Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 7
me Mas'ud din ya fi Abdul? Karewa ma in wani kyan Mas'ud ke rudarki kin san Abdul ya zarta shi nesa ba kusa ba sai dai ya nuna masa hasken fata, mutumci, karamci shi ma ba daga nan ba ga shi shi ma ya fito daga tushe me kayu ian ganin ki share wani Mas'ud daga zuciyarki ki rungumi abd....." Ta katse ta da cewa Malama na ji ya isa haka ai ba sai kin kushe shi ba za ki tusa min wani ra'ayi na daban, banza mara rike alkawari wai yau ke kike kushe Mas'ud duk da amanar da ya danka miki duk kuma da amincin da ke tsakaninku. Ta ce ko me a ki ce sai dai ki ce gaskiya ce duk inda ta zo dole a fade ta. Tsawon kwana biyu Huwailat tana mata nasiha har zuciyarta ta so ma karkata ta kan yi tunanin maganganun iyayanta musamman ini ta tuna irin gwagwarmayar da suka sha wajen dawainiyar su amma a ce yau rana tsaka za ta bijire musu ta kwan da sanin cewa 44 duk gidansu ba wanda ya samu wannan damar sai ita, dole ta hakurewa zuciyarta Mas'ud ta tabbatar Allah ne bai yi nufin aurensu ba, tun da shi kansa Abdul din ba wai tana jin kinsa a zuciyarta ba ne ilal dai dan tuni ta sawa zuciyarta kaunar Mas'ud ne ainma in ba haka ba ai shi ma ba shi da makusa a yawancin lokuta yakan burge ta har ta dinga jin da ba dan kaunar Mas'ud da ta mamaye zuciyarta ba da shi ne namiji na farko da za ta kaunata amma duk dahakan babu lefi takan ji kaunarsa a zuciyarta duk da dai ba za ta iya kwatanta shi da Mas'ud ba. A daran ta nemi gafarar iyayenta tare da amincewa da auren Abdul sukayi farin cikitare da yi mata fatan alheri gami da nusar da ita martabar aure da umartar ta da ta yi wa mijinta biyayya. A da ta kudurce in suka hadu za ta goge shi tas kan hada ta da ya yi da iyayanta amma fa babban abin da ya fi ba ta haushi da shi shi ne yadda ya zo ya raba ta da masoyinta. Cikin dan. kankanin lokacisa ka tsaida lkacin aure wata biyu masu zuwa. BA RI MU JE WAYE AABDULZAHIR. bdulzahir haifaffan garin kano ne cikin ugnuwar Yola, mahaifinshi Alh. Nasir yana da mata hudu da 'yaya ishirind, ahudu, mahaifiyarshi Haj. Maryam ita ce ta uku a gurin mahaitinsu babbar uwar gidan tana da 'yaya goma me bi mata 'ya'ya bakwai sai mahaifiyar Abdulme 'ya'ya hudu, Maijidda ita ce ta farko sannan Abdul sai alkassim sannan auta Zakiyya. Amaryar kuma an da 'ya'ya uku. Alh. Nasir irin attajiran nan ne na 45 kawai za ka kalla ka tabbatar da hakan. da. Yanayin gidan Duk da dai yanzu sai rufin asiri yawancin 'ya'yansu ma'aiaktan gwamnati ne wasu kuma suna taba kasuwanci. Abdulzahir ya yi karatunsa daga primary zuwa University, fan kasuwa ne yana shigo da kaya daga Rasashen Asiya zuwa gida Najeriya yana da rufin asirinsa dai-dai misali, dan kusan duk 'yayan gidansu ya fi wadata. A tin shekaru hudu da suka shige soyayya me karfi ta kuillu tsakaninsa da 'yar aminin babansa na kud da kud wato Aysa. Duk dangunansu ba wanda be san da soyayar da ke tsakaninsu ba. abu har yakai ga maganar aure, tun kimanin shekara daya ba ya lokacin da aka sa auresu ya yi amma saboda be kammala katafaren ginin da yake ba dole aka dage bikin. Tana zaman tsimayinshi dan a bangaren amarya da danginta tuni sun gama tanadinsu ango kawai ake jira. Kwatsam dare daya ya sauya tunaninshi a kan Aysa tun sa'ar da ya hadu da Hanifa ya yi kokarin ya danne zuciyarsa ya yakice ta amma da ya jewa mahaifinsa bsai sauyin da ya samu fafur Alh. Nasir ya ki kai da ma ilahirin danginshi hata da gun mahaifyiarshi be samu goyonbaya ba kowannensu na ganin zai 6ata dadaddan zumuncin dake tsakanin gidajen biyu. Da kayr da sidin goshi ya shawo kan mahaifinshi tare da mahaifiyarsa suka amince shi ma fin a dalilin baban Aysan ne ya rokar mishi domin zuwa ya yi ya marairaice mishi tare da nuna mishi Allah ne be nufi yin aurensa da 'yarsa ba amma ba wai dan ba ya son ta ba ya nunamishi tana nan a matsayin 'yar uwarshi taımkar yadda kannanshi suke a gare shi da yake Alh. Dattijon kirki ne sai ya karbi 46 uzurinsa tare da addu'ar alah ya yi wa 'yar tasa zabi na gari. Duk da dai an kai ruwa rana kafin Alh. Nasir ya amince kusan ilahirin danginsu in ka cire mahaifiyarsa babu wanda ya yi na'am da wannan aure a ganinsu wannan cin amana ne, musamman da yake suna sane da tsawon lokacin da Aysa ta tsaya tana jiranshi. Babu wacce abin ya fi bakantawa rai irin Zakiyya saboda a duniya ba ta da wata aminiya da ta wuce Aysa. Tun kan ta ga matar da yayan nata ya zaba a madadin aminiyarta ta ji ta tsane ta duk da matsaancin kaunar yayanta da take yi da son duk abin da yake so duk cikin yayyanta babu wanda ta fi kauna irin sa wannan akromn kam sun raba hanya. Lokacin da Aysa ta samu wanann mummunan labari ba karamin rudewa ta yi ba, ba ta taba tsammanin zai yimata haka ba ta yi kuka har ta gaji a karshe ta hakura tare da fatan Allah ya saka mata a bisa cin amanar da ya yi mata a ganinta dama can yaudararta yake yi. A bangaren Abdul kuwa shi kansa ya san bai kyautawa Aysa ba amma ya ya iyawa zuciyarsa tun ranar da Allah ya hada shi da Hanifa ya samu kansa da mancewa da duk wata mace da ke duniya mutukar ba Hanifa ba. fatansa a ko yaushe ta zama mallakin zuciyarsa duk da dai ita ma Aysan ba baya ba ce wajen kyau amma a gaskiya ba a ka kwatanta da Hanifa ba, musamman ta kirar jiki. Ya yi kokarin ya danne zuciyarshi ko su biyu ne ya hada ya aura ama ina zuciyarsa ta yi nisa da begen Hanifa a karshe ya yi mata wasika tare da tausasan kalamai yana me neman afuwarta yarubtua mata cheque na makudan kudi amma da aka kai mata ko budewa ba ta yi ba ta dawo mishi da 47 sakonsa daga bisani ma ta bar garin ta koma Zariya gurn ngin mahaifinta. Ya rage saura sati daya a fara bikin Abdulzahir da Hanifa Abdul ya dauki Zakiyya Kanwarsa zuwa gurin amarya duk da dai tia-ba ta so ba saboda ba za ta iya ce masa ba za ta ba ya sa ta bi shi. tun da suka isa kofar gidan ta yi tsaki gami da takaicin ashe ma 'yar Malam Shehu (wato 'yar talaka) ya kwaso musu, ko kadna ba ta kaunar yin wata mu'amula da talakawa. A kyankyame ta shiga gidan tana alla-alla ta ga wace sarauniayr kyan ce yayan nata ya rufe ido ya yimusu wannanr ashin kirkin. Ta isa tsakar gidan tana sallama kamar ba ta son yin maganar. Hanifa na daki ta jiyo sallamar ta fito ai ko suka yi kicibus suna kallon-kallo na wani lokaci, Hanifa ta ga bain ya yi yawa ta ce Malama lafiya kin shgo gidan mtupane kint saya kikam? Zakiyya ta bi ta da wani wulakantaccen kallo domin ta san ita ce wace yayanta ya kwaso tuntuni ya a ce ta gane ita ce ta jin cikakken sunanta gurin yayanta kai dama hotunanta da ta gani gurinsa, hotunan sun yi masifar kyau dan haka ba ta taba kawowa ita ba ce. Cikin a ta ce daman ke ce wace yayanmu ya kwaso mana? Kai amna yaya Abdul bai san me ya rude shi da ke ba yanzu dman a kanki ne ya guji kawata? Kai Allah ya kyauta wa Yaya. ya rasa wace zai waso mana sai 'yar matsiyata makwadaita dan na sna kwadayi ne ya kai ki ga son sa. Та yhi tsaki ta fice. Hanifa ta bi ta da kallo cikin takaici da tsananin mamaki ba ta taba zaton Abdul ya hada iri da irin wannan yarinyar mara mutumci koda ya ce mata zai kawo. mata Kanwarsa ko a mafarki ba ta yi zaton ita ba ce. 48 Ko da Zakiyya ta fita sai ta ce masa ai Hanifan ba ta nan ya yi mamakin hakan musamman da yake ya sanar da ita zuwansu suna tafe yana ta koda gimbiyar tasa gurin kanwarsa tare da kwarzanta kyawawan halayenta. Shi ko be san haushinsa take ji ba tamkar ta shake shi. An yi Kasaitaccen biki yadda ya dace duk da a 6angaren amarya zuciyarta na cike da matsanancin bakin ciki, ta san shi ke nan har abada sun yi banwakna da masoyinta Mas'ud. Abin da ya dada ba ta mamaki shi ne yadda mahaifiyar Mas'ud suka halarci bikin tare da gagarimar gudummawa haka mahaifinshi da shi aka daura auren don shi ne ya kasance waliyyinta ma. An kai amarya kayataccen gidanta dake Sultan Road har jama'a suka watse tana cikin kuka. Kusan tund a aka fara bikin cikin kuka take sai dai na yau ne ya tsananta ba wai dan rabuwa da iyaye ba ma a'a illa dan tunanin tsohun masoyinta shi ke nan ta san sun rabu ke nan har abada. Misalin karfe goma na dare ango ya shigo ya iske ta tana kuka ya yi lallashin duniya amma ta ki yin shiru, kai a takaice dai a haka suka kwana yana aikin lallashi sai da suka yi kusan sati a haka kullum da daddare kuka har Allah ya taimake shi ya samu hadin kanta a cikin daran ya dinga godiya ga Ubangiji da ya yi mishi kyauta da salihar mace domin ya same ta cikakkiyar mace. Sati biyu cur suka yi suna shan amarci ar daga bisani ya ci gaba da harkokinsa ita ma ta ci gaba da zuwa school. Duk wani abu da ya san zai kyautata mata si yake yi yana tsananin nuna kulawarsa a gare ta ta yadda koо tafiya ya yi yakan kirawo ta waya akai-akai dan ya ji 44 lafiyarta. Ita kanta ta san Abdul na son ta yana kaunarta fiye da yadda ta zato a baya. Ga shi ta yaba dakyawawan halayensa, ita ma sai ta dinga kokarin yakice Mas'ud a zuciyarta tare da kokarin cusa mijinta ama ikon Aah zuciyarta ta ik yadda ta yakice Mas'ud daga gare ta. Haka ta y ta fama har alalh ya taimake ta ta kawar da Mas'np gefe daya ba wai ta daina kaanrsa ba ne ilal dai ta kawar da shi ne gefe daya tare da kokarin cusa Abdul a gurinsa ita dai ta san har abada ba za ta daina kaunar Mas'ud ba amma tun da Allah be kadarto mijinta ba ne dole ta hakura ta rungumi mijinta. Sannu a hankali har Allah ya taimake ta so da kaunar mijinta ya ratsa jikinta burinta a ko yaushe ta faranta mishi tare da kokarin yin duk wani abu da zai bukata kama daga 6angaren kwanciya har zuwa mu'amular yau da kullum haka bangaren abinci daman ga ta gwana ce musamman da ta fahimci be cika son abinci me nauyi ba. haka nan ya fi so nau'in abincin Larabawa. Haka nan fangaren 'yan uwanshi tana bakin kokarinta wajan kyautata musu duk da dai ita da kanta ta san ba ta karbu ba gurin dangin mijinta musamıman tsagerun kannansa in da ta godewa Allah iyayan mijinta na Kaunarta kauna kuma ta hakika, dan daga hajiayr zua Alhajin kowanne haba-haba yake da ita, wannan dalili ya sa ba ta damu ba sosai kowa zai ki ta ma da sauki. Ta ci gaba da kokarin kyautata musu tare da fatan Allah ya sa su fahimci juna, ita kuwa ta rasa dalilin da ya sa suka tsane ta. Haka nan in abokanan mijinta ne suka zo ftakan karbe su cikin karamci a takaice dai muna iya cewa taa bakin kokarinta wajankyautatawa maigidanta shi da 50 kansa ya sna da hakan har ya kan yi mamakin yadda farat daya ta hakura da tsohon saurayinta ta rungume shi hannu bibbiyu tare da yin biyayya a gare shi, wannan dalili ya sa ba ya shayin kashe mata konawa ne duk abin daya gani ya san za ta yi sha'awarsa sai ya sai mata. Yau ranar asabar tana gida babu school ta hada lafiyayyen abinci wato Labanise Rice hade da Kidney soup, Chips & Baked Beans hade da Sardine-Omellete, a bangaren drinks kuma ta yi Carrot Drink. Karfe biyu narana tana zaune a ffalo ta hade cikin atamfa Super Holland, zuwan Abdul kawai take jira don ka'idarsa ce mutukar yana gari a gida yake cin abinci ba ya yarda ya ci a waje, saboda ta gama sangarta shi da daddadan girkinta, daman ga shi da son cink dadi sai Alah ya taimake shi ya yi katari da macen da ta iya abinici, har biyu da rabi ta gota be dawo ba, ta kishhingida kwata-kwata a 'yan kwanakin nan ba ta jind adin jikinta daga zazzabi sai ciwon kai. Misalin karfe uku ya iske ta a haka bacci ya dauke ta ya tsaya a kanta ya kare mata kallo shi da kansa ya san ya morewa mata. Ya dan shafi gefen kumatunta amma ko motsi ba ta yi ba sai ya shiga yi mata susar tsutsa a tafin kafarta abinda ya san ba ta so. Nan da nan ko ta tashi ta rike hannusna shi kuma yana yi mata dariya ta kalli agogo ta dan bata rai sai yanzu za ka dawo? Tun dazu ina ta zaman jiranka har yunwa ta sani bacci. Ya ce sorry my Dear, mota ce t ayi mint siya a hanya kin san da tuni na karaso, ni ma kina raina. Tun lokacin da na ga loakini cin abincinmu ya yi na san kuma halinki ba za ki ci ba sai kin jira ni. Ya ja hannunta zuwa Dining table yana bude kwanukan abincin kamshi ya cika mishi hanci ya girgiza 51 kai tare da yaba mata kamar yadda ya saba ya shiga ba ta a baki har sai da ya tabbatar ta koshi sannan ya fara cin nasa, sai kuma ya ga ta dafe kai ya ce lafiya? Ba komai. Ba komai.? Ya dan taba kanta ya ji shi zafi rau ya yi saurin sakin spoon ya tallafe ta zuwa cinyarsa ya ce me yake damunki ne? ta ce kai ne yake min ciwo sai dan zazzabi da nake ji. Tsam ya tashi ya koma daga falo ya zauna bisa carpet ya dora ta a cinyarsa ya shiga shasshafa mata ruwa yana yi mata sannu ita ko ta daďa shagwaggwabewa har da dan kuka. A haka Huwaila ta iske su za ta juya ya ce shigo mana yau gida ba lafiya. Ta karaso a tsorace lafiya? Me ya faru?" ya nuno Hanifa ga ta nan ba ta da lafiya ba ki ga yaddda ta fada ba? ta dan girgiza kai, to Allah ya kyauta, kun je asibiti ne? a'a ai yanzu an dawo na iske ta a haka, amma shi ne ka ce har ta rame daga cutar kwana daya ko yini daya ma zan ce, na san ma ba na raba dayan biyu kila juna biyu ke gare ta: Ya ce meye kuma juna biyu? Ta yi dariya ganin yadda ya rude kai ko ka fi kowa sani ta fada tana dariya ya dan bata rai Allah Huwaila ba ki da kirki matar tawa tana cuta ki dinga wannan dariya. Hanifa ta ce Abdul kyale ta ta karaci tsiyarta tashi ka kai toilet amai ke taso min. da sauri ya sungume ta zuwa toilet. Kashegari suka je asibiti sakamakon da aka gaya musu ya sa su farin ciki, wato ciki ke gare ta na wata biyu gaba dayansu haka Alah ya yi su da son yara a cikin satin Abdul yana da tafiya kasar South Korea amma saboda laulayin da take fama da shi sai ya janye tafiyar haka ya shiga tarairayarta, ita kuna tana shagwaggwabe masa da yake irin cikin nan ne me laulayi be samu lafiya ba sai da 52 cikin ya kai wata biyar sannan ta fita daga laulayin duk da hakan dai ya kan talalfa mata da wasu abubuwan ga shi dai suna da masuaiki har biyu amma sam ba ta yarda su yi wame gidanta abinci tia ce takan daure ta yi. Lokacin da cikinta ya cika wata tara gaba dayan duk wata tafiya sai ya dakatar da ita, fatansa a ko yaushe Allah ya sauke ta lafiya. Tana shirin shiga wata na goma Allah ya taimake ta ta haifi sankacecen saurayi me kama da ubansa sak, ba karamin farin ciki Abdulzahir ya yi ba. Ranar suna ta zagyao yaro ya ci sunan Kakansa wato nasir.an yi kayataccen suna na gani na fada haka nan kayan da ya hado mata tamkar na lefe babu lefi dangin Abdul sun zo in ka cire Zakiyya don daf da za ta haihu sai da suka yi kaca-kaca a dalilin izgilanci da wulakanci da take zuwa har gia ta yi mata. A ranar dai da abin ya ishe ta ta wanek ta tas duk abin da ke tsakaninsu ba ta taba fadawa Abdul ba. lyayan Hanifa su ma sun yi bakin kokarinsu don har gara sai da uska yi mata, sun ji dadin aydda ta kwantar da hankalinta ta rungumi mijinta shi ma kuma Abdul ya san ya yi sa'ar surukai ya fauke su tamkar iyayansa, ko yaushe cikin yi musu hidima yake. So da kauna gami da fahintar juna ya dada wanzuwa a tsakaninsu duk wanda ya je gidan sai ya fito yana me sha'awar yadda ma'auratan suke gudanar da rayuwarus cikin tsananin kaunar junansu. Abdulzahir har mamaki yake yi ashe Hanifa za ta kaunace shi haka ganin yadda ta sawa ranta kaunar tsohon saurayinta. A bangaranta ita ma tana mamakin yadda yake tarairayarta gami da shagwaba ta. Ita dai tana iya cewa 53 matsalarta daya wato dangin miji gabanta har faduwa yake yi ta ji ya ce za su gidansu don ta san ba za ta je ta dawo ba tare da ranta ya baci ba, ballantana a ce ana wani taron suna ko biki har ta ji ta dawo a darare take wulakanci ko sai wanda ta gani, a gurin hajiyar Abdul ne kawai take samun karbar arziki, dan dai-dai da 'yan dakinsu Abdul din ba Kaunarta suke ba, In ka cire kaninshi Alkasim wannan kam tasu ta zo daya shi kuma ba mazauni ba ne, habaici ma kadia ya ishe ta. Ita dai kam da da hali da ta ce da Abdul ya sauwwake mata halartar duk wani taro na 6angaren danginsa amma ta san ba za ta iya ba don zai bukaci sanin dalili, ita kuma ba za ta so ta hada shid a 'yan wuanshi ba ko dan- kar ta Kara yini wani bakin jinin. Tun da ba ta da tabbacin ko yana sane da irin kiyayayr da suke gwada mata. A nan 6angaran kam tana iya cewa Abdul ya fadi don kwata-kwat aba shi da kula tana iya cewa mutum ne me sakaci da yawa amma in ban da wannan ba ta ga abin ki a halayyarsa ba. hakika tana son sa tana son halayyarsa. Hakika idan ka san Hanifa a 'yan shekarun baya idan ka gan ta a yanzu ba za ka shaida ta ba, ta kara kyau nesa ba kusa ba ta yi haske ta yi 'yar kiba irin ta hutun nan da ganinta ka san tana cikin daula cikin kuma kwanciyar hankali. A bangaren ci da sha babu abin da ta rasa, kai hatta da iyayanta irin hidimar da. yake musu ta isa. Nasir wanda ake wa lakabi da Walid ya zama abin so a tsaknain iyayansa barin Abdul don in yana gari a ko yaushe suna tare da yaron, ko makaranta za ta je tun da ya fara shan madara shi yake renonsa haka nan in yana gari shi yake kai ta school ya fauko ta sai dai in yana dawani uzurin ne za 54 sa Driver ya dauko ta, in kuma ba ya gari ne akwai Driver da yake kai ta ya dauko ta ya zuwa yanzu shekara daya ya rage ta kammala NCE dinta. ***** ***** ***** Da misalin karfe hudu na yamınacin ranar asabar Mas'ud ya dira a filin jrigin sama na Malam Aminu Kamo, sanye yake da bakar coat ya tsuke wuyansa da neck tie ya kafa bakin glass a idonsa da ka gan shi ka ga dan hutu. Yanayin faşar jikinsa kadai ma ya sai ya tabbatar maka da hakan. Yana saukowa daga step din jrigi ya nufi mahaifinshi da suka zo taryarsa, suka rungume juna cikin tsananin farin ciki daga bisani ya gaggaisa da sauran kannenshi suka shiga mota suka rankaya zuwa gida. Aabu daya ke yawo a kwakwalwarshi, abu daya ke da burin gani, abu daya yake fatan kasancewa tare da shi har illa Masha'allahu. Abu daya yake da burin ya malake shi, shi kadai a duniyar nan, wato sarauniyar zuciyarsa HANIFA. Suna tafe a motar suna hira amma shi jin su kawai yake tuni zuciyarshi ta tafi ga sahibarsa yana ayyana irin fairn cikin da za ta yi da yadda zai gan ta saboda zuwan bazatan da ya yi mata. Sun isa gida ya tarar da Mamanshi tana zaman jiran isowarsa ai ko ya kankame ta cike da farin ciki, bayan tsawon lokacin da aka dauka al'ummar gidan suna masu nuna fairn cikin dawowar dan lelen gidan Mas'ud ya isa turakar mahaifinshi ya iske shi a falo kan kujera ya zube a kasa ya dada kwasar gaisuwa daga bisani ya ce Abba ga 55 1 result din ka gani da fatan wannan zai sanyayar maka da zuciya a kan Gacin ran da na sanya ka. Alh. Khalil ya karba cike da dokin ganin abin da ke ciki, ai ko yana gama duabwa ya yi godiya ga Ubangiji kana ya yabawa dan nasa saboda fitar da shi kunyar da ya yi. Be taba tsammanin zai samu Good Result haka ba, ya kasa boye farinc ikins ahar sai da ya bayyana masa tare dayi masa addu'ar fatan alheri. Cikin jin dadi Mas'ud ya ci gaba da godewa Mahaifinsa bisa jajircewar da ya yi har ya kai ga wannan matsayi. Cikin jin kunya ya ce, Abba shi ke nan komai ya shige ko? Kuskuren da na yi a baya a yafe ınin, dan haka nake sake neman yardarka na ci gaba da neman yarinyar da nake so. Ya yi murınushi sannan ay ce, Haba Mas'ud ai komai ya shige sai dai a kiyayi gaba kowae yarinya ce kake nema ka sanar da ni da zarar kun dai-daita mu je nenan maka aurenta. Yana shafa kai tare da sunkuyar da kai ya ce, Abba ai yarinyar dai da ka san ina nema ce 'yar wajen Malam Sa'ad, tuni mun fuskanci junanmu, aynzu abin da ka ga ya dace sai a aiwatar. Mas'ud na jiran ya ji abin da mahaifinsa zai e amma sai ya ji shi dif kamar an dauke wuta ya yi kasake kamar me tunanin wani abu da ya ga an dau tsawon lokaci sai ya ce, Abba ya na ga ka yi shiru? Ya dna yi firgigit alamar tunani yake sannan ya ce, shi ke nan yanzu dai je ka ka huta ba tare daya kawo komai ba ya yi sallama da shi ya nufi gurin mahaifiyarsa. Ya iske ta a Dining Holl ana ta jejjera masa kwanukan abinci da aka girka masa. Ta tare shi da farin ciki a'a har kun gama gaisawa da Alhajin sai ka je ka dan 56 watsa ruwa ga baincin nan ka ci domin yau da kaina na yi maka duk irin kalar abincin da kake so. Ya yi murmushi kai mama na gode, kina shagwa6a ni da yawa amma bari na je wata'yar unguwa yanzu zan daow. Haba daga dawowarka ko ina ne ka hakura ka htua tukun. Mamaki yi hakuri Mama gurin haniffa za ni aynzu zan dawo. Wace Hanifa?" ya dan zaro ido haba Mama kar dai a ce kin mance ta? Sai a lokacin ta tuan ta ji gabanta ya buga dam da karfi sosai. Be kula da yanayin da take ciki ba ya fita da fan sauri mama bari in sauri in je ko na dawo da wuri. Lokacin da ya isa gidansu Hanifa ba kowa a wajen ya jima yana neman wanda zai masa iso sai Allah ma ya taimake shi Malam Sa'ad dawowarsa ke nandaga kasuwa. Yana shirin shiga gida da sauri yafito daga motar ya tarye shi, Malam na jin muryar ya shaida Mas'ud ne, nan da nan ya juyo ciek da farin ciki yana a'a yau bakini turai ne a garin namu? Ya bude musu shagon dake makale a kofar gidan, bayan gaisawar da suka yi suka shiga tambayar lafiyar juna gmai da yar taba hira. Sun jima a shagon har Mas'ud ya Kosa babu abinda yake burin gani irin sahibarsa ga shi yana jini nauyin Malam balalntaa ya saya turo masa ita. shi kuma ya kasa faukar haske da dai ya ga bain ba na Karau ba ne sai ya danne 'yar kunyarsa ya ce, Malam ko za a samu yaron da zai kirawon ita. Wa ke nan?" Malam ya tambaya. Abin ya fan ba shi mamaki, amma dai ya се. Hanifa man. Hanifa kuma? E Malam ko ta yi tafiya ne? nan da nan fuskar Malam ta saya mamaki ya kama shi dan shu ko kadan be yi tsammanin ba shid a labarin ta I aure ba, ya 57 higa girgiza kai ya rasa yadda zai yi ya sanar da shi har dai Mas'ud ya tsargu ya shiga tambayarsa lafiya. Da dai Malam ayn gaba mafita ilal ya gaya mishi gaskiyar lamarin duk da ya san yaron zai kadu amma boye gaşkıyar babu abind a zai haifar. Ya yi ta maza ya zayyane mıshı abin da ya faru ya kara da yi mishi nasiha. Ga Mas'ud kuwa muna iya cewa suman zaune ya yi don komtosi yakasa yi har Malam ya dan tsorata sai da ya fan girgiza shi sannan ya dawo hayyacinsa kana ya dau lamarin kamar a mafarki ya Rkara nanata tambayarsa ga Malam don a turo masa Hanifa amsar nan dai da bai fatan ji ita ya sake ji. Take ya dimauce ya shiga sambatu kai har ta kai shi da zub da hawaye, shi dai Malam sai aikin lallashi yake yi amma tamkar yana tira shi har Umma dake cikin gida ta jiyo hayaniya

Chapter 4 of 7