Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 7
office din mu ce dole ki bi ta ba tare da kin taka ba. To bari ki ji da office din da me office din ba su wuce in taka su ini kwana lafiya ba. Da fadin haka ta sa kai ciki ainihin ofishin ba ta yi kokarin hana ta ba saboda sanin matsayinta a gurin mamallakin office din. Yana zaune a kan kujera ya daga kanshi zuwa sama gami da runtse idanuwanshi a lokacin da yake karkada kafafunshi da alamar ya yi zurfi cikin tunani. Ta kare mishi kallo sama da kasa da alamunar ashin kwanciyar hankali a tare da shi. cikin sanda ta sidada ta bayanshi hannu ta zira ta bayanshi ta rungumo shi gami da dora kanta gefen kafadunsa da sauri ya dawo daga duniyar tunanin da yake. Kamshi ya doki hancinshi wanda hakan ya tabbatar mishi da Gimbiyarshi ce,. Be yi kokarin juyawa ba sai kawai ya zira hannu ta baya ya janyo ta jikinsa. Sun dade a haka har zuwa lokacin da ta yi dabarar janye jikinta. Ya lumshe ido Hanifa kin kyauta ke nan? Kin kyautawa rayuwata ke nan? Bayan kin san rashinki zai iya haddasa mummunan sakamako a gare ni why Hanifa? kar ka zarge ni Mas'ud, ko kadan kar ka tuhume ni, ni kaina 29 na shiga damuwa de rashinka to apma ya zan yi Abba ya matsa ya takura za ka tausayawa halin da nake ciki yavin da ka gan ni a gida, iyaycna sun tsangwame ni sun yanke duk wata alaka a tsakaninmu a dalilin kaunarka Mas'ud. Ya girgıza kai gami da cije lebe me ya sa Abba zai haka? Mc ya sa Abba va kasa fahimtarmu? Shin ya mance da matsananciyar kaunar da ke tsakaninmu Hanifa? ta girgiza kai cike da damewa bar wannan batu, bar wannan batu Mas'ud hankaliamu ya karkata wajen samun mafita, to sai dai sun jima suna tatteunawa ba tare da samu mafitar ba. A waui yammaci ma suna tare bayan sun kare aikata wacce suke ganin za ta fisshe su Mas'ud din ne ya fara cewa ni fa wannan zaman ya ishe ni ya kamata mu san abin yi a ko da yaushe ba u da yan cin kasancewa tare da ke sai dai ua wasu daidaikun lokuta, lokaci ya yi fa da ya kama tara bayyanawa Abba niyyar aurena a gare ki. Abin nufi na turo magabatana. Ta katse shi da cewa Uhm! Mas'ud mu dai kara lokaci amma wallahi Abba kai da ma umma suna cikin dumi a halin yanzu. Ni ban san me ya sa ba sun yi fushi da ni da kai ba ki daya. Za ka yi mamkai irin wahalar da na ke sha kafin na kai ga isa wajenka. Kin dai nace ne amma ai da na gwada sa'ata, kin mance Abban yana da masaniyar dumbin son da nake miki? Mu dai kara lokacin kamar yadda na ce ni na fi ka hangen abin dakai ba ka riga ka hango ba. sannu a hankal kisan a ko da yaushe suna tare da juna domin aikata masha'a kusan koda yaushe akwai dabarar da take yi domin isa ga wajenshi to shi dai bai isa ya ko taka kofar gidansu ba. Sannu a hankali tun Abba da Umma ba su fuskane! halin da 'yarsu ke ciki ba har suka kai ga gano abin dake akwai abin daya dada ta'azzara ciwon Malam Sa'ad yayin da 20 Umma ke cikin damuwa kashi-kashi ga Hanifa bo ta san ma suna yi ba domin dai idauta tuni sun ruga sun ruf da bin ZABIN ZUC)YARTA. Tana kishingide a gefeushi yayin da ta yi pillow da cinyarshi a lokaci guda kuma yana wasa da kanannuu kalabar da take kanta, ina ga karshen wannan kumbiya-kumbiya ta zo karshe, domin na samo mana mafita, kin gane ko?" Ci gaba da maganarka ta ce da shi saboda zumudi to wane abu take so a dai waanan lokaci da ya wuce ta mallaki Mas'ud dinta. Ya ci gaba la cewa, abin danake nufi me zai hana ki shiryawa komawa karatunki ina ga wannan ita ce hanya daya tilo da za mku fake mu ci gaba da gudanar da rayuwarmu yadda ya kamata. Mutukar ba haka ba wallahi ganinki ma dungurungum sai ya gagare ni. Duba ki gani yau kwana nawa rabon da ke sakamakon takunkumin dakike ciki? Ta yi ajiyar numfashi da jin wani sanyi a zuciyarta wai me ya sa ne tun farko ta kasa wannan tunani ya aka yi basirarta ta toshe ne? to sai dai kuma in da ba kasa a nan ake gardamar kokawa, ta ya za a yi ta fuskanci iyayenta da wannan batu a yadda suke jin zafinta tamkar su gangama wuta su jefa ta ciki, ai ko Abba be mata adalci ba tun fil'azal ya san da irin matsanancin son da take masa. Tana tsugune a gaban mahaifinta kirjinta sai dukan uku-uku yake saboda tsoron abin datake shirin tunkara. Ta vi karfin hali dai, muryarta a sanyaye, Ta ce Abba na zo neman wata alfarma ne a gåre ka, da fatan za ka slaren ahwayena. Be ce mata komai ba tsawon lokaci ya girgiz. kai sannan ya се wace alfarma kike nema? Wace alfarma ce ban miki ba Hanifa? Ta dan sunkuyar da kai, dan Allah Abba so nake na ci gaba da karatuna. Me ya hana ki ci gaba? Me ya hana ki karasawa a can baya? Shashanci ko? Saboda kin kekashe 30 zuciyarki kin yi watsi da ingantacciyar tarbiyyar da muka fora ki kai, kika shiga aikata alfasha a doron kasa ko? Ki sanı ko me kake yi kome ka aikata shi za ka je ka riska ranar gobe kiyama (Ranar nan me ban tsoro). Ki yi duba cikin Alkuir'ani mai girma aya ta 281 cikin Suratul Bakara inda Allah yake cewa, "Kuma ku ji tsoron wani yini wanda ake mayar da ku a cikinsa zuwa ga Allah sa'annan kuma a cikawa kowace rai da abin daya sana'anta." Ina me dada jan hankalinki ki tuba ki koma ga Ulbangiji ki yi kokarin karkata zuciyarki zuwa ga aikata alheri. An akarbo daga dan Abdullahi Nu'umanu dan Bashir ya ce, na ji Manzon Allah (S.A.W) yana cccewa, "Hakika a jikin mutum akwai wata tsoka idan ta gyaru dukkan jiki ya gyaru idan ta baci dukkan jiki ya baci, na'am ita ce ZUCIYA." Bulhari da Musulim ne suka rawaito wannan badisi. Hadisi na 6 Arba'una Hadisi). a ZUCIYA BA TA DA KASHI ki yi kokarin tankwasa tankwasata a duk lokacin da take kokarin kai ki ga halaka. Shin ya 'yata ba kya tsoron ranar da Ubangiji yake fadi cikin littafi me tsarki, "A ranar da harsunansu da hannayensu da kafafunsu suke bayar da shaida a kansú game da abin dasuka kasance suna aikatawa." (Suratul Nur: Aya ta 24). Bayan Ubangiji ya hane mu ya kuma gargade mu da aikata alfasha a wurare da dama cikin Alkur'ani me tsarki alal misali cikin suratul Nur aya ta 2,21,30. ko ko kinfi so ki kasance daga cikin wadanda Ubangiji madaukakin sarki ke fadi a cikin suratul Furkan aya ta 68: "Kuma ba su yin zina, kuma wanda ya aikata wancan zai gamu da laifuffuka aribanya masa azaba a ranar kiyama kuma ya tabbata a cikinta yana wulakantacce." Shind an Allah wace riba ce ke tattare da wannan aiki? Zina babbar illa ce a rayuwar dan 32 adam mafi muni zina da aurenki, ki yi gaggawar tuba ki koma ga Ubangiji irin tuban da Ubangiji ke fadi cikin littafi me tsarki (TAUBATAN NASUHAN) domin shi ne Gafurur Raheem me yawan afuwa ga bayinsa, amma ki sani ni ba zan ba ki lasisin sabon mahalicci ba da yawuna ba wannan karatu da kike son komawa, fakat tashi ki ba ni waje. Jikinta ya yi sanyi da kalaman mahaifinta, anya ko tana kyautawa rayuwarta? Me ya sa ba za ta yi hakuri da Mas'ud ba? ZUCIYA BA TA DA KASHI, take zuciyarta ta ba ta amsa da cewa har abada ba za ta taba daina son Mas'ud ba yadda ba za ta iya taßa rayuwa ba tare da shi ba hanyar ke nan dai ta yi kokarin lallaßa mahaifinta. Tsawon lokaci tana aikin rokon mahaifinta a kan dai bukatar da ta zo masa da ita, Hanifa ba tun yau ki ka fara bujircewa bisa turbar da na saka ki ba karatu ga shi ga ki nan ki yi duk abin dakika ga zai fisshe ki tunda ni ban isa na hana ki ba, Allah ya sani kuma ke ma shaida ce na yi bakin kokarina wajen sauke nauyin da ya dora min. kamar yadda Malam Sa'ad ya zata karatun da take ikirarin yi shi ne dai lasisin sheke ayarta da Mas'ud zahirin magana in banda 'yan daidaikun lokutan da takan shiga makarantar da sai mu ce ba ta ma san hanyar makarantar ba sai dai duk abin dadalibi yake yi wala attendance, test, exam, tamkar da ita ake yi sakamakon tsaya matan da Mas'ud ya yi zahirin magana in ka ga daular da take ciki za ka yi mamaki ko dayake dama can suna cikin rufin asiri to amma iirn yanda yake mata bari da naira abin zai daure maka kai to sai dai kuma wala Abba ko Umma da ma ma kannanta babu me ko saurarar abin datake da shi kai duk wani abu da ke da alaka da ita sukan kyamace shi sannu a hankali kusan ko yaushe suna tare da Mas'ud ta zame masa tamkar matarshi babu kunya babu tsoron Allah a 33 halin yanzu dai idanewansu ya gama rufewa ba su shayin kowa sai tir da Allah wadarai ke fita daga bakunan al'uroтa tare da aza laiun a kan iyavansu. Lamarin Mas'ud kam sai gaba yake yi al'amaru ana dada sharnic.wa yayin da a ke samun mummunan gibi da2 ofishinsa ba sau daya ba, ba sau biyu ba Alhaji Khalii Ya sha jau kunnanshi gami da yi mishi nasiha dangane da la'marin rayuwa to amma me? Ta inda ya ji ta nan yake fita ma'ana ba ya daukar ingantacciyar hanyar da mahaifinshi ke kokarin isar da shí to sai dai me? Hanifanshi kadai yake so ita kadai ke gabansa (Ubangiji ka raba mu da irin wannan son, son da zzi kai ka ga halaka. Yanzu saboda Allah Malam haka za mu zubawa yarinyar nan idanu muna ganin abin datake yi? ni da kai muan da masaniyar abin datake yi anya Malam? Ina jiye mana abin kunya fa? Yau she kuma? Tun yaushe abin kunya ya riske mu, abin kunyar da ya wuce wanda muke ciki yanzu? Sai kuma ya sassauta murya sa'ilin da hawaye ke zubo mishi Na rasa yadda zan yi da yarinyar pan, na rasa inda zan saka kaina, na yi fadan na yi nasihar duk a banza, saboda Allah wace irin tarbiyya ce ban dora yarinyar nan bisa turbar ta ba? to me kike so na yi da ya wuce na zubawa sarautar Allah ido,? Ni kam ban sen abin dana yi wa Ubangiji ba ya jarabce ni da wannan musibar, bakin gwargwado na yi kokarin sauke nauyin da Ubangiji ya dora min to me na yi wa Allah kuma? Da sauri ta katte shi, haba Malam kamar ba masani ba, ka yi hakuri ka dogara ga Allah ka kuma yibiyayya a gare shi a bisa dukkan wani abu da ya same ka me kyau ko marar kyau wannan shi ne cikar imani, addu'a kawai za mu bi ta da ita Allah ya shıryar da ita. Yana kokarin magana tari ya ci karfinsa a lokaci guda haki ya tasar masa ya dinga wani irin nishi gami 34 da dafe kirjinshi da Seur Ucoma ta yo kansa sannu Malam, sanru Ubangıjı ya yye maka wannan larura. Cikin dan kankanin iokaci ya fita hayyacinshi a yayin da Um.nant ake neman agaji. A kuma dai-dai lokacin ne Hanifa ta dawo а kidime ta yı yo kan mahaifinta amma ko kafin ta isa gare shi wata irin tsawa Umman ta daka mata ba shiri ta ja baya jiki na tsuma. A gaskiya baba mutukar ba za ka yi kokarin fitar da damuwar da ke zuciyarka ba jiniuka na shirin kaiwa ga matakina karshe, ya kamata ka yi kokarin fitar da duk wani abu da ke addabar zuciyarka. Cewar likita Mannir ya koma kallonshi ga Umma, ya kamata hajiya a dinga kokarin kaucewa duk wani abu da zai kai ga tayar mishi da hankali don ingantuwar lafiyarshi. Jikinta ya yi sanyi saboda larurar babanta me ya janyo masa haka? Amsa ita ce Gacin ranta to me zai hana ta shawarci Mas'ud ya zo su yi aure kamar yadda ya nema tun a baya, ko babanta ya samu nutsuwa har lafiyarsa ta inganta. Suna tafe a mota kan hanyarsu ta zuwa Kaduna wajen kasaitacciyar Dinner da suka shiryawa babban abokinshi Ammar domin taya shi munar samun kairn girma daga captain zuwa major. Mas'ud ta ce da shi. be jiyo ba saboda hankalinsa da ya tattara bisa titi ya aka yi Princess? Ka gane ko Mas'ud ya kamata ka yi waui abu fa. Kamar yaya fa Abin nufi lokaci fa ya yi da ya dace ka yunkuro daga lamarin aurenmu, Abba ya danu da halin da nake ciki yana cikin matsananciyar damuwa duk a dalilina. Ya yi shiru kamar wanda aka zarewa laka, tun bayan daidaituwar lamuransu ya ji maganar aure a tsakaninsu babu ita ma'ana abin dayake kwadayin samu ga shi nan available . duk lokacin da yake bukatar kadaicewa yana da damar hak1, 35 to me kuma zai sa su damu kansu damaganar aure bayan sun yi amannar shi da ita sun aminta da juna ma'ana sun zama mkallakin junanshi? Shi dai kam a nashi ra'ayin kamar zamansu haka ya fiye musu komai, to amma ya za a yi ta fahıka hakan? K gane ko Hanifa ko mun yi aure ko ba mu yi ba mun zaallakin juna, to me zai sa ki bijiro mana da wani batun kukаm Tа бata rai ban fahimce ka ba? kana nufin haka za mu yi ta zama? Kin kasa fahimta ta ba hakan ne manufata ba, amma dai ina ga kamar lokaci be yi ba ma'ana ba na so mu takaita rayuwarmu, mu tauyewa junanmu 'yanci, komai da kika gani lokaci ne. Cikin kufula ta ce, to na fahimce ka na kuma fahimci inda ka sa gaba, kara so ka tagayyara rayuwata ko Mas'ud? Na gode tsaya sauke ni kawai kowa ya kama gabanasa a lokacin da take kici-kicin bude motar da sauri ya rike hannunta sorry Hanifa kin kasa fahimta ta ne, amma duk mu bar wannan batu zabinki shi ne zabina ki ba ni lokaci zan aiwatar da abin dakike so. Ka kyale ni Mas'ud na gane kai mayaudari ne. No Hanifa har abada babu batun yaudara a tsakaninmu. Be gushe ba yana lallashi har ya shawo kanta. Da misalin karfe hudu suka isa garin Kaduna sai da suka fara yada zango a Gamji Gate nan cikin Kabala Kostin nan din ma dai aka kara aikata batacciyar sannan suka yi wanka suka kimtsa da misalin karfe bakwai dai-dai suka yi wa Halal Hotel tsinke dake Isa Kaita Road, inda za a gabatar da gagarumin shagalin, galibi mazajen dake wajen tare suke da iyalansu in ka dauke tsirari su din ma suka bi 6angaren da aka tanada dan masu iyali sai dai fa zahirin gaskiya martaba da kimar da musulunci ya tanadarwa ma'aurata ba su tare da ita. 36 Uban taro Ammar ya yi murna da isowar abokinshi, be yi zaton zai zo ba, kai be ma son zai zo ba sakamakon tabarbarewar lamura a tsakanninsu duk a dalilin fadin gaskiya, to fa tun daga lokacin zumunci ya yi rauni a tsakaninsu amma ko sa'ar da ya hada ido da Hanifa sai farin cikinshi ya koma ciki annurin fuskarshi ya bace. A dakile ya amsa gaisuwarta babu alamar sakin fuska a tare da shi, yana takaici gami da bakin cikin halin da kamillaliyar yarinyar (А baya ke nan) ta jefa kanta a ciki, shi shaida ne domin daga ita har shi kansa Mas'ud din yana da tabbacin a baya mutanen kwarai ne be taba tsammanin haka ba, kai yaushe ma ya taba zaton haka za ta farui da abokinshi, mutumin da ya kasance ma'abocin kyamar alfasha da sauran kaba'irai. Jikin Hanifa ya yi sanyi ranta ya 6aci da wannan kaskanci da Ammar ya yi mata, ba ta taba zato ba, ba ita ba hatta shi kansa Mas'ud din bai ji dadin abin daya yi mata ba, kafin a kai ga kare taron tuni sun fice abinsu. Suna tafe kan hanyarsu ta komawa Kano a cikin daren tana ci gaba da yi mishi mita dangane da abin daAmmar ya yi mata ta ci gaba da c ewa, Ka ga irin abinda nake nuna maka ko a gabanka dai ga abin dindaunka ya gane maka, yanzu in aurena kake fa wa ya isa ya yi min wannan tozarcin? Tabbas haka ne ya kamata ya yi wani abu a kai, to saidai gaskiya yana ganin kamar ba ta cancanci zama matarsa, uwar 'ya'yansu ba, kai zamansu a haka ma ya fiye musu komai, ba ya ra'ayina ure a daiwannan lokaci. Duk irin Allah wadarai da tofin alatsinen da al'umma ke musu ba su san ma suna yi ba, habaice-habaice da gulmace-gulamace da al'ummar unguwarsu ke gudanarwa a kansu duk dai be dame ta ba, masoyinta kadai ke gabanta. Tana tsugune a gaban mahaifinta bayan da ta sunkwi da kai cikin sanyin murya ta ce, Dan Allah Abba ka yi hakuri 37 ka amincewa bukatata, ba ni da burin da ya wuce wannan Abba, ina me neman yardarka kt amince da maganar auren da ke tsakaninmu da Mas'ud, tsoro da rasbin sanin natsayin da ka dauke shi ya hana shi isowa gare ka. A duk inda tunanin dan'adam yake dan gane da tabarbarewar wannan zamani to ya wuce uan, ke da kanki kika zo nemawa abokin fasikancinki aure ko?dukiya rashin kunya da lalacewar abokin shashancinki wato ke kin wucе nan ko? Abadan abidina ban amince ba, ban yarje aure a tsakaniniku ba, ban amince ba ni Sa'adu ba ko zan tabа amincewa ba, ina yi miki nasiha ki tuba ki ji tsoron Ubangiji ki koma gare shi ki fita harkar yaron nan, abadan abidin na yi muku katangar karfe a tsakaninku aure kam babu shi muddin rai. Muryarshi ta sauyą, cikin yanayin damuwa ya ci gaba da cewa, "Yaron nan ya cuce ni, ya cuce ni, sakayyar Ubangiji ce a tsakaniomu." Saboda Allah me ya sa mahaifinta ke mata haka? Me ya sa yake son yi mata karan tsayc a rayuwa? Hakika Abba yana shirin aiwatar da íummunan gibi a rayuwarta mutukar zai katange tsakaninta da cikamakin rayuwarta, dan dai ita yarinya ce me biyayya sai a nemi tauye rayuwarta saboda Allah? A ko da yaushe fadan Abbanta shi nc ta bar abin datake yi to me ya sa Ahba yake kokarin mai da hannun agogo baya? Kullum jiya i yau, lafiya ta kasa ingantuwa a gurin Malam Sa'ad ko don kasancewar mutum ne me mutukar saka abu a zuciyarshi? Shin ina zan sa kaina ni Malam Sa'adu kullum lamarin yarinyar nana sai gaba yake? Da wane ido al'umma za ta dube ni? Ubangiji ina ma ba ka kadarto yarinyar na. fitowa daga tsatsona ba ko na huta daga musibar da ta jefa 38 ui.... Da sauri Umma ta katse shi, Umn. Malam kada ka yi butulci ga Ubangiji a bisa ni'imar da ya yi maka, 'ya'ya nawa Ubangiji ya azurta ka da su? Nawa ne daga ciki suka kasance lalatattu? Hakika ka fi ni sanin amsar hakan. Ka yi hakuri ka godewa Ubangiji da ya shiryar maka da ragowar, mutane nawa ne za su hayayyafa amma babu na zabe a ciki? Saboda Allah in dai ba butulcewa Ubangiji za mu yi ba ya zama dole mu gode masa Ba zana so ka kasance daga cikin mutanen nan da ubangiji ke fadinsu cikin Jittafi me tsarki a kan rashin yarda da kaddara, "Idan sha shfe shi ya kasa hakuri" (Suratul Ma'arij aya ta 20) mu yi h akuri mu dogara ga Allah domin ita din ma bamu fitar da raid a shiryiwartaba mu dai ci gaba da yi mata addu'a. cikin karaya ya ce, Kayya, kayya na tsinke da lamarin yaarinyar nan kullum abu ba sauki sai gaba ni fa na san irin zantuttukan da suke zuwa kunnuwana jama'a ba su yi mana adalci ba sun dora lefin kacokan a kanmu.sabi da Allah da me zan ji wallahi ubangiji ya karbi ruhina ya fiye min daga wanan rayuwar da nake ciki shiga jama'a ya yi min wuya saboda ina jin kunyar abin dajinni na ke aikatawa al'uma kuma ta kasa yi min adalci, zantuttuka na 6atanci duka kai na da zuri'ata. Sai kuma ya shiga shsssheka kamar zai kuka yarinyar nan kin cuceni kin mana babbar illa a rayuwa ta da sauran 'yan uwanki dama zuria'rmu baki daya.... Sai kuka ya kwace masa yayin da umman ta shiga lallashi hakuri za kai malam hakuri za ka yikomai yai zafi maganinsa Allah, mu ci gaba da yi mata addu'ar neman shirya da sannu Allah zai dubc mu. A dai-dai lokacin misalign karfe goma ne na dare hard a 'yan mintuna Hanifa tai sallama ta shigo tin bayan fitar ta da 39 safe kenan in ban da rashin maid a sallama a addinan ce babu kyau da ba za a amsa mata ba cikin sanyin murya Malam sa'ad ya amsa yayin da Umma ta amsa a ciki. Jikinta a sanyaye ta ce Sannu Baba in ce ko ba jikin ba ne? gangar jikina da zuciya baki daya ba za su taba gushewa daga wannan larura da ki kai silar jefa ta ba mutukar ba tsamme kanki ki kai daga wannan mummunar dabi'a da kika saka kan ki a ciki ba, wannan ita ce rana ta karshe da zan ja hankalinki ki ji tsoron ubangiji ki janye kanki, ki tsarkake kanki daga musifar da kika jefa kanki a ciki ki je ki duba ki hanga daga basirar da ubangiji yai miki shin abin dakike yi dai dai ne? duk abin dakika ganin shi ne dai-dai ki dauka ki yi amfani da shi. Tofa Abba ya bata babban Assignment kanta ya dau caji ta hada ta tara daga maganganun, mahaifinta daga bisani ta rabe karya da gaskiya shin wane za ta dauka kenan? Maganar mahaifinta na bisa turba ma'ana yana a ma'aunin gaskiya, a hannu daya kuına lamarinta da Mas'ud ne a ma'aunin karya to me ye abin yi take zuciyarta ta shiga zaba mata abin datake ganin shi ne dai-dai, ta dau kashi na biyu ne? Wato lamarin ta da Mas'ud ko ko ta bi zabii na daya ma'ana batun mahaifinta wanda hakan ke nufin tai bankwana damasoyinta abin kaunarta kenan a lokaci guda zuciyarta ta karyata hakan. Kai ina hakan ba zai yiwu ba har abada ba za ta tab a rabuwa da Ma'ud ba ba za ta taba yin saken da zai subuce mata ba tana sonsa, tana sonsa so mara iyaka. Uhm! ZUCIYA KENAN ZUCIYA ВА ТА DA KASHI. Take'ta bi zabin zuciyarta ma'ana tai ruko da karya tai shika da gaskiya, malam Sa'ad ya fuskanci babu alamun sauyi ko sassauci daga lamarin yarsa kullum abu sai gaba yake abin daya dada 40 ta`azzara larurar shi ako da yaushe jinin sa sai hawa yake babu alamun yin kasa hart a kai ga jininshi ya kai ga mataki na karshe malam Sa'ad kam na jin jiki. Ako da yaushe Hanifa na kokarin tunasar da Mas'ud lamarin aurensu bad an komai ba said an damuwar Mahaifinta to amma a duk lokacin da tai masa maganar hakan sai yai dabarar sha shanar da zancen.. Yau da gobe be gushe ba sai da ya shashantar da ita ta ma dena yi amsa maganar baki daya. A 'yan kwanakin nan ciwo ya matsawa malam Sa'ad Kwarai da gaske a duk lokacin da ya tasar masa sai ya yi kamar ba za kai ba ‘yan uwa da abokan arziki duk sun karaya da wannan larurar tashi amma a hakan take sa kafa ta fice domin gudanar da abin datake ganin sh ne daidai a rayuwar ta, saboda rashin jin kai a wannan lokaci dai kwanan gidansu ma be dame ta ba idan ma harta kwanan to be wuce kwanciyar bacci ce ta kawo ta ba. A wannand aren ma a kan idon Malam Sa'a d ta dawo ttin bayan da ta fita d safiyar jiya ba iya ce mata komai ba illa ido daya saka mata malam Sa'ad yai kuka yai kuka har ya gode Allah, wayewar gari da sanyin safiya jikin nashi ba dadi ciwo ya fina da hailala da salati kadai kai ke fita daga bakinsa. Ta kintsa ta hade cikin yadin tissue da akai amsa dinkin 'yan birni me mutukr bayyana surar jikin bil'adama dinkin ya dame ta tsam yayin da kan ta ke dauke da kananun kalba da aka jona su da izgar doki kunbunangta an fente su da fentin bature, tana gab da fita tai arba da mahaifitana yayin da umma ke kansa tana mishi fifita gami da yi masa sannu fuskarta knshe da matsananciyar damuwa da alama ciwon ya fin a ko yaushe. 무 Sannu Abba ta fada cikin tausayawa a lokacin da ta rusuna a gabansa ba zai iya tashi ba saboda halin da jikins ke ciki a hakan ya kokarta ya tattara dan raagowar numfashinsa sai dai duk da haka hakin be rabu da shi ba ban da ina tsoron ubaagiji d hиmа Кокаrin sauke nauyin da ya dora min da ra dai-daita kin a yi miki mugun baki kin bi duniya ko na huti daga wannan kunci da kika sanya mu to na riga na san b wani alfanu a tattare da hakan abu daya zan ce miki shi ne duk abin dabawa ya yi me kyau ko a kasin haka shi zai girba tin daga nan duniya har zuwa ranar gobe kiyama. Don Allah Abba.... Ya katse ta ya isa bana son duk wani furucinki na gode Hanifa. Da fadin haka ya mai da kai ya kwanta ko ki tashi ki ba ni waje ko kuma ina iwa tar miki da duk abin da zucivata ta rayan, ba shiri ta mike tana shawara da zuciyarta ta koma ta zauna saboda larurar mahaifitana Abin nufi ta hakura da muhimmin abin dake gabanta kenan. Amma kuma in tai haka ba ta kyauta wa masoyina ba. Bayan ta san tsawon watani suna shirye-shariyen wannan tafiya wato yawon bude ido ko kuma mu ce yawon shan iska domin more rayuwarsu, me kama dai

Chapter 3 of 7