Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 7
yi fal, ta kuma mutu. Sai can kuma ta sake walkawa, sai ya ce. 'To yau kuma aikin nawa da gama na uku babu ko da hutu sai in shiga na hudu? To amma ai ba komai, ai ni 24 Tauraruwa Mai Wutsiya ba zama na zo yi a wannan wuri ba, saboda haka bari in farka daga wannan rarumi nawa, in gama abubuwan da suke gabana. Wannan fitila ja kafin a yi haka sai ta face, wata kofa ta bude, sai kuwa wadansu mutane suka fito cikin wadansu kayayyaki na karfe su biyu, kayansu iri daya. Kuma dukkan su suna rike da wadansu wayoyi a hannayensu na dama da na hagu. Sannan kuma a bayansu ga wadansu irin jakunkuna na karfe sun goya. Fuskokinsu duk a rufe, kuma ko tafin hannayensu duk sun rufe su da safa ta roba, a daidai inda ya kamata hancinsu ya leko sai wadansu wayoyi masu rufe da roba suka leko don su ba su damar samun shakar iska. Ko da fitowar wadannan mutane sai Muhammadul Ziyara ya dube su da kyau, kuma dai-dai, ya nisa, to amma bai ce komai ba. Sai can kuma ya ji magana kamar ta mutane, to amma ta surka da wata 'yar kara kamar dai daga rediyo take fitowa. Abin da ya ji an ce kuwa shi ne, "Kai samari, ka keta mana haddin kasa, saboda haka sai ka biyo wadannan ma'aikata biyu ku zo cikin wannan gida domin a yanke maka hukunci. Ko ka fara yin gwale-gwalen da za a sara maka." Yaron nan, nan da nan ya tashi ya wuce gaba, wadannan mutane biyu kuma suka bi shi, kamar ba mutane ba, sai tafiya suke yi kamar wadanda su ke a sankare, su ba sa magana. Suna jin abin da ake cewa, ba sa waige sai juyi, kuma su ba sa tausayi ga mutum a kan dukkan aikin da aka sa su. Suka shiga wannan gida, shi wannan yaco babu abin da ya fara karo da shi sai wadansu manya-manyan kwalabe cike da magunguna, da wadansu dogayen tebura wadanda aka rufe samansu da wata irin shimfida mai kama da siminti. To amma shi wannan yana kyalli kuma yana da wadansu jefin baki-baki a jikinsa. Sai kuma wadansu bututu tsukakku masu wani dan mariki, irin wadannan kuwa akwai kamar talatin, sai kuma wadansu famfuna masu 'yan Kananan daro a kasansu. Ga kuma wadansu 'yan kayayyaki dai na karfe masu kama da jiragen sama. To daga can karshen dakin da suka fara shiga sai ya ga watą siffa kamar ta mutum, sai dai wannan baki ne, kirin kuma, babu alamar fuska ko wani abu, sai dai kawai wata waya da ța fito wajen bakin mutumin. Daga wannan siffar ce fa ya ji magana ta fito inda ya ji an ce, "Tsaya nan!" 25 Tauraruwa Mai Wutsiya Nan kuma ya ji kamar an kafe shi, sai kuma aka ci gaba da cewa, "Ku wuce da shi daki na takwas." To a lokacin kuwa suna daki na daya ne, inda ya ke babu komai sai kawai wafansu 'yan tarkacen kwalaben magunguna, saboda haka suka kama hanya suka shiga daki na biyu, wanda shi kuma babu komai sai ainihin kayan alatu kawai. Dabensa dai na katako ne wanda aka shafe da mai, sai kyalli yake yi, ga wata irin shimfida mai dan karen tsada da taushi an baje ta. A kowace kwana daga cikin kwanoni hudu na wannan daki kuwa akwai wata irin bindiga wadda ke hade da lantarki. Kuma da mutum ya shiga wannan wuri ba tare da izini ba su wadannan bindigogin ba wai sai an harba su ba, a'a, da kansu za su shiga harbin mutum. Watau su wadannan bindigogin sun zamo masu aiki da kansu ke nan. Akwai kuma wadansu 'yan kujeru wadanda su ke a kewaye da wani teburin abinci da ke tsakiyar dakin, su kuma kowannensu yana da wata waya wadda ta hadu da ita daga karkashin shimfidar da ke dakin, kuma idan mutum bai lura ba, to babu yadda za a yi ya iya fahimtar cewa akwai waya da ta hadu da wadannan kujeru. Su ainihin wadannan kujerun kuwa an ce idan mutum ya zauna kansu yana iya mutuwa ta fizgar lantarki. Suka wuce daki na biyu, suka nufi na uku, inda suka tarar da wadansu irin tsuntsaye manya-manya, masu gashin zinare, su kuma wadannan kewaye su aka yi da wata 'yar katanga gajeriya wadda ta kawo wa mutum kirji. An kuma shirya ta yadda duk abin da ya ta6i katangar, idan dai ba an riga an cire hade-haden da aka yi ba ne, to in dai har ya fi wannan tsuntsun girma, to ka tabbata zai ji an yi wurgi da shi. Da an yi wurgi da shi kuwa zai je rijiyar same 'yar tsidau. Wato a saman dakin akwai wani lungu inda cikinsa duk kaifafan masu ne, kuma zamowarsa kamar rijiya, to amma a sama, shi ya sa aka sa mata suna rijiyar sama. Kuma saboda wadannan tsinukan masu, sai ana kiranta 'yar tsidau, to tuntube dadin gushi, kuma mutumin da ya gama sokuwa a rijiyar saman nan in ya zo fadowa ba fa zai fado a kan dabe ne ba. A'a zai wuce kai tsaye ta wata kofa da takan bude da kanta ya yi kasa iska ta wajajjaga sauran jikinsa. Da suka wuce daki na uku kuma sai daki na huďu inda banda macizai da duwu (bakar kunama) babu komai. Su kuma 26 Tauraruwa Mai Wutsiya wadannan macizai ba wai na Allah Ta'ala ba ne, wadannan macizan da duwun duka ainihin su, Sarkin wannan birnin ne ya kago su da taimakon ma'aikatan kimiyyarsa. A dakin ne kuma aka yi rubutu kamar haka: Alfaharin birnin Kage-Kage. To su wadannan kunamai da macizai kowane daya a kalla ya fi girman akuya, wato su kunamun ma ke nan, to amma ainihin macizan in aka tara su tsibin kowane daya ya yi kamar girman bajimin sa. Aikin su kunamun nan kuwa shi ne in aka sa dunkulen kasa a bakinsu aka ta da injinansu, kuma aka koma aka sa kashin su tsuntsayen nan na daki na uku a cikin kwayar idon su macizan nan, to su kuma aka ta da injinansu, in kwayar idanun macizai guda biyu suka haska dunkulen kasar da ke bakin kunamun, to sai ka ga dunkulen kasar nan ya zama lu'ulu'u, wanda kowa ya san abu ne ba mai karamin amfani ba. Sannu a hankali kuma har suka iso daki na biyar, wannan dakin kuwa babu komai sai irin kunamar nan da suka wuce a daki na hudu. To amma wannan kunamar guda daya ce kurum, kuma ita wannan kantareriya ce. Ta yi kamar girman irin kananan motocin nan, to amma ita ba wai aikinta kamar na wadancan ne ba. Ita kam da an ta da ita ko ka fi kowa, ba ka iya wuce ainihin wannan daki, tun da samun ka za ta yi, ta murkushe, kuma ko kana da bindiga, kowane irin makami ka rike, ba zai yi mata komai ba. Sai kuma daki na shida, wanda ya ke shi wani katon daki ne cike da gadaje. A wannan lokacin kowane gado akwai mutum yana barci, ko da yake dai ba wai maza ne duka ba, har da mata. A lokacin ne ma ya yi tunani a zuciyarsa ya ce, "Dubi wadansu ma'aikatan dare su da rana suke barci." A wannan dakin banda su wadannan mutane da ke kwance babu ainihin wani abin lura kuma, sai dai karar inji da ke tasowa daga daki na gaba, sai ji kake rim-rim-rim! Suka wuce zuwa daki na bakwai inda suka sami mutum biyu suna gyare-gyaren injina, kuma suka ga wani injin ruwa mai kusassari sai murdawa yake yi barkatai. A wannan dakin ne suka raba suka shige kuma aka ce kada ya yi tari, in ba haka ba injin zai murde shi, don duk wanda ya je wannan wuri babu izini, to sai tari ya turnuke shi sannan wani inji ya hadiye shi. 27 Tauraruwa Mai Wutsiya Sai kuma ga su tsundum a cikin daki na takwas inda wata murya ta ce a kai wannan yaro. A dakin ne fa akwai wasu 'yan dakuna har guda bakwai, kowane daki da inda yake iya tafiyarwa cikin dakuna da suka keto. A nan ne kuma aka ba wannan yaro wani irin abin sakawa a kunne. Sannan kuma aka kawo wani don ya nuna masa yadda ake aiki da injinan nan, kuma aka sa shi ya taba injin wurin, amma kafin ya ta da shi, sai da aka je ainihin dakin ita kunamar, aka ajiye wani dan rago. To da ya tayar da injin a kamar minti biyu, sai aka ce ya kashe ya kuma je ya ga abin da wannan dan rago da aka kai wurin. Ko da ya je sai ya tarar an mai da wannan naman dan rago lakai-lakai. Ko kuma ma ya zamo kamar fatar ragon, in dai ba don kara tsawo da ta yi ba, sannan sai aka dauka aka jefar da shi ta taga, iska ta sami nata. Bayan da ya gama wannan aikin ne sai ya ce, "To mene ne manufar wannan irin aiki da kuka yi wa wannan rago?" Sai kuwa aka ba shi amsa cewa ai wato an yi wannan ne don shi kansa ya sani cewa, in ya yi wasa ya bar wani 6era ya shigo wannan wuri, bai yi masa haka nan ba, to shi ma ya tabbata babu abin da zai same shi, illa irin wannan karshen. In ko ya zauna ya yi aiki tsakani da Allah, to zai sami saki bayan an gafarta masa laifinsa na kutsawa Kasarsu. Muhammadul Ziyara nan ya kama aiki gadan-gadan tare da amfani da injina ba ji ba gani. Dare da rana, safe da yamma, sai dai kawai wani lokaci akan kawo masa abinci ya ci, sannan ya ci gaba da aiki. Ga mai koya masa aiki, ga masu gadinsa. Haka dan talikin nan ya dinga yi har kwana takwas, sannan shi wannan mai garin ya kira shi don ya sallame shi saboda irin aiki mai kyau da ya yi musu. MUHAMMADUL ZIYARA YA KOMO DAGA SAMANIYA A lokacin da aka kira Muhammadul Ziyara don a sallame shi, sai ya ga an hau da shi wani bene, inda ya je ya tarar da wani mutum ya kinkime a kan wata kujera mai juyawa, duk inda mutum ke so ya juya ta. Ko da shigarsu, mutumin na duban sashen da ke duba kofar dakin ne, watau yana mai juya wa kofar dakin nan baya. To sai kawai ya waskata kujerarsa ya juyo yana duban kofa. Waje daya kuma ga wata 'yar kujera cike da kayan 28 Tauraruwa Mai Wutsiya shaye-shaye iri-iri, kuma ga wafansu mata can waje daya suna zaune suna jiran kowane irin umarni daga wannan Sarkin nasu. Sai yaro ya shiga ya yi gaisuwa, ya nuna cewa kuma lallai ya ji dadin zaman da ya yi da wannan masarauci tare da talakawansa, kuma ya yi murna da irin ilimin da ya samu daga gare su. A wannan lokaci ne fa sai wannan Sarki ya yi wuf ya tuna da shashancinsa da ya sa ya nuna wa wannan yaro dukkan dabarunsu, kuma sai ya yi tunani, ya dauko wani dan kuttu na karfe wanda ya yi kama da karamar rediyon hannu. To amma shi wannan Wayalis ne, watau wanda mutum zai iya magana da wani wanda ya ke yana da ainihin irin wannan Wayalis din. Da shi wannan Sarki ya yi mui da baki sai can yaron nan ya ji an bude kofa daga bayansa ya ga wani ya shigo da wani abu kamar kokon kai, amma na karfe da wata waya yana hade da jikin shi wannan koko-kokon. Sai aka yi wuf aka sa wa wannan yaro a ka. Ko da aka ta da injin sai idanun yaron nan suka yi burwai kamar wanda ya suma, ko kuma za a cire wa rai. Bayan kamar dakika talatin da ta da injin nan sai kawai yaron nan ya ji duk ya mance da dukkan irin abin da ya sani a game da gidan nan da ya yi bauta na kamar kwana takwas, abin kamar a mafarki, amma hankalinsa dai yana nan tare da shi, saboda haka ainihin abin bai 6aci kwarai ba. Sarkin nan ko da ya san abin da ya yi, sai ya yi wata 'yar gajeriyar dariya irin ta keta. Sannan ya tambaye shi cewa me ya yi a makon da ya wuce? Yaron nan kuwa sai ya ce, “Ai shi bai yi komai ba banda hutu da barci.” A nan ne shi wannan Sarki ya san cewa lallai wannan ya samu, kuma yanzu ba shi da sauran tsoro na game da wannan yaro, yadda yake ba zai iya gayyato masa komai ba, ko kuma kowa ba zai je inda ya ke cin duniyarsa ba. To a wannan lokacin ne kuma ya tambayi yaron nan don ya ji ko yana so ya koma birbishin kasa? Yaron ya ce, kwarai kuwa wannan abu ne ai wanda yake so. To ainihin wannan Sarki sai ya sa aka ba shi zinare cikin gwangwanin taba daya, kuma ya ba shi riguna ya sa don saboda tun da gadon nan ya sauke shi yana saye ne da wando da kuma wadansu 'yan takalma, da kuma 'yar tsumman singiletinsa. Bayan da ya sami wannan kaya kuma, sai aka sa mutanen nan guda biyu da suka fara tarbo shi lokacin da gadon nan ya fado da shi a kan wannan garin su mayar da shi kasa. Da suka fita daga dakunan, wadannan mutane biyu sai suka 29 Tauraruwa Mai Wutsiya kama hannun wannan yaro, sannan suka ta da injinsu suka tashi sama, tare da wata 'yar kara mai dadi. Bayan da suka yi sama ne sai can kuma suka sauko kasaKasa suka yi ta yin kasa har suka iso wajen hazo, suka keta shi. Suka wuce suka yi ta yin kasa dai har suka fara hango wani sashe na duniya mai itatuwa, ko ma mu ce dazuzzuka da ruwa. Kuma ga shi ta zamo a kewaye sai ka ce wani dan wuri da aka shata, amma kuwa sai ka ga duk zafin tafiyar mutum ba zai cim ma wannan wuri da samaniya ta hadu da kasa ba. Bayan da suka kusa kasa, sai mutanen nan suka karkata kawunansu ta wajen hagu sai kuwa ya ji wata magana kamar daga rediyo wadda ta ce ku ajiye shi ko a ruwa ko a dawa duka daya ne. Bayan ya ji haka ne kuma, sai ya ga sun yi kasa sun nufi wani kasurgumin daji da shi. Can sai ya ji su kaya-kaya cikin ganye, suka yar da shi a wannan wuri, sannan suka sake matsa injinsu suka sake ta shi suka nufi sararin samaniya. Shi dai sai ya daga kai yana ta kallon wadannan mutane biyu, har suka bace masa. A wannan lokaci kuma sai ya nisa ya kuma nemi gindin itaciya, ya sami wani dan guntun itace ya gyaggyara wurin ko ya sami dan sarari ya zauna, ya kishingida a kan tushiyar itaciyar don neman ya sami barci, domin kuwa ya jima idanunsa ba sa samun hutawa. Da kwanciyarsa kuwa sai barci ya share shi, ya kuma dinga yi ba ji ba gani. Yana cikin barci ne fa, sai ya fara mafarki wai ga shi ya tafi taurari, kuma ma har daga can wai ana yi masa shirin zuwa wata inda zai sheke ayarsa, sannan kuma ya ci karensa ba babbaka. To duk dai a cikin mafarkin sai ya ji wai an ce da shi wai yanzu ya soma aikinsa na shida ne, watau a irin gwaje-gwajen da za a yi masa saura daya ke nan ya sami zuwa ga taurari. Kuma burinsa ya cika ke nan game da irin abin da yake nema ya samu. Har gogan naka ya ci gaba da tunawa da yarinyar nan da ya gamu da ita a birnin Malala, kuma har ma wai ga su suna sheke ayarsu a cikin birnin Taurari. To a wadansu lokuta in mutum ya yi mafarki, sai ya tarar karya ne. To amma akwai wani lokaci da mutum kan yi mafarki wanda ya ke kusa da gaskiya, domin ko da zai zamo mutum ya yi mafarki, sannan kuma daga baya abin ya zamo ya faru, to sai mutum ya ce mafarkinsa ya kusa zama 30 Tauraruwa Mai Wutsiya gaskiya. Ainihin abin da mutum ya samu damar yi shi ne kadai gaskiyar. Yaron nan dai ya yi ta mafarke-mafarke yana ta kuma shara barci a wannan gindin itaciya har rana ta zo ta cim masa a inda yake kwance, rana ta fara gasa shi ya farka firgigi da tsammanin ko yana kan gado ne yana kwance. To amma sai ya ga ashe ba haka ba ne, yau yana kwance ne a cikin ciyawa, kuma ko darajar tabarma babu balle a ce ya sami gado. Yunwa ta fara kama wannan dan taliki kuma a wannan daji babu abin da ya mallaka banda zinare din nan da aka ba shi tsaraba wanda kuma shi yana ganin ba shi da wani amfani tun da ya ke ma a wannan lokacin da karin waina suka ba shi da ya fi masa wannan tarin dukiyar wadda ba ta amfani wajen ci, in dai ba birni mutum ya isa ba. Kuma a wannan lokacin bai san Gabas ko Yamma ba, kuma ko da ya sani din ina za shi? Babu alamun gida a gabansa ko bayansa, saboda haka sai duk abin ya dame shi. Kuma ya rasa ainihin abin da yake ciki. Ana cikin haka din ne sai ya ji an runtse masa ido daga bayansa, ko da jin haka kuwa, wa kake tsammanin shi zai zata a zuciyarsa? A'a, wa kuwa banda yarinyar nan da ya gamu da ita a birnin Malala, to amma ko da aka sakar masa fuska, ya juya da murmushi don ya ga yarinyar nan, ina, sai ya ga Kolin Koliyo ne. To duk da haka dai an ce da babu wawa gara da wawa, balle shi wannan ma ya wuce gaban wawa sai dai dodo. Gama dodo shi ne aka ce ba a yi masa magana gadangadan sai dai ko rada. ya Yaron nan sai ya gaishe da Muhammadul Sama, shi kuma amsa yana mai farin ciki da irin kwazon da yaron nan ya nuna masa, har kuma ya ce zai yi wa yaron nan albishir. To ko kafin Kolin Koliyo ya yi wa wannan yaro albishir, sai yaron nan ya tare shi ya mika masa ainihin kwayoyin zinaren nan da ya samu daga inda ya fito, aikin gwaji na hudu. Kolin Koliyo ya karba ya yi murna da kwazon wannan yaro kuma ya yaba nagartarsa da kuma gaskiyarsa. Ya sa masa albarka, sannan ya ce masa, "To saboda wannan abu da aka yi ina so in yi maka wani adalci, watau ko da yake yanzu ne za ka shiga aiki na biyar, to amma in ka tuna ka taba zuwa cikin tsakar dare ka gaishe ni, wata rana da na fito daga cikin wata 'yar tauraruwa mai wutsiya. Har na samu na ba ka wata 'yar kwalba." Yaron nan 31 Tauraruwa Mai Wutsiya ya ce masa, "I, haka ne." Ya kuma tsaya tsai, yana sauraron yadda shi wannan mutum zai karasa zancensa. Kolin Koliyo ya ce, "Tо na mayar da wannan gamuwa da ka yi da ni ta tarihi, muhimmiya, kuma na mayar da wannan aikin gwajinka na daya wanda ya mayar da yawan ayyukan gwada ka da aka yi zuwa biyar. Yanzu kana cikin na shida. Da ka gama wannan kuma sai shirin na bakwai kuma na Karshe ke nan. Yaron nan fa murna ta kashe shi, yana jin yunwa da, amma kuma sai har ya mance ma da wannan yunwa da yake ji don saboda ya ji cewa sauran aiki daya kawai ya rage a gabansa maimakon biyu, kuma da ya gama zai kai ga samun cikon burinsa. Muhammadul Sama, sai dai ya 6ace ya bar Muhammadul Ziyara da murnarsa. Muhammadul Ziyara sai ya shiga yawo а cikin dajin nan yana tafe yana waka don saboda murnar irin wannan labari da Kolin Koliyo ya ba shi. Yana tafe ya wuce wannan itaciya, ya taka wannan busasshen ganye ya wuce, ya tsunki wannan furen yana kallo, ya ta da wannan tsuntsu, ya tsallake wannan rami. Ya dauki 'yar wannan tsakuwa ya yi jifa da ita, kai yaron nan dai yana ta ayyuka iri-iri, har ya kai wata 'yar korama wadda ta ke cike da ruwa, kuma shi wannan ruwan shar da shi, kamar babu abin da ya taba shiga cikinsa. Yaron nan ya ji a lokacin jikinsa ya fara danko, saboda haka nan sai ya tuttußе kayansa ya ajiye a bakin rafin nan, shi kuma ya zamo daga shi sai dan kamfai, ya yi kuwa tsalle ya fada cikin ruwan nan, tinjim!! Da ya fada ya yi ta wanka ya guggurje daudar da ke jikinsa, ya goge hakora. Ya wanke kansa, ya dai fito fyas, babu dauda a jikinsa. Ya gama wanka ke nan kuma yana shirin ya fito ya dauki wandonsa ya sa, ya je ya sake hutawa tun da rana ta kusa faduwa, sai ya ga wani biri ya je har ya dauke kayansa ya sa wando, ya kafa hula. Kuma yana kokawar sa rigar yaron nan, to amma ta ki sawuwa, sai Muhammadul Ziyara ya yi nitso cikin ruwa ya bullo ta gaban rafin nan ya fita daga cikin rafin a hankali sannan ya mamayi birin nan don ya kwace kayansa, sai kuwa ya ji wani birin ya yi kuka. Shi kuwa biri mai wando ko da jin kukan dan'uwansa, sai ya tabbata babu lafiya kare ya sha taba, sai ya yar da rigar nan ya yanka a na kare, yaron nan kuma ya danna ya bi 32 Tauraruwa Mai Wutsiya shi. To abin ka da abin da ba sabo ba, sai shi birin nan wandonsa ya kwance kuma tun dama ya yi masa yawa, sai kuwa wandon ya tadiye biri, sai gani kake biri na faduwar 'yan bori, sai ya fadi ya tashi, ya kuma sake faduwa. Shi kuma yaro sai bin sa yake kamar wadanda ke wasan buya. Ya waska nan ya garzaya can, sauran birai kuma sai suka taru suna dan kugi kamar suna ta dariyar irin abin da birin nan da yaro suke yi. Da kyar dai daga karshe yaron nan ya samu ya sha kan shi wannan biri ya kama shi ya zare wandonsa ya kuma koma ya dauki hularsa da rigarsa ya sa. Su birai din sai suka kuma zamo sun shaku da yaron nan, kowane lokaci sai ka gan shi cikin dajin nan tare da a kalla biri daya. Yaro yana ta garari a wannan daji har dare ya yi, ya ga cewa lallai ya kamata ya sami wuri ya kwanta, ko ya hutar da kasusuwansa. A wannan lokaci sai ya ga biri ya hau sama ya kwanta a cikin wani dan amaku watau shi birin nan ya sami tsakanin reshe da reshe ya yi wani dan gado inda zai iya mike bayansa. To ko da wannan yaro ya ga wannan abu sai shi ma ya ce toai lallai shi ma ba a bar shi a baya ba wajen irin wannan alatu na daji. Sai ya nemo 'yan siraran itatuwa guda biyu, ya kuma tayo kalgo ya zo ya sami wata itaciya mai wadansu rassa guda biyu wadanda ya ga alamar cewa lallai 'yar tazarar da ke tsakanin wadannan rassa za si iya daukar tsawonsa. Saboda haka kuwa sai ya sami wadannan siraran itatuwa guda biyu, ya daura daya ta wannan sashi na wannan reshe, daya kuma a daya 6ari. Ya koma daya reshen, ya kama karshen kowadanne siraran itatuwan nan ya tamke su da kyau a jikinsa, yadda watau idan mutum ya koma waje daya zai ga kamar an daura igiyar wanki ne, to amma guda biyu, dukkan su suna daure da rassa biyu kuma da 'yar tazara a tsakaninsu, yadda inda za a cike tazarar ta tsakaninsu za a iya kwanciya ba tare da damuwa ba, sai dai ko in mutum mai mugun barci ne. Da yaron nan ya koma da baya ya ga cewa komai ya yi, sai ya je ya samo kalgo da yawa ya zo ya yi ta hada wadannan danyun kiraren itatuwa yana daurewa datsan-datsan, har ya cike tsakankanin reshe, da kuma tsakanin karamin itacen nan da dan'uwansa. Abin ya tashi gwanin kyau, kuma kai da gani ka ga gadon lilo irin wanda aka yi shi ta hikima, da dabara daga wajen 33 Tauraruwa Mai Wutsiya birai. To bayan da gado ya samu sai kuma ya je ya samo ganyayyaki masu taushi ya zo ya barbaza su a kan wannan gado nasa da ya yi, sannan kuma ya zo ya kwanta ya sami rurumi. A wannan ranar dai ya gode wa biran nan saboda agajinsa da suka yi da samun gadon barci. Ya kuwa yi ta sharar barcinsa ba tare da wani abu ya dame shi ba. To yaron nan ya yi ta barci har gari ya waye, har birai suka farka, sannan rana ta fara washewa da irin dan shudi-shudin nan nata na sheki, kuma iska tana dan busawa a hankali yadda kowa da kowa zai ji dadinta. Itatuwa da ganyayyaki sai busawa suke yi a hankali suna rangaji. Abin dai gwanin ban sha'awa. To amma yaron nan duk bai farka ya ga irin wannan ni'ima ta kyakkyawar safiya a daji ba. А maimakon haka ma sai ya shiga mafarkin wai ga shi an sa shi a daki mai kunama za a ta da inji, to ita kunamar ta yi kokarin ta gudu, amma sai wani ya zo ya rike ta abin kuwa ya zo a dace lokacin da wani ya rike a cikin mafarkin nan sai kuma birin nan da ya taba dauke masa wando ya sa, ya zo ya kama shi. Nan take kuwa Muhammadul Ziyara ya kwalla ihu kuma ya zabura daga kan gadon nan nasa, ya ma yi sa'a ne, da ya tuntsura kasa, kuma babu shakka da ya ji ciwo, domin irin surkukiyar da ke karkashin wannan itaciya sai wanda ya gani. Ko da farkawarsa sai abin ya ba shi mamaki kuma da kunya saboda irin wannan abu da ya farka ya gani, shi yana tsammanin za a kashe shi ne sai ya

Chapter 4 of 7