Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 7
kayatacciyar kwålliya ta yi ba taa salalma da mahaifiyarta umma za ta shiga makota a yi mata kitso sai ta jiwani yaro ya shigo ya ce ana sallamá da ita, abin ya ba ta mamaki ita ba zance take yi ba hasali ma babu namijin da take saurara tun da ta san mutukar Malam ya amince da nutsuwarsa zai ba shi iznin ya fito ne ita kuma abin da ta tsana ke nan saboda burinta na yin ilmi me zurli wannan dalili yasa ta kin saurarar kowa duk da ta san karatun da take yi ma ba a son ran mahaifinta ne, tana iya cewa Allah ne kadai ya kadarto za ta yi amıma ban da haka da tuni tana dakinta Kila ma da tarin 'ya'ya kamar yadda ya faruda sauran 'yan uwanta. U'mma ta ce ana miki magana kin tsaya sororo da ke ki sallami yaron mutane. Ba tare da ta kalli mahaifiyarta ba ta ce ka ce ba ta fita zance. Umna ta tabe baki gami da harararta daman tasan amsar da za la bayar ke nan ita kam abin yana damunta yarinya kamar wannan a ce har yanzu ba ta saurarar samari a ko da yaush tana shakkun dangane da al'amarin tata, ta kan yi 16 yar zaotn ko aljani ne ya auri 'yar tata da ba ta son saurarar samari. Hanifa na kula da kallon daumman ta yi mata ta yi sauri ta shige dakinta kitson ma ta ce ta fasa dan kar ta fita ta hadu da me sallamar. Ta kara jiyo maganar yaron yana cewa wai dan Allah ta daure ta je mutumin da ya dauko ta daga bata ne ran nan ya zo ya duba ta ne. ai da sauri ta fito daga dakin ta zari takalımi har ta kai ga bakin sro ta ji Umma na cewa ke kanki daya kuwa?" ta tsaya sooro sai kuma ta kalli kanta a nan ta gane ba mayafi a jikinta. Ta yi saurin koma wa ciki Kannanta Nasiba da Nusaiba hade da Umma suna yi mata dariya. Ta dade a dakin sannan ta leko ta ce Umma dan Allah ki bawa Nasiba ta kai mishi tabarma. Wa fa? Wanda yake salama. Da wa? Kai umma wallahi kin gane. Cikin jin dadi ta ce to ai na san halinki ne na sani ko ba za ki fita ba nan da nan ta sa a ka kai masa sbauwar tabarma hade da ruwan sanyi a sabon kwanun sha. Ba ta bukatar saya kaya sai 'yar kwaskwarima da ta dada yi ta yafa yelon mayafi sai da ta fakaici idon Umma sannan ta fita saboda kunya da take ji. Ta isa soron ta ga ba kowa sai ta dan leka waje ta hango shi ya jingina damota sai tai ciki yana ganin ta ya biyo bayanta. Ta dan rakuße geffe daya ta gaishe shi cikin nutsuwa. Ya amsa cikin sakin fuska ya ce, yaya mun same ku lafiya?" ta ce lafiya lau. Ya ce kin ji ni shiru ko wallahi tun ranar da muka rabu Abbana ya aike ni Abuja sai a daran jiya na dawo, na so na zo tun a jiyan sai na ga dare ya yi, ina fatan ban yi lefi ba. kanta na sunkuye ta ce, Laifin me? Haka za ki ce ashe ke ba ki yi kewata ba, ni ina can ian ta tunaninki ashe ke tuni ma kin mance da ni ko? ta girgiza 17 kai haka ne man ga shi ko sunana ba ki nemi ki sani ba, ni da na damu da ke ai tuni na nemi sanin sunan naki. Ta ce to ka yi hakuri ka gaya min sunan naka. Sai da na roka Pl;ease a gafarce ni ya dnayi murmushi ya ce sunarа Mas'ud Khalil ina zaune a unguwar gadon kaya ina fatan kin ganc? Ta ce, E ya ce kin san wani abu? Ta girgiza ka mamana da kannena duk sun ce a gaishe ki. Ta zaro ido ina suka snani har za su ce a gaishe ni? Ya yi murmush kina shakka ne? to ai gani na yi ba su sanni ba. Ya girgiza kai lallai ba ki san irin matsayin da kike da shi a zuciyalą ba wallahi tun ranar da na gan ki na sanar da su ai ni na samu matar aure. Gaba dayansu ba ki ga yadda suka y farin ciki ba musamman kanwata Fauziyya dan wallah kuna yanayi da ita haske kawai za ta nuna miki ke kuma k fita tsayi ashekaru ma na san za ku yi sa'annin juna ton dai kin ji abin da ke zuciyata kauna ce nake miki tsakani d Allah yaya naki ra'ayin yake a game da ni.?" Ta yi shiru ba ta ce komai ba ya kara tambayar ita dai ta rasa amsar da za ta ba shi domin wannan dabas yake da sauran samarinta, kai da dukanin wani namiji m (amma fa a wajenta) tun farkon ganin ta da shi ta ji ya tsay mata a zuciya tana son sa tana kaunarsa yadda baii za misaltu ba abin da ba ta taba ato ba wato soyayar wani d namiji a zuciyarta a kusa haka a yadda ta tsarawa zuciyanu sai ta kammala karatunta ta zama cikakkiyar Malama makaranta sai ga shi ta tsinci kanta dumu-dumu cika Kaunarsa. Ya ce ba ki ce komai ba. Kanta na sunkuye ta ce ka ba ni lokaci tukum. Bali amince ba ke nan? A'a ni dai kai min wannan alfarmar. Y ce to shi ke nan yaushe kike ganin zan dawo? Ta da 18 fuskarta ai ni ba na zance. Kamar yaya fa? Ina nufin Malam ba ya barin mu fita ba tare da an nemi izininsa ba. ban fahimta ba fa, ina nufin sai ka nemi izinin Malam idan ya amince shi ke nkan ko yaushe ka iya zuwa. Ya yi murmushi shi ke nan in dan wannan ne ba matsala hakan kuma ya dada taabtar min na yi dacen kamialrm ace 'yar manyan mutane, ko shari'a ma ta yarda ka fara neman iznin mahaifin yarinya tukun. Yawancin hirar shi yake yi ya fuskanci har yanzu ta ki sakin jiki da shi ya bkuaci zai tafi ya miko mata rafar naira hamsin (5,00) amma ta ki karba ya dauka irin abin nan ne na Malam Bahaushe amma sai ya a da gaske take, ba yanda bai yi ta karba ba ta ki da ya bukaci sanin dalili sai ta nuna amsa mahaifitna zai yi fada. Bai dada yin mamaki ba sai da ya sa a ka kirawo Kannanta su Nusaiba ya ba su nasu kudin amma fafur suka ki karba, dole ya hakura ya tafi yana tunanin irin kyakkyawar tarbiyyar da yaran suka samu. Kamar aydda al'adar gidan Malam Sa'ad take mutukar kana nemar 'yarsa sai ka fara neman izininsa shi kuma zai yi bincike a kanka da ma iyayenka in ya ga mutanen kwarai ne shi ke nan ya ba ka izini in ya samu akasin haka ya kan fito karara ya ba ka hakuri ka nemi wata. Jama'a da dama na yaba halayyar Malam Sa'ad da ma na iyalansa. A daran ranar wakilan Mas'ud suka zo nemaawa dansu izninf ara neman auren 'y arsa. Malam ya yi farin ciki da hakan bayan ya yi dogon bincike dangane da Mas'ud da iyayansa ya tabbatar mutanen kwarai ne ya ba su izini. Bayan kwana uku Mas'ud da yammacin ranar asabar ya dira gidansu Hanifa bayan tsawon mintuna ta fito 19 sanye cikin ghana Wax ta lillibe kanta da wani dan yalolon mayafi ta gaishe shi a kunya ce kamar yadad ta saba tambaye ta mutanen gida tare da isar da sakon Mamans da kannanshi a cikin gida kuma Umna ta bayar da kunu zazi me sanyi hade da gashasshen kifi a kawo masa. Yara suka gaishe shi cikin ladabi ya dinga jan su da hira gami yi musu tambayoyi dangane da karatunsu ya gamsu da fahimtarsu daga bisani suka mike za su tafi ya su gaishe Umına. Ya miko musu leda cike da kayan zaki suka karba zanebensu daya Malam ko Umma za su yi fada sh kuma da ya fi su sai ya ce ai yanzu mun zama daya ni m ai yayanku ne tun da zan auri yayarku kun ga Malam ba za yi fada ba tund a ya san ni ma fansa ne sannans uka karba Bayan fieewarsu ta ce ka sha kunun mana. Ya co wane kunu ban ji matsayina ba gurin Princess. Taу murmushi sunan da ka sa min ke nan? Ayce kwarai kuw domin ke ce gim iya sarauniyar zuciyata. Ke ce dai ha yanzu ban san abind a ke zuciyarki ba dan haka ke nak jira. Ta dna yi jum saboda nauyinsa da take ji da kyar dai daure ta ce ni mana amince kin amince da me?" sai ta kal shi ki fada man. Dakyar dai ta cije kunayrta ta fada amince da kaunarsa a zuciyarta. Ya skai wani gwauron nufinashi gami da godiya Ubangiji har ya ba ta dariya ya ce, dariya ma kike min ki san Allah tun daga ranar da na bar nan ba na cikin nutsuw ina ta zulumina msar da za ki ba ni ina tunanin in na samu akasin hakan ban san yanda zan sa raina ba, ke kila ma zautu saboda kaunarki. Ta ce, da da ba ka ganni ba fa? D ban gan ki ba kika ce kin ga kin ba wa kanki amsa ke nau yanzu kam tun ranar da Allah ya fora idona akanki Allab 20 па ya dora min so da kaunarki a zuciyata. Ya ci gaba da bayyana mata irin kaunar da yake mata har dai magariba ta kawo kai suka yisallama tare da alkawarin zai kawo mata Kanwarsa. Tana isa gida yabayar da kaya ak awo mata ya yi saurin tashin motarsa dan kar ma a daow masa da shi. Ta kaiwa umma kayan suka duba suka ga cosmeties ne hade da kayan zaki sai wata 'yar guntuwar takarda da ya yi rubutu kamar haka. My Princess, "Da fatan kin isa gida lafiya ga kaya nan babu yawa ki yi hakuri abinka da students ki gaishe min da Umma da Malam.. Your Husband M. KHalil Da Malam ya zo a ka nuna masa kayan sai da ya yi fadan me ya sa ta karba ya gargade ta kar ta kara karba ta rike mutuncinta a karshe ya sanyawa kayan albarka. Da dai ta ga komai ya kankama sai ta zayyanewa Kawarta kuma aminiayrta Huwailat bayan shegantakar da ta yi mata a karshe ta sawa lamarin albarka. Kamar yadda ya yi mata alkawari ya kawo mata Kanwarsa Fauziyya yarinya me hankali da nutsuwa, hakika ta yaba da zabin da yayanta ya yi ta kuma yaba da hankalinta da karamcinta ta tabatar da maganar yayanta da ya ce suna kama da ita ga shi kusan tsararta ce dangane da karatu ma duk suna mataki daya wato form five nan da nan suka zama kawayen juna kusan duk karshen week Fauziyya na hanyar zuwa gidansu Hanifa ita ce dai ba ta 21 taba zuwa ba a dalilin gidan surukanta ne. Kawarta ta yarda da uzurin nata. Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah har ta kai sun samu kimanin watanni shida da haduwarsu a dan tsukin wannan lokacin sun dafa fahimtar juna sun shaku kwarai da gaske kowanne na kokarin nunawa dan uwansa Kaunar da yake masa duk wanda ya kalli yadda suke gudanar da soyayarsu dole su burge ka cikin hankali da n utsuwa ba tare da sun kaucewa Ubangiji ba. Tun tana far-dar da shi ganin banbancin da yake tsakaninsu tun da ta fahimci dan masu hali ne sabanin ita da sai dai godiyar Ubangiji har dai ta fahimci kaunarta yake da zuciya daya ga shi ta fahime nutuin ne me saukin kaı dan tuni gidansu ya zama tamkar nasu in dai ya zo mutukar Umma na nan sai ya shiga ya gaishe ta, tun tana jin nauyinsa har ta saki jiki da shi sukank dan taba hira. Shi ko Malam ya mayar da shi tamkar mahaifinshi yana sakewa ya yi hira da shi sosai, a yawancin lokuta tare za ka iske su suna cin abinci in har ya kai dare ke nan. Haka nan kannanta su Nusaiba sun shaku da shi kai yawancin danginsu sun san da soyayar dake tsakaninsu haka a bangaren Mas'ud abin har ya zarta nata bangaren a dalilin tsananin kaunar da iyayansa suke masa kai da ma sauran 'yan uwansa muna iya cewa halinsa ne ya janyo masa haka domin akwai shi da sanin darajar mutane da girman na gaba da shi, iyayanshi da sauran Kannanshi kai dama sauran danginsa kowa ya yi na'am da zabinsa burinsu Allah ya kawo ranar bikin. Mama mahaifirshi har kyautuka take wa Hanifa kama datga sarkoki zuwa cosmetics da dai 22 sauran su, ita kanta Hanifa tana ayyanawa ranta ta yi sa'ar surukai masu Kaunar ta. Dangane da kyaututtukan da yake mata har sai da Malam ya yi masa magana ya daina shi zai ba shi 'yarsa ne dan Allah dan kuma mutumcinsa da na iyayansa duk da haka dai jefi-jefi yakan yi mata alheri duk da kasancewarsa dalibi hakika shi kansa ya san ya dace da macen kwaria, me son sa da gaskiya, ba wai don abin hannunsa ba, abin ya yi karanci a wannan zamanin ke nan, inda idon 'yammata ya bude da shegen son abin duniya ba su ba ma hatta da iyayansu kan dauki mace a matsayin jari, sam ba shi da fargaba ko kokwanto dangane da son da take masa burinsa daya ya kamımala karatunsa a yi auransu. a ***** ***** ***** Mas'ud Khalil haifaffan unguwar Gadon Kaya ne cikin birnin Kano shi ne da na farko gurin mahaifansa yana da kanne ukuk Nasir, Nazir, sai autarsu Fauziyya. Mahaifinshi Alh. Ibrahim Khalil (Wanda suke cewa Abba) tsohon ma'aikacin gwamnati ne ya rike mayan mukamai har daga baya ya yi ritaya ya shiga har kokin kasuwanci yana shigo da motoci daga Republic of Benin (Cotonou) yana sayar da su a kasar nan yana da gidajen sai da motoci akalla guda hudu. Mahaifiyarshi kuma sunanta Haj. Saratu suna ce mata Mama. Fara kyakkyawa ga kyan hali da girmama bako. Duk da kasancewarsu masu wadata ba su da wulakanci ba su daukan kansu wani abu ba daga ita har mai gidanta ga su da taimakon na Kasa da su. Wannan kyawawan halayan nas 'ya'yansu duk sung ado shi. 23 Sun tarbiyyanci 'ya'yansu yadda ya dace dan haka yaran suka tashi da ingantaciyar tarbiyya. Mas'ud fan kimanin shekara ashirin da hudu wankan tarwada kyakyawa da shi, ba shi da wata makusa a jikinsa ya yi karatunsa tun daga primary har zuwa University ya kammala Degree a fanninsa Engineering a halin yanzu yana yin bautar kasa ne. Sun hadu da abokinsa Ammar tun zamanin yana secondary. Hanifa kuma sai mu ce ita A bangaren ma haifaffiyar jihar Kano ce cikin unguwar 'Yar Maishikafi mahaifinta Malam Sa'ad da mahaifiyarta H. Hadiza dukansu 'yan usulin Knao ne wanda tushensu ya samo asali daga garin Kiru, dukansu yan dangi ne gaba da baya. wadanda suka samu kyakyawan usuli Allah ya azurta su da 'ya'ya har guda biyar dukansu mata babbar ita ce Ummu Salama sai Ummahani sai Hanifa, Nusaiba da- Nasiba yayyant abiyu dukkansu an musu aure tun suna 'yan shekara goma sha hudu. Iyakar karatunsu primary domin wannan al'adar Malam ce da yarsa ta cika shekara goma sha uku zuwa sha hudu zai aurar da ita ga wanda ya zabа mata ko kadan ba shi da ra'ayin `yarsa ta yi makarantar boko primary dinima fannin Arabi suke yi ilmin addini kam wannan ba a maganarsa domin duk cikin 'ya'yansa babu wanda be sauke ba hatta da kananan sun ksua hattamawa mutum ne me gudun wulakanci dan haka yadage wajen nemawa iyalinsa fan abin da za su'da sauran hidindimun yau da gobe. Mutun ne me tsananin kula da tarbiyyar iyalinsa ko kadan ba ya Kaunar ya ga sun yi wani abu da zai janyo musu abin kunya dan haka da wuya ka ga 224 yaransa ko da a kofar gida ne in ka gan su a waje za su makaranta ne ko wani aike me muhimmanci. Sai dai fa duk da wannan tsananin nasa mutum ne me son jan iyalinsa a jiki ya shaku da 'ya'yansa Kwarai da gaske sai dai duk da haka duk lokacin da suka yi wani kuskure ba ya raga musu. Sana'arsa shi ne sayar da yadiddika da kananan atamfofi (Super Print) a kasuwar Kurmi a kullum ya kan fita misalin karfe takwas na safe sai Karfe biyar yake dawowa idan an yi sallar isha'I yakan zauna da faliibansa wanda galibinsu magidanta ne hade da dattijai a nan kofar gidansa yana karantar da su ilmina ddini. domin Allah ya hore masa ilmi sai misalin karfe goma zai shiga gida ba za ka kara ganinshi a waje ba in dai ba wani uzuri ba sai kashegrar mutum ne da ya san darajar mutane hade da makwabta. Mutanen unguwarsu suna jin dadin zama da shi sukan yi kokarin yin koyi da kyawawan halayenshi musamman yadda yake kulad a tarbiyyar iyalinshi. Hanifa 'yar kimanin shekara goma sha biyar doguwa me kyan jiki ba ta da wani matsanancin kyau. Wanan tarwada ce idanunta matsakaita masu kyawun gani hancinta dogo siriri bakinta madaidaici haka nan ga shin kanta ma babu laifi abu faya da za ka so ka yi ta gani a jikinta shi ne Allah ya yi mata baiwar jiki mai kyau irin jikin nan ne da ke boye shckaru, ita kanta ta san Allah ya yi mata baiwar jiki me kyau msuamman in ta yi la'akari da yadda Kawayenta kai da saurna jama'a ke tanka mata. Tana makarantar yammata ta Sani Mainagge tana SS II. A kullum ta Allah da misalin karfe biyu da rabi takan tafi Islaniyya wato shahararriyar makarantar nan Gwadabe 25 Maitasa wadda take daf da gidansu. Da dadadre kuma takan je makarantar dare a nan lungusnu kafin ta kwanta bacci takan kara daukar karatu gurin mahaifinta dan haka Hanifa Allah ya hore mata sanin iilmin addini. Babban burinta shi ne ta zama cikakiyar Malamar makaranta ta koyar kamar yadda a ka koyar da ita. Sai dai ta san abu ne me wuya mahaifinta ya kyale ta ta tafi higher insititution, secondary din ma da yaya ya bar ta sai da aka sha wuya kafin ya bar ta shi ma din da taimakon wan mahaifinsa sannan ya bar ta. Dadin dadawa a lokacin da ta kammala primary ba ta fi shekara goma ba ga ta da karamin jiki musamınan da ya lura yarinya ce me hazaka dan har headmaster dinsu sai da ya zo ya aroke shi ya bar ta ta ci gaba da karatu ya kuna lura duk da karancin shekarunta yarinya ce me nutsuwa wannan dalili yasa shi ya kyale ta. Ya dai kudurcewa ransa ne da zarar ta tasa zai cire ta ya zaba mata miji ya aurar daita har dai t akai zuwa aji uku ya so ya cire ta ya aurar da. ita tun a lokacin msuamman da yake akwai masu neman auranta amma sai ya sauya tunani domin ya lura tana mtukuar son karatun ga shi Allah ya ba ta basira. Wata rana ya yi kiranta ya yi mata nasiha ta ci gaba da rike mutuncinta ya amince ta ci gaba da karatunta har alah ya kawo mata wanda take so daga nan ne fa zai aurar da ita ba wani abu ne ya sa shi yin haka ba ilal tsaanins on ta da yake don duk cikin 'yia'yansa ba wanda yake so irin ta babu kuma wanda ya fi yi masa biyayya kamar ta ya yi kuma la'akari da sauyawar zamani. Tsananin farin cikin da. ta yi ba zai misaltui ba ko a mafarki ba ta taba tsammanin zai amince ba, a zatonta karatutna ya zo karshe. Ta yi shirin rungumar duk wanda mahaifinta ya zaba mata dan haka ta 26 yi alkawari ga mahaifinta za ta guji yin duk wani abu da zai tagfa mutumcinta tun daga wannan lokacin ta dada dagewa da karatunta, tana ganin nan gaba ma zai amince ta je har Higher Institution ko da wasa ba ta taba saurarar saurayi ba da sunan zacne kozuwa suka yi ta kan ba su hakuri ta kwan da sanin hakan abin da zai janyo mata har dai zuwa ranar da Allah ya haſa ta da Mas'ud in da gaba faya tunaninta ya sauya. Sun samu kimanin shekara daya suna gudanar da tsaftatacciyar soyayyarsu mai cike da so da kaunar junansu, saboda shakuwa ya game jikinsu har ta kai ba sa iya yin cikakken. 48 hours ba tare da sun ga juna ba. Soyayayrsu ta zama abar kwatance ga 'yammata da samari da ma al'ummar unguwanninsu. A wannan lokacin tuni ya kammala hidimar Kasa yana aiki a kamfanin samar da hasken wutar lantarki na kasa. Ana daf da fara maganar aurensu Alh. Khalil ya nema mishi Admission a kasar Japan domin yin mastering Degree dinsa, saboda wani buri da yake da shi a zuciyarsa. Mas'ud ya yi mutukar farin ciki domin babu abin da ya ke so irin ya ga ya zama cikakken Engincer a fannin KereKere, amma a wani bangaren an zuciyarsa yana mutukar bakin cikin rabuwa da gimbiayrsa na tsawon wani lokaci amma da ya tuna kokacin da zai Kare karatunsa dai-dai lokacin ne ita ma za ta kammala dan haka yake ganin komai ya zo dai-dai ke nan. Musamman in ya tuna nisantar tasu zai ba ta kwarin gwiwar tunkarar final exam da ke gabanta. Ba Karamin kaduwa ta yi ba da ta ji tafiyar gani take shi ke nan da ya je can zai samu wata ya mance da ita 27 sat da kyar ya shawo kanta ya yi alkawarin zai dinga hugw mata waya duk Kashen sati. Ya je har gidan babbar aminiyarta Huwailat ya danka mata amanarta. Kiraye-kirayen salar da ya cika mata kunne sli ya dawo da ita daga dogon tunanin da take yi muna iya cea kusan kwana ta yi tana kuka. Sai da tayi kusan sati ba ta jin dadin jikinta ta san kuma abin da ya haddasa mata ciwon dole ta dinga tursaa zucıyarta don ta rage tunanin masoyinta. Ta ci gaba da karatunta yadda ta saba, Kawancensu da Fauziyya ya c gaba da gudana. Kamar yadda ya yi alkawari duk karshen sati yakan bugo mata waya ta hannun abokinshi Ammar, haka nan yakan aiko mata da kudi da `yan kayan ciyc-ciye duk ta hannun Ammar ta sha fada masa ya daina wahalar da kansa amma ya ki dole ta hakura take karba, a gaskiva tana iya cewa ganin juna ne kawai da ba sa yi amma a ko yaushe suna tare a waya, dan har ta kai duk bayan kwana biyu sai ya yi kiranta yana me dada jaddada soyayyarsa а gare ta. Fatansa a ko yaushe ya kammala karatunsa ya dawo su yi aure. Watansa goma cif da tafiya Hanifa suka fara final exam sun fara da WAEC daga baya suka rubuta NECO. Suka kammála jarrabawarsu cikin nasara tare da fatan sanmun kyakkyawan sakamako. Ranar da suka rubuta jarrabawarsu ta Karshe Mas'ud ya yo waya ta sanar da shi ya yi murna Kwarai da gaske tare da yi mataalheri a Karshe ya ce ta jirayi gift dinksa ya sanar da ita saura wata biyu su kammala. Malam da umma duk sun mata fatan alheri a Rarshe ya ce karatu ya Kare sai aure ko ta yi dariya cikin jinn kunya. Cikin dare ma tana jiyo su suna tattauanwa 28 dangane da maganar aurenta. Tana ta mamakin wannan dokin da suke tamkar ba su taba aurarda ya ba sai a kanta. Awannan shekarar ne Nusaiba ta shiga secondary Nasiba kuma sai shekara mai zuwa. Kwanaki ba wuya game sauran nufmashi har ga shi an yi kimanin wata shida da kammala karatunta amma babu Mas'ud babu dalilinsa ba ma rashin dawowarsa ne ya fi dainunta ba ilal rashin bugo mata waya da sam ya daina yi, rabon da ta ji shi a waya an yi wata hudu ko biyar ko sakon gaisuwa babu, ga shi dai Ammar zai zo kamar yadda ya saba amıma ko sau daya bai taba yi mata maganarsa ba, ita ma sai ta share dan kar ya ga ta damu da shi da yawa, kai abu dai ya ci gaba tun tana tunanin ko ba shi da lafiya ne har ta daina tunanin hakan don suna yawan haduwa da Fauziyya ba ta taba ce mata haka ba hasali ma sukan yi hirarsa sosai tare da hirar bikinsu saboda gaba daya a ka shriya za a yi bikinsu har dai ta fara tunanin ko ya samu wata ya mance da ita ne nan ma ta kan yi saurin akwar da wannan tunanin dan ko a mafarki ba ta fatan hakan ta faru kai abu dai ya dagule mata ta kasa sanar da kowa halinda suke ciki ilal dai ana yawan tambayar ta me ya same ta saboda ramar da ta yi. Tunani ko ba a maganarsa, hakika ta shiga cikin daımuwa ko da a mafarki ba ta kaunar ya subuce mata ita duk ba wannan ne ya fi damunta ba illa matsa mata da iyayanta suka fara yi dangane da auranta, su gani suke kamar lefinta ne. rannan kwatsam Fauziyya ta zo mata da labarin aurenta sati biyu masu zuwa a dalilin wanda zai aure ta ya matsa a yi bikin saboda shi ba mazaunin kasar ba ne. 29 Gabanta ne ya fadi me ke nan hakan ke nufi tun da ta san tare a ka shirya za a yi aurensu kamar ta ce ya maganar nasu auren? Ya maganar yayanta? Wane hali yake ciki yanzu?' shin ya mance da alkawarin da ya yi ne? kai da dai tambayoyi masu yawa amma sai ta kasa sanar da ita musamman in ta tuna banbanci da ke tsakaninsu kar su ga zalamarsu ko su yi tunanin wani abu dan ko ita Fauziyyan ba ta san abin da ke gudana da Yayan nata ba. ta 'danne zuciyarta ba tare da ta bari ta fahimci wani abu ba ta yi mata fatan alehri daga nan suka fara shirye-shiryen biki. Sati biyu na zagayowa aka sha shagalin biki ango ya dauke amaryarsa suka barkasar abind a ya dada kwantar mata da hankali shi ne yadda a lokacin bikin dangin Mas'ud da ma mahaifiyarsa suka dinga haba-haba da ita duk inda ta shiga sai nuna ta ake. Huwailat

Chapter 2 of 7