Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 7
shiga cikin damwua a dalilina balle har na bijirewa bukatarsa to a karshe dai na yi biyayya ga mahaifana na fitar da Suhaila diyar wani kwara da muka hadu da ita a can Kasar labanon (mahaifarta kenan) shekarun baya. Wayewar gari bayan an daura aurenmu kwatsam sai wayar gari na yi Abbana ya na me dankamin takardun izanin daukar ma'aikaci (Admission letter) a can kasar Japan tare da bisa da passport dina dana Amarya ta suhaila ban sani ba ban kuma sani ba ba kuma shiri nab a ne. Na tabbata lokacin da sakonnan ya isa gare ki tini mun dage ko kuma ma mun isa kasar Japan. Kar ki damu kar ki taba sa damuwa a zuciyarki a duk ranar da Allah ya dawo da ni zamu ci gaba da kasancewa kanmatsayin da muke kai a karshe ina me dada jaddada kaunata a gare ki ki riken amanita kar ki ha'ince ni har zuwa lokacin da zan dawo mu ci gaba da rayuwar mu yanda ya kamata. Naki har kullum. Mas'ud Khalil. La'ilaha illah anta subahanaka inni kuntu minazzalimin: babu wanda ya cuce ni face ni kaina da na bi son zuciyata ni Hanifa na shiga uku na banu na lalace na riga nna gama daidaita kaina abin data fara tuhumar kanta da shi kenan. Suma ta yi ko ko mutuwar tsaye ce ita dai ba ta sani ba ta dai ji daukewar numfashinta ne na wucin gadi har dai daga bisani numfshinta ya daidaita sai dai tai fa tan ta mike a haka 56 daga da irin wannan rayuwar a hannu daya kuma tana me nazari tare da tuhumar tsohon masoyinta da lefin yaudara, butulci, cin amana kai ba ta ma san da wane irin suna za ta kira tsohon masoyinta Mas'ud ba! Ya cuce ta ya yau da rayuwar ta ya riga ya gama nakasta mata rayuwa. Ba ta dada shiga cikin tashin hankali baba ta kuma dada fuskantar ba a cikin karamar masifar ya je fata ba, sai lokacin da lafiyarta ta kasa inganta wasu irin kurarraji suka feso mata a gabanta ga amsifar kaikayi da wai irin ruwa me masifar wan da wajen ke fitarwa tin tana nuku-nuku har ya zamanto ta fara zarya a asibiti ama babu wani sauki ciwo sai gaba yake. Ta dade akan layin har zuwa lokacin da layin ya zo kanta mace ce doguwa me kyan diri tana sanye da farin gilashi me kara karfin gani (Medical glass) a shekaru za su kusan rubanya nata akwai wani dan karamin katako me kunshe da cikakken sunanta wato Dr. Sa'adat Bello a gaban teburin ta tarbe ta da fara'a 'yan mata meke tafe da ke ne? tai hamdala gami da ajiyar zuciya domin a tsawon lokacin da tai tana ziyartar asibitin bata taba dacen samun mace ba, ta yiwa likitan gamsasshen tai shiru tana dogon nazari sa'ar da ta gama jin abin dake akwai. Ko za ki karamin haske na daga sauyin yanayin da kika sami kankai ciki tin bayan fara wannan larurar, abin nufi akwai was alamomi da kika lura da su a gareki. Da sauri ta ce kwarai likita domin wanna abu kam na damunta ta dai rasa me share mata hawaye ne ta ci gaba da cewa Ina yawan yin fitsari akai-akaiwanilokacin ma me zafingaske wajen fitar fitsarin sanan wani ruwa me kauri na fitowa daga al'aurata ga yawan kai kaikayi da gabana ke min ga yawan ciwonmara da baya. 57 Likita ta girgiza kai gami da'yan rubuce-rubuce daga bi sani ta yi mata wasu gwaje-gwaje har zuwa lokacin da ta tabbatar da abin datake zato 'yan mata kina ji ko? Hanifa ta tattara hankalinta, kwarai ina ji likita, yauwa to kin gane ko a dan binciken da nai miki da kuma amsoshin da na ji daga gare kin a gano matsalar da ke addabar ki wanna matsalar ba wata ba ce face ciwon SANYIkasancewar alamomin da ke nuni da kamuwa da wannan cuta a kwai su a gae ki kamar yanda kika she da min ta dafe kirji cikin saauri ciwon sanyi likita? Na shiga uku ni Hanifa na banu na lalace. Relax 'yan mata kar ki damu da yawa mutukar za ki bi sharudan d azan gindaya miki cikin yardar ubangiji za kir abu da wannanlarura, ta ci gaba da cewa da farko dai taimakon daya kamata a bawa me wannan ciwo shi ne: na farko maganin yaki da kwayoyin cutar maganin hana fitsari mai zafi, maganin hana ki kaikayi, yin amfani da magungunan kashe kwayar cutar (Dettol). To sai abu na gaba shi ne magungunan da mai cutar ya kamata ya sha:, na farko maganinkashe kwayar cutar maganin kare lafiya da kuzarin jiki, maganin kariya. So duk na yi nazari na rurrubuta miki magunguna da ya kamata ki yi amfani da su kusan duk baya sati biyu sai a je ganin likita da alama magungunan basa karbarta dalilin kenan da ya sa doctor saa'dat ke rubtua mata nau'oin wasu magunguna masu kyau da dan karan tsada sai dai kuma lafiyar nan dai dake nema taki samuwa a kullu yaumin jiya tafi yau wannan abu kam na bawa Likita Sa'a mamaki duk wasu ingantattun magunguna masu yaki da wannan cutar ta bata amma ba nasara. Lamarin ubangiji kena ya kan kyale ka ka yi abin daka ga dama illa iyaka ka jirayı sakamako mutukar ba tuba ka yi ba. 58 Dr. Sa'adat ta girgiza kanta gami da tuhumar patient dinta anya ko Hanifa kina amfani da magungunan nan yanda ya kamata ta girgiza kai gaskiya ban jin haka ykamata ki sani ba karamar larura kike tare da ita ba ki tsaya ki nutsu ki mai da hankali kar ki yiwa rayuwar ki ganganci domin akwai illolin da ke tatare da wanna cuta a jikin dan adam ka dan daga cikin sun e:- Tana hana haihuwa (mata da maza), tana kashe kwayoyin haihuwa ga mata, tana kasha manin da namıj, mafi muni daga cikin illolinta shi ne tana iya zama HIV (Kwayar cutar da take kawo kanjamau). Ina me baki shawara ki nutsu ki mai da hankali wajen yaki da wannan cutar, Duk da cewa ana daukan tsawon lokaci kafin a rabu da ita amına idan aka maid a hankali ana amfani da magunguna na kawar da kwayar cutar, cikin yardar ubangiji za a rau da ita, to duk dai da cewa akwai hanyoyin da ake kamuwa da wannan cutar alal misali:- Yin amfani da makewayi mara tsafta barkatai, shaker iskar numfashi, sai uwa uba ta hanyar jima'i ta dan girgiza kai cike da alamun damuwa 'yanmata ki yi hakuri hakika kin kamu dawannan cutar ne ta wannan hanya ta karshe wato ta hanyar jima'l kuna a gaskiya cutar ta miki babban kamu domin ta jima a jikinki ba tare da an dau kwakkwaran mataki ba. Hanifa tai shiru tai zugum lana tinani lallai hakika ba karamar masifa Mas'ud ya jefa ta ba ya cuce ta va gama da rayuwarta ya gudu ya bar ta da cuta me wuyar sha'ani kaicona ni Hanifa ta fada gami da share hawaye. Lamarin duniya akwai bantsoro duk inda dan adam ya kai ga zatonsa be haka nantake ba a halin yanzu ko kudin da za tai jinayar larurar da son zuciya ya haifar mata bata da shi 59 kai rayuwar ta mata kasance gwanin ban tausayi kusan komai na ta ya kare ba da ta shi bata kuma da me ba ta duniya tia mata ba dadi domin ta riga ta gama juya mata baya duniya me juyi kenan kusan ba ta da kowa a halin yanzu, 'yan uwan mahaifinta sun yi fushi da ita fushi me tsanani tin bayan 6acewar mahaifiyarta da 'yanuwanta wanda a fili take cewa bakin cikinta ne ya bazama su shiga duniya bakin cikin ta ne dai yai ajaliyar mahafinta kazalika dan uwansu wannan dalili yasa suka kaurace mata suka yi fushi da ita babu me shiga huruminta kai ita da mutumin da bashi da dangi duk daya suke domin hatta da al'ummar unguwa sun kyamace ta sun kaurace mata babu wata dangantaka a tsakaninsu. Kimaniu shekara hudu kenan tana cikin wannan larura ta rame ta kekashe ta fita hayyacinta, gaba daya ta fita kamanninta saboda wahalar ciwo da zulumin rayuwa abin dakan danganta ta da ciwon nan me karya garkuwar jikin danadam (Aids) tana ji tana gani akai mata kazafi aka lakana nata wannan mummunar cuta to waye ba zai yarda ba ta dauke da cutar? Bayan a baya tabi duk wata anyar da za a iya kamuwa da cutar ba? Abin datake tuhumar kanta da shi kenan kusan to dai komai da take da shi ya kare dangin mahaifinta sun fita sabgar ta sun kasa tallafa mata babu ruwan su da sha'aninta al'ummar unguwa sun yi shakulatin bangaro da lamarinta babu me agaza mata babu me tallafa mata duk da halin ha'ulain da take ciki. Tai kuka taitakaici tai nadamar abubuwan da ta shukawa rayuwarta ta dinga tinano da ingantcciyar kana kyakkaywar rayuwar da mahaifanta suka dora ta akai amma ina! ZUCIYA ta rinjayeta ta kasa aiki da abin dayake shi ne daidai ta kasa tankwara ta ga zuwa mikakkiyar hanya to yau dai ga dai zuciyarta ta raba ta da farin cikin ta muddin ranta 60 Eh, Mana mahaifin ta ya mutu da bakin cikinta duk da kyautatawarsa gare ta mutum me mutukar kima da daraja a zukatan al'umma amma sai da ta mayar da wannan alfarmar da ke gare shi har al'umma na tuhumarsa da sakaci ga iyalnshi bawan Allan da be ji ba be gani ba da ya yi bakin kokarinsa wajen haka iyalinshi bisa hanya ingantacciya. Mutum me hakuri kawaici da gudun zuciya amma kuma sai da ta kure'shi yai fushi da ita fushi me tsanani da har ya koma ga ubangijinsa yana me bakin cikin halin da take cikı sanadiyyar bakin cikinta gami da abin abin kunyar da ta jaza musu saboda Allah ina za ta kai hakkin wannan bawan Allah, bawan Allan da ya kyautata mata ya inganta rayuwar ta yake kokarin share mata hawayen duk abin dåta zo da shi gwargwadon iko amma kuma shi tai wa wanan sakayya ina za ta kai hakkinsa hakkinsa kadai ya isa ya dai-dai ta mata rayuwa tabbas ba za ta taba ganinda kyau ba wayyo ina ma bata bi SON ZUCIYARTA BA. to son zuciya daman 6acinta. Mahaifiyarta ta yi kaura ta bazama duniya dama sauran'yan wuyanta duk a dalilina shin ina zata ga da kyau a rayuwarta? Ta tina da dinbin so da kaunar da ke tsakaninta da 'yan uwanta dama iyayenta amma duk a yau ya kau ni Hanifa duk ni na tarwatsa hakan hakika ban ji dadi ba ban inganta rayuwar iyayena ba kamar yanda su suka ingatan ni Hanifa na yi asarar rayuwata. Ta tina da kalaman mahaifiyarta a cikın wasikar bankwana da tai mata sai ta sami kanta da rusa kuka marar misaltuwa hakika ba karamar cuta Mas'ud yai mata ba a baya ta yi zaton ba ta da masoyin da ya fishi a she ba haka bane bayan shekaru, hankali da tsinkaye da hangen nesa duk ya fita kasancewarsa namiji amma duk ya kasa nusar da ita yana ji yana gani ta bijircewa iyayenta tai musu tawaye ta 61 saba musu ta musguna musu ta jefa su cikin abin kunya a idanun al'umar da take mutukar ganin kimarsu har ga shi karshe ta jefa su cikin uku ba me yawan gaske. Duk adalilin son da take masa amma shi fa duk da son da yai ikirarin ya nai mata idanunsa be rufe ba zuciyarsa bata makance ba bare har ya kasa bin umarnin mahaifansa alhalin yana ji yana gani ta bijirewa mahaifanta bata makance ba bare har ya kasa bin umarnin mahaifansa alhalin yana ji yana gani ta bijirewa mahaifanta duk a dalilinsa a karshe me ya gwada mata? Ya fita hankali da nutsuwa gami da hangaen nesa da uwa uba biyayya ga iyaye bayan cewa mace akafi sani a wannan fagen. Abu mafi muni daga cikin cutar da yai mata ya maishe ta abar hutawarsa daga bisani ya yaudare ta ya ha'ince ta ya butulce mata ya kuma ci amanar kaunar da ta gwada masa bayan ya gama fata mata rayuwa ya riga ya gama 6ata record dinta. Ya tsallake ya bar ta cikin kuncin rayuwa bayan day a ci amanarta yai aure da wata macen da ba ita ba bayan ita a dalilínsa na ta auren ya salwanta ta aikata unubı me girma (ZINA) duk dai a dalilisan duk da kasancewar a baya ya sha tabbatar mat a da zai aure ta da zarar ta kashe auren ta to hakan ba ta yiwu ba har sai da me afkuwa ta afku Allah ya bayyanar wa da tsohon mijinta ha'intar da take mata.ashe batta sanı ba yaudararta yake yi ita ba komai b ace a gare shi face abar hutawarsa, ta watsar da kima da darajar da ubangiji ya danka mat a. ashe ba ta sani ba shirme take maganar aure a tsakaninsu babu shi domin tini ya gushe daga zuciyar shi kai hakika ba karamar cuta yai mata ba da kuma ZUCIYARKІ ba! Ta bawa kuma yau ta amsa saboda son zuciya idanunta ya rufe ta kasa hango tarin zunubin da take kwsarwa kanta duk 62 adalilin bin son zuciya, ZUCIYAR DA BA TA DA KASHІ. Maimakon tayi kokarin lankwasa ta zuwa g aikin alkhairi amma ina! Zuciya ta riga ta rinjaye ta ta makantar da idanunta, kunnuwanta kai da makonai nata. Sakayyar ubangiji a wannan lokaci sai ta riski kanta da matsanancin so da kaunar tsohon mijinta soyayya ta hakika burinta kenan be wuce ta malake shi ba amma ina! Yai mata nisa aure ya riga ya harınata a tsakaninsu a badan abidin zuciya ta riga ta kai ta ta baro. To sai dai abin be tsaya a nan ba shin saboda Allah ina za ta kai hakkin 'yan uwanta? Daga dai irin musifar data jaza musu hakika wanda ta sabarwa suna da yawa ba ta kyautawa rayuwar ta ba ina ma ba bi son zuciyar ta ba to ZUCIYA CE BА ТА DA KASHI. Ta kasance cikin matsaanciyar damuwa ga lafiyar ta da ta kasa inganta ga uwa uba kazafin mummunar cutar nan da aka yi mata wanda ya haifar da gagarumar tsana da tsangwama daga hannun al'umma muiukar tana cikin wannan gari cikin wannan hali tabbs za ta davvama ne cikin bakin cikin rayuwa kwananta be kare ba wahalana shirin kashe ta wayewar gari ta hada 'yan komatsanta ta tai banakwana da garin ta na haihuwa tia da kanta ba ta saa inda ta dosa ba.... Allah sarki rayuwa kenan me juyi lamarinta akwai wuya ta kan zo maka a duk idna ka dauke 14 留南沙我 Shekara Ishirin da daya cif kenan dabarun isohuwa Hanifa gida ko kuma muce tsohuwa lya kamar yanda sunanta ya koma a halin yanzu a tsawon wannan shekarun wahalar rayuwa kam ta shhata har bata fatan dai-dai da dakika da daya 63 ta tina tin bayan barin ta gida ta zauna a garuruwa da dama na Kaar nan Kaskanci da wulakanci kai dama duk wani abu d ke tagayyara rayuwar bil adam tsohuwar iya ta fuskanta wahalar duniya kam ta sha ta bayan tsawon shekarun da ta yi tana fama da cutar nan da tai silar al'umma ta kyamaceta ta tsangwame ta hart a ras ainda za ta sanya kanta a duniyar nan. Tai aiki tai bauta ta yi duk wani abu da ke azabtar da jikin bil'adama duk dan ta samu abin daza ta inganta lafiyarta amma kullum jiya I yau duk abin da ta samu kan tafi wajen neman magani irin aikace-aikacen da ta yi ba ita da kanta ba za ta iya lissafa su ba. Rayuwar tai mata kunci duniayar tai mata ba dadi zuciya ta kai ta ta baro ta gama kaskantar da rayuwarta. Al'umma na kyamatarta dalilin warin da take yi rowan da ke fita daga jikinta ya haifar da hakan dalilin kenan dab a ta jimawa a duk inda take aiki ko aiki kam na wahala amma a karshe sai ai mata wulakanci a yi mata korar kare tai kuka tai nadama gami da neman gafararubangiji a bisa musibar da tsohon masoyointa ya jefa a she ba ta sanı ba ba karamar cuta yai ma ta ba yau ita ce ta zama abin kyama ga al'umma ta dinga tinano irin ni'imtacciyar rayuwar da ta tashi a cikinta duk da cewa iyayenta ba mawadata ban e to amma suna da rufin asirinsu dai-dai gwargwado. Wane irin gata ne iyayenta basu nuna .mata ba har abada ba za ta taba mancewa da wannan ba bata taba zuwa neman wani abu gurin mahaifitana ko mahaiiyarta ba tare da sun share mata hawaye ba mutukar suna da yadda za su yi mahaifinta mutum me hakuri da sanin ya kamata me jumurin neman na kansa da son kyautatawa iyalensa mutumin da ya sadaukar da rayuwar shi dan rayuwar susta inganta haka abin yake gurin mahaifiyarsu mace me kokarin share musu hawaye 64 a duk lokacin da bukatr hakan ta taso dukkan ilahirin abin data samu ya kan kare ne a kanshi barin ita da tafi fifita ta kasancewarta 'yar fari da ta gwada mata kauna fiy da sauran 'yan uwanta. Amma a yau gad a abin d ta saka mata. Ta bazama ta bar garin da tai shekara da shekaru a cikinsa duk a dalilin bakin cikinta mafi munin abu da baza ta taba mancewa da shi ba shi ne yanayin da suka rabu da mahaifinta yana me tir da allah wadai da ita har ya bankwana da duniya wannan abu n zuciyarsa saboda Allah ya ko zata ga da kyau? Mas'ud ya gama da ita ya gama da rayuwarta ya kuma kaita ya baro tsakanin da shi sai dai sakayyar ubangiji tabbas ta san ta so shi a baya a halin yanzu ta gano cewa tin fil azal so da sha'awa ta rinjayi komai amma babu batun kauna a tsakaninsu idan harda kaunar ta fisabillillahi da basu kasance a halin da suka jefa kansu ciki ba da kuma be yadda ya jefa ta cikin musifa ba tabbas so da sha'awa ne a tsakaninsu babu batun kauna tun shekarun da suka gabata ta gama gano mutumin da take sonsa ta ke kuma kaunar sa. Kauna ta hakika kauna ta dan Allah shi ne mutumi kaunace ta domin lillahi wato tsohon mijinta Abdulzahir da ta ha'ince shi duk da kyautatawarsa gare ta. In banda ZUCIYA DA BA TA DA KASHI me kamar Abdul zahir har me zai yi da wani da namiji to amma ina! Kaddara ta riga fata ZUCIYA BA TA DA KASHI, ta riga ta rinjaye ta (Har kululm bawa ya kasance me neman tsari da zuciyarsa). Hajiya Sauudat ita ce macen da ta dade tana aiki tare da ita ita ce kuma matar da tai silar fitar da ita cikin larurar da take ciki tsahon shekaru duk da cewa ba karamin kudi ta kashe ba saboda ciwon ya ci karfinta tsohuwa iya ba za ta 65 taba mancewa da wannan 'yar tahalika ba mace me kyautayi da sanin darajar bil'adama idan muka kawar da wannan halin nata za mu ga cewa farat daya Allah ya hada jinsu da wannan baiwar Allah ta riski kanta da kaunarta gani da tausaya mata. To fa tin daga lokacin suke tare duk da cewa ba wani dadewa tayi a gidan ba domin duka duka ba ta zarce shekara shida a gidan ba. Aikinta a gidan be wuce kula da yara ta shaku da yaran fiye da zaton mutum wannan dalili ya dada kara dankon kauna a tsakaninta da uwar dakinta sun zauna a garuruwa kamar biyu har zuwa yanzu da suke zaune agarin Oshogbo babban birnin Jahar Osun. Sai dai kuma me gidan be cika zama a gidan ba saboda yawan aiyuka yau ka ji sh awanan gari gobe ka ji shi a wancan kai wani lokacin kasar dungurungum yake bari dalilin kenan da sai tsohuwa iya tadau tsawon lokaci ba ta sanya me gidan a idonta ba musamman da yake a duk lokacin daya sami damar yin hakan ya kan tattara su lokacin shi ne ga iyalinshi mace daya tilo kenan taıkar da dubu domin duk da kasancewar sun manyanta girma cimma su hakan be hana su aiwatar da dandasheshiyar soyayya ba. Yanda take ji da shi take kuma kyautata masa haka shi ma yake sonta ya ke kuma kyautata mata mutum ne me Kokarin kyautatawa iyalinshi da ma duk wanda yake Karkashinsa halayyarsa dabi'unsa ya kan mata kama da matsawon mijinta mutumin da ba za ta taba dena kaunar sa ba a badan abidina a wasu lokutan ma takan ga kamar ta san shi wasu shekaru can da suka gabata to amma kamar ce domin ta kasa tinano inda ta san shi rikicin tsufa ne kawai abin datake ayyana a ranta kenan aduk lokacin da tinanin hakan ya zo mata. 66 A halin yanzu shekarunta hamsin da bakwai zahirin gaskiya za kai tsammanin ta fi haka nesa ba kusa ba alamun tsufa sun bayyana a gare ta Karara to yanzu ne ma tad an yi kyan gani dalilin zamanta gidan Hajiya Saudat. Abu uku ke zuciyarta abu ukun nan ne dai muddin rai ba zai taba gushe ma ta ba burinta tunaninta kai dama komai ya ta'allaka ne a kan abu ukun nan wato mahaifanta da yan uwanta, mijinta sai daya tilo da Allah ya huwace musu a mace yake a raye yake ba ta sani ba tin bayan barinta gidan mahaifisan ba ta kuma sanya shi a ido ba, so da kaunar gudun jininta ako da yaushe shi ke zuciyarta. Sai abu mafi mahimmanci a rayuwar ta shi nebatun mahaifanta 'yan uwanta da kuma me gidanta burinta kenan ta gansu ta nemi afuwarsu amma ina! Ba za ta ce ga a duniyar da mahaifiyar ta da Rannenta suke ba amace suke a raye suke Allah ne masani duk da cewa ta san inda tsohon mijinta yake wato Ainihin garin ta na haihuwa to amma ina abadan abidin ba za ta iya kusantar inda yake ba shin da wane ido za ta kalle shi to sai dai babban abin day a fi tsaya mata shi ne batun mabaifinta, Gwanda ragowar zata iya neman gafararsu idan da rabon ganawarsu to shi fa? Bayan tini ya riga yai bankwana da duniya ya tafi yana me dauke da bakincikinta ba tare da ya afuwanta mataba mun sani cewa ranar gobe kiyama nafsinafsi ne ma'ana kowa ta kansa yake yi, ita ce ranar nan da Allaly (S.W.T) yake fadi cikin al'kur'ani a gurare da darna misali cikin suratu Abasa inda ya ke cewa: "Ranar da m tum yake gudu daga dan uwansa, da matarsa dal ubansa, da matarsa da diiyarsa, ga kowane mutum a ranar nan akwai wani sha ani da ya ishe shi. Aya ta 34 zuwata 37.A To shin ita da ba ta wanye da mahaifanta iafiya baya za ta yi kenan a badan abin ba za ta taba samun nutsuwar 67 zuciyarta ba tai kuka tai takaicin halin da ta bari zuciyaarta ta sanya ta a ciki a duk lokacin da ta tina haka ta kan yi kuka na fitar hankali to a duk lokacin da irin hakan ta faru hajiya Saudat ta kan matsa mata da tambaya amsar da ta kan bata dai daya ce wato mahaifanta ta tuna da suka riga mu gidan gasiya a duk lokacin a ta ji haka ta kan amsa mata ne amma a can kasan zuciyarta tai amannar akwai abin dake damun wannan baiwar Allah. Ta lura da kyau gaba daya rayuwarta ta taa'allaka ne wajen bautawa Ubangiji da neman gafarar ubangiji yawanacin lokuta bakin ta ya kan kasance ne cikin azumi nafilfilun cikin dare kuwa babu ranar fashi kai a kusan ko da yaushe ba samun yin bacci saboda tahajjidi haka nan ida da rana ne har zuwa yamımaci mutukar ba wani aikin take ba za ka iske cikin ibada ne kai ko aikin take yi zaka iske ta rike da carbi a hannunta to zancen ta kalamanta halavar ta duk abin koyì ne ga me neman tsira ranar gobe kiyama. Hajiya Saudat ta kan ji dama ita ce a matsayi irin aa tsohuwa iya tabbas ta ci ribar rayuwa to sai dai duk das haka takan yi kokarin koyi da kyawwan dabi'unta. Tsohuwa iya kenan ma'abociyar iba da matar da ta sadaukar da rayuwarta wajen bautar ubangiji tare da neman gafarar sa mace me tarin sanin ilmin addini da kokarin aiki da shi macen da tsufa dawahalar rayuwa be sa ta gaza daga bautar ubangii ba tare da neman gafarar sa mahaifanta, 'yan uwanta tsohon me gidanta dama dan da Allah ya huwace imusu kan kasance sawun gaba wajen nema musu rahamar ubangiji. A ya suma shirye-shiryen taifya babban birnin tarayya Abuja domn taya babban AMinin me gidan murnar bude katafaren karnfenin sarrafa kayan cid a sha na gwangwani. 68 Tare da taya shu murnar samun shugabaneım yan kasuwa na Kasa bakı faya. Gia yanda tsohuwa iya Jag a iyayen gipata na y in gagarumın shum domin ta ya abokin me gidan murnat farincıkin abin Alkhairin da ya same sbi ta san ba karamn matsayi mutumin yake da shi ba. a kashe garin ranar da za ya ga yi gagarumin shi ne tare suka dira Abuía suka yi masauki a katafaren gidan da ya zama mallakınsa ya tanade shi domin saukar iyalınshi asokoro. Wayewar gari sun yi ta ne cikin ruguntsimun shagalin taya abokinsu murnar gagarımim ci gaban abokin mai gidanta ya samu. Da misalin Karfe hudu na yanmaci yalın Alhaji Abdul, suke gabatar da nasu gagarumin shagahnea harabar katafaren gidanshı, cikin wadan da suka halarei taron. hat da tsohuwa iya dame dakinta da madaukacın yalınta. Kusan duk wani abu su Hajiya Saudat ke gabatar da shi wanda hakan ke nuni da matsayın da take da shi a iya gane-ganen tsohuwa iva da kuma irin gawurtattun atta zirai da tat aikra Katkashms zahirin gaskiya ba ta taba ganin gida me kyau haka ba kan ba tama taba ganin ko me kamar sa ba ta saki bakı tana kallon ikon Allah tamkar bakauyen da ya fara shiga birni.A duniyar nan kuwa akwar wata matsala ko damuwa a tattare ga ahalm gidan nan? Tabbas babu mutumin da Allah yaiwa ni ima irin wannan me kuma ya rage masa da ya wuce kyátitata tsakanin sa da mahaliccinsa abin da take rauwa zucryarta keu an Wata yar kakkaywar yarinya yar kimanin shekara bivar ta tawo da gudu yayın da 'yar uwarta ke bive mata da alamun dai tsokana tar vo a dai-dai lokacin ta dire kan tsohuwa tya

Chapter 5 of 7