Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 7
kawai sai jijiyoyi su hade. Da ma duk inda aka gutsura, sai ka ga jini ya makale a jikin gundulmin, ba ya gangarewa kasa. To bayan an gama wadannan aikace-aikace ne sai aka ce Muhammadul Ziyara ya kwanta a wani gado don a karasa aikin. Da ya kwanta sai aka kawo wata katuwar kwalba aka ajiye kusa da shi, aka kuma kawo wadansu bututu sirara na roba aka sassarkafa masa. Aka ce ya rufe idanunsa, ya rufe, aka tsaga hannayensa guda biyu a daidai inda magudanar jini ta ke, aka sassa wadannan bututan roba, to fa a wannan lokacin ne Muhammadul Ziyara ya sami allura mai sa barci daga wurin wannan likita. Ko da aka yi masa allurar nan sai ya shiga barci. Sannan kuma da yin barcinsa sai likitan nan ya shirya yadda duk jinin Muhammadul Ziyara zai kwararo ya koma cikin kwalbar nan. Aka kuwa kwashe manya-manyan kwalabe biyu masu kama da tulun ruwa, na jinin dan talikin nan. Likitan nan da ya sami wannan jini sai ya zuba wa jinin wadansu ruwan magunguna a ciki, sannan ya kawo wani irin garin magani fari ya zuba, ya dai yi 'yan hade-hadensa ya gama, sannan ya je ya mayar wa da Muhammadul Ziyara jininsa duka. Ko da mayar da jinin nan nasa sai ya farka, ya tashi ya zauna ya ji kuma kamar shi kansa ba shi da lafiya, wannan lokacin ne fa likitan ya gane lallai shi wannan dan taliki ya sha wuya, saboda haka sai ya je ya kai masa ruwan zafi ya sha, sannan kuma ya yi masa allura mai sa karfin jiki. Bayan wannan allurar kuma sai ya yi masa wata mai kashe tabbai, ana yi masa wannan allura mai kashe tabbai sai ya ga dukkan tabban da ke jikinsa hatta wadanda ya yi lokacin yana 40 Tauraruwa Mai Wutsiya dan mitsitsi sun shafe, sai ya koma kamar wanda aka haifa a yau. Muhammadul Ziyara sai ya tashi a kan gadon da aka yi masa aiki ya je ya zauna wajen da Likitan nan ya ke. Likitan ya gaishe shi sannan ya gaya masa cewa lallai bayan kwana bakwai babu wani abu da zai gagare shi, kuma komai ya ga ana yi shi ma in ya so ya yi, saboda haka babu abin da ya kamace shi sai ya samu ya nufi hanyar garinsu ya sami hutu na ko da kwana shida. To daga lokacin dukkan abin da ya so sai ya yi, kuma a cikin lokacin da yake hutawa ne zai san cewa lallai shi wannan garambawul da aka yi masa ya yi daidai. Kuma dukkan man da aka sa in ya jika, to shi ke nan sai ya shiga sha'aninsa. Muhammadul Ziyara sai ya yi godiya kuma ya yi sallama da wannan likita ya kama hanyar garinsu, yana mai mamakin abin da zai faru idan wannan garambawul ya zauna sosai a cikin jikinsa. Can kuma sai ya ji ma ai ko mene ne dai, to ai ya riga ya gama ainihin abubuwan da suka kamata, kuma abubuwan da suka rage masa kawai su ne zuwa gida ya ga mutanen garinsu da kuma zuwa taurari. Maganar dawowa ko oho, shi dai in ya samu ya kai ga biyan bukata, to ko me ya faru ya riga ya yi namiji a wannan duniya mai wuyar kamawa. Muhammadul Ziyara na cikin tafiya sai ya hango wata 'yar bukka a gabansa. Gabanta kuma ga rijiya ga guga ga kuma dan gora, saboda haka ma sai ya ga cewa to me ya kamace shi in ba ya yi maza ya je ya dauki wannan gugan ya debo ruwa a rijiyar nan ya kuma zuba a cikin goran nan ya yi alwala kuma ya yi Salla ba? Nan da nan kuwa ya isa gindin wannan rijiya, ya debo ruwa ya yi alwala, sannan ya yi Salla. To ko da gama Sallar, sai ya ga ya kamata ya yi sallama a rumfar nan ya yi wa mai wurin nan godiya, tun da ya haka rijiya, sannan ya ajiye irin wadannan abubuwan don amfanin jama'a. Ko da ya yi sallama sai wani dan tsoho ya leko ya ce, "A'a yaya ne dan samari, ko lafiya?" Sai kuwa yaron ya gaya masa cewa shi yana neman hanyar Karinda ne, kuma sai ya ga guga da sauran abubuwa har ya yi Salla, shi ne kuma ya yi zaton lallai akwai mutum a wannan daki har kuma ya yi sallama don ya gode masa. Abin ya bai wa tsohon nan sha'awa na irin hankalin wannan yaro har kuma ya yi mamakin irin son addininsa, saboda 41 Tauraruwa Mai Wutsiya haka ne ma har ya sawa Muhammadul Ziyara albarka, kuma ya kawo dukiya mai yawa ya ba shi, sannan ya ba shi mutane guda uku suka taya shi daukar kayan nan, kuma ya ce su wadannan mutanen za su kai shi har Karinda, watau garinsu. Muhammadul Ziyara tare da mutanen nan guda uku sai suka dauki kaya suka fara tafiya, suka kuwa yi ta yin sauri har suka fada kan wata shahararriyar hanya wadda za ta kai su Karinda. Suna fadowa wannan hanya kuwa sai Muhammadul Ziyara ya gane hanyar kauyensu kuma sai ya shige gaba suka yi ta tafiya, har suka kusa da wannan garin. A lokacin da suka kusa da garin nan na su Muhammadul Ziyara wanda shi a garinsu an san shi ne da Kilba, sai ya ce su wadannan mutane uku su je su shiga Karinda su tambayo masa baffan Kilba wanda ya bar garin tare da Kolin Koliyo, in an nuna musu shi, sai su ba shi wannan kaya sannan su gaya wa baffan nasa cewa shi Kilba yana tafe. Mutanen nan suka kama hanya suka isa gari, shi kuwa suka bar shi nan yana zaune a gindin wata 'yar bishiya. YA JE SALLAMA GARINSU Ko da shigar mutanen nan cikin garin Karinda da kaya niki-niki, sai mutane suka fara kallon su, wadansu kuma sai nuna su ake yi da baki ana ta mamakin daga ina irin wannan kaya ya fito? Wadansu irin 'yan karambanin nan sai cewa suke yi, "Sannunku, ai ga hanyar gidan Sarkin nan." Su kuwa sai su kyale su kawai. Can suka hadu da wani yaro dan saurayi wanda shekarunsa za su yi kamar Kilba suka ce da shi, “Sannu samari, don Allah ko ka san Kilba na Kolin Koliyo?" Sai wannan saurayi ya ce, "Kai ku kyale wannan yaron banza wanda ya dauki ransa ya makala ga abin da ba ya yiwuwa, ai ma yanzu mun san ya riga ya mutu domin yanzu 'yan yara kanana ma ba za su san shi ba, ku yi dai gaba ku tambayi Musku tsohonsa, tun da yana da jakuna watakila zai iya daukar muku kayan naku." Su wadannan mutane sai mamaki ya kama su, suka dai yi shiru da bakinsu saboda irin wadannan maganganun banza da wannan saurayi ya fada. Ba su yi nisa kwarai ba kuwa sai suka gamu da wani dan tsoho yana saye da shudiyar riga rike da carbi yana ja. Yana kuma tafe a dudduke, sai suka gaishe shi. Nan da nan kuwa ya amsa yana mai fara'a kuma ya tambaye su ko su baki ne. Suka ce 42 Tauraruwa Mai Wutsiya haka ya ke su baki ne, sai kuma suka tsaya shiru dukkan su, shi yana mamakin su na sun gaishe shi, su kuma suna mamakin yadda ya tambaye su ko su baki ne. Can sai ya ce, "Ai ba don ku baki ba ne na san da ban sami gaisuwa daga gare ku ba, domin mutanen garin nan sun mai da ni wani wawa, wai na rude, dana ya bi wani aljani ya mutu ni kuwa ina nan ina ta yi masa addu'a ya dawo lafiya. Abin dai sai hakuri su mutanen yanzu domin in banda shakiyanci ba abin da suka tsare, babu tsayuwa da sakankancewa da ikon Allah, sannan kuma lalaci da sharri da rashin tausayi da son abu ya yi musu yawa. Sai dai Allah Ubangiji ya kiyaye bayinsa." Mutanen nan sai tausayi da al'ajabi ya lullube su, suka dai yi kokarin sakaya wannan tunani da ya sarke zuciyarsu, suka tambayi wannan tsohon ko ya san Musku mahaifin Kilba? Sai kuwa tsohon nan ya ce, "Ai ni ne Musku." Ya kara da tambayar su ko lafiya suke neman sa? Sai suka ce ai lafiya lau, sai dai ya juya su tafi gida domin dansa Kilba shi ya aiko su, kuma ya ce a gaya masa yana isowa an jima. Musku fa dadi ya kashe shi, murna ta kama shi, nan take ya yi godiya ga Ubangiji Madaukakin Sarki, sannan ba tare da nuna wata razana ko gigicewa ba, sai ya juya yana jan carbinsa suka nufi gidansa, yana mai imani ga Ubangiji da hakkakewa da cewa kyakkyawar aniya ko yaushe takan sami hanya mai kyau. Suka isa gida, aka shiga da kaya gida aka kuma sanar da mutanen gida cewa Kilba yana zuwa. Aka kawo wa wadannan mutane tabarma suka zauna, sannan aka shiga shirin yin abinci don baki. Musku kuwa sai ya zauna a zaure yana hira da wadannan baki. Shi kuma Kilba lokacin da aka bar shi a wajen garin nan ashe ya kira Kolin Koliyo don ya zayyana masa ainihin irin abin da ya faru kuma da irin abin da ya samo a hanya. Kolin Koliyo ya ba shi zinaren nan da ya karba a daji lokacin da ya koma daga sama, don kila zai so ya yi tsaraba da su. Sannan ya gaya wa Kilba cewa su wadannan kayan yana iya amfani da su. Bayan sun gama zancensu, sai Kolin Koliyo ko kuma Muhammadul Sama ya gaya wa yaron nan cewa bayan kwana biyar ya yi sallama da mutanen garinsu ya kuma tafi ya same shi a bayan gari da yamma don su je su yi tafiyarsu. Kilba ya yi murna da abin da Kolin Koliyo ya gaya masa, ya yi godiya 43 Tauraruwa Mai Wutsiya sannan kowannensu ya kama gabansa. Kolin Koliyo ya bace, shi kuma Kilba ya kama hanya ta shiga garinsu. Ko da Kilba ya shiga garin nan nasu kuwa sai mutane na ta mamakin ko ainihin Kilba ne ko kuma wani ne. Wadansu sai su zo su tambaye shi don dai su ji kwakwaf, wadansu kuma sai su yi ta kallon sa suna mamaki, wadansu kuwa sai su tuno da lokacin da ya janyo musu aljani mai sunduki, sai su ce, "To Allah ya kiyaye, ga wannan hatsabibin yaro kuma ya komo." Wadansu kuma sai su sake duban sa su ga irin kayan da ya sa, sai su ce, "Lallai wannan inda ya tafi din nan ba tafiyar tsiya ya yi ba. Mu kuwa har da muna tsammanin ya mutu." Har sukan kara da cewa, "Da mutum zai dage a yi tafiya ta neman dukiya ai ka ga da abin ya fi mutum ya zauna jagwab a gida, yana neman na fura a wurin wadanda suka dage suka yi aikinsu." Kai duk garin dai sai surutai za ka dinga ji iri-iri. Shi kuwa Kilba kafin ya kai gida mutane sun shiga rakiyarsa, abin ma ko kunya mutanen ba su da ita, da ana ta zagin tsohonsa, to ga shi kuma yanzu sai yabon sa ake yi da kwarzanta kokarinsa don a je a sami dan abin karyawa a wurinsa. Yaron nan wato Kilba ya isa gida ya tarar da mutanen nan da suka daukar masa kaya na zaune tare da tsohonsa. Ya dakata tukuna ya gaishe da tsohonsa, sannan ya sallami wadannan mutane da suka rako shi, suka yi tafiyarsu. Daga nan sai ya ce wa sauran jama'a su koma tukuna yana so ya je ya yi wanka sannan can bayan magariba in ya gama Salla, sai jama'a su zo domin su gaisa. A lokacin da kowa ya watse, sai manyan 'yan sana'ar kawai aka bari, wato masu roko, su ne suka nace har da aka so a kafa kida, to amma sai ya ce shi ba ya son kowa ya dame shi. Kilba fa ya shiga gida mahaifiyarsa da dai sauran jama'ar gida duk suka zo suka sake ganin sa don kuwa ya yi wani girma saboda dadewa da ya yi rabonsa da wannan gari. Bayan Kilba ya natsa sarai, sannan ya sami damar gaya wa mahaifinsa ainihin abin da ya faru, mahaifin nasa kuma ya yi masa godiya saboda dauriya da ya yi don ya sami abin da yake so, kuma ya yi masa fatan ci gaba da dauriya, kuzari kuma da samun amfanin abin da yake yi. Kilba sai ya yi ta kyauta da riguna da zannuwa da kayayyaki iri-iri, sannan kuma aka shiga gina wa mahaifin nasa 44 Tauraruwa Mai Wutsiya wadansu soraye har ma da bene. Idan ko aka gama wannan ginin to Malam Musku shi zai zamo mutum na farko da ya yi bene wannan gari na Karinda. a A garin nan aka yi ta harka ana jin dadin kwazon wannan dan saurayi, kuma har wadansu yara masu tasowa suka kuduri aniyar ba za a bar su a baya ba wajen neman ilimi da sauran hulda daban-daban na duniya. Kilba sai ya yi kwana biyar a kauyen nan nasu, kuma ran na biyar din da zai tafi ya raba wa iyayensa sauran dukiyarsa da ta rage, ya gaya musu cewa shi ba ya bukatar ko kadan daga cikin ta don saboda babu wanda ya san abin da zai samo a wannan fitar tasa. Iyayen nan nasa suka kuwa cika da farin ciki, suka kuma yi masa fatan alheri a kan dukkan abin da zai yi suka kuma yi masa fatan dawowa lafiya. Kilba ya zagaya abinsa ya fita daga garin nan ba tare da sanin jama'a ba, ya je inda ya kamata da ya sami Kolin Koliyo, to amma sai ya tuna ya mance da zoben nan da yarinyar nan tasa Bintun Sarauta ta ba shi, kuma yana bukatar daukowa amma ga lokaci ya kure. To kamar wasa sai ya mika hannunsa wejen fuskar gidan nan nasu, sai kuwa ga zobe ya zo. Nan fa sai ya shiga tunani, ya ga cewa lallai watakila aikin nan da likitan nan ya yi masa shi ya sa shi a irin wannan madaukakin hali. SUN TAFI ZUWA TAURARI Ko da gama gane cewa aikin likitan nan ya yi, sai Muhammadul Sama ya bullo ya kuma kece da dariya, sannan ya ce wa Muhammadul Ziyara ko da shi yana tsammanin ba tare da an yi masa aikin nan ba zai iya zuwa taurari? Muhammadul Ziyara sai ya yi murmushi kawai kuma ya gaishe da Muhammadul Sama kamar yadda ya saba. Daga nan ne fa sai suka tashi sama, suka je suka sauka a wani gida kuma a cikin dokar daji inda suka shiga gidan suka tarar da abinci a shirye. Suka ci, sannan suka dauki wadansu wadanda aka sa su a cikin wani irin kwano mai kyakkyawan murfi, suka fita abinsu. Da suka fita kuma sai suka tarar da wani fili babba, kuma a gefe ga wani daki, sannan a cikin wannan filin ga wani katon jirgi kamar na sama, to amma shi wannan jirgin ba shi da fikafikai, kuma kafafunsa kamar kibiya su ke, guda biyu daga wajen gindin. Wato 45 Tauraruwa Mai Wutsiya kamar daga wajen inda dan tozon nan na bayan jirgin sama ya ke ke nan. Ko da saukarsu a wannan wuri, sai wadansu mutane biyu suka fīto daga wurin suka gaishe su, sannan ne shi Muhammadul Sama ya ce, "Karfe biyar to a lokacin kuwa wajen karfe hudu da kwata ne, to ko da ya ce karfe biyar din nan, sai shỉ Muhammadul Ziyara ya ga wadannan mutane sun nufi wani katon agogo wanda ke tsaye da Kafarsa a kan kasa sun gyara hannuwan agogon sun sa shi kan karfe biyar daidai. To a wannan lokacin fa wani an shirya lokacin tashin wannan jirgi ke nan wanda zai ga ainihin taurari. Daga lokacin kuma sai shi Muhammadul Sama ya kama hannun Muhammadul Ziyara suka je suka shiga cikin wannan abu mai kama da roka da wata 'yar kofa Karama kuma wadda suka kama suka rufe. Shi wannan daki yana kulle ne dukkansa yadda babu iskar da za ta shiga, to saboda haka ne ma shi Muhammadul Sama ya dauki wata irin 'yar jaka mai robobi da suka haďu da jikin wannan jirgin ya saka a hancinsa ya daure, ya kuma nuna wa Muhammadul Ziyara ainihin nasa abin shakar iskar. Ko da suka daddaura wadannan abubuwa, sai kuma suka nemi kujera suka zauna. Sannan kuma suka ajiye abincin nan nasu a cikin wata 'yar kwasfa inda yake ko kwai aka ajiye ga alama ba zai fashe ba, ballantana abinci. Su kujerun guda biyu ne kawai a cikin wannan injin din, kuma suna duban juna. Watakila don masu tafiya su rika samu suna dan ganin juna ne. To a cikin wannan injin din har ila yau akwai wani agogo daga can kolin wannan daki, kuma wannan lokaci da suka riga suka shiga har suka zauna, lokaci ya nuna karfe biyar saura minti ashirin da biyar ne. To da karfe biyar ta yi kuwa wannan inji zai tashi don ya kama hanyarsa ta zuwa taurari. Ainihin shi agogon da suka baro a waje shi ke aikata motsin wannan injin din. A cikin shi wannan injin akwai wadansu injina masu nuna irin motsin da wannan jirgin yake yi, kuma akwai wadansu akwatunan magana da su mutane biyu, da suke kasa, sannan akwai wadansu akwatuna na zayyana. Watau masu nuna hoton inda jirgin nan ya nufa ta amfani da haske mai amfani da karfin lantarki. Akwai kuma tsani guda daya a irin wanda a kan nade din nan. Sannan ana iya ganin cikin wannan wuri ta amfani 46 Tauraruwa Mai Wutsiya da lantarki, ko kuma ta bude sakata ta daya wadda 'yar kankanuwa ce. Bayan ita akwai wata roba mai kaurin gaske wadda ta jikinta ne ake iya ganin waje in ana cikin shi wannan jirgin. Su Muhammadul Ziyara na cikin zama a cikin wannan jirgin sai suka ji an ce, "KU SHIRYA." Ko da jin haka kuwa sai Muhammadul Sama ya kama wadansu 'yan igiyoyi na damara ya daura a jikinsa, sannan kuma ya ce wa abokin tafiyarsa shi ma ya faura a jikinsa sannan kuma ya ce ya daura, suka faura suka natsa. Sannan suka duba agogo saura dakika goma sha daya, sai can kuma ta akwatin nan nasu na karbar sako, sai suka ji ana kirga kamar haka, "Tara! Takwas! Bakwai! Shida! Biyar! Hudu! Uku! Biyu! Daya! Sifiri!" To da zarar fadin sifiri din nan sai kawai suka ji sun yi sama cul!! Kamar an harba kibiya. Daga waje kuwa inda suka tashin sai ka ce an yi gobarar gidan mai, sai hayaki kawai suka bari na tashi bul,bul yana ta yawo a kan wadansu kafafu inda shi wannan inji ke sauka. Su kuma mutanen nan biyu sai suka koma suka sake tura agogon nan suka kai shi kan karfe daya, sannan suka dauki waya suka buga wa su 'yan Kolin Koliyon nan da suka harba su, ba da daďewa ba cewa wannan jirgi nasu zai juyo ya komo kan kasa da karfe daya na dare daidai. To da shi Muhammadul Koli ya ji abin da aka ce sai ya ce wa Muhammadul Ziyara, za su yi 'yar tafiya zuwa cikin taurari na 'yan awoyi kadan kawai don saboda shi wannan jirgin ba ya iya wuce kamar awa takwas rabonsa da doron kasa, kuma za su isa taurari kafin wannan lokacin da awa guda. Shi wannan inji sai cillawa yake yi kamar walkiya, wadannan su kuma sai ganin irin abubuwan da suke wucewa suke yi ta cikin zayyanar da ke cikin wannan jirgi nasu. Suna ganin gizagizai da kankara wani lokaci, sai kuma sararin sama. Shi wannan inji nasu na cikin tafiya sai suka fara hango taurari, saboda haka shi Muhammadul Ziyara sai ya fara nutsawa don saboda ya ga abin da ya yi ta neman gani tun tuni, kuma a wannan rana ga shi ya fara hango su kuma zai shiga cikin su, watakila ma ya sami wani abu a cikin su. Suna nan dai cikin wannan jirgi nasu har suka ji ya tsaya da gindinsa a kasa watau su wadannan kibiyoyi da ke gindin 47 Tauraruwa Mai Wutsiya jirgin sun kafu a kan wata tauraruwa, suka duba kuma sai suka ga wadansu irin mutane marasa Kashi, watau dukkan su ba su da wata alamar kashi a jikinsu kuma ga su 'yan kanana kamar 'ya'yan tumaki, sai kuwa suka daina kallon ita wannan zayyana din, suka kama kofa suka bude, suka kuma sa tsanin nan ya fada kan ita wannan tauraruwa. Sannan suka kawo madubin ido masu duhu suka sa don saboda ita wannan tauraruwar wai tana kusa da rana fiye da duniya. Ko da saukarsu a kan wannan tauraruwa sai suka ga ashe katon wuri ne da kuma mutane masu zama a wurin. Shi Muhammadul Ziyara wannan wuri bako ne a wurinsa, to amma shi Muhammadul Sama da ma dan gida ne, saboda haka sai ya kama tafiya kawai a kan irin wannan ta6o na zinare, sai shi kuma Muhammadul Ziyara ya bi shi. To sai dai kuma shi ainihin wannan wuri kafuwar shi da girman shi bai yi daidai da na duniya ba, saboda haka sai suna jin su kamar karmami ne, wani lokacin ma sai sun tashi sama. To shi Muhammadul Ziyara ainihin a nan ne ya san aikin nan da likitan nan ya yi masa abu ne amintacce kuma mai amfani a gare shi da taurari. Ita wannan tauraruwa da suka sauka a kan ta sunanta Auriya, kuma katuwar tauraruwa ce cikin taurari, saboda haka ne shi ainihin Muhammadul Sama ya sauka a wannan tauraruwa. Kuma ita wannan Auriya din tana da wadansu duwatsu guda hudu bakake a kowace kwana tata, watau Gabas, Yamma, Kudu da Arewa. Wannan kuwa shi ya sa akan hango taurari sun ba da wadansu 'yan kusassari guda hudu, dalilin shi ne, dukkan kasar wurin gwal ne, watau zinare, kuma akwai duwatsu hudu wadanda su ke bakake ne, to idan rana ta haska tauraruwar, sai zinaren nan ya ba da fal, mu kuma da mu ke a nan duniya sai mu hango kyallin wannan dusa ta zinare da dan baki-bakin wadannan duwatsu. Su Muhammadul Sama sai suka yi ta tafiya har suka kai daya daga cikin wadannan duwatsu. Ko da isarsu sai suka fara ganin mutanen nan Kanana marasa kashi, suna zuwa suna kama musu jiki. Shi Muhammadul Sama ya riga ya saba, to amma shi Muhammadul Ziyara sai duka abin yana ba shi tsoro, don saboda yana cikin tafiya sai ya ga wani dan mutum ya saukar masa a gaba lagwai, sannan can ya ji wani karami ya hau masa hula da dai sauran irin su. 48 Tauraruwa Mai Wutsiya Suna cikin gwagwarmaya da wafannan 'yan mutane wadanda sunansu, ko kuma mu ce kabilarsu ita ce LagwaiLagwai, sai suka iso kofar wannan katon dutse inda suka ga su mutanen nan dai suna gadi. To amma ko da ganin Muhammadul Sama sai suka dauko wani zandareren makulli suka shiga kikikikin bude kofa. Da budewar su sai kuma ma fi yawansu suka dafe murfin, suka samu suka bude kofar. Ko da jawo kofar sai suka ga wadansu mutane biyu, kuma sun fito da wata irin hula mai kama da tauraro, suka bincika ko suna son ganin Tauraruwa ne? Suka ce, "I.", har Muhammadul Sama ya fada wa wadannan cewa shi ne ya iso tare da bakonsa. Nan da nan sai wadannan mutane suka yi ciki suka fito suka ce wai an ce su shiga. Suka shiga wani tankamemen daki, sannan kuma aka rufe wannan gangamemiyar kofa ta karfe. Suka nufi inda ita tauraruwa ta ke don su yi gaisuwa. Ita wannan Tauraruwa wata 'yar tsohuwa ce wadda ita ce ke da wannan garin, kuma duk wadannan mutane mayakanta ne, kuma ta yi wannan gida ne a cikin dutse, ta amfani da hakoran mutanenta ne. Ita ke ciyar da su kuma a yi musu komai da suke so. Ko da matar nan ta hango bakin nan nata sai ta kori dukkan Lagwai-Lagwai da ke wannan dakin suka fita, suka shiga wani dan Karamin daki da ke cikin shi wannan din. Ko da suka isa wurinta sai ta tashi ta yi musu barka da zuwa, sannan ta tambaye su koTSRES sun sha wuya a hanya? Muhammadul Sama ya gaya mata cewa ba su sha wuyar komai ba, to amma ya kawo bakonsa wanda tun tuni yake ta fatan Allah ya kawo shi taurari. Saboda haka ne ma ya ce to bari ya jawo shi wurin ainihin uwar taurari, kuma mai taurari, wadda saboda hasken dukiyarta da ta ajijjiye a cikin wadannan taurari ne aka sa wa ainihin su taurarin sunanta. Kuma ita ta ci gaba da sarautar dukkan wadannan taurari da suke gani. Muhammadul Ziyara ya yi mamaki kwarai na irin wannan dukiya da wannan mata take da ita, domin ainihin a wannan dakin hatta gadon da matar nan ke zaune a kai an yi shi ne da zinare da lu'ulu'u, sannan kuma ko'ina a dakin sai hasken wadannan karafa masu daraja kake gani suna jingine kawai kamar ba a son su. 49 Tauraruwa Mai Wutsiya Ita tauraruwa mace ce mai kama da 'yan Adam, tun da ita tana da Kashinta ba kamar sauran jama'arta ba, kuma akwai wata mata wadda suke tare, wadda take kamar ita ce ke yi mata abinci, ko kuma sauran ayyuka da za su bukaci sauri don saboda su Lagwai-Lagwai kowa ya san ba za su iya yin saurin girki ba. Duk daben dakin matar nan zinare ne, sai ado da aka yi masa da lu'ulu'u da azurfa, saboda haka mutum wanda ya ke daga kasa, bayan ba shi da nauyin kirki, sai kuma ya yi kokari ya daddaga don saboda kada ya fadi. Sai kuma su hauren giwa su kuma an yi ado da su. To amma su wadannan duk lokacin da ake bukatar su sai kawai a aika kamar irin mutanen nan Lagwai-Lagwai kan kasa watan duniya inda za su sami giwa su far mata da cizo sai sun ga sun kashe ta, sannan su yanke hauren su kai wa uwargijiyarsu, watau Tauraruwa. Bayan shi Muhammadul Sama ya bari sun natsa sai ya gaya wa ita wannan Sarauniya cewa wannan da ya kawo ya zo ne ya gaishe ta kuma ya sami albarka don saboda ya sha wuya kwarai kafin

Chapter 6 of 7