Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 7
ta zo ta sanar da ita result ya fito suka je suka amso babu laifi result ya yi kyau ta samu 3 credits 2 pass 1 Distinction a 6angaren WAEC ke nan a NECO kuwa ta samu fiye da haka. Gabanta na faduwa saboda sanin abinda zai je ya dawo tsakaninta da mahaifinta ta dai daure ta iske shi a falosna yana lazimi sai da t abari ya kammala ta russuna ta gaishe shi daga bisani ta mika mashi resutl din nata gami da yi mishi bayanin kowanne dalla-dala. Ya karba yana mai nuna farin cikinsa da yaba mata kan kokarin da tayi. Ta dan rissinar da kanta ta ce Malam daman wata alfarma na zo nema. Ya yi murmushi fadi ummata wace alfarma ce na yi miki mutukar ba ta fi karfinia ba (da yake ainihin Sunanta sunan mahaifiyarsa ne, an sakaya ne ake ce mata lanifa). 30 Ta ji kwarin giwa, Daman Malam dangane da karatuna ne nake neman yardarka na ci gaba da karatuna..... ba ta karasa ba ya daka mata tsawa ya ce, kina hauka ne?" kin san abin da kike fada? Wane irin akratu kuma? Duk wanda kika yi bai ishe ki ba, ko dan kin ga na kyale ki wato kin girma kin yi ilmin da za ki juya ni ke nan, to bari ki ji na zuba miki ido ne na ga gudun ruwanki da an yi zance sai ki ce ya kusa dawowa to shin shi zai yi jiranki ko ko ke za ki yi jirans,a ni na soma tsinkewa da zancen yaron nan, ca nake kin ce shekara daya zai yi ga shi har yana shirin yin ta biyu. Ca nake tare aka ce za a hada bikin da na kanwarsa ba ga shi ita har an yi nata, so kike ni na vi ta zuba miki ido ina kallonki, to bari ki ji na ba ki nan da wata uku ko ki fito da wani wanda kike so ko kuma na aura miki wani kamar yadda na yi wa sauran 'yan uwanki. Tana kuka ta ce dan Allah Malam ka yi ahkuri ka ga ni ma ba laifina ba ne shi ma kuma akwai uzurin da ya dakatar da shi ya ce karshen shekarar nan zai dawo. (Ta yi wannan karyar ne dan ta kare Mas'ud ko da wasa ba ta fatan wani abin da zai kawo matsala a tsakaninsu). Ta shis yi mishi daddin baki da yake ita gwanar iya magana ce Allah ya yi mata wannan abiwar kam a ci gaba da cewa, shi ya sa nake neman yardarka na.ci gaba da karatuna a maimakon zaman haka. Allah yana dawo da shi shi ke nan na hakura sai kazartar da duk abinda va dace. Wallahi Malam ka san ina kaunar ka ina gudun bacin ranka ba zan yi duk abin da zai zubar mana da martaba ko mutumeinmu ba, jikinsa ya yi sanyi ya ce shi ke nan ki ba ni lokaci zan yi tunani. 31 Ba a fi sati biyu ba ya ba ta izinin ci gaba da karatunta duk da an kai ruwa rana kafin Umma ta amincе a cikin wata daya ta gama yin duk abin da ya dace dace dangane da karatunta ta faca zuwa makarantar da ta dade da burin shigarta wato F.C.E. Kano. Da yake ra'ayinsu ya zo daya da Huwailat sai ya zamanto suna department daya ne bangaren Education tana karantar English/Sos. A wannan lokaci ne Ammar ya tafi Rasar South Africa kamfanin da yake wa aiki ne ya tura shị can har gida ya zo suka yi sallama ta kara tabbatarwa shi ke nan ta dada nisa da Mas'ud a ko da yaushe takan yi tsammanin zai bugo mata waya to ga shi wanda yake sada ta da shi ya tafi abin mamaki har zuwa lokacin da zai tafi yana sake nanata mata ta rike alkawarin abokinshi. Ta dai fahimci ba wanda ya fuskanci abind ake tsakaninsu ga rashin Fauziyya wace sukan yi hirar yayanta da shi ta fan ji sanyi abu dai ya dada cabe inata, dan ma a ko da yaushe Huwailat na kwantar mata da hankali tare da nuna mata kila akwai uzuirin da ya tsaida shi dan daga baya ta zayyane mata duk abin da ke gudana a tsakaninsu. Sannu-sannu suna karatu har suka kai zangon karshe na shekarar sun yi jarrabawa an musu hutun karshen shekara. Wata ranar Asabar da yamma ta yi wanka ta nemi iznin mahaifiayrta za ta je shopping centre. Ta kimtsa cikin atamfa 'yar Koddebuwa ruwan kasa dinkin me sharp ne ya fito mata da ainihin surar jikinta ilal dai ta yafa yalwataccen mayafi, takalmi da jaka bakake hakika kayank sun yi mata kyau domin ita bain a jikinta ne duk munin kaya in ta sa shi sai sun yi mata kyau. Ga shi Malam ba da gana nan ba wajen wadata iyalinsa in ka ga sutturun da suke sa wa sai 32 ka yi zaton 'ya'yan masu hali ne haka nan ta fannin abinci dama karatunsu. Ta sai Sahad Store ta nufi bangaren cosmetics ta shiga zabo tsadaddun turarruka da yake Alah ya yi ta da son kamshi. Turare komai tsadarsa mutukar a ya yiimata takan siye shi, hakika takan dada yin kewar Mas'ud domin tun da ya fahimci ita ma'abociyar son kamshi ce yakan siyo mata tsadaddun turaruka masu kamshi babu turaran da ta fi so irin (Pleasures). A duk lokacin da zai kawo mata turaren yakan hado mata da shi. Yakan ce mata Hanifa babu wani kamshin turarc da na fi so irin 'Pleasure' saboda haka nake so a ko da yaushe ki dauwama cikin kamshinsa kamkar yadda a ko yaushe shi ne abin shafawata. Wannan dalili ya sa ba wani turaren da ta fi so irin sa. Ta yi sa'a ta same shi a store din cikin hanzari ta debi guda biyu amma kuma da ta duba kudin dake jiki sai ta ga kudin da ke jakarta ko guda daya ba zai sai mata ba. tayi mamakin tsadar turaren. Ta ayyanawa ranta lallai ba karamin kudi Mas'ud yake kashe mata ba a bangaran turare ma kawai. Tana ajiye turaran da zummar ta samu me dan saukin kudi ta siya sai ta ji magana daga bayanta ana cewa, "Haba 'yamınata ya za ki ajiye wannan daddadan turaran.?" Ba ta ce komai ba dai ta ci gaba da abin da ke gabanta. Ya Kara matsowa daf da ita tare da daukar turaren. Ya kalle ta ya ce a gaskiya kar ki wuce wannan turaran duk wadannan babu me dadin kamshin kamar sa. Ta jiyo ta ga wannan sarkin ancin ai ko idonta ya yi karo da wani dan kyakykawan matashi ta rasa me za ta ce masa domin ya za a yi ta sanar da shi kudinta ne ya yi short. 33 Sai ta daure fuska na gode. Da tayin da ka yi min Malaım amına ba nid a ra'ayinshi. Ya yi murınushi gamid a zura hannu cikin aljihu ya tsare ta da itokin ga ko duk wadannan babu turaren da ya dace da ke irin wannan. Ni kuma ba ni da ra'ayinsa yaya ke nan? Ta fada cike da kosawa da surutun nasa. Ya yi murmushi mai da wukar amma na san kin fada ne kawai alhalin ba haka abin yakc a zuciyarki ba koba haka ba? mamaki ya kam ta sai kuma ya ce na fahimci haka ne ta yanayin kamshin turaren da ya ke fita daga gare ki ai ko ta tuan kafin ta fito ta feshe dan ragowar da ya yi mata saura. Ya ce ko na yi karya ne?* ta kalle shi tsawon dakikoki sai kuma ta dauke kanta ta yi bangaren maya-mayai tana zaba, a nan ma gwana ce, akwai ta da son mai me kamshi be gaji ba dai ya sake bin ta bari in taya ki zabar man ko. Ya dauko dan karamin kwando ya dinga diban duk wanda ya zo hannunsa yana zubawa har sai da kwandon ya cika. Ta kai hannu za ta dau wani may a dai-dai lokacin shi ma ya kai hannunsa yana kokarın dauka. Sai ji suka yi kowanne ya dauki hannun ſan uwansa ba tare da sun sani ba. Tayi saurin janye hannunta har ta ba shi dariya ya се kamar wanda zai cinye ki. Ta yi gaba za ta shige ya ce ga ajiyarki. Ta kalli tulin maya-mayan ta kada kai za ta yi gaba yà dan tari gabanta ko ba ki ji ba ne. na saka? Kwarai kuaw to ka rike abinka na gode. Ya ce Allah sai kin karba. Ta rike baki ta na mamakinsa sai kuma dariya ta kubисе mata. Ta ce, yau na ga ikon Allah, dan Allah Malam ka kyale ni. Ya ce in kina son na kyale ki sai kin karbа. Та fan ratse ta gefe ta shige shi ma ya bi bayanta suka jera tamkar ango da amarya. Ma'aikatan store din suka bi su da 34 allo cike da sha'awar wannan jaririyar soyayyar. AnAn zo vajen biyan kudi akai total din abin da ta siya aka zuba a cda za ta ba da kuddin aka ce Oga ya biya. Ta san wanda ke nufi dan haka ta ki yadda da ta ga sun ki karbar kudin ai ta hakura ta fita. Tana fita ya bi bayanta ya iske ta a arabar kantin ya sha gabanta ya tsaya yana murmushi ya e, 'Yan mata za mu rabu ba ki gayan sunanki ba. ta ce Malam ka yi hakuri sanin sunana ba shi da wani amfani a are ka, a ganin ki ko? To ni sunana Abdulzahir ba Malam ba. Malam din nan ta fita daga bakinki, kin gane ko. Тa kalel shi akwai ya ce kin san Allah in ba ki gaya n ba za mu i ta tsayuwa a nan. Tabbatar zancensa haka ne dan da lama irin mutanen nan ne masu shegen naci dabara ta fado nata tace sunana Bilkisu. Ya ce, to Malama bilkisu zo na kai ki gida ko. Ta ce a'a na gode ni Malamar nan ta fita daga bakinka bilkisu nake. Ya gyada kai to shi ke nan a yi min afuwa bisimilla mu je in kai ki ko? Ta ce yanzu kai kana ganin ya dace daga ganin mutum sai na shig amotarsa, wa ya sani ma ko dan.... Ta kasa karasa maganarsawa ya kwashe da dariya bari na karasa mi ko dna yankan kai ne ko? Amıma kuma ko yankan kai nake ina ga kanki ba zai tsada ba ko? Ta dan runtse ido sakamakon kunya da ta kama ta ya ce shi ke nan na yadda da uzurinki bari na samo miki taxi. Kan ta yi magana ya isa bakin titi har ya tsaida mota. Tana nazarin wace karyar za ta yi mishi tun da ta san titi kawai za tą tsallaka ta karya kwanar unguwarsu amma da ta tuna hakan zai ba shi damar sanin ainihin hakikanin sanin unguwarsu sai ta bi shi a hakan. Tа се masa tana unguwar Aisami sai da ya ga shigar ta motar mnan ya bude but din motar ya zuba tarin wasu kaya a 35 cikin ledodi sannan ya mikawa Driver 500 kudin mota mutumin ya karba cike da mamaki abin da be fi a ba shi #50 ba sai ya shiga yi masa godiya yaa dan leko jikin window ya ce masa ka fa kular min da mata kar wani abu ya same ta. Cikin hanzari ya ce to yallabai Allah dai ya saka da alheri. Sai da ya ga bacewar motar sannan ya shiga tasa ya tashe ta ya tafi. Suna zuwa dai-dai kofar gidansu ta tsaida dan tasi din nan ya kalle ta cikin fargaba tamkara wace ta ke shirin kwace kudin ya ce ba kin ce unguwar Aisami zan kai ki ba. ta yi murmushi saboda ta karanci abin da ke zuciyarsa sannan ta ce ba wani abu ka sauke ni a nan na fasa zuwa can din da sauri ya fito ya firfito mata da kayan da ke but din sai da ta ga kulewar me motar ta dan waiwaiga ta ga ba me bin ta sannan ta shiga gida. Bayan ta yi salah ta shiga bubbude kayan. Mamaki ya kamata ganin tsadaddun turarukan da maya-mayan da ke ciki, ta jinjinawa wannan mutum wanda ta yi masa lakabi dama wayo domin ta san ya zuba adashin da ba zai dawo ba, ko kuma ta ce ya zuba a bankin asara. Ta san ba ta yadda za a yi ya gano inda take. Ban da ma shirme daga haduwa da mutum ka kashe masa wannan makudan kudi ita kam ta san Allah ne ya kashe ya ba ta, ko da wasa ba ta nunaawa mahaifiyarta kayan ba dan ma kar wani abu ya biyo baya. Kashegari da yamma aka aiko ana sallama da ita. amma ta ki fita abin mamaki mutumin be yi zuciya ba sau hudu yana sake turowa ta je na karshen ne ya hada ta da girman Ubangiji ta je. To sannan ne ta fita ta ga wannan wane uban 'yan nacin ne. Tana isa soro ta iske wani kyakkyawan saurayi a tsaye ya sha hartin da wando na 36 Galila Kamshin turare sai tashi yake a jikinsa. Ta dan kalle shi tana nazarin ina ta taba ganin wannan kyakkyawar fuskar, amma ta kasa tuanwa. Ta dan rakube daga jikin bango ta gaishe shi a mutum ce ya amsa tare da jin dadin haka. Ta dan yi shiru tana satar kallonsa don gaskiya ya burge ta ba ta taba zaton za ta ga bakin mutum me kyau haka ba. ya dan yi gyaran murya har ta dan ji kunya ta kama ta. Bilkisu ya kika zo gida? Yana fadar haka ta gano ko waye ta rufe fuskarta da tafukan hannunta tana dariya. Ya ce ya kika rufe ido? Ka yi hakuri dan Allah. Da kika yi min me? Ni dai na ce ka yi hakuri na yi lefi. Nli ba ki yi min lefin komai ba, ba ka hakura bha ke nan? Gaskiya ban hakura ba domin kin wahalar da ni da yawa, kin san tun jiya nake nemanki? Ta ce a yi dai hakurin dai. Ya kura mata ido ta yi saurin kawar da nata shi ke nan na hakura amma kar ki kara,. Ta daga masa kai. Ya ce ta ina zan fara ne bilkisu? Au haka za ka ce ba ka hakuran ba ke nan? Ya yi murmushi to shike nan na gyara Hanifa. Ya ci gaba da cewa, a gaskiya Hanifa tun da Allah ya sa na gan ki kaunarki ta shiga zuciyata kauna ta fisabilillahi daga ni har ke dai mun mallaki hankalin kanmu, in dai Allah ya sa in amince a shirye nake na aure ki amına ban san abin da yake zuciyarki ba ni dai kin ji abin da ke zuciyata. Ta fan yi shiru na wani lokaci sannan ta ce, Hakika na gode da kaunar da ka gwadan ni ma kuma ina kaunarka kamar yadda addinin mu na Islama ya uamrce mu damu kaunaci junanmu sai dai kuma inda a ka samu akaisn ni ian da wanda nake so hasali ma mun yi alkawarin aure a tsaknainmu dan haka nake ba ka hakuri da ka je ka samu 37 kika ce ma? Ni na mance, ki macne da shi. ta harare shi, in mance da shi fa ka ce ya yi dariya, to a yi min afuwa amma abin da kike nufi ni ba shi nake nufi ba, to me nake nufi? A'a mu bar dai zancen. Ya shiga marairaice mata har dai ta ce ya ba ta lokaci za ta yi tunani, a kai sun dade su na hira har ya gangaro kankaratunta ya ce shi ma kanwarshi tana FCE a department din da take a karshe dai suka yi sallama. Tana shiga gida a ka biyo ta da tulin kaya mamaki ya kama ta tana ayyanawa ranta wannan mutumin Kila kudin ne suke masa kaikayi ganin yadda yake facaka da su. Ta sota mayar amsa da kayan amma kafin a gama shigo da kayan tuni har ya tafi duk da haka ta kudurce in ya dawo za ta mayar masa da kayansa da ta nunawa mahaifiyarta kayan fada ta hau ta da shi daman kuma abin da ta zata ke nan. Kwana uku a tsakanin Abdulzahir ya dawo ita har ga Allah ta mance da shi ta mance da sun taba haduwa da shi domin Mas'ud dinta kadia take so shi kadai ke zuciyarta a ko da yaushe kai ita ko sunan mutumin ma ba ta rike ba domin ba shi ne a gabanta ba. Lokacin da ta fita suka gaisa ya bkuaci jina msarsa sai ta diririce don maganar da suka yi ma a nan ta bar ta ba ta sake tuanwa ba sai a yanzu sai ta tsinci bakinta ta furta amincewa bukatarsa ba tare da ta shiryawa fadar hakan ba. shi ko dadi ya cika zuciyarsa yana ganin nan gaba zai iya shawo kanta. Har ta kai duk bayan kwana uku sai ya zo. A hankali a hankali suka soma sabo cikin dan kankanin lokaci suka shaku duk da ba wata maganar soyaya a tsakaninsu har ta kại ga duk al'ummar gidansu sun saba da shi musamman ansiba da Nusaiba har gidan yayyanta sai da ta kai shi amma kuma ta kasa bayyanawa kowa matsayinsa 39 a gare ta. Hutunsu ya kare suka koam suka ci gaba da karatunsu a kulluma ddu'arta Allah ya karkato da Mas'ud gare ta. Ya dawo suyi aurensu kamar yadda suka shirya. Yawan zuwan da Abdulzahir yake gidansu har ya sa suka saba da Huwailat don saboda nisan da ke tsakanin unguwarsu 'Yankaba da makarantarsu ya sa ta dawo wa gidansu Hanifa sai week end take koamwa gida. Sabo mai karfi ya shiga tskaninsu. Ta kan yi mamakin abin da kawar tata ta gaya mata dangane da alakar da ke tsakaninta da Abdulzahir ita kam tana kallon su ne kawai, ta tabbata su kansu zukatansu sun aksa amincewa da hakan balalntana ita. A duk fadin dinsu babu wanda 'yan department Hanifa ta tsana ko kuma muc e ta tsani halayyarta irin wata Zakiyya nasir. Yarinya ce me mutukar jiji da kai, da son nuna isa kowa kuma ya yarda da halayayr ta ce girman kai, dan haka ba sa shiri ko kadan. Kafin ta fahimce ta, ta kan yi mata magana amma sai ta share ko ta amsa a dakile har dai ta fahimce ta ita ma ta shiga share ta musamman da ta fahimci ta raina mata kura ne tund a ta fahimęi yawancin wadanda take hurda da su 'ya'yan amsu kudi ne. a koda yaushe ka gan su su biyu. Wato ita da Aysa wace ta kasa fahimtar kawarta ce ko'yar uwarta ce domin shakuwar tasu ta kai inda ta kai, sai dai abin mamaki sam halin Zakiyya da Aysa ba daya ba ne. Aysa akwai saukin kai ga ta da karamci duk da ita ma da alama 'yar masu halin ce sukan dan gaisa da Hanifa ko dayake lefin Zakiyya ya so ya shafe ta tana ganin duk ‘ya'yan masu hali fadin ran tsiya ne da su, wannan dalili ya sa in ba ta kure ba ba ta yi mata magana. 40 kwata ba Nu shirya mata ba dan haka kan Galibai ya fи A want yanme an ytmunn test waeee kwatienll d vake Zakiyya yarinya ce me mastiar kokari nai Лунн и bukact taimakonta duk da itu me ba baya by ce bn Zaklyya Rudundune ta da rattabo niyyar mata amsoshin tamboyin a paper t akardar ta fadin ta eilla wa Aужи дbin auisayi NAİ idon invigilator dat-dui kan cinyar Hanita a dar-dal lokacin faa paper ya budn yu kai ya kan Hanifa yu Karaso daf da tt yu wanda ga abin dake ciki ya kalli Hanita ya eillo jikinta mikr, fikinta ke Bari ya ee, na kama ki sat ki nuna wanda Nitm na tawa tu shijga ba shi hakuri amma ya Ki ya ma Kwace takardarta ya soke ta ya umarce ta da ta fita ta tabbatar kalli Zakıyyn ta ga da ta yi asmar waman test din. Ta ta janyo ta fauke kanta kammar ba tu sitn abin da Aysa mata ba, haushi ya dacla kama ta ta kurna kalli San Hanifan ti pa gaban daya ta rude ta yt sranda kawai tun da ta kanta. ta gane ita a kai niyyar jefawa abin ya facda ko dan Hanifu mutumein ta ayyanawa da zuciyarta ba za ta nuna Aysa ba ta ke gwada mata ummm ya zama dole ta nuna Zakiyya ko dan albarkacin izgilancin da take gwada shayin mata. Ba ma wai don abin da ta janyo mata ba, ba tare da komau ba ta nuna ta duk da dai da fari ta so ta musn wannan ya abu da ya faru shi ya janyo suka fadi a subject din sai shekara mn zuwa su maimaita wannan hukuncind a aka sassauci yi musu ke nan a matsayin Malamin ya yi musu ke nan. Tun daga lokacin gaa mai tsanani ta dada shiga tsakaninsu daman kuma tuntuni Zakiyya na jin haushin Hanifa saboda kafin zuwanta ita da wata 'yar kabilar Ibo su suka fi kowa Kokari a ajinsu amma da zuwan Hanifa ta 41 doke su a 6angaren Hanifa abin da ya fi ba t ahaushi shi ne Zakiyya yadda ta dauki gaba da ita duk da sanin cewa ita ta janyo mata wanan abu dan haka take ganin ita ba ta ji haushinta ba sai ita ce za ta dau gaba da kiyayya ta dora mata, gaba dayansu daga ita har Aysan ta hada ta watsar da su kallo ma ba su ishe ta ba. Hanifa da Abdulzahir sun samu kimanin watanni bakwai suna tare a duk lokacin da ya bijiro mata da maganar soyayya ta kan datse shi shi kuma ya ci gaba dajuriya don ya san me nema yana tare da samu har kuma wannan lokacin babu Mas'ud babu labarinsa. A 'yan kwanakin nan Abdulzahir ya matsa mata dangane da maganar aurensu, ya kan nuina mata wanda take tsananin kaunar da yana son ta yadda take son shi ai da tuni ya dawo sunyi auren. Da yake zancen duniya ba ya buya tuni yia samu labarin abin da ke wakana saboda haka yake kara karfafa gwiwa kila rabonsa ce a duk lokacin da ya yi mata complain a kan hakajn takan ji haushinsa tana ganin yand so ya yi mata fatan tsiya ne, dan kwanaki har fada suka yi a kan ya ce yana ganin yaudrar ta kawai yake yi shi ya sa ya ki dawowa sai daga baya suka shirya. Yau ranar juma'a bayan an yi sallar isha'I Malam ya yi kiran Hanifa zuwa falosna ta iske umma a ciki tana ganin haka jikint aya yi sanyi ta samu gefe ta zauna. Bayan 'yan nasihar da ya yi mata ya sanar da ita iyayan Abdulzahir ne suka zo neman aurenta, shi ne ya kirawo ta ya ji ra'yainta. Wai ai ji ta yi kamar an soka mata mashi a kirji a diririce ta ce Malam me ka ce? Ya ce abin da kunnanki ya jiye miki. Bakinta na rawa ta ce dan Allah Malam ka yi ahkuri shini ka mance da maganar Mas'ud ne? 42 ya ce na mance sai yanzu da kika tuna min fitsararriya, to bari ki ji tuni na share maganar wannan yaron daga zuciyata na edai kyale ki ne har Allah ya fito miki da wani wanda na yaba da nutsuawrsa ga shi ko Allah ya amsa addu'ata ni da kaina na yi bincick na tabbatar da yaron nagari ne ya fito daga uzri`a tsatatacciya ni yanzu ba wai ra'ayinki nake nema ba na kiraow ki ne in fita hakkinki na sanar da ke in kuma kin ki wallahi wallahi kin ji na rantse zan ahda ki da duk wanda na yi ra'ayi daman dan na yi alkawari zan ba ki zabinki ne amma tun da kina son yawo da hankalina zan yi maganinki. Cikin kuka ta ce dan Allah Malam a aika gidan su Mas'ud din a ji abin da iyayansa za su ce 'wallahi Malam na sna yana so na..... ba ta karasa ba umma ta daki bakinta cikin fada ta ce, to fitsararriya tun da kin fi mu sanin abin da ya kamata sai ki gaya mana abin da ya kamace mu mu yi, in ban da ma shashanci kin taßa ganin inda mace ke jiran namiji ko ko kin taba ganin inda iyayan mace ke zuwa neman aurenta ga dangin mijinta? Wato sai mu kwadayayyu ko. Su iyayan nasa inda da gaske suke ai ko da baya nan sa iya zuwa su zartar da wata magana me kwari, shin wa kika ga ya zo?" ni ina ganin Malam kai kake mata sako-sako, shin ta fi 'yan uwanta ne ko ko su sun fi ki ladabi da biyayya ne? daman ni tuntuni na tsani karatun nan na ce ka aurar da ita tuntuni ka ki kai kana ganin yarinya ce me ladabi to ga irin karatun taurin kan da ta yi yo mana nan, kai fada dai sosai har sai a Malam ya dakatar da ita, a karshe a ka ba ta zabi ko Abdulzahir ko kuma ya hada ta da duk wanda ya ga dama. 43 Da da daddare ita da Huwailat suna daki Huwailat na kwantar mata da hankali duk abind a ake ciki ta sani ta shiga yi mata nasiha da ta bi iyayanta cikin kuka Hanifa ta ce wallahi Huwaila ba wani abu ya fi dagan hankali ba irin haliln da Mas'ud zai riski kansa mutukar ya zo ya tarar na yi aure, kin san dai irin kaunar da muke wa juanmu, ni na fi tausaya masa fiye da kaina, shin yaya zan yi da alkawarin da muka daukarwa junanmu? Ta ce a gaskiya Hanifa kin kasa tsayawa gaskiya kin san dai Malam ko umma ke ko mu nan kawayenki babu wanda ya taba sukar Mas'ud a baya, tun da ko kika a kowa na ba ki shawara ki hakura da Mas'ud ki rungumi Abdul a gaskiya ina ganin kamar yaudrar ki yake yi inba jhaka ba ya za a yi ya kyale ki ba wani bayani ko shi ko iyayansa, ni in ban da abinki da

Chapter 3 of 7