Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 6
abin da mutane suka gaza ganewa,har ina tunaninna yi SADAUKARWAr burina ga mutane don na tsira da mutuncina. To amma na kasa jure hakan, ina fatan na yi auren da zan samu nutsuwa وو Alhaji Mande ya murgina kai yana fadin. "Ban ki ta taka ba, amma hujjar ida 99 mutane za su dubeka da ita na ke nema...o Alhaji Atiku ya ce. NAJNOOR113 SADAUKARWA-I "Tunda ka gaza fahimta ta, bari na fada maka matsalolin da na ke samu da matana, ba wai don ina alfahari ni mai gaskiya ba ne, zan fada maka sirrina ne don ka zamo adali a cikin lamarin da mutane ke zargina da shi". A nan ya kwashe masadukkan matsalolin da suka raba shi da matansa yá fada masa, daga karshe ya dora da cewa. "Na sanya wa raina na hakura da aure akan wannan dalili tunda haka Allah Ya tsaro min, amma da ya ke ba ni ke tsarawa kaina rayuwa ba shi yasa na hakura da abin da Ubangijina ya tsara min, kuma ina zuba wa sarautar Allah ido". Alhaji Mande ya yi shiru cikin nazarin maganganun "Alhaji Atiku, hakika yaji kamshin gaskiya a maganar tasa, domin duk wanda zai yi mu'amala da shi zai tabbatar shi akili ne, bare kuma ga iyalansa sai dai da ya ke akwai wasu mazan da a waje suke muminai a cikin gida azzalumai, shi yasa ba lallai ne a yarda da hujjar da zaj bayar ba. NAJNOOR 114 K SADAUKARWA-1 ce. Bayan wani dan lokaci, Alhaji Mande ya "Na gamsu da bayaninka, na tabbata kuma idan da rai da rabo, Allah zai amshi bukatunka Ya baka mace wadda ka ke muradi... Hakika Zahra'u yarinya ce mai tarbiyya da kamun kai, wadda duk fadin unguwar nan zan iya rantse maka babu wadda za ta kamo ko da sawun kafarta ne. Mahaifinta Malam Audu mai almajirai ya tsayu tsayuwar tsayin daka wajen tarbiyyar yaransa, shi yasa duk wanda zai dube ta zai dauka matar aure ce, na yi mamaki matuka kai da ka ganta ka sanya wa ranka ba ta da aure. ban san abin da Allah ke nufi da hakan ba, wata kila kai ne abokin rayuwarta... Lallai idan ka samu nasarar auren Zahra'u zai yi wahala ka samu wata 6araka daga gareta, sai dai idan daga gareka ne matsalar za ta kunno kai" Alhaji Atiku ya ji wani sanyi-sanyi ya ratsa zuciyarsa da ya ji ba ta da aure,. fuskarsa ta yalwatu da murmushi, ya сe. NAJNOOR-115 SADAUKARWA-1 "Wanda ke son zuwa hajji a ka ce an biya masa umra zai yi wasa ne da damar da ya samu? Ai sam hakan ba mai yiyuwa ba ne, shin yanzu me ye abin yi?" Maganarsa ta karshe ta ba wa Alhaji Mande dariya, ya ce. "Abin yi ai ya rage gare ka, wai tsohuwa ta auri jikanta". Su duka suka yi dariya, sannan Alhaji Atiku ya cе. "Maganar gaskiya na yarda da maganarka na cewar ta samu tarbiyya a gidansu, amma duk da haka zan Kara lokaci kafin na je gare ta, ka kara bincikawa ko a wani wajen ne ka ji ba ta da wata matsala, ban so na yi gaggawa na aureta na same ta da wata matsalar a dawo ana cewa halina ne, duk da ban isa na tsallakewa hakan ba idan Allah Ya tsara. Alhaji Mande ya ce da shi. "Ba ni da shakku akan duk wani bincike da zan kuma yi zai haifar da alkhairi, sai dai kamar yadda ka ce din zan sake bincikawa ko NAJNOOR 116 SADAUKARWA-1 don gudun kada na shugabancin lamarin na dawo ina da na sani" Alhaji Atiku ya ce. "Ba ma fatan hakan ta kasance, kullum fatanmu idan muka yi niyyar alkhairi Allah Ya tallaba mana mu ga alkhairin a ciki... Tana makarantar boko?" Alhaji Mande ya ce. "Eh to, kwanaki na ji an ce ta gama sakandire, wanda shi ma abin ya ba wa kowa mamaki ganin duk 'ya'yan Malam Audu ba sa karatun boko sai akan Zahra'u... Ban sani ba ko za ta ci gaba... kai ba na tunanin ma za ta ci gaban" Alhaji Atiku ya jinjina kai cike da farin ciki, ya ce. "Na ji dadin hakan, don wani lokaci karatun mace idan ya wuce sakandire ana samun matsala, duk da dai wasu rashin zurfin karatun ma na haifar da wata matsalar, fatan dai Allah Ya sa ba ta da tsayayye". Alhaji Mande ya ce. NAJNOOR 117 SADAUKARWA-I "To wannan ne ban sani ba, don ko tana da shi, ka'idar Malam Audu yaransa ba sa zancen dare, kuma ba a kofar gida suke hira ba, bare wani ma ya gansu Alhaji Atiku ya sake jinjina kai, ya ce. "Wallahi tun yanzu ma na soma samun nutsuwa akan lamarin, ina ganin kamar kakata ce ta yanke saka". Suka sake yin dariya su duka, Alhaji Mande na shirin yin magana Hafiz suka iso bakin motar shi da abokinsa Habib. z "Yauwa Hafiz, kwara da ka dawo, dama mun gama kai na ke jira" Inji Alhaji Atiku yayin da suke kokarin fitowa daga motar shi da Alhaji Mande. Habib ya rusuna ya gaishė da su, sannan Alhaji Atiku ya takawa Alhaji Mande zuwa kofar gidansa. Sun shiga motar, Hafiz ya dubi Habib ya ce. A th "To abokina, sai ka shigo goben ko, don Allah ka cika alkawari Habib yana dariya ya се! NAJNOOR118 SADAUKARWA-1 lafiya "Kada ka damu, Allah Ya sauke ku Ya ce, "Amin", Sannan ya tayar da motar suka soma tafiya: Alhaji Atiku da farin cikinsa ya kasa boyuwa ya dubi Hafiz ya ce. "Rage sautin kira'ar nan na baka wani albishir Cike da dokin jin abin da ya sanya mahaifin nasa farin ciki ya kai hannu ya kashe rediyon ma gaba daya, tare da tattara nutsuwarsa zuwa ga mahaifin nasa, ya се. "Ina jinka Abba, daga ganin yanayin fuskarka akwai dadadan albishir a tare da kai" Alhaji Atiku ya kara yalwata fuskarsa da murmushi ya ce. "Auren dai zan Kara" Yanayin fuskar Hafiz ta sauya zuwa yanayin tuhuma da kuma tausayi, ya lura idanun mahaifin nasa sun rufe yin auren shi ne kwanciyar hankalinsa, dazun fa da suka taho ya ke masa zancen zai kara aure, shi bai dauki maganar gaske ba ganin yadda lamurran suka NAJNOOR 119 SADAUKARWA-I kasance, sai ya dauka zuwa yanzu din dai zai iya hakura, ashe da gasken ya ke, ko dai dama neman auren ne suka zo yi gidan Alhaji Mande ba maganar fili ce ta kawo su ba? "Wata yarinya ce na gani daga dukkan alamu ta fito daga gidan mutunci, kuma ganinta kawai da na yi sau daya jikina ya ba ni ita ce macen da na ke mafarkin samu, don haka na tuntubi Alhaji Mande ya ke sanar da ni tarbiyyar gidansu din dai irin wacce na ke so ce... To yanzu mun aje magana da shi zai Kara bincikawa don kar ai aikin da na sani". Jin hakan ya sanyaya wa Hafiz rai, don ya yi tunanin addu'arsu ce Allah Ya karba ya hada mahaifin nasa da irin macen da ya ke fatan samu, sai dai kamar yadda shi mahaifin nasa ya fada, matan ba tukwane ba ne bare a kwankwasa a ji wacce ta fi kwari, daga ganinta cikin lullubi sai a ce ta gari ce? Amma kuma ai ya ce masa Alhaji Mande ya tabbatar masa da ingancin tarbiyyar gidan su yarinyar, wanda a saninsa Alhaji Mande NAJNOOR 120 SADAUKARWA-1 kamilin mutum ne mai yakana, zai yi wuya ya fadi abin da babu shi a bayyane. Cike da farin ciki ya ce. "Kai amma zan fi kowa farin ciki idan har a ka same ta da kyawawan halayen da ake fata, ina kuma goyon bayanka dari-bisa-dari akan haka, Allah Ya tabbatar man da abinda ya fi zama alkhairi". garı Alhaji Atiku ya ce da shi. "Amin, kai ma Allah Ya ba ka mace ta وون Murmushi Hafiz ya yi, tukunna ya сe. "Gaskiya zan fada maka Abba, sati biyu da suka wuce na hadu da wata mata a wajen aikina, tana da nutsuwa da kamun kai, sai dai matsalar da na ke tunani ita ce, na fuskanci kamar matar aure ce, don tana da kamewa irin ta matan aure, sannan wani وو namiji ne ya ke kawo ta Alhaji Atiku ya yi dariya sosai, ya сe. "Kamun gafiyar baidu ke nan, kai kanka ka ce kana ganin matar aure ce, to don NAJNOOR 121 Π SADAUKARWA1 i me za ka sanya zuciyarka a ragayar da ba za ka iya fita ba?" Ι と a g n ha ni SC ka : ya ha fal na kv ga Ar tat ya Shiru Hafiz ya yi, kuma fuskarsa ba ta gushe daga murmushin da ya ke yi ba, don mahaifinsa shi ne abokin shawararsa, ya kasa hakuri ne ya boye masa ya ga kwara ya fada masa wata kila zai taya shi da addu'a Allah Ya cire masa sonta. Alhaji Atiku ya ci gaba da cewa. "Wata kila kuma ba matar auren ba се, kamewa ce irin ta gidan kwarai wadda ake son kowacce mace ta same ta, don haka sai ka dage da addu'a idan ba matar auren ba се kuma alkhairi ce a gare ka Allah Ya ba ka ita, ni ma zan ci gaba da yi maka addu'ar da na ke maka ta fatan samun abokiyar zama managarciya" Ya ji dadi ainun à ransa, shi dama ya san mahaifinsa mai karfafa masa gwiwa ne akan duk wani abu na alkhairi, yа сe. "Amin Abba, kuma gobe idan Allah Ya kaimu zan bincika na gano shin matar auren NAJNG SADAUKARWA-1 ce ko ba ta da aure. Idan tana da aure zan rungumi hakuri, har Allah Ya zaba min mai kyawawan halaye kwatankwacin wanda na ga ta siffantu da su. Idan kuma ba ta da aure, to fa zan ce maka na samu. sb s) Kunya ta sa ya kasa karasawa, sai shi Alhaji Atikun ne ya ce. sb Ka samu mata ko? Daina jin kunya, kai abokina ne kuma dana ne". Haka suka iso gida cike da jin dadi da nishadi, musamman Hafiz da ya ke ganin lokaci ya zo na farin ciki a gidan nasu. Suna tsayawa da motar Alhaji Atiku ya fito ya shiga cikin gida, yayin da shi kuma Hafiz ya IHNAGU ja motar zuwa wani wajen. nimoSai da ya zo kwanciya ne tunanin ya sha masa kai, wato tunanin Fadimatu, shi kam zai yi ittifakin son da ya kewa Fadima kusan ya fi wanda ya ke wa Rufa'atu duk da kuwa ita ce wadda suka dade kuma ya fara so a rayuwarsa, sai dai shi so ya gaji haka, shiga NAJNOOR 123 SADAUKARWA-1 ya ke ya kurda inda duk mutum bai yi tumaninsa ba, don haka ba zai yi jayayya cewar Fadiima ta yi masa shigar burgu ba. Takaicinsa daya rashin tabbas da ke t dawainiya da lamarin nasu, hakika yana cikin a taraddadin tabbatuwar Fadima wadda ba ta da aure, domin alamomi sun bayyana kansu na n cewar ita din mai auren ce, amma duk da h kokarin da ya yi na ganin ya taushi zuciyarsa n ta hakura da son matar wani hakan ya ci tura, S don haka ya sanya wa ransa hakuri da k kaddarar da ta zo masa, mai kyau ko mara kyau. y Fata da burinsa ta zamo mallaki a gare ha shi, musamman don ta maye masa guraben fa filayen da ya rasa na cikon farin ciki a n zuciyarsa da rayuwarsa gaba daya, domin k kowane dan Adam ba shi da kwanciyar ga A ta ya hankali muddin bai dace da matar aure ta gari ba, wadda za ta iya ba wa 'yalyansa tarbiyyar kwarai mai nagarta, NAJ 124 SADAUKARWA-I Kuskure daya ne ya ke ganin ya tafka, na saurin sanarwa mahaifinsa lamarin, anya bai yi kuskure ba? Koda ya ke ai dama ya sanar masa yana tunanin tana da aure. Da haka dai ya samu baccin ranar ya dauke shi. Washegari da ya je kamfani yana zaune a ofis dinsa, zuciyarsa ta azalzale shi ya fito harabar kamfanin don ganin ko zai gam-dakatar da ganin Fadima. Bai wani jinkiri ko tsayawa shawarar yin ko barin ba, kai tsaye ya fito harabar ya tsaya a jikin motarsa. Kamar ko yaushe bai fi mintina goma da tsayuwa ba ta danno kai, wannan karon abin ya ba shi matukar mamaki, domin ita kadai ya gani tạ shigo cikin harabar kamfanin sabanin kowace rana da namiji ne ya ke kawota akan mashin dinsa. Tafiya ta ke cikin nutsuwa ba ta ko duban gefenta, illa gabanta inda ta ke takawa ke nan. Ya shiga tunanin me ya hana matashin ya kawota a yau kamar yadda ya saba? NAJNOOR 125 k is n b a g n h n S R : ya h fa ni SADAUKARWA-1 Amsar da ta gaza samuwa ke nan a gare shi, illa binta da kallon kawai da ya dinga yi har ta kusa shigewa ta gefensa, ga dukkan alamu ba ta lura da wanzuwarsa a gurin ba, babu mamaki domin ai ba ta cikin yanayin da za ta iya lura da shi din. Mace mai tafiya tana waige-waige ita ce ta ke ganin kowa har idan a ka yi katari da marasa kamun kai ko kuma masu irin surutun nan, sukan kasa tsallakewa kula wanda suka gani koda kuwa ba ya cikin irin mutanen da ya kamata su kula a lokacin, ma'ana wadanda kula su ko rashinta ba ya amfanarsu da komai. Zuciyarsa ta ayyana masa kawai ya tanka mata, wani tunanin. kuma da ya yi na rashin dacewar hakan ya hana shi. Har dai ta shige ajin da suke daukada k karatun yana tsayc sagale da baki, abin da ya lura da shi, kullum tana sauya kayan da ke g A jikinta, hijabi dai ce kamar ba zasu wuce guda ta y biyu wadanda ta ke da su ba, tunda shi dai a iya saninsa da ita hijabai biyu ne ya ke 126 SADAUKARWA-I ganinta da su, idan ta saka wannan yau, bayan kwana biyu ko uku sai ta sauya. Hakan yana bayyanar da rashin wadatar arziki da suke fama da shi. Haka a bangaren kayan da ke jikin nata ma dai ana gane rashin da suke da shi, domin kusan kayan duk sun koke, hatta da takalman kafarta da yá nacewa ganinsu sau biyu ya lura akwai karancin babun dai a tare da ita. Sai dai duk wannan bai zamo nakasu ko wata madogara da za ta rage karfin sonta da kaunarta da ko yaushe suke kara cushe masa zuciya. Bayan dan gajeran lokaci da ya dauka a gurin, ya nufi ofis dinsa ya zauna, hakika yau yana muradin tattaunawa da Fadima, sai dai ya rasa azancin da zai yi amfani da shi, hanyar da ya ke da ita ta zuwa ajin nasu yayin da lokacin daukarsu, karatu a darasinsa, to ga shi ba shi ne ya ke daukar nasu a yanzu ba. Har dai tsayin mintina ashirin yana zaune a cikin wannan yanayi, zuwa can sai ga wayar Habib ta shigo wayarsa. Hannunsa har NAJNGOR 127 SADAUKARWA-1 rawa ya ke wajen dauka, ya kara ya kunnensa yana fadin. "Haba Habib wallahi ka ba ni mamaki, har sai yaushe ne za ka sauya halinka ne na rashin cika alkawari? Na dubi tsayin lokacin da ka dauka kana wannan halayyar, tun fa muna sakandire a ce duk lokacin da ka ce za ka zo guri ba za ka zo ba? Yanzu me kake nufi da ka kira ni? Daga can bangaren Habib ya yi dariya ya ce. "Dadina da kai azarbasi da rashin hakuri. To ga ni nan cikin harabar kamfaninka, dama kira na yi na ji kana ofis ne, don ban ga motarka a harabar ba". Ya ce, "Da wannan an tura, tsohon banza biko ya ce in ba a mayar masa ba ina wa dana riko Suka yi dariya su duka, yayin da Habib ya kashe wayar ya nufo ofis din Hafiz. Yana zama ya mika masa hannu suka yi musabiha, Hafiz ya dora da fadin. NAJNOOR 128 SADAUKARU'A- "Haba ai na dauka halin za ka yi min, ka san a duniya babu abin da na tsana irin mu yi alkawari da mutum zai zo ko za mu hadu da shi lokaci kaza ya ki zuwa da wuri, sai na ji kamar na makure shi ya mutu don tsananin bakin ciki” Habib ya yi dariya ya сс. "Kai kuma ga ka da bakar zuciya ba, sai ka ce za ka ba wa mutum wani abu". Bayan sun gaisa ne, Habib ya ce. "To ka ce na zo game da matsalar da ke damun zuciyarka, wadda har ta ke hana maka bacci, shin wace matsala ce? Nai san dai a rayuwa babu abin da ke wahalar da kai irin biro da takarda, idan akwai abu na biyu da za a dorar to kuwa na'ura mai kwalwa ce... Shin mene ne labari? Ko kuwa da gaske ne labarin da na ke samu na cewar ka samu wata budurwa 'yar Katsinawa masu asirin gado ta sarkafe maka zuciya da nau'in asirin nasu?" An famo masa inda ya ke masa kaikayi, don har yanzu idan za a ambaci Rufa'atu ko NAJNOOR 129 ☐ 1 1 S y ha fe na a SADAUKARWA-1 wani labari da ya shafe ta yana jin kaunarta na nukurkusar masa zuciya. a Gangare daya Kuma yasan Habib ba shi da masaniya game da mu'amalar da ya yi da Rufa'atu har kawo rabuwarsu, tunda ba wani shahararren haduwa suke yi ba, abokai ne dai wanda makaranta ce jigon haduwarsu, kuma ana mutumta juna da karrama uzurorin juna, shi yasa duk lokacin da suka hadu sai ka dauka suna tare ne koda yaushe. Murmushin karfin hali Hafiz ya yi, ya Ce meb "Ko daya ba ma akan 'yar Katsinawa la ba ce, wata jarabawa ce la same ni Habib na rasa yadda zan yi da zuciya ta wadda ta ke azalzalata da kuma tunzurani fadawa tarkon halaka Bis Habib yaa dan call fito da idanu waje yana kallonsa cikin rashin fahimta, ya cе. "Ban gane tarkon halaka ba? Ina takawa da zuhudun da nasan ka da su Hafiz? Subhanallah. kai kuwa me ya kaika barin NAJNOOR 130 SADAUKARWA-/ zuciyarka kusanci da shaidan la'anannc har ya ke kissima maka shiga hurumin da ba na halak ba?" Hafiz ya cije laßbansa cike da jin zafin abin da zuciyarsa ke raya masa game da matar da har lokacin ba shi da tartibin sanin makomar rayuwarta, ya се. "Na rasa yadda zan yi ne Habib, da ina da iko da zuciyata da ba a kawo yanzu ina tare da wannan gambon da ya gama nakasa min rayuwa ba, har na iya kiranka domin kawai na furta maka... Habib wallahi rayuwata tana cikin hadari akan SOYAYYA! وو Ná tabbatar ni ba mai sa'a ba ne... Da sauri Habib ya katse shi da cewa. "Ashe ka san gaibu tunda har ka tabbatar ne ba hasashė kake ba?" Hafiz ya girgiza kansa, yana fadin. "Ba nufina ke nan na sanin gaibu ba, abin da ya faru da ni ne a baya akan budurwar da ka samu labarin na yi mu'amala da ita 'yar Katsina, da kuma wannan da zuciyata ta kamu NAJNOOR 131 SADAUKARUA-1 da tşananin sonta shi ne yasa ni wannan magana Bai boyewa Habib komai ba, ya sanar masa duk yadda, lamarin ya kasance na tsakaninsa da Fadima, amma bai ba shi labarin dalilin rabuwarsa da Rufalatu, wadda mahaifinsa yasa ya rabu da ita ba, domin yana ganin wannan sirrin gidansu ne wanda bai kamata ya bayyana shi ga wani ba. (Kuma haka din ne, ya kamata 'yan uwa mu kasance masu zurfin ciki, ba komai ne ya kamata mu fadawa aboki ba, gudun mummunar shawara, musamman abin da ya shafi umarnin mahaifa, shaidan ya fi rinjayar zuciyar mutane ga bijirewa umarni. Allah Ya sa mu dace da rayuwa ta gari mai inganci, ameen). Da ya kare ba shi labarin, Habib ya girjgiza kansa ya çe. "Gaskiya ni kaina na jiujinawa sakacin da ka yi wa zuciyarka haka har shaidan ya makwabtace ta tana bijiro maka son wadda ba NAJNOOR 132 SADAUKARWA-1 ta dace da ka so ba, haba wannan wane irin al'amari nc mai kama da almara, daga ganin -mace sai ka nace lallai ita kake so bayan kuma kana tunanin tana da aure, tunda har ga shi mijin nata ne ma ke kawo ta? Wallahi ka ba ni haushi da takaici Hafiz, kuma da na san haka ne da ba zan zo gare ka ba... Sai dai tun da shawarata ka nema, gaskiya ba zan ja ka da nisa ba, ina shawartarka da ka hakura ka janye daga son matar mutane, ka rarrashi zuciyarka ko da ta ki ba ka hadin kai ka tursasata gujewa fadawa halaka..." Tun kafin ya Karasa Hafiz ya runtse idanunşa yana jin wani abu na yi masa yawo a kirji, ya rasa yadda zai kwatanta yadda ya ke jin Fadima a ransa. Lokaci, daya kuma ya ji ya cika da jin haushin Habib wanda ya ke ikirarin ya rabu da Fadima, domin a ganinsa duk wanda ya ke neman ya ba shi shawarar rabuwa da ita ba 'mai sonsa ba ne, ina ma laifi a ba shi shawarar NAJNOOR 133 SADAUKARWA-I yadda zai same ta a matsayin matarsa ko da ta kasance matar wani ba wai a ce masa ya hakura da ita har abada ba. Suka yi shiru na tsayin wani lokaci, kafin daga bisani Habib ya katse shirun nasu da cewa. "Wannan ita ce kadai shawarar da na ke ganin ta dace na ba ka, idan ka ji ke nan, idan kuma ka nace har ka kai kanka fadawa tarkon matar aure sai mu ce Allah Ya fidda A'i daga rogo, don tun kafin aje ake shawara kuma an baka" Hafiz ya ce, "To na gode Habib Habib ya yunkura ya се. "Ni bari na wuce". Shi ma Hafiz ya yunkura yana fadin. "Mu je na taka maka". Suka fito daga cikin ofis din zuwa harabar kamfanin, dai-dai lokacin da suka kusa kaiwa ga mota ne Hafiz ya hango Fadima ta fito daga cikin ajin da suke NAJNOOR 134 SADAUKARWA-1 daukada karatu. Gabansa ne ya sake yankcwa ya fadi, murya kasa-kasa ya ce da Habib. "Ka ganta nan ta fito" Habib ya juya a hankali ya kai dubansa ga Fadima, yana fadin. "Ba ka dai daddara ba ke nan?" Hafiz ya yi shiru bai ba shi amsa ba, ganin Fadima din ta kusa isowa inda suke, shi ma sai bai sake cewa komai ba, ya shiga kokarin bude murfin kofar motar. "Yallabai barka da war haka" Ta fada bayan ta dan rusuna. Ya amsa mata cikin kulawa. "Yauwa Fadima, ya ya karatu?" Ta ce, "Alhamdu lillah". Sannan ta dora da fadin Haba malam Habibu idan ba yakimai ya kawo gaba?" Da sauri Habib ya juyo yana dubanta, shi dama tun da ya ji, muryarta ya yi, tunanin ya isan mai muryar. amma hankalinsa bai kawo ita ba ce, ya cey SAJNOORS135 SADAUKARWA-I "Batula dama ke ce?" Kai tsaye ta ce masa. "Au kana nufin ba ka gane ni ba?" Ya сc, "Та ya za a yi na gane ki kina sanye da al'adar taki, kuma kin san ni ba nace wa mace kallo na ke ba barc na shaida ki ta farad daya". Hafiz dai sun saka shi rudani, wato ma Habib ya santa shi yasa ya ke ba shi shawarar ya rabu da ita? Ko kuwa mene ne manufarsa akan haka? Shin matar auren ce ko kuwa? • Fadima ta ce, "Ai ko dai, amma na dauka Yaya Isma'il ya fada maka a nan na ke training din computer?" Yà girgiza kai yana fadin. "Wallahi ban sani ba, maganar ba ta hada mu ba... Ina ya ke ne ko ba shi ke kawo ki ba?" Ta ce, "Shi ke kawo ni, yau ya tashi yana fama da matsanancin ciwon kai ne shi yasa bai samu kawo ni ba, yanzu ma sauri na ke na koma gidan na ga ya jikinsa NAJNOOR136 SADAUKARWA-I Habib ya ce, "Ah to mu je mana na ajiye ki, tunda ni ma gidan na nufa". Ta ce, "Ai kuwa na gode, Allah Ya saka da alkhairi" Hafiz dai bin su ya ke da kallo, har Habib ya bude mata mazaunin gaba daga gefen direba ta shiga, shi ma ya shiga, sannan ya samu bakin magana. "Mutumin zan shigo unguwarku da yamma" Habib ya dan harare shi eikin sigar wasa. Ya сё. "Kurugus! Tatsuniyar ta kare ba sai, ka shigo ba". Hafiz na niyyar sake tofawa, Habib ya zuge gilashin moțarsa, sannan ya tayar suka fice yaná yi wa Hafiz dariya ta cikin motar. Mamaki, da kuma alajabi suka lullube zuciyar Hafiz, a yau dai ya samu saukin zafin rudanin da ya ke ciki a game da Fadima, domin idan har shi mai fahimta ne a cikin zantukan da ya ji Habib da Fadima din sụn NAJNOOR 137 SADAUKARWA-1 tattauna zai iya tantance matsayin da ya kamata a dorata a kai. Tabbas ba matar aure ba ce, kuma wanda ya ke kawota yayanta ne mai lakabin YAYA ISMA'IL, idon haka ne kayansa sun tsinke a gindin kaba ke nan? Karin hasashen nasarar tasa ma da Habib ya kasance ya san ta, wata kila ma unguwarsu daya, ko kuma 'yar uwarsa ce. A şanin da ya yi wa Habib adali ne, mai kuma taimakon abokansa a tun zamanin rayuwarsu ta makaranta, ya san zai yi wahala ya kife masa ciki bai taimaka masa ya mallaki Fadima a matsayin matar aurensa farin cikin rayuwarsa ba. A haka Hafiz ya wanzu cikin farin ciki tsayin yinin wannan ranar, da yammaci lis ya dauki hanyar gidan su Habib. Sai dai ya taki sa'a, domin Habib din ba ya gida, da ya kira wayarsa yana dauka ya ce. "Dama mun yi da kai za ka zo ne?" Hafiz yana dariya ya се. NAJNOOR 138 SADAUKARWA-I "Kar mu yi haka da kai mutunina, na fa ce maka zan shigo da yamma ko?" "Amma me na ce maka? Ina ce na се tatsuniyar ta kare ko? Fadima da kake gani matar aŭre ce, matar abokina ce don haka sai ka sa hakuri ka kuma kiyaye, don zan iya daukar kowane mataki a kanka don kiyaye hakkin auren abokina..." Daram! Gabansa ya sake yankewa ya fadi, wannan wane irin lamari ne haka, komai ya ke ganin nasara sai kuma hakan ya sha ruwa? Yanayin da Habib ya yi maganar a wannan lokaci ya nuna sam ba ya cikin annashuwa, kamar ma ransa a бace ya ke, wanda hakan ke tabbatar masa da lallai maganar tasa hakan ta ke, Fadima matar aure ce! Saboda haka murya a raunane ya ce. "Yanzu don Allah kana ina? Wallahi ina son ganinka". NAJNOOR 139 SADAUKARWA-1 Habib ya ce, "Gaskiya babu dama, ka yi hakuri idan na samu lokaci zan zo har inda kake da kaina". Hafiz ya sake marairaicewa kamar zai yi kuka, ya ce. "Don Allah kada ka yi min haka abokina, sanin kanka ne ina cikin wani irin rudani, wanda ya kamata a ce na samu masu tausar zuciyata don samun maslaha ga ...rayuwata وو Habib ya katse shi. "Tunda har ka san kana cikin rudanin, ai abu ne mai sauki ka cire kanka a ciki, domin mutumin da bai san yana cikin rudani ba shi ake hangowa rudanin har ai tunanin hanyar da za a bi a cire shi..." Shi ma Hafiz din ya tare shi da cewa. "Na lura abokina ka dauka da zafi, Allah Ya huci zuciyarka, idan dai Fadima ce na hakura da ita har abada..." Habib ya sake tare shi. NAJNOOR 140 SADAUKARWA-I "Ba ma sai ka kuma ganinta a kamfanin naka ba sannan za ka nacewa sonta?" Kafin ma ya ce wani abu tuni Habib din ya kashe wayar, Hafiz ya yi zugudi ya ma rasa mai ya ke masa dadi a duniya. Ya dauki tsayin lokaci zaunc a mota yana' tunanin abin yi, kafin daga bisani ya ja dogon tsaki ya ce. "ZUCIYA DA SHAIDAN! Allah ka raba mu da sharrinsu!" Ya tayar da motar ya sa kai zuwa gida. *** *** *** Abu kamar wasa, Hafiz ya daina ganin Fadima a kamfaninsa tsayin kwanaki hudu. Abin ya ba shi mamaki matuka, duk da dai a bangare daya bai kamata ya yi mamakin hakan ba, tunda Habib ya sanar masa cewar ba za ta kuma zuwa ba. Lallai yanzu ya tabbatar ya aikata babbar katobara, me ma

Chapter 5 of 6