Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 7
ana zama a irin wadannan kujeru ba, sai ya kura wa yarinya ido kawai. Ita kuwa sai ta yi dariya, ta je ta kama hannuwansa ta zaunar da shi kan kujera, sannan ta ce da shi, "Yau ne sunanka dan samari domin haka ne na kawo ka fadata, na sa kuma Muhammadul Sunanye ya je ya zabar maka suna mafi kyau da tsari." 9 Tauraruwa Mai Wutsiya Yarinyar nan sai ta ci gaba da yi wa Kilba bayani cewa shi Muhammadul Sunaye din nan yana da sunaye iri-iri, kuma yana iya zabar wa mutum sunan da ya fi dacewa da shi, wanda kuma ya ke cike da sa'a, yadda ya ke ko da mutum zai shiga cikin wani hadari idan dai zai iya kiran wannan suna nasa, to ka ga wani dan'uwansa wanda ke da sunan wanda kuma ya fi shi fasaha, da lakanin abin, ya zo ya cece shi. Tana gama wannan magana sai ta sake tafa hannayenta sau biyu, sai can ga 'yan mata wadansu daban, sun zo sun durkusa, sai ta ce da su su tafi su shirya musu abinci, da za su ci su biyu, watau ita da wannan yaro. Yaron nan dai mamaki ya kama shi, sai kallon ta yake yi don bai taba ganin namiji da mace suna cin abinci tare ba. To can wata sai ta zo ta ce wa yariyar nan, "Ga ruwan can an shirya don wannan bako namu mai martaba." Yarinya sai ta ce, "To, ai sai ka tashi domin in kai ka wurin wanka ko ka yi wanka ka ji dan dadi-dadi." Kilba ya mike suka kama tafiya a kan shimfidu har suka kai wani dan karamin daki a can sakon shi wannan babban dakin. Da kusantarsu da wurin kuwa, sai ya hangi wata yarinya na tsaye cikin ladabi tana jiran su su isa, ta bude musu kofa. Da isarsu kuwa sai ta bude kofa sannan ta koma waje daya ta tsaya. Shi gogan naka ko da bude kofa sai ya nemi ya fara shigewa daki, to sai ita wannan da ta bude dakin ta tsare shi, matar ta fara shigewa tukuna sannan shi kuma ya shiga. Wannan kuwa ya ba shi mamaki. sa yi Da fa shigarsu sai ya ce, "To mene ne dalilin da ya kika fara wucewa gaba, sannan ni?" Sai wannan yarinya ta murmushi, ta ce da shi, "To ai ka san kai namiji ne ko?" Ya ce, "I." Sai ta ce, “To ai ka san kowane lokaci ya kamata namiji da ya ke shi yana da mazakuta a jikinsa ya rika lura ya ga ko'ina aka je matarsa ce ké gaba, ko kuma akalla matar da suke tare da ita, ta wuce wurin lafiya, kafin shi ya wuce. Dalili ke nan kuwa mu nan muka saba mu ga najimi ya rika tabbatarwa matarsa ta wuce kofa kafin shi ya shige. Yaro ya yi murna da jin wannan bayani maí faranta zuciya tare da annuri da wadansu kalmai kuma masu neman bayani. To amma duk da haka bai nemi bayanin komai ba, tun da ya gan shi cikin wani dan daki da wani katon daro cike da ruwa, ga kuma madubi a waje daya a jikin bango, ga soso ga sabulu. Ga 10 Tauraruwa Mai Wutsiya wani katon kyalle wanda ya ji cewa wai ana kiran shi tawul, watau abin tsane ruwa bayan mutum ya yi wanka. Yarinyar nan ta ce da shi ya tube ya shiga ruwa ya yi wanka, in ya fito ya goge jikinsa da tawul. Ta kuma buda masa wani wuri kamar kabod inda ya ga riguna, da wanduna, da huluna iri-iri, ta ce in ya gama ya fece kansa, ya kuma sa rigunan da yake so, sannan ya sa takalma, da dai dukkan abin da yake so ya sa. Kuma idan ya ji bai gane wani abu ba daga cikin abubuwan sai ya matsa wani dan kullutu da ke jikin bango. Sannan sai ta fita, ta sakaya masa kofa, ta ce, 'Sai ka fito.' Dan Kolin-Koliyo sai ya tube 'yan tsummokaransa, ya zubar a kasa, ya fada tsundun cikin daron nan, yana ganin kamar kududdufi ne. To shi bai san ruwan zafi ne ba, ai kuwa sai nan da nan ya zabura ya kwada ihu, ya kuwa tashi, ya shiga matsa dan kullutun nan da aka nuna masa. Shi bai san ashe Kararrawa се yake matsawa ba. Yarinya nan da nan ta je a guje, duk tana ta mamakin ko me ya faru. Ko da shigowarta sai ta ga mutum a tube, ta yi mamaki, kuma nan da nan sai ya ji ta ce, "A'uzu Billahi. To nan da nan shi kuma sai ya ji 'yar kunya, ko da yake da ma ya riga ya suturta gabansa, sai dai ya ji kunyar kauyancinsa ne kawai, sai ya ce mata, "Shin wannan ruwan haka ya ke da zafi?" Sai ta amsa masa ta ce, "Ai haka ya ke, mun ga ka fito cikin sanyi, shi ya sa muka ga cewar ruwan zafi zai fi kyau. Ai sai ka kokarta haka nan ka ji ko ka iya yi." Kilba ya ce, "To ai ni da ma so nake in ga haske a dakin domin ko da kika fita sai na ga duk fitilun dakin sun dushe, amma yanzu da kika shigo sai dakin ya cika da annuri ga haske ga ni'ima.' Yarinya dai sai ta yi murmushin nan nata mai sa yaro ya manta cewa ya yi na Sauna, ya yi karo da itaciya, don saboda manta kansa da ya yi don tunaninta. Nan kuma ta sake sallama da yaron, ta ce masa sai ya fito ke nan. Yaro fa ya shiga wanka. Yana ta tunani, ya fara jin ainihin yarinyar nan dai ta fara shiga masa cikin kashin ransa. Wani wajen kuma yana tunanin ga shi wai za a sake rada masa suna, sai ka ce wani jinjiri. Ga shi kuma shi har yanzu yana so ya isa ga taurari, to kaka-tsara-kaka, goma da goma sai dan gata. Karo da karo sài rago, ba a sanin rago kuma sai an kara, saboda haka ya ce zuciyarsa 'shi kam ya dage 11 Tauraruwa Mai Wutsiya wa wannan niyya tasa ta cim ma taurari, kuma ko ta yaya ya yi niyya kuma za shi. Yaro dai ya gama wanka tsaf, har da dan shasshafa mai, da fece kai, ya tabbata dai ya fito fyas. To amma me, abinka da bakauye, duk da kayayyakin da aka nuna masa ya kidime sai ya daura tawul, ya kifo sauran aka, ya fito wai shi ya sa wata riga ta burgewa. Nan take kafin ya fita sai da ya duba madubi ya ga kansa har ya ce, "Lallai yau zan burge in cashe." Ba shakka zai burge amma ba wai don rigar tawul ba. To yana cikin wannan shirmen ke nan sai ya ji an kwankwasa kofa a hankali watau abin kamar an kada wata 'yar ganga mai zaki, sai ya tabbatar yarinyar nan ce, sai kuwa ya ce, 'Shigo! Sai ta shigo ta yi masa barka da gama wanka. Ta bude dan kabod din nan kuma ta ce masa ya zabi kayan da zai sa, To shi kuma da ragon azanci maimakon ya ce a'a, ita ta zabar masa, sai ya je ya shiga daukowa. To ainihi kuwa shi cikin kabod din da sashen kayan mata da na maza, a maimakon ya fara dauko wando, sai ya tsallake ya dauko tofi mai kyalli da daukar ido. Nan da nan sai ya ji yarinya ta kyalkyace da dariya. Kamar ya sani sai ya yi maza ya yar da tofin, sai ta ce masa, "Ai ga wajen kayan maza nan." To a lokacin ne fa shi wannan yaro ya dauko bakin wando, bakar shat da jar kwat, da kuma jar hula, sai dai ta ga lallai bai saba sa kayayyakin ba, sai ta ce, "Bari dai in dauko maka." Ta dauko masa farar kwala da shat, ta mayar da bakar, ta dauko masa bakar kwat ta mayar da jar, sannan ta dauko farar hula ta mayar da jar. Dan samari fa nan take ya ci adonsa ya yi tsaf ya je ya duba a madubi, sai ya kyalkyace da dariya saboda tunawa da ya yi lokacin da ya cukumude da tawul ya je yana duba madubi wai shi ya burge. Yarinyar nan sai ta kamo hannunsa suka fita daga dakin, suna tafe tana rausaya tana dan dubansa da wutsiyar ido. Daga nan sai Yarinyar nan ta nufi da shi wajen cin abinci inda suka tafi suka zauna a tebur. Aka kawo kayayyakin abinci kamar su inabi, dabino, gwanda, lemo, ayaba, da kek, da miya wadda akan sha ta da ludayi kawai, da masa irin wadda a kan ci da miya wata dabam, da hanta, da madara da ti, da kuma wasu irin 'yan hankici na takarda, da kuma burodi da man shanu mai 12 Tauraruwa Mai Wutsiya gishiri, Watau irin daskararren nan wanda a kan shafa a jikin burodi don a ci. To yau fa ake yin ta, yau ga wanda zai zare hannu ya wanke shi ya sa shi cikin debi da kanka, ya warba a baki, ya cire idon daddawa ya yar waje daya, ya ci gaba da cin abincinsa, har ma wani lokaci idan an yi rafkanuwa wani dan kuda ya fada a yi nama da shi. Tun da ya ke ainihin shi wannan yaro a gidansu yakan sha lami ne, ranar ko da za a yi miya mai nama lallai ranar za a yi gayya a gidansu tun da za ta zamo rana ce ta musamman. Yau ga shi Allah ya kawo shi inda zai ci abinci ba ma a kan tabarma ba, a'a wai a kan tebur, kuma ba da hannu ba, a'a wai da wadansu cokula masu yatsu da kuma wadansu iri-iri har da wuka. To ka san kai da kanka ainihin wurin ma zai ba mutum tsoro balle irin wannan shirgi na abinci da aka kawo. Yarinyar nan fa sai ta ce da yaro ai za su fara taruwa don a raďa masa suna. Nan da nan kuma sai ta dauki cokali ta shiga shan miya, sai shi kuma ya shiga kallon ta galau, kamar wanda ya ga ana saran mutum, shi kuwa ba shi da karfin hanawa. Domin shi wannan yaro banda a wannan rana bai taba ganin ana shan miya haka nan tsirarta ba. Yarinya ta dube shi ta yi murmushi ta ce, "Ai sai ka dauki abin da kake so ka yi ta ci don yanzu ba mu da lokacin 6atawa." Yaron nan ya dauki ayaba ya saka a baki da bawon da komai. Yarinya kuwa ta dube shi ta ga ya 6ata rai saboda yana jin zaki-zaki da daci-daci, shi kuwa bai sakankance da irin wannan abincin nata ba, har ya shiga tunannin ko ma guba ce aka zuba masa cikin wani abu mai zaki. Yarinya dai ta ga shi wannan dan taliki bai gane wa irin wannan harka ba, saboda haka sai ta kawo gutsuren waina da miya ta hada ta ci, shi kuma ya gani, saboda haka nan sai shi ma ya dauki wainar yana ci. To sannan ne ya ji dan dama-dama, daga nan kuma komai zai ci sai ya dakata sai ya ga ainihin abin da ta yi sannan ya yi. Ko da yake shi inda duk ake sa cokali, ko cokali mai yatsu, shi hannu yake sawa, domin tun da ya ke bai taba rike ainihin koshiya ta itace ba, balle cokali ko kuma wata uwa wai cokali mai yatsu. A haka nan dai aka kokarta har aka samu aka gama cin abincin, daga karshe kuma ya dauki abin goge hannu, watau irin 'yar takardar nan da akan yi amfani da ita don kare datti a riga, ya nemi ya tsoma ta a miya domin ya foye shi, shi ma 13 Tauraruwa Mai Wutsiya cikin ciki. Nan da nan sai yarinya ta agaji yankin nan ta nuna masa amfaninsa. Da aka gama sarai sai aka kawo wa wannan yaro ruwa ya wanke hannayensa, wata yarinya kuma ta kawo wani tawul a cikin tire na azurfa aka goge wa Dan Kolin Koliyo hannu. Ko da gama goge wa gogan naka hannu sai ya dubi rigarsa da kyau don ya ga ko miya ta zuba a jiki. To ya yi sa'a dai miya ba ta zubar masa ba ko dis. Da suka tashi daga kan wannan teburi na cin abinci sai suka je suka shiga wani lambu na fulawa da furannin kallo iri-iri. Suka je, suka zauna a kan wani gado wanda aka kafa shi mai lilo, yaron nan ya hau gadon yana mai mamaki da taʼajibin irin yadda dan Adam ya yi ya kago yadda aka yi wannan irin gado mai đan karen dadin hawa. Suna nan zaune a cikin lambu sai ya ji ana ta hura kakaki da bigila irin na sarauta, ya duba haka sai ya hango mutanen da suke wannan aiki a kan benayen fadar nan wadda samanta ruwa ne, kasanta ruwa, Kudu da Yamma Gabas da Arewa duk ruwa ne, ya kare wannan fadar dungum dinta. 'Yan mata na gama busarsu sai ya fara ganin jama'a ana ta tafiya ana shiga ainihin katuwar farfajiyar nan da suka fada ciki lokacin da yarinya ta shafe masa fuska da hankici. Su dai suna zaune a wannan wuri yarinya ba ta cewa komai, sai fuskarta ke sheki kawai, shi kuwa wannan yaron ko da dan hakin wurin, ba shi sha'awa da mamaki yake yi. Can kuma sai ga shanu an kawo guda biyu, daya fari, daya kuma mai fari da ja da kuma baki, aka tsayar da su aka ce shi wannan yaro ya je ya tabi kowanne daga cikinsu domin kuwa da su ne za a rada masa suna. Yaron ya je ya yi kamar yadda aka umarce shi ya yi. Sannan aka tafi aka yanka shanun aka fede su, aka cire hantar kowanne, sai aka gasa aka yanka aka kai wa yaro da yarinya suka ci. Aka kawo lemon kwalba aka ba su a cikin wani dan kofi da ake zuba irin wadannan shaya-shayen. Lokacin da suka gama dura dan wannan lemon nasu sai ga wani mutum ya iso musu kamar daga sama shi da matarsa. Shi mutumin nan wani kosasshe ne, yana saye da fararen kaya, amma da damara ta fata baka, yana sanye da wata hula da ta yi kama da roka ko kuma jirgin sama a kansa. Ita matar tasa kuma tana sanye da wadansu 'yan kayayyaki masu launin sararin sama, kuma da 14 Tauraruwa Mai Wutsiya takalma masu tsini, ga kuma hula ita ma ta sa irin ta wannan mijin nata. Ko da isowarsu sai shi wannan mutumi ya dan duka irin na ban girma ya ce, "Bintun Sarauta yau ga ni na zo wajen shirin namu, kuma ina tsammanin shi Muhammadul Suna ya riga ya shirya." Sai Bintun Sarauta ta amsa ta ce, "Na yi murna da jin haka kuma ina tsammanin yanzu an gama shirya mana komai.' Ta ci gaba da tambayar yaron nan cikin murmushi ta ce, "Ko ka san wannan mutumin?" Sai yaro ya kada kai da nunin kamar ya san shi, to amma bai ce komai ba. Sai ta ce, "Wannan shi ne Muhammadul Sama, kuma waccan ita ce Bintun Sama, watau matarsa, ina fata in ka gan su wata rana za ka iya shaida su?" Sai yaron ya ce, "Haka ne in dai ban shaida wannan yanzu ba, to nan gaba kuwa zan shaida su dukkan su, kuma na yi murna da saduwa da su." Shi yaro yana ganin aihinin shi wannan mutum shi ne Kolin Koliyo, duk da haka dai bai ce komai ba sai ya ja bakinsa ya tsuke kawai. Bintun Sama sai ta ce, "To yanzu me ake jira?" To in gaya maka kafin ta rufe baki sai ga 'yan mata biyu sun iso, sun rusuna, sun ce, wai fada ta hadu, kuma su kawai ake jira. Sai fa 'yan matan nan biyu da suka zo suka ja musu gora, amma fa ba ta makafi ba, irin ta masu ido, kuma masu gata ko a masu idon. Da shigar wannan kungiya cikin fada sai kowa da kowa ya mike kuma dukkan ilahirin wadanda wannan ayari ya tarar a cikin wannan fada bayan da ya mike sai da ya sunkuyar da fuskarsa don saboda tsananin girmamawa. Su hudun nan sai suka wuce ta tsakiyar mutanen da suka yi dafifi a kan gefen dama da hagu na wannan shirgegen daki. Su kuma wadannan mata da suka yi rakiya sai suka je bayan kujerar da wadannan za su zauna suka dauki mafitai suka shiga aikinsu, watau yi wa wadannan mutane masu martaba a wannan gari na cikin tsakiyar ruwa fifita. Yaron nan kuwa sai ya kalli nan, ya kalli can, ya ce wannan a zuciyarsa, ya ce wancan, har ya kiyasta a zuciyarsa cewa, to, ya shiga kasa saura kuma ya hau sama gun taurari in ma da sarari gun wata. Da wadannan suka zauna, sai kuwa sauran jama'a duka suka zauna, sai kuma kowa ya yi tsit yana jiran ya ji irin jawabin da Bintun Sarauta za ta yi. To amma kafin ta yi magana, sai da shi Muhammadul Sama ya tashi ya ce, "Ko da yake na sani ainihin 15 Tauraruwa Mai Wutsiya Mai Martaba Bintun Sarauta, kuma Sarauniyar Birnin Malala, za ta so yin magana saboda babban bako da muka yi, to amma na ga kafin ta ce wani abu zan kira mawaka da makada su dan kada mana ganga, don kowa ya dan ji dadin da mai martaba za ta ji. To amma kafin in kira su masu kida da waka zan fara nuna wa jama'ar Malala cewa mu ne na sama, kuma mu ne na ruwa, a yanzu da ya ke fadar tana da girma, ga ta tankamemiya, kuma akwai fili a sama, to zan yi iyo a sama, don kowa ya ganar wa idanunsa ya san mu ba wasa muke yi ba. Nan take sai shi wannan dan taliki ya mika hannayensa biyu sama ya yi wata 'yar dariya. To in gaya maka kuwa abin gwanin ban mamaki, kafin kiftawa da Bisimilla sai Muhammadul Sama ya yi sama, ko kuma mu ce Muhammadul Koli ya yi koli, don kuwa ita yarinyar nan ta ce sama ne, don kada wannan yaro ya gane cewa wannan ainihin Kolin Koliyo ne. Jama'a sai tafi ake yi, ana cewa, "Lallai na Koli, gaishe ka! Naka shi ne na farko shi ne kuma na sama!" 'Yan yara kuwa sai suka rude sai gani suke kamar zai fado musu a ka. Tsofaffi kuwa sai mai da tarihi ake yi ana cewa ai wane ne dan wane, jikan wane, mai abu kaza da kaza. Bayan shi wannan Muhammadul Koli ya gama shawagi a sama, ya kusan saukowa sai ya sako irin kyastun nan da akan kyasta shi ya kama wuta, ya ba da launi iri-iri, ya kuma haskaka wuri. Nan ne fa wuri ya kara dagulewa, sai kirari ake yi masa, ana cewa mai taurari a hannu, wata ma nasu ne. To a nan ne kuma kai wannan soko watau dan Kolin Koliyo ya yi shirme, ya shafa a guje. To, abin ka da bakauye, shi ma sai ya fita a guje. Ya garzaya ke nan sai shi Muhammadul Koli ya fado daidai gabansa ya rike shi. Abin dai ya zamo kamar ya je ne ya tare shi. Aka yi ta tafa wa wadannan mutane gaba daya. Su kuwa su Bintun Koli da Sarauniyar Malala sai murmushi kawai suke dokawa. Can su wadannan mazan suka dawo suka zauna lafiya abinsu. Tafi ya lafa, can kuma zance ya yi sauki, sai Muhammadul Koli wanda ya ke kamar Wazirin garin ne ya tashi ya ce, "To jama'a mun yi murna da wannan dan taro da aka yi, kuma yanzu za mu kira shahararren mawakin nan namu watau Muhammadul Waka da kuma sahibarsa Bintun Waka su fito tare da 'yan kada gangunansu, su rera mana wakoki irin 16 Tauraruwa Mai Wutsiya wafanda za mu san lallai yau muna nishadi kuma muna yi wa babban bako barka da sauka. Da gama maganarsa sai ya zauna, jama'a duka aka sake fashewa da sowa tare da tafi. Ana tafin nan da sowa, masu ganguna na fitowa, masu siriki suka fara ziza busa, kuma masu ganga suka shiga fan kwankwasa ta kwas, kwas, kwas. To a nan fa wuri ya sake yin tsit kowa na jiran ya ga sarautar Allah, kuma sarautar ganga, da siriki da kuma Muhammadul Waka da Bintun Wake. Abin na yi ne, masu ganga fa suka fara doka ta, ga busa, ga kuma wadansu suna tafi lokaci-lokaci. Wuri ya rude, dattijai suka fara kada kafa, limamai na girgiza kai, sannan yara na kada gindi, kowa dai kidan nan ya soma tsima shi. Kuma kowa babu abin da yake jira sai ya jin irin wakar da za a yi. Sarauniyar Malala kuwa sai idanunta kawai suka yi rau rau suka kuma cika da annuri da hikima, kuma sai ta rika kallon masu kida tana duban shi wannan yaro watau Kilba. To amma ina! Shi gogan naka sai yi yake kamar ya tashi ya carke da rawa, kallo kuwa kamar an sa kugiya ana jan idanuwansa an kafa su ga masu kidan. Can kuma ana cikin wannan kida sai mai ganga ya yi zarya ya yi kamar zai fita fage. Ya matse gangarsa da kyau ya kuma kada ta, sai kowa idanunsa suka bude, kowa ya san cewa lallai ba kawai ba, wannan irin ziyara, da makadin nan ya yi, sai kuwa aka ji wata murya mai dan karen zaki da dadi ga zalaka, ta yi wata 'yar waka mai dadi da sanyaya zuciya. Kowa ya duba haka sai ya ga ashe ainihin Bintun Waka ce ta fara rera irin wakokinta, can kuma Muhammadul Waka shi kuma sai ya fito da nasa salon, yana rawa yana waka, ita kuma tana rawa tana kada kuturi tana kuma kada mama. Kai abin dai da ban sha'awa, kowa sai dadi ya kashe shi. To daga nan kuma sai aka gama waka, sannan ne kuma sai ga wani tsoho ya shigo fada da dogon gemunsa duk ya yi fari, kuma yana yafe da wani irin tafkeken farin mayafi, kuma ga tasbi ya rataya a wuyansa. A hannunsa kuma ya riko turaren wuta wanda zai yi amfani da shi wurin radin suna. A bayansa kuma wadansu samari ne da 'yan mata ke biye da shi. Kowannensu da turaren wuta da furanni а hannunsa, suka zo tsakiyar wannan tafkekiyar fada suka zauna, suka sa wannan turaren wuta da tsohon nan ya dauko a tsakiya. Wato suka yi wa turaren wutar zobe, kamar yadda zobe kan 17 Tauraruwa Mai Wutsiya kewaye dan yatsa. Can kuma aka kawo wadansu kwalaben turaren manya-manya aka ajiye su waje daya, sai malamin nan, wato Muhammadul Suna, ya je ya kira shi wannan yaro bako, Kilba. Da ya je, aka zaunar da shi a tsakiyar mutanen nan da suka kawo turaren wuta. Malamin ya yi 'yan wadansu addu'o'i sannan aka kara turaren wuta a cikin turarurrukan nan na turaren wuta. Hayaki ya tashi, aka kawo wadannan turare kuma aka yi ta yayyafa wa Kilba. Malami kuwa, sai addu'a yake yi, can sai aka ga wani haske mai karfin gaske ya haskaka wurin fal kamar walkiya. Kowa sai gabansa ya fadi. To amma da ganin wannan haske mai kyallin gaske sai jama'a suka ji an ce, “Allah ya raya Muhammadul Ziyara! Amin!" Nan da nan sai shi malamin nan da 'yan mukarrabansa suka bace. Shi kuma Muhammadul Ziyara wato Kilba sai ya gan shi kawai shi daya babu kowa. Babu dai masu rada masa suna, babu 'yan kida, babu 'yan kallo dukkansu. Babu su Muhammadul Koli, hasali dai babu kowa. Kai sam ma a dakin da ya ke da ba a gan shi ba yanzu, ya gan shi ne kawai a wani daki karami wanda a cikinsa akwai gado babba guda daya, gadon kuwa da shimfidunsa da komai, ga madubi dogo irin wanda mutum zai ga dukkan jikinsa in ya ga dama, da kuma wata kofa 'yar karama wadda za ta kai mutum zuwa wurin wanka da bayan gida. To me wannan dan taliki ya iya illa banda ya san na yi? Ko dai ya yi barci ko kuma ya nemi yin kikikin fita daga wannan daki. To amma idan ya nemi fita ma ina za shi? Ga shi kuma duk ya gaji, saboda haka sai ya ce to, tun da ya kammala da gwaji na biyu ai ya kamata ya kwanta ya huta wa dan tsumman ransa. A lokacin ne kuma sai ya hau gado ya kwanta, amma ya rufe ido zai yi barci ke nan sai ya ji Kolin Koliyo ya ce, "I to ka sami suna yanzu ina fata ka yi matukar murna!" MUHAMMADUL ZIYARA YA HAU GADO MAI TASHI To bayan da Ubangidan Muhammadul Ziyara, watau Muhammadul Koli ya yi masa murnar rada suna, sai ya ce da shi ai ya kamata ya kwanta, ya huta don kuwa ya dade yana wahala a wannan rana. To amma fa ya ci gaba da tuna masa cewa wannan lokaci ba na sake ba ne, saboda haka kada ya yi ta barci na babu 18 Tauraruwa Mai Wutsiya gaira babu dalili, domin kuwa dukkan ſaukacin mutumin da yake son kansa da arziki, da kuma ainihin rufin asiri, to, ba ya tare wa barci. Domin me, mutum na cikin barci ne ake iya zuwa a kashe shi, ko wani muhimmin rabo ya wuce shi. Ya ci gaba da cewa ba wai yana nufin ko kada yaron nan ya yi barci ne ba, a'a wato da dai mutum ya yi dan barci nadari, to, sai ya farka ya shiga yin abin da yake tafe da shi. Domin kuwa ya sani cewa lokaci ba abu ne mai jiran Sarki ba, balle bafade. Duniya kuwa babu wanda ya zo domin ya zauna a cikinta. Yaron nan ya ji duk abin da wannan dan taliki ya fada kuma kafin a yi haka sai ya ga wannan mutumin ya bace. A wannan lokaci sai yaron nan ya tashi daga kan gadon nan ya je ya shiga dakin nan na wanka inda ya ga akwai daron nan wanda ya taba wanka a cikinsa, da kuma wani dan

Chapter 2 of 7