Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 6
haife ba ta isa ta tsawatar ba, yanzu matsawa yara, ita kuma da yake mai tsananin 59 ME GARI YA WAYA? 3 son yaran ce sai ta biye mishi suka ci gaba da sangarta yaran ba tare da sauke nauyin da Allah (S.W.T) ya dora musu ba. Kwanaki biyu tana wannan nazari ta cimam Ambassador a turakarsa tayi mishi duk abin da ya dace sannan ta soko mishi da batun diyarshi, ni ko Alhaji ko wane irin laifi yarinyar nan ta yi maka ai sai a afuwanta mata, ba ka tausayawa halin da take ciki ne? haba-ban yi tsammanin haka za ta shiga tsakaninka da yaranka ba.... Katse ta yayi gami da 6ata rai, "Kaltum abin da yarinyar nan ta yi min ba na jin zan yafe mata nan kusa, irin dai abin da ya faru a lokacin aurenta duk ba sai na yi miki bayani ba amma a ce duk ba ta hakura ta saduda ba ta cі gaba da bibiyar yaron nan marar tarbiyya (Tahir). Haba wane irin zub da mutumci ne haka ko ko in ce wace irin rashin tarbiyya ce haka? A nan ta datse shi, "Yauwa Alhaji abin da nake so ka fahimta ke nan. Tambayar da ya kamata tuntuni ka yi wa kanka ke nan, rashin tarbiyya! Kana ganin ka ba ta ingantacciyar tarbiyyar da ta kamata dan musulmi ya samu?" Cikin fusata ya ce, "Wace irin tambaya ce wannan?" Та сe, "A'a kwantar da hankalinka Alhaji ka tsaya tsam ka yi nazari da kyau, lillahi warasulihi kana ganin ka ba ta tarbiyyar da ta dace?" Ta muskuta, Alhaji mu cire duk wani son zuciya mu kuma yi wa yarinyar nan adalci, duk abin da ya faru ta fayyace min ta kuma gane kuskurenta kuskuren da mu ya kamata mu nusar da ita kazalika ta kuma nemi afuwarınu, to saboda Allah dan meye ba za mu 60 ZAINAB KABIR BIROMAN afuwanta mata ba bayan ko ma menene mu ne sila. Eh! Da mun tsaya mun kau da son rai mun ba ta tarbiyyar da ta dace tun kan GARI YA WAYE da ba mu riske kawunanmu cikin wannan yanayi ba. Yanzu kam da GARI YA WAYE mana sai dai kaiwa mu dukufa wajen lalubo bakin zaren." Bayani fa take ta sakar masa ta ko ina ba tare kuma da ta tsame kanta ba cikin masu daukar alhakin wannan kuskure ba. To fa Ambassador ya yi shiru ya yi zuru sai zufa ke feso masa, hakika akwai kamshin gaskiya a maganganun matarsa. Kwana daya, biyu, uku kai har tsawonsati guda Ambassador bai ce da diyarsa komai ba a wannan yammaci ne ya dawo daga ofis yana zaune yana hutawa a falonshi ta yi salama ta shigo ta yi fari ta rame akwai yanayin rashin kwanciyar hankali a tare da ita duk da cewa ta dan warware daga rashin lafiyar da ta yi. Kanta na duke kamar ko yaushe ta shiga neman afuwar mahaifinta cikin kyakkyawan lafazi tare da nuna nadamarta, tuni zuciyarshi ta gama karaya, kauna da tausayin diyar tashi ya gama mamaye zuciyarshi, musamman tun lokacin da ya gama gano nashi kuskuren, gaskiya da sun bata ingantacciyar tarbiyyar da duk haka ba ta faru ba, ainma dai dan ya hora ta ya kuma dada sa ta a saiti sai ya dake ya ki nuna damuwarsa a kanta duk da har cikin zuciyarsa ba ya jin dadin halin da yake ganin ta a ciki. To amma babbar damuwarshi halin da yaron yake ciki da kuma rashin sanin makomarsa, zahirin gaskiya ya san'yarsa ta gwadawa yaron halin rashin da’a a kan idonsu ma wane bore ne ba ta yi ba. 61 ME GARIYA WAYA? 3 Fuskarshi a daure babu alamun walwala a tare da shi ya shiga fadin, "Zan iya goge wadannan kura-kuran da kika tafka ne tare da goge shi a zuciyata a ranar da Allah ya fito da mijinki kika kuma nemi afuwar irin rashin da'ar da kika aiwatar mishi, ina jin wannan ne kadai zai iya kankare mikin da kika dasa min a cikin zuciyata. Daga haka bai Kara cewa komai ba ya tashi ya shige daki. a Ta sami dan sassauci a zuciyarta, tun lokacin da dad dinta ya bayyana mata abin da ke zuciyarsa akalla yanzu yana amsa gaisuwarta duk da dai babu wani sakin fuska tare da shi ahalin yanzu tunanin ta ya fi karkata ne a kan mijinta, to amma kunya da kuma tunanin fuskar da zai kalle ta da shi shi ya fi damunta, tabbas ta sani ba ta kyauta ta masa ba a iya żamansu, watanni dai-dai har bakwai yana daure a gidan kaso dai-daid a rana daya ba ta taba tunanin ziyartar shi ba, anya ko ta kyauta? Ai ido ba mudu ba a ka ce ya san. kima, ko ma menene ya zama dole ta kawar da kunyarta da ma duk wani shakku ta fuskanci mijinta. Mutum daya ne ya fado mata wanda take ganin shi kadai ne zai iya yi mata jagora (sameer) to ko shi din ma tana shakku gami da kunyar tunkararsa musamman idan ta yi la'akari da abin da ya gudana a kwanakin baya. Abu na farko da ta fara yi shi ne fuskantar Sarki mabuwayi maigirma da daukaka, addu'arta a ko yaushe Allah ya kubutar mata da maigidanta ya kuma daidaita tsakaninsu. Karo na biyu ke nan tana taka rashin sa'a tare da barwa baba mai gadin sallahu gurin aminin mijin nata, sakon ba ya isa gare shi ne ko ko menene? Ba ta da wata hanyar da za ta sadu da shi face dai ido-da-ido din. 62 ZAINAB KABIR BIROMAN Ba ta gaji ba dai, da sanyin safiya ta isa gidan, sun gaisa tun kanta tambaye shi yake shaida mata wannan karon ta taki sa’a. ta fito da kwarin gwiwa daga cikin motar bayan da ta gaisar da baba maigadin. dattijon kirki mai iya rike mutumein kansa ba kamar nasu sakaran maigadin ba, tana so ta tambaye shi rashin isar da sakon ta ga Samcer din, tana kuma shakkun hakan. Zuciyarta ma sai ta fi karkata ga sakon ya isa gare shi ya ki dai zuwa ne kawai ko don yana jin haushinta ko kuma ma ya riga ya yi fushi da ita, in tai la'akari da abin da ya gudana a kwanakin baya. A nan jikinta ya yi sanyi, rashin kyautawa kam ta yi shi, to amma babu gudu babu ja da baya daga abin da ta yi niyya, don haka ta yi shirin daukar duk wani laifi da za a dora mata. Sashen Hajiya Hindatu (Mahaifiyar Samir) ta nufa a babbabn falon nata ta riske su, Sameer din da kuma mahaifiyarsa. Da fara'a ta karbe ta, "A'a Heedaya ce a gidan namu?" Ni ce Momy ta fada gami da russunawa Momy ina kwana? Lafiya lau Heedaya. Ta janyo ta taso, Zauna mana sai ka ce wata bakuwa, ya mutanen gida da Alhajin? Kowa lafiya Momy sun ce ma a gaishe ku. To madalla haka ake so. Ta sauya zancen ki ci gaba da hakuri da yardar Allah gaskiya za ta yi halinta nan ba da jimawa ba, mu dai kam mun shaida fanmu ba zai aikata wannan mummunan aiki ba. Abdul mutumin kirki ne da ne na kwarai, dan haka ki kwantar da hankalinki ki ci gaba da jajircewa da hakurin nan da aka san ki wata rana sai labari. Kanta na duke tana sauraron nasihar gami da ambaton kyawawan halayyar maigidan nata. 63 ME GARI YA WAYA? 3 a Jikinta ya dada sanyaya. wai me ya sa ne ta kasa gane hakan tuntuni ne sai yanzu da lokaci ya riga ya kurc? Na gode Momy. Ta fada a sanyaye. Ta kai dubanta gare shi kansa na wani 6arin tamkar ma be san da wata halitta wurin ba, ina kwana Sameer. Ta fada cikin raunanniyar murya. Da alama ma bai son amsa gaisuwar ganin yadda ya amsa a gajarce fuskarshi babu yabo babu fallasa kai ka ce ba shi ne Sameer din nan mai barkwanci ba. Shiru-shiru babu wanda ya ce da wani Rala tsawon wani lokaci, fuskantar wani abu ta yi ko kuwa, mikewa ta yi bari in duba kitchen na sama miki wani abin. A ladabce ta ce, a'a Momy dama kin bar shi na riga na yi break na fito. Uhim a yi haka bari dai ini je din. In ba so kike su o'oh a tuhume ni da kasa bawa matarsu abinci ba. Murmushi ta yi gami da sunkuyar da kai, shi ma murmushin ya yi to sai dai da fitarta annurin fuskarsa ya 6ace. Shiru dai be ce mata ba ita ma ba ta ce masa ba, kai ya yi ma kamar be san da mutum a gabansa ba. Bai fasa daga abin da yake ba ya kamımala tsaf daga karin kumallon da yake. Da gasken dai bai san da itan ba, yunkurawa ya yi da niyyar tashi cikin rawar murya ta ce, "Sameer ba ka ji sakona bane gurin baba maigadi? Wane sako fa? Ya dube ta. Ina ce ya gaya maka sau biyu ina zuwa nemanka har ma na nemi alfarmar ya turo ka tun da muna ta samun sabani. Kada kai ya yi, Auwoooo! Ina ce wani sako ne na daban. A kaikaice ya dan dube ta rashin zuwa na na da nasaba da rashin samun sukuni samakon wani babban gibi da ya shafi rayuwata, abu mai matukar mahimımanci a gare ni da ma duk wani mai kaunata. Sa kai ya yi sosai zai fita da sauri ta ce. Dan Allah ka saurare ni Sameer abin da ke tafe ni da ke 64 ZAINAB KABIR BIROMAN nan. Kamar ta sha gabansa saboda gudunkada ya subuce mata a ganint a shi ne kadai mutumin da zai iya sada ta da abin kaunar ta kana tauraron zuciyarta. Agogon da ke hannunsa ya duba, kada kai ya yi ya kuma kada kai, lokaci ya kure be sake ko duban ta ba ya tafi abinsa, tana Samcer, Sameer amma ko ya waigo ya dube ta. wani irin abu ta ji ya tsaya mata a zuci, ta dade a hakan har ma ba ta san san da hawaye ke zubo mata ba a haka Hajiya Hindatu ta riske ta. A'a ya kuma haka Heedaya? Ke da muke yaba miki wajen dakiya da hakuri, haba kar ki dada samu cikin damuwa mana. Hannu ta sa ta share hawayen da ke zubo mata, yauwa ki kwantar da hankalinki kin ji, shi mai gaskiya yana tare da Allah. Mikewa ta yi na gode Momy bari na wuce. Damota kika zo ne dan na ga fitar Sameer ay ce kun riga kun yi salama ko? Eh Momy. Da na san ba jimawa za ki yi ba ai da ya kai ki gida. ba komai Momy tare da driver muke. Tafiya take da kafafunta ba ta ko sha'awar shiga motar domin direban daya kawo ta ta sallame shi tun kafin shigar ta gidan. Da me za taji ne? me ya sa Sameere zai yi mata haka? Me ya sa zai kasa yi mata hanzari? Shi ne kadai mutumin da take ganin zai iya yi mata jagora, me yasa zai yi mata haka? a lokacin da take mutukar bukatar taimakonsa, a lokacin da take matukar so da kaunar abokinsa da nadamar abin da ta yi masa, so da kaunar da ta ke jin zai iya fasa kahon zuciyarta. Duk inda ta kai ga son su hadu da Sameer abin ya ci tura karara ya guje mata ya ma mai da ita kamar wata sauna, ba ta yi fushi ba ba ta kuma gajiya ba ta ci gaba da bibiyarsa. 65 ME GARI YA WAYA? 3 A yau dai sai ta yi mai gaba daya ta cimma sa a ofis, karyarsa dai ya ce zai wulakanta ta a gaban jama'a, dole ne ya mutumta ta ya kuma darajata ta in dai kaunar da yakewa abokinshi ta domin Allah ce. Ba ta ko saurari sakatariya ba da ta sha yi mata shamaki, ko don rashin sanin matsayinta ne? ko ko wani dalili ne na daban? Kusan a lokaci guda suka shiga da sakatariyar. Sakatariyar na wani irin huci tamkar ta fisgo ta a tunaninta ire-iren 'yammatan da suke mu'amala da su ne tana matukar kishi da jin zafin hakan, ita kadai ya cancanta a so ta duk da ta fuskanci ba ta ciak wani daďa shi da kasa ba. Yana zaune kan daya daga cikin kujerun da ke ofishi a gabansa faffadan teburi ne mai dauke da tarin takardu da alama aikin ya cunkushe mishi ko ko ba ya ra'ayi ne? kanshi ya dago da zummar ganin abind ake wakana a lokacin da Sera diyar Baburawa ke kokarin janyo kafadunta, tsawa ya daka mata, ke wace irin sakarai ce ne? in ce ko kanki ya motsu ne? kallon shi ta yi, da ke nake? Ya tambaye ta. Cikin yaran nasara take shaida masa keta dokar ofishin nasu da ta yi (shigowa ba bisa ka'ida ba) shin ba ki san wace ce ba ne? kai ta kada. Shi ne za ki nunawa mutane halin rashin da'a. Ya ja dogon tsaki, maza kama gaban ki ba bukatar ganinki a nan. Rufo kofar da ta yi ya yi dai-dai da fuskantar junan su, ya rasa me zai çe mata sai kawai ya kau da kai, ita ma kau da kan ta yi gami da tame fuska. "Duk wani kuskure da dan'adam ya yi ya kuma gano hakan har ma yake kokarin neman afuwa ya kamata a tsaya a saurare shi a fahimce shiba wai a dinga guje masa 66 ZAINAB KABIR BIROMAN ba. Kuskure ne na san na yi na kuma fahimta don haka ne nake neman tallafi daga gare ka ka sada ni da abokinka na nemi afuwarsa harma na bayyana mishi radadin kaunarsa da ke zuciy..." Datse ta ya yi cikin fusata ya juyo ya dube ta, "me kike nufi ne? me hakan ke nuſi ne? ko kuwa makuwa kika yi-ne? to idan makuwa kika yi ki tsaya da kyau ki fahimta Sameer ne aboki kana dan uwa, masoyi ga mutumin da kika sha bayyana rashin kaunarsa a zuciyarki, wannan kalamai naki tamkar tatsuniya na dauke su, ya kamata ki rufe da kurunkus shi ke nan ta kare." Numfasawa ta yi da niyyar magana, katse ta ya yi da hannu gami da kadamata kai, “ki yi hakuri ba ki da wani abu da za ki gaya min, kun hada kai ke da saurayinki domin kai shi ga halaka ya tafi ya bar muku duniyar ku sha kuruminku. A'a ya girgiza kai burinku ba mai yiwuwa ba ne za mu yi iya bakin kokarinmu wajen tabbatar da gaskiya." Hawaye ne ya zubo mata a lokacin da ta kama murfin kofar da niyyar fita, "Kazafi ko zargi kuskure ne wannan na ji na kuma saurari duk abin da ka ce sai dai bai zama dole na aminta ba, ka tsaya ka fahimta ko kada ka fahimta, ka aminta ko kada ka aminta wannan duk daya ne abin da na furta shi ne a zuciyata ba gudu ba ja da baya daga kaunar dan uwanka, ruwanka ne ka yi duk yadda za ka dai sasanta daya mu, ruwanka ne kuma ka bijirewa hakan, kauna ce aminci ma daya ne, in dai aminci da kaunar nan gaskiya ne." Kwakwalwarsa ta gama hautsinewa da kalaman yarinyar, tsawon yinin ranar zuciyarshi sai kai kawo take a 67 ME GARI YA WAYA? 3 tuanninsa ba wani ne ya jazawa dan uwansa wannan halin da yake ciki ba face ita matarsa, ta kuma zo ta guje masa har ma take sauraron mutumin da yake da yakinin shi ne silar faruwar wannan lamari ga dan uwan nasa. Meye dalilinta na dawowa daga rakiyar tasa? Me ya hado su? To sai dai duk wannan tunani nasa yana rugujewa a lokacin da ya hango kalamanta na karshe, gaskiya ne "Kauna da aminci daya ne... in dai kauna da amincin nan domin Allah ake yin su..." Wannan ya share ya kuma tunkude duk wani zargi da ke zuciyarsa. Kuskure ne kam ya tabbatar da babu wanda ba shi da irin nasa (wato a tsakanin ma'auratan). Kwanaki hudu a tsakani yana nazarin abin yi, fushi ta yi ko menene har yanzu dai ba ta sake ce masa komai ba, bayan ko ita ta san abin da ke zuciyarta na daga kunci da rashin sukuni. Duniyar ta rikice mata har ma ta rasa tudun dafawa, ko ina ba dadi, ga fargaba da tsoron da ya cika zuciyarta na hakkin mijinta muddin shi ko ita suka fuskanci Ubangijinsu a wannan hali da suke ciki ba ma kamar ita, hakika ta kasance daga masu hasara domin ta kasa yi wa mijinta da aljannarta take karkashinsa biyayya. Har cikin gidan ya shiga sashen Ambassador sun gaisa tare da alhinin halin da ake ciki, sun jima suna tattauna matsalar da ke gabansu, a kokarin da suke na samun kwararren mai kariya (lawyer) da zai ci gaba da kariya ga Waheed. Ba su gamsu da aikin da mai kariyar da yake kare shi a halin yanzu ba, ganin yadda ake ta samun nasara a kansu duk da kasancewarsa kwararre ne a wannan fanni. Bayan sun gama tattaunawar ne ya tura a ka kirawo Heedaya kamar yadda shi Sameer din ya bukata. 68 ZAINAB KABIR BIROMAN Ta shigo rike da hannun mardiyya jikinta sakaye da yalwataccen hijabi, russuna wa ta yi ta amsa kiran mahaifinta kamar dai ko yaushe tana fuskantar rashin fuska daga mahaifinta tamkar ba dad din nan nata da yake shagwabata ba, har ma shi Sameer din ya fuskanci haka ya mike suka yi musabaha domin daman fitar yake harama. Tana rike da hannun mardiyya ta gaishe shi, babu wata fara'a tare da ita. Akwai yanayin damuwa da fargaba a tare da ita bayan ramar da ta yi ba ta kara ce masa komai ba illa sunkuyar da kai, yanayinta ya ba shi tausayi, kai sai ya ji wani iri ma a zuciyarshi tare da tuhumar kansa na rashina dalcin da ya gwada mata, ai mace daman mai rauni ce. Na zo ne domin neman afuwarki a bisa rashin kyautawar dana yi miki, bayan ko Allah ne kadai ba ya yini kuskure, don haka ina mai ba ki hakuri da kuma alkawarin tallafa miki gwargwadon hali domin sabinta tsakanin da dan'uwana. Wata irin ajiyar zuciya ta saki, na gode Sameer abin da tun farko ya kamata ka yi ke nan ba ka yi fushi da ni ba, na rasa yadda zan yi da rayuwata Sameer. rayiuwata na cikin wani irin kalubale ko ina babu dadi, uhm shin yaya zanyi da hakkin dan'uwanka a bisa kuskuren da na tafka? Ka taimaka min Sameer ya fahimce ni na tuba na gane kuskurena, ba na fatan kara kwatanta abin da ya gudana. Na yi mishi ba dai-dai ba ni na sani, shin ya za a yi mutumin da ka yi wa irin haka ka nuna mishi kiyayya karara ya tsaya ya fahimci tsantsar kaunar da kake masa, kauna mai tsafta, kaunar da babu 69 ME GARI YAS WAYA? 3 algus a cikinta. Wallahi ina rantsuwa da Sarkin da ya halicce ni ina kaunar dan uwanka da zuciya sahiliya, hakika na dade ina jin wannan abin a zuciyata amma shedan da sharrin zuciya sai su rinjaye ni. Ina neman tallafinka Sameer ka taimaka ya fahimce ni, domin na san kauna da amincin da ke tsakaninku. Ka taimaka min mahaifana fushi suke da ni duk dai a kan hakan, kai kanka ka fahimci hakan. Na rasa sukuni na rasa jin dadin zuciyata Abdulwaheed kadai nake so, shi ka fai nake kaunata a zuciya da gangar jiki baki daya, haka na kuma fahimci shi kadai ne mutumin da yake kaunata da gaskiya, ka mance da baya Sameer ka taimaka min. Bai tari numfashinta ba har sai da ya bari ta amayar abin da ke zuciyarta. Nasiha yake mata bayan da ya gama kwantar mata da hankali da kuma nuna mata martabar aure da sakamakon duk wanda ya wulakanta sunnar ma'aiki. Ya ci gaba, "Don haka ina fatan hakan ba za ta sake faruwa ba duk da cewa na san kowa ba zai rasa nashi dan kuskuren ba, to amma zahirin gaskiya kuskuren ya fi ta'allaka ne a kanki domin ke ce karama ke kuma kike karkashinsa, to don menene za ki kasa yi masa biyayya? Har ma ki dinga kebancewa da wani namijin da ba muharraminki ba? wannan kuskure ne. wannan kadai ya ishe ku gaba dayanku afkawa akan musibar da za ku rasa kanta, aure sunna ce ta Ma'aiki bai kamata a yi wasa da ita ba, har ma a wulakanta shi, abin da ya gudana a baya ai ya ci a ce ya wuce sai kuma kokarin shimfida managarciyar rayuwa, amma duk ku 70 ZAINAB KABIR BIROMAN kuka ce a'a kuka kasa yi wa junanku afuwa, to yau dai ga ki a durkusite kina begensa a lokacin da shi kuma yake fuskantar hukuncin barin duniar dungurungum." Kuka ta saka, dakatar a ita yu yi. "A'ah ba kuka za ki sa ba, ku kuka jawa kanku da aurenki saboda Allah ki dinga sauraron wani kato to yau ga abir da kika janyo masa, dominn ba na kokonto dar'uw a zai taбa aikata wannan mummunan aiki ba faee sn lahir." Da sauri ta dube shi, “Kai na ka yı hasashen haka?" ta ci gaba, "gaskiya ne ni kaina na dade ina hasashen haka har zuwa lokacin da wasu dalilai suka sa na dáda gasgata haka." Ta dada tattara hankalinta, "Sameer zan sa rigar aiki domin karyata zargin da ake yi wa mijina domin ni kaina na yi imanin Abdul ba zai aiksta wannan ta'addanci ba. Abin da nake so da kai ka yi kokarin sada ni da shi, ya tsaya ya fahimce ni domin ko meye ya ta'allaka ne a bisa goyon bayan da ya ba mu, domin in har ba mu fahimci junanmu ba ma iya samun nakasu. Abdul ya yi fushin da ni ni na san haka, sakamakon shaidan da ‘yan kanzaginsa da suka shiga tsakanin mu, musamman da yake akwai abin da ya gudana a tsakaninmu a ranar da abin zai faru, na san wannan kadai ya isa ya rike ni, ni da kaina sai daga baya ne na soma gano bakin zaren. Kamar yadda ya alkawarta karo na uku ke nan yana ziyartarsa duk dai a kokarinsa na sulhutan su amma ya tsaya ma ya saurare shi koya fahimce shi ina. Duk da cewa ganin nashi ba abu ne mai sauki ba da kuma rashin 71 ME GARI YA WAYA? 3 isasshen lokaci. Duk wata kafiya da tarin kai da yake tunanin zai fuskanta abin ya fice gaban haka. Daya bayan daya yakan kasance cikin tunanin nau'in zaman da suka yi da yarinyar da irin rashin ladabin da ta nuna masa, da kuma tsantsar kiyayyar da suka gwadawa junansu, abu na karshe mafi kuma muni matarsa da cikin wani wanin ma babban makiyinsa. Cuta kam yarinyar ta riga ta yi mas ababu zancen afuwa a tsakaninsu. Yanayinshi kawai za ka kalla da zai tabbatar maka da cewa ba ya cikin kwanciyar hankali, ya yi baki ya rame ga kasumbar da ta cika fuskarsa, kai ba ka ce Waheed din nan ne dan kwalisa ba.cikin sanyi-sanyi amma akwai yanayin bacin rai a ciki yake yin furucinsa, na vi mamakin haka daga gare ka ba, a matsayinka na Kina dan'uwana, amma kake kokarin raina min tunanina, a zatonka na sauya ne daga bigiren da nake, yarinyar nan ta cuce ni ta kuma gwada min kiyayya ba tun yau ba amma kuma kake kokarin mai da ni kamar wanda bai san ciwon kansa ba, kaunar ganin ta ba na son yi, ballantana har ka yi kokarin sada ni da ita. Ta cuce ni, ta cuce ni, ta yi min babban gibi a rayuwata. Tahir! Heedaya! Ba don komai zan so in fito ba, ba don jin dadin wata rayuwa ba sai domin in dandana muku gubar da kuka dasa min a zuciyata. Katse shi ya yi, "Haba malam ka dinga adalci a cikin lamarinka mana, shin in har Heedaya na da laifi kai ba ka da shi ne? kai ne fa babba kai ne kuma jagora, 72 ZAINAB KABIR BIROMAN wane irin zama ka yi da yarinyar nan? Shin menene ba ta gani ba daga gare ka? Tsana da tsangwama da nuna halin ko in kula duk kai ne amma a hakan ta jure ta yi hakurin zama da kai har ma ka sanya ta cikin damuwa sakamakon halin da kake ciki, in har ka amince ta nuna sha'awar ta taimaka...." "In kuma ban amince ba fa?" Ya tambaye shi. Kallon shi yake ba shi da niyyar tanka masa, ya ci gaba da fada, "In har sai yarinyar nan ce za ta yi silar fitar da ni daga wajen nan to in dauwama a wajen nan, ka je ka shaida mata tun da kai dan sako ne." fada yake gami da fadar zafafan kalamai a gare ta da shi kansa Sameer din. Shiru ya yi har ya yi ya gama be fusata ba, ya bi shi sannu a hankali, daman shi ba ma'abocin fushi ba ne da kuma cewa shi ya fi kowa sanin matsalar. Kwantar da harshe ya yi yana yi masa nasiha gami da jan hankalinsa a kan kyawawan lafuzza. Shi daman gwani ne wajen tsara magana, bai gushe ba har sai da ya tankwarar da zuciyarshi. Ya ci gaba, "Na sani cewa Heedaya ta saba maka, to amma mu dauka cewa kowane bawa ajizi ne Allah (S.W.T) ne kadai ba ya kuskure don haka sai mu yi mata afuwa mu manta da abin da ya gudana. Abu daya ne nake so ka fahimta a wannan lokaci yarinyar nan tana yi maka kauna ta hakikatan, ba na jin in ba ta kaunarka za ta shiga wannan halinda take ciki, ta damu ainun fiye da zatonka. Ka san lamarin Ubangiji babu abin da bai iyawa 73 ME GARI YA WAYA? 3 shi mai iko ne a kan komai a kuma lokacin da ya so, don haka ba abin mamaki ba ne ganin ta riski kanta a wannan hali. Kamar yadda ka sani ne kiyayya ta kan juye ta zama soyayya, ko da yake ko can bava ban taba daukar junanku a matsayin makiyan juna ba lace dai wani dalili da ya

Chapter 5 of 6