Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 7
ta leko ai yana ganin ta ita ma ya dire mata tare da neman tainakonta. Da kyar da sidin goshi suka lallaba shi ya tafi tare da alkawarin za a kawo mishi Hanifa har gida. Motar da ya zo da ita ma ba su bari ya tuka ta ba dan sun fuskanci ba a hayyacinsa yake ba. Yana isa gida ya iske Abbanshi tare da mama wanda daman suke zaman jiran ko ta kwana, aiko ya rushe musu da kuka yana zantuttuka tamkar tabab6e. Cikin kuka ya ce, Abba kuna gani wani ya kwacen Hanifa to wallahi ba zan iya rayuwa ba mutukar babu ita, da na san haka zan zo in tarar da ban tafi karo karatun ba. Abba duk kai ka janyo da ka katse min duk wata alaka da ke tsakaninmu da hakan ba ta faru ba. Mama ce ta daka masa tsawa kai ya isa ba ma son sakarci a kan mace za ka zo kana gayawa mahaifinka magana dan shirmen banza, daman can Allah be yi 58 matarka ba ce amma da ko shekara nawa ka yi in matarka ce za ka zo ka tarar da ita. Abba ya ce ba fada za ki yi mishi ba lallashinsa za ki yi. Ya dube shi ka yi hakuri ban yi haka dan na raba ku ba ilal dan ka mai da hankali ka yi karatui wallahi mukan mu mun ji zancen auren ne kamar daga sama lokacin kwanaki biyu ya rage a yi auren, dan haka muka mai da lamarin ga Rabbil Izzati, domin mun san daman Allah be kadartomatarka ba ce, ga mahaifiyarka nan ita ce sheda. Haka dai suka din ga lallashinsa gami da ba shi baki anma a gurinsa duk a banza, tuni tunaninsa ya tafi ta hanyar da zai bi ya kwato masoyiyasa ko ta halin kika ne. abincin da aka tanadar masa ko ta kansu be bi ba duk da matsananciyar yunwar da yake ji ya kulle kansa a daki ya rasa abin da ke masa dadi ina ma a ce be dawo ba ya tarar da wannan bakin labarin haka yake ayyanawa ransa. Kwana biyu ya yi yana zaune a gida babu inda ya je shi dai ga shi nan ne kawai nan da nan ya fita hayaycinsa don ko bacci ba ya iya yi a daran kwana na-uku ne ya kasa zaune ya kasa kwance so da kaunar Hanifa shi ke amsa murkususu a zuciya ya baza hotunanta yana kallo tun yana kukan zuci har ya fito fili yana yi tare da bubbuga hannunsa a bango. Misalin karfe ukun dare Alh. Khalil da mama suka dinga jiyo sautin kuka a dakin Mas'ud cikin hanzari suka isa suka iske shi ya kifa kai yana kuik kashirban ba sai an gaya musu e dalilin kukan ba ko dan ganin hotunanta da ke zube suka tsuguna daf da shi suna aikin lallashinsa a da sun yi fushi da shi ne sun kyale shi ganin sun mishi nasiha ya hakura ya rungumi kaddara ya ki amma yanzu suna ganini abin ya wuce wasa, dan da alama nema yake ya zauta da kansa a kank soyayyar mace. Kwana suka yi a kansa suna 59 lallashinsa tard:da tottofe shi da addu'a har suka samu ya yi bacci. Tun bayan tawowarnmaslduadanga gidan Malam Sa'ad Malam damatarsa Umma suka shiga damwua ganin halinda dan mutane ya shiga har dai a kwana na hudu Malam ya yanke shawarar zuwa gidansu lokacin da ya isa gidan ya tarar da Alh. Khalil suka gaisa cikin karamci daga bisani ya gangaro zuwa abin daya kawo shi. Abin da ya ji daga bakin Alh. Khalil bai mishi dadi ba domin ya tabatar mishi tunr anar da Mas'ud ya dira kasar ya fita hayyacinsa sun dade suna tattauanwa daga bisani suka zarce dakin Mas'ud halin da suka tarar da shi kam abin ya girgiza Malam Sa'ad. Ya shiga lallashinsa gami da yi mishi nasiha amma a banza, shi kam abu daya yake bukata shi ne ya mallaki Hanifansa ko ta halin kaka a duk lokacin da Malam ya zo yakan roke shi ya raba auran 'yar tasa ya zo ya aura masa ta, shi kam ya san ba abu ne me yiwuwa ba ko a Musulunci ma be halatta ba. abu ku lum sai gaba yake yi sai sam batu yake yi kamar taba6be da dai suka ga haka sai suka sa a ka dinga yi masa saukar Alkur'ani mai girma. gami da addu'a kusan kullum Malam yakan zo duba shi gaını da yi mishi nasiha har dai Allah ya ganar da shi ya hakura ya fauwala Ubangiji, iyayansa sun ji dadin hakan. Suka yi mishi alkawarin duk yarinyar da ya ga ta yi masa ya zo ya fada za su nema masa aurenta. Cikin dan kankanin lokaci ya mai da ramarshi komai nashi ya koma normal illa har yanzu radadin kaunar Hanifa na zuciyarsa ne sai dai yakan yi kokarin kawar da ita tunda ya san ta yi 60 mishi nisa, shi da ita kam sai dai gaisuwar mutumci, kai in dan ta shi ne ma sai ya ce kar Allah ya kara hada su har karshen rayuwarsa. shikansa ya san duk ranar da Allah ya hada su be san yadda zai yi ba, shin wane hali zai tsinci kansa ya ga matar da ya fi so fiye da komai a matsayin mallakin wani. Tun bayan barin Mas'ud gida Najeriya ya kasa mai da hankallinsa kan abin da ya kai shi so da kauna gami da tunanin abar kaunarsa Hanifa ya sa shi kasa maid a hankali ya yi karatu, karatun nasa sai ya zama rabi da rabi a yawancin lokuta lokacin da y kamata a се yana karatu amma sai ka iske shi makale da waya suna ganawa da sahibarsa, ko kuma ya baje hotunanta ya tsudnuam cikin tunaninta gami da ayyanawa ransa irin kasaitacciyar soyayar da za su yi da zarar sun yi aure. Abokananshi sun sha yi mishi fadan ya mai da hankali wajen karatui amma a banza, ai ko shekara na zagayowa ya samu mummunan kayi shi da kansa be yi mamakin hakan ba be kuma wani damu sosai ba sai mna farin ciki dayake yi ai dawo ya ga abar kaunarsa duk da sanın makudan kudin da mahaifinshi ke kashewa a kan karatun, tunaninsa ya sauya ne lokacin da Abbansa ya samun labarin abin da ya faru. Ransa ya yi mummunan baci saboda tuni sun gama shiryawa da abokanansa tare da hadin gwiwar kamfanin Honda da ke Kasar Japan za su bude Branch na kamfanin za su dinga shigo da Spare parts 61 A nan gida Najeriya idna za a dinga hada su a kamfanin. Mas'ud na cikin jerin mutanen da za su ci gajiyar abin ta hanyar samun mukami me girma mutukar ya fito da kyakyawan sakamako yadda ake bukata ko kadan Alh. Khalil be taba zaton zai ba shi kunya ba ya san ya yarda da hazikancin dan nasa sai ga shi ya yi mishi ba zata abin da ka iya sa ya rasa wannan babban matsayi. Hankalin Alh. Khalil ya tashi ya yi wa dan nasa fata-fata saboda zaton ko ya tsaya shashanci ne ya sa shi samun wannan mummunan kayi. daga bisani ne ya samu labarin abin da ya sa shi kasa mai da hankali ya yi karatu. Take ya buga mishi waya ya sanar da shi ya san halin da yake ciki tare da alkawarin mtuukar ya Kara saurarar Hanifa ko ya bugomata waya be yafe masa ba. da sharadin sai ya kammala karatunsa sa ci gaba da gudanar da soyayyarsu. Kai dokar ta yi kamari har ta kai da ya shafi duk wani wanda yake mu'amala da shi hatta da gidansu sai da ya katse duk wata alaka dake tsakani, fatanshi ya tsaya ya vi karatu ya samu abin da ake bukata in ba haka ba yana ji yana gani damar za ta subuce masa inda Allah ya taimake shi ma an fage bude kamfanin zuwa shekara me zuwa saboda wasu dalilai. Wannan dalili shi ne musababbin katse duk wata alaka da ke tsaknain Mas'ud da Hanifa, duk da haka yana rike da alkawarin da ke tsakaninsu har dai zuwa ranar da ya kammala karatunsu da gagarimar nasara shi kansa be yi zaton zai samu good result haka bal. Allah62 Allah yake ya dawo ya nunawa mahaifinshi sakamakon don ya san zai yi farin ciki tare da fatan mallaka mishi abar kaunarshi. Kwatsam kuma sai ya dawo ya tarar da wannan mummunan labari da ba zai taba mancewa ba. An bude kamfani cikin nasara Mas'ud shi nc a mataki na uku a duk fadin kamfanin. Cikin fan kankanin lokaci ya dukufa aiki ba dare ba rana. Nan da nan suka soma samun ci gaba sannu a hankali kamfanin na karbuwa. Babu wanda ya fi farin ciki irin Alh. Khalil da man kokadna ba ya jin danshi wajen dagewa da juriya gami da kwatanta gaskiya da rikon amana. Fatansa daya ya fito da mata ya yi aure ko ya zama cikakken mutum. A bangaren Mas'ud shi ma muna iya cewa yana jin dadin yadda yake gudanar da iakinsa babu abin da ya sa a gaba irin aikinsa wannan ya sa duk ya kawar da wani tuani da kunci dake zuciyarsa. Ranar alhamis biyar ga wtan takwas na shekara ta dubu biyu da biyu ranar da ta zamantotushenf aruwar mummunar rayuwar da masoyan suka tsinci kansu a ciki da misalin karfe biyar na yamma Mas'ud ya hade cikin coat ruwan makuba wace ta yi masifar yi masa kyau da ka gan shi ka ga matashi me ji da kansa ya isa makarantar F.C.E. don ziyarar wani abokinshi da suka yi karatu tare tun farkon dawowarsa yake so ya ziyarce shi Allah bai yi ba sai a yau. Ya dade a harabar makarantar yana nazarin wanda zai samu ya tambayi inda abokin nashi yake. Yana ankare da yadda yammata ke kai kawo ta gabanshi suna karairaya tuni kuma ya gano manufarsu. 63 amna shi ko a jikinsa dan ba a gabansa suke ba, kamar ane daga kanka ya hango ta zaune a gindin wata ısya kanta na sunkuye tana nazarinwa su littattafa. Tana sanye da wani danyen voil, jikinta rufe da wani yalwataccen mayafi duk da fuskarta na sunkuye hakan be sa ya kasa sheda ta ba. Shi dai be san yadda aka yi ba ya samu kansa ne a tsaye a kanta ya fan jima yana kallon ta har daga bisani jikinta ya ba ta akwai mutum a kanta. Dagowar da za ta yi ba sai ta yi arba da fuskar mutumin da ta fidda ran sake ganinsa ba. Ta saki baki galala cike da mamaki shi ma din kallon mamaki yake mata sun dade a haka sannan ya yi karfin hali ya ce, "Hanifa." Cikin raunananniyar murya. Ta dan bude baki za ta yi magana sai ta fasa ta runtse idonta gami da ciek baki ya kara matsowa daf da ita yana kiran sunanta ta bude ido tana kallon shi kawai hawaye na zubo mata. Kome kuma ta tuan sai ta yi zumbur ta mike gami da kwasar littattafanta har tana zubar da wani ta yi saurin barin wajen ganin haka shi ma ya bi ta yana kiran ta sai da suka dangane da bakin titin Kabuga sannan ta tsaya. Tana ganin mota ta tsaya ta shiga ba,tare da ta sanar da me tasin inda za ta ba. Yana tambyar inda za ta ta ce mu je zuwa, shi ko da ya fita ya tashi motar har suka kai junction din Tal'udu ba ta san idna kanta yake ba shi ko dan tasi mikewa yake kamar yadda ta umarta sai da suka kai ga karshen titin daf da kasuwar kwari ke nan sannan ta farga da inda suke. Ta uamrce shi ya karya kwana zuwa Nassarawa G.R.A. kan titin Sultan. 64 Tana isa gida daki ta shige ta kulle kanta don ba ta bukatar hayaniya ta fada gado ita dai sai ji ta yi tana kuka har da shessheka ta kasa tantance dalilin da ya sa ta kuka, nan da nan zazzabi ya rufe ta lokacin da Abdulzahir ya dawo gida ya tarar da ita-cikinw annan hali take ya rude ya shiga tarairayarta yadda ya saba duk da kin amincewar da ta yi sai da ya kai ta asibiti cikin daran haka ya kwana yana jinyarta, ko kadna ba ya kaunar duk waniabu da zai taba masa mata. Ga- Hanifa ko kwana ta yi cike da tunani barkatai, ta yi da ka ce ma ba ta je school a ranar ba ballantana ta ga abin da zai tayar mata da hankali, kai hasali ma ba ta taba sanin Mas'ud ya dawo ba ballantana ta sa ran ganin shi. A bangaren Mas'ud kuwa yadda ya natsa a bakin titi yana me mamakin abin da ta yi masa sai kuma daga baya ya tuna ashe fa wai tana da aure ba ya raba dayan biyu dalilind a ya sa ta yi amsa haka ke nan. Ya juya a sanyaye sai kumak kunyar mutane ta kama shi ganin yadda suka zubo masa namujiya kai shi yana iya cewa ma bai sna yadda-aka yi ya biyo ta har bakin titi ba duk da tazarar da ke tsakani daga cikin makarantar zuwa bakin titin haka dai ya Karasa ya dauki motarsa batare da ya tuna makasudin zuwansa makarantar ba. Misalin karfe biyui na dare ya kasa bacci idanunsa a bude suke ko ko a rufe ne abu daya suke gane masa wato Hanifa. Ya dinga tunano rayuwar da uska yi a baya da ke nan ta zama rabon wani ashe daman ba kaunarsa take ba kilama tuni ita ta mance da shi kai shi 65 Σ ma gwada ya mance da ita ya shafe ta daga babin rayuwarsa gaba daya. Me zai da mayaudari kokari yake ya cire ta a ransa amma ina zuciyarsa ta kasa yarda da hakan. Yana ganin har abada ba zai iya daina son ta ba. ya dinga tunano yadda ya ga ta kara kyau ta zama cikakkiyar mace ko da can ba baya ba ce ballantana yanzu da take cikin hutu ya dinga tunano kyakyawan jikinta shi ke nan ya zama rabon wani. "Kai ina impossible." Ya fada da karfi a yayin daya mike yana zagaye dakinsa kuma ya jingina da bango ya rufe idanunsa yana kiyasta irin rayuwar jin dadin da za su gudanar da zarar ya mallake ta. "Kai ko ta halin kaka Hanifa sai ta dawo gare ni, ni ne nake son ta nake kaunarta nake son duk wani abu da take kauna." Ya debo hotunanta yabaje yana kallo sai ta dinga yimishi gizo yana ganin akmar ita e sai ya je gare ta sai kuma ya ji ba ita ba ce zuciyarshi ta ci gaba da azalzalarshi da Kaunar Hanifa tare da kwadaita mishi ni'iamr dake gare ta ya kudure ko ta wace hanya ce sai ya malalke ta. ZUCIYA BA TA DA KASHI, Ubangiji ka fisshe mu sharrin zukatanmu, domin shi kam ya kasa daurewa zuciyarsa abin da take so take kuma angiza shi. Shi ne yake kusantar shi. Kashegari ya nufi F.C.E. dai-dai idna ya gan ta na nan ya nfua amma ko me kama da ita be gani ba. ya dade yana gararambar neman ta duk wanda ya tambaya sai ya ce be san ta ba daman ga ta ba gwanar shiga jama'a ba. ya dau tsawon lokaci a school dini amma be same ta ba 66 haka ya dinga yi har tsawon kwana uku. A kwana na ukun ne ya tuna da abokisna Isma'il wanda a dalilin zuwa wajenshi ne ya gnao abin da ya dagula masa lissafi tare da taimakon wani Malami ya sada shi da inda yake Ya iske shi a office dinsa Isma`il ya yi farin ciki da ganin abokinsa, suka rungume juna cike da farini ciki. Bayan tsawon lokaci da suka dauka suna hira isma'il ya fuskanci abokin nasa ya dulmiya wata duniya ya dan daki kafafarsa ya ce, Kai fa tsiyata da kai ke nan, da ka zauna ba ka da wani aikin yi sai tunanin wa ta ke ne? Halima ko Hanifa? Mas'ud ya dago kai cikin mamaki ya a ka yi ka ganc? Ka mance zaman mu na Japan ke nan? Shin ba ni nake maka fadan ka rage tunanin ta ba? ka mai da kai ga abin da ya kawo ka? Shin akwai wanda zai zauna da kai na tsaown awa daya ma ba tare da ya sa matsayinta a zuciyarka ba. Ka san ko yanzu ma ita na zo nema. Ban gane ba, kana nufin Hanifan? Ita fa. Me ya sa ba za ka je gida ka same ta ba? ka san wasu matan ba su cika son saurayi ya zo wurinsu a school ba. Mas'ud ya yi shiru yana nazarin amsar da zai ba shi ya san tsattsauran ra'ayinsa da arar ya ji a halin yanzu tana da aure ba zai ba shi goyon baya ba, dan haka ya dora shi da cewa sun dan samu sabani ne ko ya je gidan ba za ta fito ba. ya dinga kwatata mishi ita har dai Allah ya sa ya gane ta. An ci sa'a yana daukarsu darasin turanci ya yi mamaki don be taba tsammanin ita ce Hanifan da abokinshi ya mato mata ba. Ya kuma yaba da 67 zaðin abokin nashi don a ko yaushe za ka gan ta cikin shiga ta kammala ga ta da hazaka wajen karatu shi a da va yi tsammanin tana da aure, saboda tsabar kamewarta a nan ya tabbatar masa kwananta uku rabon da ya ga ta zo school. Ya karbi nambar wayarshi da zarar ta zo zai sanar da shi. A gida yake a office ne kai a ko ina ne Hanifa ke zuciyarshi a ko yasuhe fatansa ya sake sanya ta a idanunsa ko zuciyarsa ta yi relief daga azalzalarsa da take yi kullum ya je school fin sai Isma'il ya ce ba ta zo ba har yake shawartarsa ya jarrabawa zuwa gidan nasu ko za ta fito shi dai ya amsa da to, saboda idanshi ya rufe da wutar begenta har ya fara tuannin bin shawararsa. Cikin dabara ya samu su Nusaiba a school dinsu ya nuna kamar ya zo duba su ne ya dinga jan su da hira har ya samu abinda yake son ji ba tare da sun fahimci komai ba. Be sha wahala ba wajen gane gidan haka zai zauna na tsawon awanni yana jiran ya ga fitowarta har dai ran nan Allah ya sa ya dace ya hango ta gilashin mtar da take ciki hannutan rike da wani dan karamin yaro gefenta wani kyakyawan mutum ne wanda ya tabbatar mijinta ne. da alama unguwa za su. Ta gefensa suka zo suka shige ba tare da ta gan. shi ba. wani masifaffen kishi ya turnuke shi sai dai a wani bangaren zuciyarshi ta yi sanyi tun da ta ga abin da take bege. Sai da akai sati guda cur da haduwarsu sannan Hanifa ta fra zuwa makaranta ba wani abu da take zulumi ilal nna gudun ta kara haduwa da Mas'ud, tana 68 tsoron zuciyarta don a wannan kwanakin da ta yi fiye da rabinsu ya ta`allaka a kan tunkanin tsohon masoyinita. duk da kokarin da take na ta yakice shi ko kadan ba ta fatan sake ganinshi. Abin da take gudun kuwa shi ya faru, ko cikakken sa'a daya ba ta yi da zuwa makarantar ba suna tarc da Huwailat aka aiko kiranta daga office dini Lecturer dinsu me daukarsu darasin turanci. Ammaki ya kama ta amma da ta tuna Malaminta ne kila wani abin ne ya faru dangane da harkar karatunta ta dada suturce jikinta sannan ta isa office din. Mamaki ya kama ta ganin wanda ta tarar a tare da Malaminsu. Ta dada daure fuska ta gaida shi tare da cewa Malam an ce kana kira na? Isma'il ya dan yi murmushi kwarai ni na aika a kirawo ki amma ga me son ganin naki nan. Ya sa kai ya fita dan ya ba su waje. Ta bi Malamin da kallo, a da yana daya daga cikin Malaman da take ganin kimarsu saboda kamewarsa amma a yau kam ya zub da duk wata kima da take zaton yana da ita, in banda rashin mutumci me zai sa tana da aure ya kirawo gurin wani ko ko me ya dauke ta ne? Mas'ud ya dan gyara murya ya ce, "Ki zauna man Hanifa." Ta juyo da fuskarta gami da galla mishi wata harara ta nuno shi da yatsa, Ka ga Malam ka fita hanya ta ko ba ka san da igiyar wani a kaina ba? ko kana tsammanin ni 'yar iska ce? Ya ce haba Hanifa ni kike gayawa wannan maganar, ki yi min alfarma daya ki saurari abin da zan gaya miki....." be karasa ba ta katse shi a hasale, me zan ji daga gare ka yaudara ko sabа 69 alkawari? To ka ga ka fita hanyata ka gane ko? Ta fice abinta shi ko ya bi taa kallo ya kasa yin katabus jikinsa ya yi sanyi wai yau Hanifanshi ke yi mishi haka. Abhinda ya fi ba shi mamaki kalamanta na karshe in har shi be ce mata ta karya alkawari gami da yaudararsa ba ai ko be kamata ita ta ce masa haka ba. Ya kifa kai a table din dake gabansa sai kawai ya samu kansa da zub da hawayc. A kan mace ya zub da hawaye sau ba a dadi lallai ya kamata mu kira shi da ragon maza. Kai haka dai ya dinga nacin kiranta har na tsawon kwanaki amma sam ta ki zuwa da abin ya ishe shi ya tafi har department dinsu ya yi sa'ar ya tarar da ita a gindin bishiyar da ya fara ganinta wąnnan karon ma ita kadai ce tana dago fuskarta ta yi arba da shi tsaye a kanta ai ko ta tsora ta jikinta har dan rawa yake yi ba dan komai ba sai dan yanzun nan ta fito daga hall. Bayan sun gama daukar darasi saboda irin habaice-habaicen da Zakiyya ke mata ya sa ta fitowa ko kadan ba ta son ta biye mata ko dan darajar yayanta amma da ba dan haka ba da kullum sai sun yi fada, ita kam ta rasa dalilin wannan kiyayya da take gwada mata, abin tsautsayi yanzu kuma a ce ta zo ta gan ta da wani namijin ai kuma sai abin da ta kitsa mata. Cikin sanyayiyar muryarshi ya ce, "Hanifa ni kike wa haka ko? Yau ni kike gudu ko? Kin mance da kaunar da ke tsakaninmu?" cikint soro ta ce, "Dan Allah ka yi hakuri ka rabu da ni na gaya maka ina da aure." Ya ji wani abu ya tokare mi shi zuciya, ko kadan ba ya so ya ji wannan kalmar ta fito daga bakinta. Cikin fushi ya danki 70 hannunta ba ya tunanin jama'ar da ke kai kawo a wajen ya ce ko ki bi ni mu je office din isma'il ko kuma mu yi ta zama har wanann dan iskan mijin naki ya zo ya tarar da mu a haka don na san abin da kike tsoro ke nan ko? Gaba daya ta gama kaduwa babu abin da take tsoro irin Zakiyya ta leko ko ta fito ta gan su a haka ba tare da wata shawara ba ta bi shi. Suna shiga offic din ya tura kofar ya saki hannuta ya kifa kansa a bango yana fidda wani irin nishi ita kuma tana tsuguen ta kfia kai a kan gwiwarta tana kuka. Sun dade a haka sannan ya zo ya tsuguna daf da ita ya sa hannu ya dago fuskarta tana kokarin kwacewa ya rike hannayenta ya yi zaman dirshan a gabanta ya dora kanta a kan kafadunsa kana ya dora fuskarsa a kan bayanta, ta ji wani abu yarr ya ratsa jini da tsoka hade da gangar jikinta haka kawai sai ta samu kanta da kasa janyewa daga gare shi sai ma wani sabon kuka da ta saka. Sun dade a haka sannan ya dago fuskarta ya sa handkerchief ya goge mata hawayen da ya 6ata mata fuska. Ya rike mat ahannu gam ya fara magana а sanyaye. "Hanifa me ya sa za ki yi min haka? me ya sa za ki auri wani ba ni ba? kin san iriin matsananciyar Kaunar da nake mik? Ke kanki na san ni kadia kike so to me ya a za ki auri wani bani ba wallahi ba zan iya rayuwa ba tare da ke ba, ke kanki kin san da haka shin ina alkawarin damuka yi wa juna." Ya dada kankame hannayenta. Ita kanta jikinta ya yi sanyi ta kasa aiwatar da komai hakika abin da ya fada gaskiya ne shi kadai take so duk wanda za ta so a bayanta yake to amma ya za ta yi? Ya kara cewa, kin yi shiru ko kin daina sona ne? anya kuwa daman can kina yi min pure love? Wallahi in har ba kya kaunata gwanda mutuwata da wannan rayuwa. Ta sa hannu ta toshe masa baki hade da girgiza masa kai muryarta na rawa ta ce, "Mas'ud ka san ina son ka ian Kaunarka illa wani lamari da Ulbangiji ya aartar a kanmu. Ka yi ahkuri wallahi har abada ba zan daina son ka ba, amıma yanzu ka ga ba yanda zan yi tun da da aur....."Ba ta Karasa ba ya katse ta, "Ba na son wannan maganar, ki dai je ki yi nazari ki samo mana mafita na ba ki daga nan zuwa kwana biyu. Tana komawa gida ta tarar da Abdulzahir har ya dawo. Ta dauke kai kamar ba ta gan shi ba. gaba daya haushinsa take ji domin shi ne y ai musu katanga tsakaninta da mutumin da ta fi kauna fiye da kowa, shi kansa ya lura da sauyi da ya gani a tare da ita, da ya tamlbaye ta dalili sai ta ce kanta ke ciwo ai ko ya shiga tarairayarta kamar yadda ya saba be san gaba daya haushinsa take ji ba. Misalin karfe daya na dare wayarta ta yi kara, ta duba ta ga ba ta san nambar ba kamar kar ta dauak ai dai ta danna cikin muryar me yin bacci ta ce, "Hello, hello waye.?" A daya bangaran aka amsa da cewa, "bacci kike ko Hanifa? Ni ko ga shi tuanninki ya hana ni sakat." Ai da jin mruayr ta shaida Mas'ud ne take ta dan yi kara saboda tsoro dan suna kwance ne tare da Abdulzahir

Chapter 5 of 7