? Yace ai nan ne gidanki Suhaila nine ya kamata in zame miki uba sai kin danyi kyan gani zan kaiwa Inna ke ta ganki bana son ta ganki a haka, nama cewa Ahmad kar a gayawa kowa kinanan a bari a ganki kawai yanzu dai an jima zamu fita zuwa zaga gari ko kin gaji? Nace a'a ya tashi ya fita, tashi nayi na shiga wanka na sake bata loaci ina goge jikina na fito ina shafa, na kalli mudubi ina gyara fuskata naga kamar tadan ciko mamaki ya kamani yanda waji daga zuwana gida jiya kawai har na dan canza na tuna tafiyata Bengazi haka na rinka yamutsewa kullum na kalli mudubi sai na gane daga jiya zuwa yau na kara ramewa wanda hakan ya tilasta mun daina kallon mudubi kwatakwata ban kuma sake ba sai jiya, wata doguwar rigar na sake sanyawa mai ruwan malmo na gyara gashina na rufeshi da gyalen nan da nan sai gashi wai har na fara yin kyau na feshe jikina da turare Hamamata ta leko sai sheki take yi ta sha ado. Suhaila yayanki yana son ganinki a falon kasa nace to cikin sauri na sauka falin Kasan dashi da na saman komai nasu iri dayane su Yaya Bashir ne da Yaya Ahmad sai direban tasi tare da wani abokin Yaya guda daya suna karyawa ina shiga falon Yaya Bashir ya miko mun hannu zo nan Suhaila zo kusa dani ki zauna, naje kujerar dake kusa da tashi na zauna abokin nashi ya dakatar da shan tea din da yake yi ya rike kofin a hannu kar dai kanwarka ta Bengazi da kake yawan magana a kanta ne tazo? Cikin sauri yace itace Muhammad ni da nake ta fatan ko da bakunta tazo sai gashi jiya tazo wai har da takardar sakin aurenta a hannu abokin Yaya yace addu'a Bashir ai addu'a in dai kana yenta to Bi izinillahi Allah zai kawo maka saukin al'amari hakane in ji Yaya Bashir ga bawan Allahn da ya taimakeni ya kawo mun ita gidan nan tun daga Kano yaya Bashir yana nuna direba shi kuma yana murmushi jin dadin an yabeshi tamkar kyauta ya kawoni, mun gode kaji in ji Muhammad ya mike zai tafi yacewa Yaya Bashir ni zan koma sai mun hadu in bakuwar ta hut azan dawo mu gaisa sosai don tun wuri zan gaya maka ina ciki kar in zo in yi magana kace na yi sakaci an rigani Yaya Bashir ya dan sha 8 mur yace a'a kar ma ka fara bazan baka ita ba don kuwa ka yi mata tsufa, yayi murmushi yace ai rashin mutuncinka haka zaka hakura dole ka mayar dani surukinka ke Suhaila kar

Chapter 1 of 7