Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 7
agogo na kawo miki tunda kin ki karbar nawa, jiya. Na sa hannu biyu na karba tare da yi mishi godiya, agogon mai dan siririn igiya gwanin sha'awa na juya zan fita ya ce zo ki sanya a hannunki tukunna in gani na ce to na dawo ina sakawa, ya taimakeni ya daure mun ya tambayi lokaci na gaya mishi ya yi murmushi ya ceo ai na dauka baki san agogo ba nima na yi murmushin na tafi bayan ya bani kullin gyada mai gishiri. A jarrabawarmu ta karshe a wannan lokacin ni ce ta biyu abin mamaki sai ga Eze a na uku teacher da kanshi ya yi mamaki, har yana cewa yaya aka yi haka? Dal oa u yi gaba da teachern ta shi kuwa Eze ko a jikinshi murna ma ya i yani. Mun shigo aji biyar na kara zage uantse sosai kan karatuna shi kanshi malam mai Arabic a wannan lokacin ji dani yake yi, teacher Hakeem kuwa bana ajinshi amma kullum a lokacin break sai na leka ajinshi na gaisheshi in kuma karbi gyada in tafi wurin kawayena, muna cikin karatun second term aka zabeni cikin dalibar da zasu wakilci makarantarmu a gasar "Cowbell Competation" da makarantar ke shirin shga a office din headmaster aka turamu aka yi mana bayani tare da bamu wasiku da aka ce mu kaiwa iyayenmu ana sallamarmu da gudu na nufi ajin teacher Hakeem na shiga shi kađai ne tunda lokacin break ne Suhaila kina sanin kina kara girma kuwa? Yaya za ki fado min aji da gudu'haka? Na ja na tsaya sorry teacher sauri nake yi in zo wurinka in riga kowa gaya maka cewar ina cikin masu tafiya Cowbell competation din da za a tafi wani irin lallausar murmushi ya yi ya ce "I'm happy for your luck Suhaila, sai dai tun satin can na sani na yi shirune kawai ban gaya mik ba ina 20 nan a mecting din da hcadmaster yayi da malamai ya ce su bashi sunaycn yara 'yan aji shida masu hazaka ana cikin bayar wa malamarku ta nemi abata damar bayar da dalibarta guda daya bayani mai gamsarwa ta yi kafio headmaster ya amince da daukar daliba daga aji biyarya lumshe idonshi ya bude a hankali ya ce ina Mahari dake zan kums lumshe idonshiya buar da za ku daukowa makerantarku, na ce ka jira teacher ina zaka tafi? Ya dan yi murmushi, ya ce zan tafi karatu Suhaila,abinda ya sa kika ganni ina karantarwa a makarantar nan rasuwar mahaifina ne,ya kawo haka in banda babana ya rasu da yanzu ina shckarata ta hudu a karatuna a jami'a, ya danyi ajiyar zuciya, ya ce baka san tashin hankali ba Suhaila sai ran da ka rasa mahaili sai ki ga kun zama tamkar da kuna cikin wata rumfa maiyawan ni'ima akayayc runfar aka barku cikin zafin rana ga iska ta ko ina ruwa ma in ya zo ya bugeku na kalli teachercikin tausayi na ce ka yi hakuri teacher tunda ma ai gashi ya wucc ya dago ido a hankali ya kalleni ya ce zai wuce dai Suhaila in ina raye. A yanzu dai abubuwa sun soma gyarawa rasuwar mahaifina naga abubuwa da yawa shi yasa kullum bana mancewa da yi mishi addu'a a kowace sallah da na yi ko kin san rasuwar babana ne ya yi sanadin zuwana garin nan? Na kalleshi na ce da a ina kuke? Ya ce Yola har yanzu ma iyayena da 'yan uwana duk suna can na ce kakarka mai soya maka gyada mai gishiri fa? Ya yi murmushi ya ce a Yola take in ta samu mai zuwa ne take bayarwa a kawo min ni kuma sai in rinka ci a hankali don kar ta Kare ba akawo mun wata ba, A yanzu zan tafi jami'ar Nigeria ta NSUKKA iyayena suna Yola ko zamu sake saduwa sai Allah shi kadai ne masanin abinda zai faru a gobe amma kafin mu rabu zan baki shawara ko a wane hali kika samu kanki ki zama jarumar kanki, kar ki rinka yin fata a baki kawai rinka hadawa da jarumtakar a aikace, wani masani mai hikima sai ya ce "Lifes success is provercated more on action than in word." Kin gane? Na ce mishi e teacher sai dai bana son ka tafi ya hada hannayenshi wuri daya ya zuba mun ido cikin murmushi ya ce Suhaila kenan ya zama tilas in tafi karatu don neman ci gaba kinga yanda kike ke kadai mace a gidanku? Haka nakc ni kađai namiji a namu gdian gashi mahaifinmu ya rasu kullum fatana bai wuce in maye musu gurbin ubanmu da muka rasa ba kinga kuwa hakan ba zai yiwu ba 21 sai na tsaya da kafafuna don haka zan tafi oeman ilimi Suhaila don shi ne tushen kowane ırin alhairi a rayuwa. Na ce haka ne teacher sai dai to ina so in rokcka ya ce rokenı Suhaila ni kuwa ko menene zan yi miki, na ce ka jria mu dawo daga competation din mu kafin ka tafi gani nake kamar idan baka nan ba zan iya ba, cikin sauri ya cc no no Suhaila kar ki taba daukar haka kar ki danganta nasararki a rayuwa ga kowa shi yasa na ce miki ki zama jarumar kanki ina so in yi tasiri mai karfi a zuciyarki amma bana so ki dauka ba za ki iya komai ba sai in ina kusa dake, ba haka banc zan jira dawowarku daga gasar agaskiya ma dai jin da na yi kina cikin masu tafiya shine dalilin daga barin aikina a wannan watan, ina so in ga shirshiryenki ni da Halima in da hali ma in tayaki na ce to na gode teacher, yanzu dauki wannan takardar maza ki kawai baba a gida na ce to cikin hanzari na fita daga ajin teacher na nufi gidanmu. Gada-gadan makarantarmu ta shiga shirin tafiyarmu gasar cowbel, duk abinda ya dace ayiwa dalibai masu shirin tafiya gasa an yi mana, ana cikin haka har ranar ta iso. Ranar Talata 6/5 aka fara an kuwa kasa gasar ne rukuni rukuni har guda hudu wato ABCD, 'yan Group A za su kara da group c, group B kuwa za su yi da group D, sunan makarantar mu a group B ya fito saboda haka sai a rana ta biyu muka fara tamu gasar inda muka buga da makarantar Township primary school wacce ita a group D ta fito a haka aka fara gasar wacce aka yi kwanakin talatin cif ana fafatawa daga karshe kuwa mune muka zaına zakaran makarantarmu ce ta karbi kyauta ta farko saboda ita ce ta zo ta daga don haka kuma mune zamu zama wakilan jiharmu a gasar cowbell ta kasa baki daya, wacce za a gudanar a Legos cikin karshen shekara, mun ci gaba da karatu a makaranta ga kuma lesson din da ake yi mana da yamma a makarantar don shirin tafiya gasar kasa baki daya da zamu tafi a Legos ana haka ran nan teacher ya kriani ya shaidamun cewar jibi zai tafi Yola zai gama shiri daga can zai wuce Nssuka ina isa gida na gayawa babana washegari da safe babana ya ban envelop a like mai nauyi ya ce in kai mishi ni kuma lunda ya ce in kai mishi hotona sungumar album dina na yi wanda duk cikinshi babu hoton kowa sia nawa na kai mishi na ce ya zaba na kuma bashi kyautar babana. 22 Tcacher ya gama kallon hotunana ya zabi guda biyu wadanda ya ce sun fi masa kyau game da kyautarbabana kuwa a gabana ya bude kudine masu yawa, a ciki teacher ya yi shiru yana kallon kudin tsawon lokacin kafin ya iya yin magana, Suhaila ban san abinda zan cewa baba ba, sai dai kawai na san shi ne mutum na farko da na yi sha'awar in kusanceshi ya zame mun uba tun bayan rasa mahaifina da na yi in kin je gida ki rokar min shi Suhaila ya sanyani cikn 'ya'yanshi ya rinka yi mana addu'a, tare don ni kam na dade da rasa addu'ar mahaifi, hawaye suka taru a idon techer ni kam tuni na rigashi yin kukan cikin hanzari ya mike ya shiga rarrashina, ina tsaye gindin windon ajinmu lokacin da teacher Hakeem ya gama sallama da ticoci abokan aikinshi ya hau acaba ya tafi. Mun ci gaba da karatu mai tsanani har zuwan karshen shekara inda muka shirya muka nufi Legos an fara gasar cowbell competition ta kasa baki daya ranar Alhamis an sanyamu a group C don haka mu da A muka bude gasar an fafata gasa mai zafi a tsakanin makarantu abinda ya tabbatar wa jama'a da cewar dukkan makarantun dake wurin sun zone da niyyar tafiya da kofin da ake gasar a kanshi duk da haka cikin taimakon Allah mun samu, kawowa rukunin karshe na gasar inda zamu yi takarar kofin mu da jihar Legos ran nan kuwa tun safe teachers, dinmu dake tare damu suka kammala shiryamu ni kam-in ka ganni sai ka dauak gasar gayu na zo teacher mu ta aji biyar ta yi matukar gyarani gashin kaina ya sha adon ribons uniform dina gashi sabo ya kuma ya dauki guga ya tsaya mun kan gwiwa ga farar safa da sandal sabo sai dan siririn agogona wanda, kakata Hama ta kawo mun daga umra tsawon lokaci ana kara yi mana huduba tare da jaddada mana muhimmancin cin kofin kafin muka hallara a dakin gudanar da gasar jihar Legos aka fara baiwa damar su gabata da kansu wanda ya fara fadin sunanshi shine Abdulwaheed Akanbi sai Funke Faraye ita ce a tsakiya sai kuma Bolaji Adelekan sannan aka dawo kanmu Daniel Ison shi ne na farko sai na ce sunana Suhaila Imam daga makarantar Giring Primary School ina wakiltar Pleateau state sai kuma Ali Abbas mun fara gasar inda a zagayen farko muka yi canjaras a zagaye na biyu dana uku ma haka aka sako wasu tambayoyin guda shida muka amsa uku uku abin har ya baiwa mai gabatarwar dariya ya sake kawo wasu jihar Legos ta amsa tata 23 daidai mu kuma aka karanto mana tamu ni da Daniel muka amsa tare ina cewa B yana cewa C Quite Master ya nemi sanin amsar da zai dauka sai kawai lDaniel ya ce C sai Quite Master ya ce sorry C is not correct B is the answer shi kenan gasa ta Kare, jihar Legas ta yi nasara a kanmu ni kam kifa kaina na yi kan tebur dake gabana kuka sosai nake yi har zuwa lokacin da aka soma bayar, da kyaututtukan ban daina kukan da nake yi ba da kyar commissioner ilimi ta jiharmu wacce ita ce ta wakilci Pleateau State a wurin ta iya rarrashina har na iya karbar mana kyautarmu inda muka dauki Karamin kofin. Na fito kenan daga wurin sai ga teacher Hakeem a tsaye ya harde hannayenshi a kirjinshi ai ni kam da gudu na isa wurinshi saura kadan in Kankameshi sai kuma na ja na tsaya lah teacher ashe ka zo? Na fadi cikin murmushi tare da dora hannuna a baki alamar mamaki, congratulation Suhaila abinda ya fara fadi kenan, na rage fara'ar dake fuskata na ce to ai bamu cinye gasar ba teacher gashi ka taso daga Nssuka ka zo ganin gasar ban kuma cinye ba hawaye suka sake cika idona suna shirin su ci gaba da zubowa ya ce No Suhaila stop crying failure isn't failure unless you don't learn from it." Na sa hannu ina share hawaye ya miko nashi hannun yana tayani tare da cewa na taso daga Nsukka don ganin gasarki na ganki kin burgeni "Winning is not everything but making the effort to win is." Ma'ana ciye gasar ba shi ne komai ba amma Kulia aniyar cinyewar shi ne wani abu kin yi komai Suhaila sa'a kawai suka fi mu don haka daina jin haushi kin ji na ce to na sake muka shiga hira da teacher yana bani labarin zuwanshi Yola da Nssuka har yace wai kakarshi mai gyada tana gaisheni na yi dariya na ce a ina ta sanni da zata gaisheni? Ya yi murmushiya ce Allah na gaya mata ni da wata yarinya Suhaila muke cinye gyadarta da take aiko mun na yi idariya na ce su baba ma sun zo ya ce e na gansu a cikin wurin da muka kalli gasarku har mun gaisa da shi da Ahmad da wani Ibrahim ya ce mun shima danshi-ne amma ban ga kun yi kama ba, na ce e dan makwabcinmu ne ya sake cewa banga Bashir ba, na ce la ai yaya Bashir ya tafi Canada watanshi kusan uku kenan ya tafi karatun digiri dinshi na biyu. Very lucky shi kam wallahi I'm happy for him, na ce kaima in sha Allah kana da sa'a teacher, watarana sai labari ya yi sauri ya ce in sha Allahu Suhaila mu je in yiwa Baba 24 sallama zan koma na ce mishi to na rakashi ya yi sallama da babana na sakc biyoshi don in yi mishi rakiya na mika mishi kudin da babana ya cc in bashi ya ce gaskiya ba zan kar6a ba Subaila ai abin ya yi yawa, na zuba mishi ido ina kallonshi na cc haba teacher, babana ya maka alheri ka cc bka so? Ya yi sauri ya ce to lalle kam na yi kuskure in na yi haka ban kyauta ba, yi hakuri Suhaila in kin koma wajenshi ki yi mun godiya ki kara tuna mishi cewar ya sanyani cikin addu'o'in da yake yiwa 'ya'yanshi, na ce ai na gaya mishi ya ce zai yi maka ba zai mantaka ba don kuwa duk abinda zan zama ta fuskar ilimi kaine tushen wannan alherin, teacher ya yi murmushin jin dadi ya kamo hannaycna guda biyu danashi hannaycn ya rike ya ce duk inda kika samu kanki Suhaila na rokcki ki zama mai tsare mutuncinki ki dage kan nemarwa kanki ci gaba don babban kuskuren dan adam a rayuwa shi ne ya hada hannu ya zauna ba tare da yin komai ba, ma'ana "The greatest mistake а person can make is doing nothing." Byc bye Suhaila sai watarana watakila zamu sake saduwa wata kila kuma shi kenan in mun tun ajuna mu yiwa juna fatan alheri ya sake cewa bye bye Suhaila daidai lokacin da ya saki hannayena ya juya ya kama tafiya ba tare da yana waiwaye ba. Cikin sanyi da rawar murya saboda hawayen dake gangarowa a idona na ce bye bye teacher Hakeem Allah ya baka duk abinda kake nema a rayuwarka na alheri na gode maka da taimakonka ne na samu kawowa inda nake tsaye a yau, abinda na fadi kenan bayan tafiyar teacher gani nake tamkar iska zata dauki maganata ta kaita cikin kunnenshi ya ji abinda nake fadi game dashi. Mun dawo gida Pilato jiharmu ta yi murna da kokarinmu ta yiwa makarantarmu kyautarmu kuma dalibai ta bamu schoolarship, na yin karatun shekaru uku a kowacce makarantar secondary sch da muke so matukar dai a cikin jiha take, a makaranta kuwa komawa karatu sosai na yi a aji shida aka zabeni hcad girl, haka nan nima sunana ya shiga cikin kyallen da ake rubuta sunaycn yara da makaranta ba zata manta dasu ba, a haka na kammala karatuna na primary inda na fita ina da shekaru goma sha biyu. ASALIN IYAYENA Ni Suhaila Imam mahaifina Alhaji Mahmud Ahmad wanda 25 suka yi mishi da ake kira Imam saboda lakabin da iyaycnshi wannan sunan a dalilin cin sunan kakanshi da ya yi ba dan Nigeria banc asalinshi mutumin Libiya ne wani gari da ake kira Bengazi ya zo Nigeria ne zuwanshi na farko shi da mahaifinshi Malam Ahmad wanda yake dan kasuwa ne yana fatauci tsakanin Nigeria da Libiya in zaizo ya taho da dardumai in zai koma ya tafi da fatu ya yi abokan hulda sosai tun daga Kano, Bauchi, Plateau babu inda baya kai kayanshi in ya zo ya ci gaba da zuwa da danshi Mahmud har kawo lokacin da shi Mahmud ya kawo karfi ya soma jagorantar ayarin da babanshi yake turowa zuwa Nigeria shi kuwa Malam Ahmad ya zauna gida ya huta, a cikin wannan hali ne soyayya la kullu tsakanin Mahmud da 'yar mai masaukinsu Aisha, al'amari yayi karfi a tsakaninsu inda har Malam Ahmad ya taso daga Bengazi ya zo har Jos don ya nemarwa danshi auren Aisha, Alhaji Ali wanda shi ne mahaifin Aisha ya yi matukar farin ciki don kuwa tuni yake sha'awar halaye, dabi'u da rikon addini irin na Mahmud, inda aka samu matsala kawai shi ne wurin Hama mahaifiyar yarinyar wacce kuma ita ce matarshi ta biyu, ita kam a lokacin da mijinta ya shaida mata shiru ta yi bata ce mishi komai ba, tsawon lokaci yana sauraronta da dai yaga bata da niyyar yin magana sai ya ce mata Hama ke fa nake sauraro kin dai san ba tun yau ba nake baki labarin wannan yaron, nutsuwarshi gashi kuma da riko da addini, na kuma san zai riketa don kuwa yaron mai kokarin neman na kanshi ne. Тa се Malam ba fa bana son Mahmud bane amma nisan kasarsu nake gani yanzu a dauki yarinyar nan a kaita har Bengazi shi kenan ni kuma shi kenan? Ta soma yi mishi kuka shi kuma ya zauna shiru yana kallontá cikin nazarin al'amarin sai ya ce to ai shi ne nake so in ji ta bakinki amma ya ya zan yi da malam Ahmad dubi yanda ya taso daga kasarsu ya zo kan maganar. Ta shiga share hawayenta ta ce bani da yanda zan yi tunda bani da ikon hanaka yin iko da 'yarka in kaga basu itan su tafirda ita a barni ni kadai shi ne daidai shi kenan na amince zan ci gaba da yin hakuri in kuma kara rokon Allah ya kara mun dangana babu komai bata sake cewa komai ba. Bayan sallar Isha'i Alhaji Ali ya sake komawa wurin bakin nashi bayan sun ci abinci sun yi hira sai ya sake sako maganar da ta 26 kawo su ya ce Allah gafarta malam yana mai kallon malam Ahmad shima ya fuskantoshi suka fuskanci juna sosai sai Alhaji Ali ya cc mishi wannan yarinya da Mahmud yake so wacce ya taso ku a kanta na kasa zartar da hukuncin ba ku aurenta ba tare da aminccwar mahaifiyarta ba ba wai ina so in nuna muku mahaifiyarta tata tafi karfina bane ko kuma ita din bata amince daku ba a'a uwarta macece mai biyayya sai dai ina jin tausayinta kwarai ta wahala matuka wajen wabin Yaya Aisha ita ce 'yarta ta shida amma ita ce kadai a raye a yanzu haka wannan dalili yasa nake so in rokeku alfarma ku rokar mun Mahmud ya zabi wata cikin 'ya'yana guda goma sha uku mata maza, shirin a yanzu haka akwai sa'o'in Aisha guda uku duk wacce ya zaba cikinsu na yi alkawarin zan daura musu aure a yi biki a baku ita ku tafi tare ba sai an je an dawo ba, tunda wurin yayi nisa da yawa, ba zan ji shakkar baku ita ba komai nisanku don a dakinsu suna da yawa. Malam Ahmad ya fahimci jawabin Alhaji Ali sai ya yi mishi alkawarin shawartar danshi Mahmud da ya zabi wata abinda ya zamo mai wuya kwarai wurin Mahmud canza Aisha da wata cikin rarrashi Malam Ahmad yake gaya mishi zabi wata mana Imam ai na gansu wadanda Alhajin yake fada sun ma fita farar fata, summa fita kyau tsawo kawai ta fisu, Mahmud ya ce ka gafarceni baba ba kyau nake nema ba wurin Aisha ba farar fata ba ai na baro fararen mata a kasar mu, ita din nake so ina son tane kawai zuciyata ce ta zabar mun ita ba kuma zan iya musanyata da wata ba taimakeni baba ka taimaki rayuwata ka tausayawa maraicin uwata da na yi lokacin kuruciyata ka bar ni in auri Aisha, ta yaya zan taimakeka Imam Malam Ahmad ya tambayeshi, a hankali ya ce mishi in na zauna a kasar su za su bani ita itama Aisha ta gaya mun tana sona zata iya bina ko ina ne, to amma tana tausayin halin da mahaifiyarta zata shiga in ta tafi Bengazi ta barta a nan ta dauki lokaci mai tsawo tana kokarin fahimtar dani yanda mahaifiyarta ta dauki son duniya ta dora akanta. Maganar Mahmud ta zowa Malam Ahmad a bazata nan da nan ya fusata ya rufe dan nashi da fada don me zai ce zai baro Kasarshi iyayenshi, 'yan uwanshi, da arzikinshi ya ce zai dawo wata bakuwar kasa don kawai a bashi mace? Ka yi hakuri baba ka gafarceni in har na bata maka ya tashi ya fita. 27 Cikin kwanaki uku ana mahawara tsakanin da da mahaifi Malımud ya amince da bin mahaifinshi su koma kasarsu amma maganar sakc wani zabin babu cewa ya yi ya hakura dasu dukansu, itama Aisha ta shiga cikin matsanancin hali ganin halin da Mahmud ke ciki na kasa daidaituwar al'amari sai dai babu yandda zata yi duk da dinbin son da take yiwa Mahmud ba zata iya juyawa mahaifiyarta baya ba ta bijire ta bisu kasarsu ta barta ita kadai don haka sai ta koma addu'a har Malam Ahmad ya soma shirye-shiryen ya tasa danshi a gaba ya koma dashi kasarsu yaya aka yi yaya aka yi sai kuma ya hakura ya shaidawa Alhaji Ali cewar yaya kake gani in har Mahmud zai zauna a kasarku zaku bashi 'yarku? Alhaji Ali ya yi farin ciki ya cc sai in sanya a daurin aure tare da biki ku shaida daurin auren kafin ku tafi kasarku, haka kuma aka yi Hama ta mallakawa Mahmud gidanta da ake haya kyauta tace ta bashi har abada ya zauna a ciki shi da matarshi maimakon ya je yana neman wurin zama aka yi biki aka gama Malam Ahmad ya koma kasarsu shi kuwa Mahmud aka barshi da amaryarshi suna zaune cikin farin ciki girmamawa da kwanciyar hankali Hama kuwa tasa hannu hiyu ta rungumi Mahmud ta maidashi shi ne dan nata ta jashi a jiki, har ya saki jiki sosai da ita ya riketa tamkar mahaifiyarshi komai yake ciki wurinta yake neman shawara in kuwa ta san yana cikin wani hali to bata hutawa sai ta ga ya fita daga ciki bisa wannan dalili sai kauna da soyayya ta kara karfi tsakanin Mahmud da matarshi cikin shekara guda na zamansu ya mallaki jari mai karfi don haka sai ya tsunduma cikin harkar goro ya mallaki shago a kasuwa duk shekara kuwa in watan babbar sallah ya zo sai ya ziyarci mahaifinshi a Bengazi. Shekaru biyar da yin aurensu Mahmud ya kammala ginin gidanshi wanda a lokacin mutanen gari suka yi ta bayar da labari a kanshi da ya shirya tarewa a gidanshi sai ya debi takardun gidan Hama ya tasa matarshi a gaba suka je mata hira kamar yanda suka saba sai da za su tafi ya kawosu ya bata ya yi, mata godiya Hama kuwa ta tubure ta ki yarda ta ce ita kam ta riga ta bashi ma take dashi in banda shi da matarshi? Ganin da Hama ta yi Mahmud yaki karba ya sa ta ce to in baya so ya mallakawa matarshi haka kuwa ya yi ya tare a sabon gidanshi shi da matarshi da 'ya'yanshi guda uku Bashir, Ashiru da Ahmad bayan su kuma a sabon gida aka haifi 28 Aliyu, Jabir sai Hamza sai dai su ukun basu rayu ba. Gidanmu yana makwabtaka da gidan Alhaji Isma'ila wanda muke kira babansu Sa'a yana da matanshi na aure guda biyu Ramlatu da Hafsatu wadanda suke matukar zaman lafiya tamkar 'yan tagwaye, Ramlatu uwar gida tana da 'ya'ya tara ita kuwa Hafsatu tana da bakwai cikin 'ya'yanta akwai Ibrahim da Sa'adatu babana da babansu Sa'a sun yi zama na amana zama na 'yan uwantakar Musulunci zama na kauna da ganin girman juna gidanmu da gidansu Sa'a tamkar 'yan uwan junane a sanina babansu Sa'a ya tafi Bengazi tare da babana a lokuta dabam-dabam Babana mutum ne mai alheri gashi da wadata iyali mutune sun yi mishi shaidar cewar shi kam har Allah Allah yake yi ya ga mabukaci ya zo neman taimako wurinshi sabanin wasu masu halin da sai ka zo gabansu ka gama tona ashirin cikinka ka gaya musu halin da kake ciki sai sa shi yi maka rantsuwar karya suna gaya maka damuwarsu wacce ta dame taka ta shanye ni dai 'yar gata ce ta karshe kuma shagwababбiya ce ta kin karawa duk da tsayuwar babana kan hana shagwabanin da yake yi misali idan ya dawo gida ya tarar Inna tana yi min wani abu na shagwabawa baya gajiya da yi mata fada, wata rana ya dawo gida ya tarar Inna tana bani abinci a baki tana kirga munin loma a lokacin nan kuwa ina aji uku ne na primary school yana ganin haka ya bata fuska ya sanya hannu a aljihu ya ciro kudi ya bani ya ce maza sayo ice cream ki zo na karbi kudi na fita jikina a sanyaye don na san fada zai yiwa Inna shi yasa ya koreni ina shiga zauren gidanmu sai n aji ya fara cewa wai ni me Aisha take nufi dani ne sau nawa nake gaya miki ki bar mun yarinyar nan ta girma ashe ban ce ki daina bata abinci a baki kina kirga mata loma ba? Da gudu na juyo na shigo gidan tuni har Inna ta fara kuka tana ganina ta yi maza ta share hawayen ta kamar babu komai ta shiga kawar da kwanuka shima baba maza ya yi ya maiyace ya bar fadan na mika mishi kudinshi na ce bana son ice cream din. Tsayuwar dakan babana bai hanani zama shagwababbiya ba saboda in ya hana a shagwabani a gida to gidan Alhaji Ali fa? Da wayona na san Hama tana goyani har sai da na daina jin dadin goyon na ki don kaina ta dorani a cinya kuwa wannan bai zame mata matsala ba kullum sai na je gidanta inna taso daga makaranta 29 kullum kuwa ka'idane zan samu ta ajiye mun wani abu mai dadi in kuwa kawayena suka bini to ina shiga zan fara raba musu abinda na tarar a dakin

Chapter 3 of 7