Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 7
karamin daki, har ila yau da na bahaya. Sai ya kunna fitila, ya yi alwala, sannan ya fita ya koma ainihin dakinsa inda ya sami darduma ya shimfida ya yi ta yin salloli, don shi dai kansa bai san ainihin ko wane lokaci ne ba kuma ya dade rabonsa da yin Salla, sai dai ya yi iyakar yadda yake tsammani ake bin sa, ya yi roko ga Ubangijin talikai, sannan ya tashi ya cire rigunansa. To amma ya bar wando da singileti, takalmansa kuma ya goge su fyas yadda ba za su bata gadon ba. Ya dauko mayafi ya rufa ya kwanta shiru yana jiran barci ya dauke shi. To amma yana kwance din nan sai tunawa yake yi da zancen nan na Muhammadul Sama inda ya ce da shi banda barcin babu gaira babu dalili. To a dalilin haka ne ma ya ki cire takalmansa, yadda ko da wani abu zai faru cikin lokacin da ya ke barcin nan, to zai iya tabuka wani abu daidai gwargwado. Shi yana ta wannan tunani da sauran irinsu, gari kuwa ya yi tsit, babu kukan tsuntsu babu na namun daji. Ainihin su kifi kuma da dukkan namun ruwa da ke karkashin wannan gari, ko dai ba su da ikon yin wata mummunar kara, ko kuma a'a ita wannan shiyya an yi ta ne yadda za a yi abin fake ruwa a karkashin ruwan nan a ji shi a cikin wannan gari mai kama da birnin 'yan ruwa. Dakin nan da wannan dan taliki ya ke wato kamar a ce mutumin da ke Sakkwato ne ya tashi a cikin watan Mayu ya tafi Jos, watau lardin Kuza inda yake akwai sanyi mai dan karen dadi, to haka ni dai nake tsammanin shi yaron nan ya ji. Domin kuwa mutumin da ya ke busasshen dakin kauye ya zamo ya sami daki 19 Tauraruwa Mai Wutsiya mai injin sanyayawa, to ai lallai ka tabbata wannan mutum yana shan lagwada, bugu da kari kuma shi wannan mutum yana tsakiyar ruwa ne, inda lallai kowa ya san a irin wannan wuri sai fitila dare da rana. Bayan dukkan irin wannan alatu, ga kuma dakin nan yana kanshin turare, wanda in mutum dai ya ci abinci ya koshi ya ji kanshinsa, to lallai zai sake iya zama har sa'a goma sha biyar bai sake kulawa da ya ci abinci ba domin kara koshin da wannan turaren yake yi saboda kanshi. Sannan kuma sai ya sa mutum ya rika wani irin rawar kai saboda lallai shi kansa ya san ya sa turare na gari, ba na garari ba, irin wanda mutum zai sa ya dan yi kusa da kai kanshin ya nashe ka, ka ji kamar ka zub da dan abincin da ka dan ci. Ga wata fitila kuma mai dan karen haske wadda tilas kowa ya gan ka ya gan ka cikin ni'ima, domin ita kanta fitilar don kyalli har ta fi fari, fari. Ta taga kuma idan mutum ya leka sai ya hangi inda fitilar nan ta haska ruwa, ruwan kuma yana tafiya a hankali kamar mutum ya je ya ce tsaya in taba ka sannan ka wuce. Ga shi kuma shi wannan ruwan kamar an za6o shi ne sannan aka kwararo shi wannan shiyyar saboda kyansa. Muhammadul Ziyara na cikin kwanciya a cikin irin wannan ni'ima sai can ya ji kamar an bude kofa, sai kuwa ya farka, to amma bai bude idanunsa da 'wuri-wuri ba sai dai ya yi lamo yana jiran ya ji abin da zai faru kuma, sai kuwa ya ga ainihin Sarauniyar Birnin Malala ce ta shigo. Tana tafiya da kafar nan tata kamar ba kasa take takawa ba, ga kayan da ta sa wadannan korra da suka dace da ita. Ga fuskar nan babu hoda, to amma ko makaho da zai shafa ya san ta kyakkyawa ce, mai kyakkyawar kira, kuma idan da mutum zai lura sai ya ga a'a babu irin ciye-ciyen mala'iku din nan a fuskar, babu 'ya'yan yayyaba, babu tabo, kai fuskar dai kamar bayan gautan yalo, wanda ya gawurta, kuma ya nuna din nan, watau wanda bayansa sulisuli ne. Bintun Sarauta ta ratsa dakin nan tana tafe jikinta na sheki ta isa gadon nan da wannan yaro ke barci, ta dan lamushe zaninta daga wajen guiwoyinta ta zauna kyamas a kan gado, tun da da ma ita ba jiki take da shi irin rugaggen nan ba. To amma kuma ba ramammiya ba ce, ta dago 'yan hannayen nan nata, ga su farare fat, kamar tun da Allah ya yi su ba su taba datti ba, ko ma in ce kamar tun da aka haife ta, ba su taba yin ko da zufa ba 20 Tauraruwa Mai Wutsiya balle su yi wata uwar dauda. Ta kuwa kama yaron nan ta shiga waka tana cewa, "Raina ya canza, raina ya yi fari kuma ni kaina na canza, sabon jin dadin ya zo mini, duka saboda masoyina. To yanzu wane ne masoyina, in ba bako mai bakon suna ba, wayyo ni kaina, zuciyata ta kamu kamuwa irin ta soyayya, to ko shi bako ya zam ya sami bakuntata a cikin zuciyarsa, shi ne abin da ke damuna." Nan ne fa yarinya ta kai ga wannan wuri sai shi yaron ya mike, shi ma da rana tsaka ya koyi yin waka. Ba gadon uwa balle na uba, ya shiga cewa, "Yau ni na yi tarihi na kaina game da zuciyata, na yi matukar rudewa bisa wannan siffa taki, kuma soyayya a gare ki ta rigaya ta yi saiwa, ta girma kuma ni kawai abin ne da bakunta, sai dai a daure da halinmu na yanzu." Sai kuwa yarinya ta yi ta mamakin yadda wannan yaro ya iya waka har ta yi masa tambaya ko a ina ne ya koyi waka? Shi kuwa sai ya ce mata ai ba wani koyo ya yi ba, a'a, ainihin kawai da jin tana waka sai ya ji duk tsigar jikinsa ta tashi, ko da ta kai baitinta kuma, sai kawai ya ji ya kama ci gaba da wakar. Yarinya ta ce masa to tun da shi ma yana da zuciya mai kamar tata, a nan sai yaron ya yi wuf ya ce, "A'a, mene ne na wani damuwa? Ai ni ina son ki ne kamar in cire kwakwalwata in mika miki, tun da ya ke ko da ma da na fara ganin ki babu tunanin komai a cikin kwakwalwata banda tunanin ki." Ita kuma sai ta yi dan murmushi ta ce, "To kai bawan Allah idan ka ciro kwakwalwarka ka miko mini, to ni yaya zan yi ke nan a duniyar nan ta Allah? Tun da ni duk lokacin da ka yi tunani na sai na ji shi a cikin zuciyata, kuma na ji dan karen dadi. Kai dai yanzu abin da nake so da kai, duk lokacin da kake bukatar ganina, ga wannan zobe, ka sa shi a hannunka. Da ka cire shi daga hannunka, to zai zamo sarewa. To sai ka busa, za ka gan ni na zo a duk inda ka ke." Yaro zai karbi zoben sai kuwa ta dube shi ta yi murmushi ta ce, "Haba amintaccen sahibina, bari mana in sa maka zoben ko na rika tunawa da na sa maka zobe in ji dan sanyi-sanyi ko ba ka nan." Sai kuwa ya ce da ita, "Ki yi hakuri ya abar kaunata, kin san ina son ki, so mai dalili, kuma ina kaunar dukkan abin da kike so, don na san a cikin soyayya babu kafar ki, ko kuma cuta." 21 Tauraruwa Mai Wutsiya Yarinyar nan ta sa masa zobe, ta kama hannun nan da ta sa wa zoben ta rungume, kuma ta sunbace shi. Can sai suka zauna shiru sai kuwa ta ce wa yaron nan, "To sai ka kwanta ka huta sai wani lokaci kuma mun sadu." Da ta gama magana sai ta shafa hannunta na dama a kan fuskarsa, ya yi kamar zai yi magana amma ina, sai barci ya fyauce shi, ita kuma ta tashi ta tafi fadarta tana mai matukar tunani a kan yaron nan masoyinta. Jimawa kadan sai Muhammadul Ziyara ya farka firgigi daga barcin da yake yi. Ko da farkawarsa kuwa sai ya ji murya irin ta Muhammadul Koli ta ce, "To Muhammadul Ziyara ga lokacin da za ka sake kutsawa fagen fama inda za mu gwada ka kafin ka sami biyan bukatarka." Yaron nan sai ya yi kokari ya yunkura, don ya sauka daga kan gadon ya dauki 'yar rigarsa da kuma sauran 'yan kayayyakinsa, to amma sai ya lura ashe ma ba lokacin neman wadansu riguna ba ne. Ai ma a lokaci ko da wando ne mutum ba shi da shi a jiki bai kamata ya tashi yana neman shi ba. Dalili kuwa shi ne, da zarar kare maganar mutumin nan, watau Kolin Koliyo, sai fa abu ya sake juyewa. Wuri sai ya yi fayau kawai, dukkan kayayyakin da ke cikin wannan dakin ya zamo babu komai sai kawai gadon nan da shimfidun da ya ke a kai, da kuma shi Muhammadul Ziyara na kwance lamo a kan shi. Babu daki balle a yi zancen su madubi, dabe, da dai dukkan sauran abubuwa. To, ko ina su ke? Shi ya yi tunani, to amma yana cikin tunanin nan sai kuwa ya ga af, to shin ina daki da kayan daki suka tafi ne, ko kuwa shi ne yake tafiya? Ko kuma dakin ne ya kunshi Muhammadul Ziayara da gadonsa? Yaro ya lura ashe yana kan gado mai tashi ne. Ga shi a kwance a kan gado, shi kuma gadon da ya ke a kasansa akwai wani dan karamin inji wanda yake taimakonsa tashi. To ko fa shi Kolin Koliyo ne ya ta da injin din, ko kuma gadon mai aiki yadda ya so ne, shi ne abin da Ziyara bai sani ba? Sai dai ya ci gaba da dudduba abubuwa kawai. Amma wani abin ban mamaki kuma shi ne, ta yaya ne aka yi ainihin shi wannan kinkimemen gado na hawan mutum biyu ya fito ta wannan daki wanda 'yar kofarsa kankanuwa ce? Kafin in ci gaba da bayanin irin wannan wuri da wannan yaro ya kutsa, sai in tuno da wata 'yar magana da nakan ji, watau, "Sama tantan, kasa tantan, tsakiya sarautar Allah." To a nan shi 22 Tauraruwa Mai Wutsiya mutum da ne yanzu ake, "Sama wayam, kasa wayam, tsakiya gadonsa, ko kuma mu ce Muhammadul Zaiyara a kan gadonsa" To ai kuwa abin dai da kamar wuya gurguwa da auren nesa, yaron nan in ya daga kansa sama ba ya iya ganin komai, haka kuma in ya sunkuyar da kansa kasa, kuma in ma ya yi ta duban kasa babu abin da zai faru sai jiri ya kama shi. In kuwa ya fadi, to ina za shi ke nan? Ga Kasan babu kasa da ake takama da ita, kuma ga iska mai dan karen sanyi sai busawa take yi, kuma don tsananin sanyinta har tana karkada dan yaron. To abu dai babu kama hannun yaro. Shi dai abin da ya yi shi ne ya dauki mayafi tafkeke ya lullube jikinsa da shi. Can jim kadan ya fara tunanin cewa wai yana jin yunwa, sai ya ga wani ringimemen tsauni kamar rabin mil daga kansa, ya kuwa rufe idanunsa nan da nan, sannan ya sake budewa. To amma ko da budewarsa ta biyu, sai ya ga ainihin gadon nan ya nufi wajen tsaunin nan da shi, shi kuma tsaunin sai karar yiwowa kasa-kasa yake yi. Yaron nan fa ya rude, ya shiga yi wa gado kaimi da takalminsa kamar yana kan jaki ko doki, amma ina! Ai shi wannan gado ya rigaya ya dukufa ga zuwa inda ya nufa. Yaron nan sai ya sake rufe idanunsa, to amma wannan budewar da zai yi sai ya ga tsaunin nan ya kara sama, to da ya kara sama kuma sai ya kama wuta, sannan ya sake yiwowa kasa, abin dai gwanin ban al'ajabi, ga su a sararin Allah, babu kasa balle a gudu. Shi ba rafi ke kasa ba, balle a ce a fada alabarshi a haye da iyo. Abin na yi ne, sai yaro ya nisa, ya kuma shiga tunani na ainihin yadda zai yi da wannan alakakai. Can sai ya tuna zamansa a birnin Malala, ya kuma tuna da masoyiyarsa, ya ga wayyo watakila ga shi ya kusa halaka, kuma shi bai gan ta ba. To haka shi sha'anin so ya ke, ku dubi irin wannan hadari da dan talikin nan ke ciki, to amma maimakon ya yi tunanin yadda zai fita sai yana tunanin ainihin yarinyar da yake so. Can sai ya duba zoben da yarinyar ta ba shi, ya nisa, kamar zai yi kuka, ya fitar da rai a rayuwarsa. To can sai ya tuna da sunan da aka rada masa, kuma da abin da Bintun Sarauta ta gaya masa game da asirin da ke cikin kowane suna da shi Muhammadul Sunaye ya rada. Nan take da tunawarsa sai ya daga kai sama ya dubi tsaunin nan mai cin wuta ya kuwa kwala wa kansa kira, watau ya ce, "Muhammadul Ziyara!" 23 Tauraruwa Mai Wutsiya Sai kuwa ya ji amsa-kuwwa ta amsa masa kuwwar da ya yi. Can kuwa a saman shi daga daya fuskar sai ya ga rafi makeke ya tinkari wannan tsauni. To amma wani abin mamakin shi ne kuma, ko da yake ga kogi ana gani, kuma har ya zo ya wuce ta kan shi wannan dan taliki, ama duk da haka ruwa ko da kamar kwayar zarra bai digo masa ba. Kuma ga shi ko ana ganin sa yana ta kwarara. Wannan abu da yawa ya ke, shi dai zurfin ruwan nan ya yi kamar ya shanye dukkan wannan tsauni maí cin wuta. To saboda haka ne shi wannan yaron ya yi tsammanin cewa lallai watakila wannan kogi shi ne zai kashe wannan wuta. Ai kuwa da abin da aka yi ke nan, can sai kogin nan ya je ya auka wa wannan tsauni. To me ka yi tsammani zai faru? Ka san ko garwashin wuta aka watsa wa ruwa yakan yi kara cuu-u-u! To balle wannan dingimemen dutse da kogi, sakamakon abin dai to shi ne babban rugugi wanda ya hadu da kakkauran hayaki wanda ya turnuke wannan kewayen wurin. Yaron nan bai yi wata-wata ba, sai ya sake kiran sunan nan nasa. Ya kuwa yi sa'a, gadon nan ya sake tashi da shi ya shilla da shi ya yi sama, suka tsallake wannan tsauni. To da tsallake wannan ne fa sai yaro ya hango wani gida na karfe yana yawo a sama, da wadansu wayoyi sun lelleko daga cikinsa ga wadansu karafa kuma sun fito daga samansa sun lula sun yi sama, da suka dada yin kusa sai ya ji karar wani inji wanda bai taba jin irinsa ba. A zuciyarsa sai ya ce, "Oho, komai dai ya zo ya wuce, tun da na fice daga mummunar kuna, da rashin samun kabari, to ai ni komai ya yi! AN SA SHI AIKIN INJI Gadon nan fa sai kawai ya nufi wajen gidan nan na karfe da yaro. Kuma yana kai shi wurin sai ya ajiye shi a kan wata 'yar farfajiya, kuma kafin ka ce kwabo sai wannan gado ya басе. Yaron nan ya tabbata cewa shi wannan gado watau ya riga ya gama aikinsa ke nan, kuma yanzu sai ya yi damara ya shirya tsaf. Ya jira kuma ya ga irín abin da zai yi gwagwarmaya da shi wannan wurin. Can yana cikin wannan irin tunanin, sai kuwa ya wata fitila ja ta yi fal, ta kuma mutu. Sai can kuma ta sake walkawa, sai ya ce. 'To yau kuma aikin nawa da gama na uku babu ko da hutu sai in shiga na hudu? To amma ai ba komai, ai ni ga 24 a Tauraruwa Mai Wutsiya ba zama na zo yi a wannan wuri ba, saboda haka bari in farka daga wannan rarumi nawa, in gama abubuwan da suke gabana. Wannan fitila ja kafin a yi haka sai ta face, wata kofa ta bude, sai kuwa wadansu mutane suka fito cikin wadansu kayayyaki na karfe su biyu, kayansu iri daya. Kuma dukkan su suna rike da wadansu wayoyi a hannayensu na dama da na hagu. Sannan kuma a bayansu ga wadansu irin jakunkuna na karfe sun goya. Fuskokinsu duk a rufe, kuma ko tafin hannayensu duk sun rufe su da safa ta roba, a daidai inda ya kamata hancinsu ya leko sai wadansu wayoyi masu rufe da roba suka leko don su ba su damar samun shakar iska. Ko da fitowar wadannan mutane sai Muhammadul Ziyara ya dube su da kyau, kuma dai-dai, ya nisa, to amma bai ce komai ba. Sai can kuma ya ji magana kamar ta mutane, to amma ta surka da wata 'yar kara kamar dai daga rediyo take fitowa. Abin da ya ji an ce kuwa shi ne, "Kai samari, ka keta mana haddin kasa, saboda haka sai ka biyo wadannan ma'aikata biyu ku zo cikin wannan gida domin a yanke maka hukunci. Ko ka fara yin gwale-gwalen da za a sara maka." Yaron nan, nan da nan ya tashi ya wuce gaba, wadannan mutane biyu kuma suka bi shi, kamar ba mutane ba, sai tafiya suke yi kamar wadanda su ke a sankare, su ba sa magana. Suna jin abin da ake cewa, ba sa waige sai juyi, kuma su ba sa tausayi ga mutum a kan dukkan aikin da aka sa su. Suka shiga wannan gida, shi wannan yato babu abin da ya fara karo da shi sai wadansu manya-manyan kwalabe cike da magunguna, da wadansu dogayen tebura wadanda aka rufe samansu da wata irin shimfida mai kama da siminti. To amma shi wannan yana kyalli kuma yana da wadansu jefin baki-baki a jikinsa. Sai kuma wadansu bututu tsukakku masu wani dan mariki, irin wadannan kuwa akwai kamar talatin, sai kuma wadansu famfuna masu 'yan Kananan daro a kasansu. Ga kuma wadansu 'yan kayayyaki dai na karfe masu kama da jiragen sama. To daga can karshen dakin da suka fara shiga sai ya ga wata siffa kamar ta mutum, sai dai wannan baki ne, kirin kuma, babu alamar fuska ko wani abu, sai dai kawai wata waya da ta fito wajen bakin mutumin. Daga wannan siffar ce fa ya ji magana ta fito inda ya ji an ce, "Tsaya nan!" 25 Tauraruwa Mai Wutsiya Nan kuma ya ji kamar an kafe shi, sai kuma aka ci gaba da cewa, "Ku wuce da shi daki na takwas." To a lokacin kuwa suna daki na daya ne, inda ya ke babu komai sai kawai wadansu `yan tarkacen kwalaben magunguna, saboda haka suka kama hanya suka shiga faki na biyu, wanda shi kuma babu komai sai ainihin kayan alatu kawai. Dabensa dai na katako ne wanda aka shafe da mai, sai kyalli yake yi, ga wata irin shimfida mai dan karen tsada da taushi an baje ta. A kowace kwana daga cikin kwanoni hudu na wannan daki kuwa akwai wata irin bindiga wadda ke hade da lantarki. Kuma da mutum ya shiga wannan wuri ba tare da izini ba su wadannan bindigogin ba wai sai an harba su ba, a'a, da kansu za su shiga harbin mutum. Watau su wadannan bindigogin sun zamo masu aiki da kansu ke nan. Akwai kuma wadansu 'yan kujeru wadanda su ke a kewaye da wani teburin abinci da ke tsakiyar dakin, su kuma kowannensu yana da wata waya wadda ta hadu da ita daga Karkashin shimfidar da ke dakin, kuma idan mutum bai lura ba, to babu yadda za a yi ya iya fahimtar cewa akwai waya da ta hadu da wadannan kujeru. Su ainihin wadannan kujerun kuwa an ce idan mutum yа zauna kansu yana iya mutuwa ta fizgar lantarki. Suka wuce daki na biyu, suka nufi na uku, inda suka tarar da wadansu irin tsuntsaye manya-manya, masu gashin zinare, su kuma wadannan kewaye su aka yi da wata 'yar katanga gajeriya wadda ta kawo wa mutum kirji. An kuma shirya ta yadda duk abin da ya tabi katangar, idan dai ba an riga an cire hade-haden da aka yi ba ne, to in dai har ya fi wannan tsuntsun girma, to ka tabbata zai ji an yi wurgi da shi. Da an yi wurgi da shi kuwa zai je rijiyar same 'yar tsidau. Wato a saman fakin akwai wani lungu inda cikinsa duk kaifafan masu ne, kuma zamowarsa kamar rijiya, to amma a sama, shi ya sa aka sa mata suna rijiyar sama. Kuma saboda wadannan tsinukan masu, sai ana kiranta 'yar tsidau, to tuntube dadin gushi, kuma mutumin da ya gama sokuwa a rijiyar saman nan in ya zo fadowa ba fa zai fado a kan daße ne ba. A'a zai wuce kai tsaye ta wata kofa da takan bude da kanta ya yi kasa iska ta wajajjaga sauran jikinsa. Da suka wuce daki na uku kuma sai daki na huďu inda banda macizai da duwu (bakar kunama) babu komai. Su kuma 26 Tauraruwa Mai Wutsiya ne yanzu ake, "Sama wayam, kasa wayam, tsakiya mutum da gadonsa, ko kuma mu ce Muhammadul Zaiyara a kan gadonsa" To ai kuwa abin dai da kamar wuya gurguwa da auren nesa, yaron nan in ya daga kansa sama ba ya iya ganin komai, haka kuma in ya sunkuyar da kansa kasa, kuma in ma ya yi ta duban kasa babu abin da zai faru sai jiri ya kama shi. In kuwa ya fadi, to ina za shi ke nan? Ga kasan babu kasa da ake takama da ita, kuma ga iska mai dan karen sanyi sai busawa take yi, kuma don tsananin sanyinta har tana karkada dan yaron. To abu dai babu kama hannun yaro. Shi dai abin da ya yi shi ne ya dauki mayafi tafkeke ya lulluße jikinsa da shi. Can jim kadan ya fara tunanin cewa wai yana jin yunwa, sai ya ga wani ringimemen tsauni kamar rabin mil daga kansa, ya kuwa rufe idanunsa nan da nan, sannan ya sake budewa. To amma ko da budewarsa ta biyu, sai ya ga ainihin gadon nan ya nufi wajen tsaunin nan da shi, shi kuma tsaunin sai karar yiwowa kasa-kasa yake yi. Yaron nan fa ya rude, ya shiga yi wa gado kaimi da takalminsa kamar yana kan jaki ko doki, amma ina! Ai shi wannan gado ya rigaya ya dukufa ga zuwa inda ya nufa. Yaron nan sai ya sake rufe idanunsa, to amma wannan budewar da zai yi sai ya ga tsaunin nan ya kara sama, to da ya kara sama kuma sai ya kama wuta, sannan ya sake yiwowa kasa, abin dai gwanin ban al'ajabi, ga su a sararin Allah, babu kasa balle a gudu. Shi ba rafi ke kasa ba, balle a ce a fada alabarshi a haye da iyo. Abin na yi ne, sai yaro ya nisa, ya kuma shiga tunani na ainihin yadda zai yi da wannan alakakai. Can sai ya tuna zamansa a birnin Malala, ya kuma tuna da masoyiyarsa, ya ga wayyo watakila ga shi ya kusa halaka, kuma shi bai gan ta ba. To haka shi sha'anin so ya ke, ku dubi irin wannan hadari da dan talikin nan ke ciki, to amma maimakon ya yi tunanin yadda zai fita sai yana tunanin ainihin yarinyar da yake so. Can sai ya duba zoben da yarinyar ta ba shi, ya nisa, kamar zai yi kuka, ya fitar da rai a rayuwarsa. To can sai ya tuna da sunan da aka rada masa, kuma da abin da Bintun Sarauta ta gaya masa game da asirin da ke cikin kowane suna da shi Muhammadul Sunaye ya rada. Nan take da tunawarsa sai ya daga kai sama ya dubi tsaunin nan mai cin wuta ya kuwa kwala wa kansa kira, watau ya ce, "Muhammadul Ziyara!" 23 Tauraruwa Mai Wutsiya Sai kuwa ya ji amsa-kuwwa ta amsa masa kuwwar da ya yi. Can kuwa a saman shi daga daya fuskar sai ya ga rafi makeke ya tinkari wannan tsauni. To amma wani abin mamakin shi ne kuma, ko da yake ga kogi ana gani, kuma har ya zo ya wuce ta kan shi wannan dan taliki, atma duk da haka ruwa ko da kamar Kwayar zarra bai digo masa ba. Kuma ga shi ko ana ganin sa yana ta kwarara. Wannan abu da yawa ya ke, shi dai zurfin ruwan nan ya yi kamar ya shanye dukkan wannan tsauni maí cin wuta. To saboda haka ne shi wannan yaron ya yi tsammanin cewa lallai watakila wannan kogi shi ne zai kashe wannan wuta. Ai kuwa da abin da aka yi ke nan, can sai kogin nan ya je ya auka wa wannan tsauni. To me ka yi tsammani zai faru? Ka san ko garwashin wuta aka watsa wa ruwa yakari yi kara cuu-u-u! To balle wannan dingimemen dutse da kogi, sakamakon abin dai to shi ne babban rugugi wanda ya hadu da kakkauran hayaki wanda ya turnuke wannan kewayen wurin. Yaron nan bai yi wata-wata ba, sai ya sake kiran sunan nan nasa. Ya kuwa yi sa'a, gadon nan ya sake tashi da shi ya shilla da shi ya yi sartta, suka tsallake wannan tsauni. To da tsallake wannan ne fa sai yaro ya hango wani gida na karfe yana yawo a sama, da wadansu wayoyi sun lelleko daga cikinsa ga wadansu karafa kuma sun fito daga samansa sun lula sun yi sama, da suka dada yin kusa sai ya ji karar wani inji wanda bai taba jin irinsa ba. A zuciyarsa sai ya ce, "Oho, komai dai ya zo ya wuce, tun da na fice daga mummunar kuna, da rashin samun kabari, to ai ni komai ya yi! AN SA SHI AIKIN INJI Gadon nan fa sai kawai ya nufi wajen gidan nan na karfe da yaro. Kuma yana kai shi wurin sai ya ajiye shi a kan wata 'yar farfajiya, kuma kafin ka ce kwabo sai wannan gado ya бace. Yaron nan ya tabbata cewa shi wannan gado watau ya riga ya gama aikinsa ke nan, kuma yanzu sai ya yi damara ya shirya tsaf. Ya jira kuma ya ga irín abin da zai yi gwagwarmaya da shi a wannan wurin. Can yana cikin wannan irin tunanin, sai kuwa ya ga wata fitila ja ta

Chapter 3 of 7